Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sallama na kike cewa yafi hakan"
"Baba bazaka ganeba ne a bar zancen kawai"
Shiryawa tayi cikin atamfa anyi mata dinki simple na doguwar riga,sai daurin ture ka ga tsiya da kuma gyalen rigar a kafadarta,tayi kyau sosai dan ba karamar kyakykyawa bace (kyan dan macijiba)kuma tafi saka abaya,ko kuma riga da wando,haka in bata ga dama ba sai tayi sati bata daura dan kwaliba sai gyara gashi kawai takeyi ta daureshi.
Hanyar waje tayi su bingo suna biye da itah a baya,kicibis sukayi da manjo yana shigowa,yah saka wata babbar riga wanda takusa ta yadi goma,a ina ya samota oho,dan dama manjo ba dai shigar hauka ba,taba ce a hannunsa tana hayaki ga kuma wani kwalli dayasha kaman dan farauta,
"Yawwa ke dama ina nemanki zamuyi wata magana"
"Wacce maganar ka bari saina dawo akwai wani abu dazanyi manage yanzu"
"Ke ni zakice zakiyi wani mange(manage),maganar muhimmancin nima nake tafe da itah"
Har zatayi magana saikuma ta gyara tsayuwa tareda cewa,
"Ina jinka manene"
"Ehe yawwa zancen soyayyarki keda sule maye,inaga maganar zatayi karfi tunda ni yayanki nashiga ciki,yanzu hak nace yabani sadakinki dubu talatin,kuma yabani duk da ma na dan ci dubu biyar a ciki,kinsan sha'anin rike kudi abinka da mutum mai dan uzuri,hhhhhhh amma tunda naga yana sonki sosai nasan zai karo cikaton kudin.
Kai dole ma ya ce yanason ki duk da irin tantirancin da kikeyi ,akwai kyau ne musamman idan kikidau wanka"
"Toh yanzu dai kagama magana mai muhimmancin ko kuma da saura har yanzu kai"
"Ke kina rainani fah,dama sanda na dawo kulu tacemin kin mata rashin kunya kyaleki kawai nayi saboda sule abokina yana sonki"
"Allah koh,haka akayi kenan,duk zancennan ka barsu idan na dawo sai muyi shi"
Jijjiga kai kawai tayi tana Murmushin mugunta ta shiga mota suka tafi itada karnukannata.

Wajen da ta ajiye surayyah ta tafi domin jin yanda ta kaya,yauma a zaune take saidai dayake su mugun dawa sun tafi aiki daga itah sai C.I.D shikuma bashida magana sai leken asiri koh bera ya sara masa.
Sameemah tana shigowa surayyah ta tashi tana gaisheta duk da a gida koh uwarta sai taga dama take gaisheta.
C.I.D ne ya matso tareda yimata bayanin abinda yah faru dazu,mika mata wata takarda yayi yana cewa,
"Ranki ya dade ga wannan paper burgune ya kawota dazu wai yayan surayyah ne yabayar,yayi signing din yaan neman a sake masa kanwarsa,tun dazu muje jira ki iso gashi kin ce kar wanda yakiraki shiyasa na zauna ko zaki zo"
"Okay shikenan babu matsala,zaku iyah maida ta gida,amma ban yadda tasan wane waje take ba,na gama da wannan shafin"
Saida ta gama kallon signing din ta tabbatar shine kafin ta rufe paper cike da murnar nasarar da ta samu.
"Amma shugaba nafadamiki cewa nima fah a nan wajen zan zauna"
"Eh kuma nima na fadamiki idan baki kawo signing din yan uwankiba bazan daukeki ba ai,koh kin mantane?"
Sunkuyar da kai surayyah tayi cike da jin haushi saidai ta kudiri aniyar karbo izini dan itah taga wajen zama inda yayi dadai da ra'ayinta.
Wani bakin kyalle aka saka mata a idonta har sannan sai cuna baki takeyi wai sameemah bata yadda da itah ba,ita kuwa ko kallonta batayiba har su ka isa kofar gidan yayannata a mota,C.I.D yah fito ya budemata kyallen fuskarta da kuma motar kafin ta fito,cikin gidan yayannata ta shige koh kallon sameemah batayiba.
Suna ganin shigewarta gidan suka bar wajen.
Mahmoud ne a zaune shida matarsa haka ma iyayennasa suna zaune a daya kujerar kowa yayi jugum sun rasa ma me zasuyi,ko sallama surayyah batayiba haka ta shigo tana wani cika,dukkansu tashi sukayi suna kallonta da mamkin ko kwarzana babu a jikinta,bayan hoton da aka turomusu duk jikinta ciwone.
Mahmoud ne yafara cewa,
"Ke ya na ganki kaman babu abinda yasameki baayan jiya video da suka turomin nishi kike yi kaman zaki mutu"
"Ba abinda suka min,duk nice nayi saboda su saka ka bada kudi,dan cewa nayi zan taimakesu,amma wannan shugabar tasu ta ce wai bazata karbi kudiba saka hanunuka kawai take bukata a wannan paper"
Da bakin ciki sir Mahmoud bai san lokacin daya zabga mata mariba da kuma yin boll da itah,kuka ta rusa tana kallon ummahn ta,itama kawar da kai tayi da a wannan fadan babu dama tayi magana dan surayyah ce bata da gaskiya.
Haka ya dak at a saida tayi lis tukunna ya barta.
Cikin sheshshekar kuka tace,
"Kuma an taimakesu din,naga inna ce ka bani kudin hanani kakeyi,ka bawa su yaya Najeeb,kuma koh kasheni zakuyi saidai kuyi,ni yanzuma idan nasamu dama wajenta zan koma aiki.
Dan takaici shigewa daki yayi kaman zai tashi sama,itakuwa mahaifiyar su ce tazata daga kwancen da take tace,
"Gaskiya bakyaji surayyah,duk wuyar dayasha ganin kin fito ashe da hannunki a ciki,saiki tashi mutafi gida ai kafin ya karisa ki"
Da haka uwar ta jata suka tafi nasu gidan,shikuwa uban dama dayajj abinda yafaru tun da farko yabar gidan.
A cikin mota kuwa sameemah ce ta kalli C.I.D,tace,
"Kafadamin inda zan ajiyeka dam akwai wajen da zanje daga nan"
"Ahh KO Ina ma kika ajiyeni duk dayane"
Fakawa tayi gefen hanya ta saukeshi kafin tayi hanyar gidan alhaji bala direct,tun kafin ta kai ga shiga cikin gidan tayi wani murmushin migunta.
Da shirinta tazo dan jiyah C.i.d ya fadamata duk wani shiri da alhaji balan yakeyi akanta,kuma dama tayi tunannin hakan,dan a rashin muyumci irin nasa,da kuma itama irin tsiyar da tayi masa tasan bazasu kare iyah hakaba.
Shi bazai fasa daukar fansaba itama kuma bazata daina yaki ba har sai ta hau kan kijerar shugabar vigilantee tukunna,saboda tarihin da takeso ta kafa bazai tafiba saida wannan kujerar tukunna.
Danna kai tayi cikin ainihin gidansa kuma tasan yanannan. Mai gadine ya bude mata kofa ta shige kafin yamayar da get din yah rude.
...........hmm mm D'an sa ma yadawo yana nan.😂🤣😂


*+______________________+*
*ABIN YABO BOOKSHOP*
Kasuwar Rimi Kano
Tel:📞 *07038339244*


❤❤SADY-SAKHNACEH❤❤

Kar ku manta da

#comment
#share
#like
#follow.

____** *GIDAN GANDU* **____
❤❤By sadi-sakhana❤❤


Wattpad username:SAKHNA03

❤25❤

Saida ta gama saitawa kafin ta fito daga cikin motar,hanyar dazata kaita cikin gidan ta nufa tana wani shekar iska.
A bakin kofar tayi sallama wata mata da alama mai aikice ta amsa mata,
"Matar Gidan tana cikine?"
"Eh hajiya tana nan bari nayimiki iso da itah "
A kujera ta zauna kafa daya kan daya,wasu samarine suka shigo guda biyu suna ta magana,har saida sukayi wata hanya kafin daya daga cikinsu ya kula da itah.
"Lah umar wallahi wannan zazzafar yarinyar danake fadamaka na hadu da itah a club toh wannan ce"
Yafada yana nuna sameemah,itama kallonsa tayi sau daya dan taganeshi sarai,shine yace mata sunansa tukur. Cigaba yayi da magana tareda tsayar da ummaruje a waje daya.
"Kai ban gane ba fah ko yar uwarkuce,naga ta sake a falon daga gani ba zuwanta na farko ba kenan"
Da yayi niyyar share abin amma daga kallonta dayake shima dan duniyar ne,cikin sakanni yaji ya fola mata shima.
Komawa falon sukayi suka zauna,ummaruje ne ya daga girar barin dama yana lashe baki kafin yace,
"Yan mata me ne sunanki,abokina yace kun hadu a club daga gani kema yar hannunce wato ta hannun damanmu"
"Like father like son"
Sameemah ta fada a ranta,dayake ta sha kansu iyah rashin mutunci,kara daga kafarta tayi tana wani jijjiga ta irin ta shegun matannan,saida tah ciji lebenta ta gefe da hakoranta kadan kafin tah kashe murya tana cewa,
"Uhm Wai ni sunana sameemah saidai banji sunan gwarazan mazanba kuma?"
Ummaruje ne yah washe baki har kunne kamar gonar auduga kafin yace,
"Sunana umar,ina karatu a abroad sannan nan gidanmune kuma nikadaine a namiji a wajen babana sai kanwata da tayi aure"
Yah karisa magana yana kafafa,shikuwa a bangaren Tk mamaki abin yabashi domin yasan haduwarsu ta baya da itah batayi kama da wannan da take zaune ba,shikansa badan yagane fuskar ba zaice sanja ta akayi,waccer fuskarta banu annuri ga kuma uban shaye shayen da tayi,amma wannan idan ka ganta saika ce ai batasan menene fushi ba,dan fuskarta sai murmushi takeyi da annuri.
Hada ido sukayi da Tk da kuma sameemah,wani kallo tayi masa na alamar gargadi,cikin sauri kuwa yah sauke idon tareda wayancewa yana dariya.
Suna ta tadi dukkansu babu wanda yah kulada zuwan alhaji falon shiga hajiya Mairo,jerowa sukayi ko wannensu kaman zai fashe dan kiba,musamman ma hajiyah mairo sai huci takeyi.
Tsayawa su sameemah sukayi da tadi ita da ummaruje wanda ya zare sai surutu yakeyi kawai dan yaga wannan kyakykyawan Murmushin a fuskar sameemah.
Hajiyah mairoce ta tambayi ummaruje tareda cewa,
"Kai daddy wannan kuma fah a ina kuka samota?"
Sameemah ce ta hada ido da alhaji bala wanda yake feso gumi a akan fuskatarsa ta kyasta masa ido batareda kowa yah kula ba,
"Ahh mommy nima anan na ganta ,nayi zaton fah kin santa,tana jiranki ne ki fito"
"Ahah ni bansantaba kwata kwata"
Tun kafin sameemah ta bude baki zatayi magana alhaji bala yayi sauri ya rigata saboda yaga niyyar ta kenan ta tona masa asiri,
"Ahh hajiyah sai yanzu nagane ta ,ai yar gidan aminina ce,yayi min zancen tana neman kudin makaranta toh shine nace ta zo ta karba"
"Ayyah to ai bazata tsaya anan ba sai tayi magana kuma"
Wani Murmushin sameemah tasake yi masa mai nuna alamun ka ceci kanka,shikuwa ummaruje jin abinda akace gameda sameemah cikin sauri yace,
"Lah Ashe kema student ce,allah ya taimaka,amma da kin bani number ki ko zamu sake gaisawa dan yanzu fita zanyi foot ball ba lallai na dawo na sameki ba "
Yana gama fadan haka yabawa sameemah wayarsa,itakuwa kodan taga yah alhaji bala zayyi cikin innocent smile ta karbi wayar ta saka masa number tah.
Tun wajen yayi tsallen samun nasara kafin yah fita aka bari daga alhaji sai hajiyah,itama hajiyah mairon Murmushin takeyi ganin abinda dannata yayi,
"Yarinya ki saki jikinki kinji,idan da wani abunma kizo kanki tsaye,babu wata matsala"
Sunne kai tayi kaman yar arziki tace,
"Nagode hajiyah allah ya jikan mahaifa,yasaka muku da alkhairi"
"Ameen ameen diyar albarka,menene sunanki"
"Sunana sameemah hajiyah"
"Kai suna kuwa mai dadi,yah dace dake sosai"
Da haka hajiyah ta koma sashenta tabar Alhaji bala a tsaye wanda yayi simmm kamar gunki.
Sameemah ce ta tafa hannunta kafin yadawo hankalinsa,
"Amma seemah menene wannan kikeyi da iyalina,musamman umaruje wanda ba hanunsa a komai kike son ki cutar dashi"
"Ka ga dakata cutarwa kuma bashi numbar ta shine cutarwa,cinyeshi kaga nayi komai,sannan abinda nakeyi sunansa wasa"
Ta gama maganar tana kyalkyalewa da dariyaar mugunta,
Takaicine yakama alhaji bala yarasa ma mai zaice,ganin tsayuwar ta gagareshine yasa ya samu kujera ya zauna wanda take facing din sameemah.
Yanzu dai mudawo zancen gaskiya,duk abinda zakiyi kar ki taba iyalina,kowa yah ajiye iyalai a gefe,idan kuma ba haka ba kinsan kin fi kowa iyalai sama dani,zan iyah daukar mataki"
"Lahhh alhaji bala gwanda da kafadi abinda yake bakinka,toh bari kaji in fadamaka,ba abinda zai shafeni dan ka taba wayannan mutanen,koh zai dameni ma ba sosai,saboda wadda naso a duniyah sama da komai ta tafi ta barni kuma na rayu,dan haka uban kowa ma yah mutu,idan aka jajanta na sati daya kowa ya koma harkarsa.
Bar ganin na fadi hakan kuma,allah yasa naji ko mura wani yayi a cikin gidannan ace da hannunka...........hmmmm danka zan dauke mubar kasar dashi muyi rayuwa,sai yagama makancewa akaina na nuna masa video ka sanda kake kokarin yin lalata dani,idan ciwon zuciyah ya kamashi sai na dawo na barshi a can😎"
Tun daga jin bayanin irin ta'asar da sameemah zatayiwa dansa yasa yasha jinin jikinsa,saidai bai kai ga komawa hankalinsa ba yaji ta cigaba da cewa,
"Kai maganar da kayi ma,ka karawa kanka yanzu bayan na siye zuciyar hajiyah mairo da kuma danka,saina saka yarka taji batada wata kawa mai shirin zama kuma yar uwa a zuciyarta sama dani,saina ga yanda zakayi dani idan sukaji ka illatar dani,kuma kana kokarin keta min haddi a video"
Saurin toshe kunnensa yayi tareda cewa,
"Yah isa haka mai kikeso ne kika zo gidannan iye?"
"Abu kadanne,naji labarin shirin da kakeyi a kaina,Toh ka daina banaso sannan batun bani kujerar vigilantee tana nan babu inda zaraje,dan har na karbi takardar ixini a wajen shugaban yan sanda,dan haka ka shiryah zuwa wani sati,in kuma kak ji baza ka ki ganiba.
Ina nan a kan bakana babu inda zanje"
Saida yasauke ajiyar zuciya na babu yanda zayyi kafin yace,
"Shikenan naji,amma batun d'ana please karkiyi wasa da zuciyarsa kinga baisan komai akanki ba"
"Zai sani a hankali karka damu,ai yanada hankali ba mahaukaci bane shi,dan haka in yayi kuskuren hanya zan saita muku shi,sai kuyimin godiyah na cigaba da aikin da iyayene ya kamata su dinga yi,kun sakaltashi da yawa yana bukatar gyara daga irinmu"
Zaro glass dinta tayi daga cikin jaka ta toshe fuskarta dashi,har ta isa bakin kofah ta dawo tana cewa,
"Ahh alhaji zan tafi amma bakazo kun gaisa da motarka ba,ko ka daina santa ne bansaniba"
Ganin dan bakin ciki bai kulata bane yasa ta fita tana Murmushin mugunta.
A can Gidan su surayyah kuwa yau sati daya kenan kullum tana cikin aiki,ko an saka ta ko ba a sakata na zata tashi tayi,tunda ta dawo daga hannun sameemah kaman an sanjata haka ta zama,ummanta sai murna takeyi.
Yauma zaune hajiyah Sa'aden take bayan sun gama aiki dan d'anta dayake aiki da sojoji yau zai dawo garin,Kwallah mata kira takeyi amma babu itah babu labarinta sam,abu tun safe har wajen yamma,lokacin yayannata har ya iso yah huta,shima daya tambaya cewa akayi bata nan.
Shigowa tayi tana sanda hanyah,bata ankaraba saijin maganar mutum tayi a bayanta,
Juyawa tayi taga ashe yayantane da zaizo yau,
"Daga ina kike haka tun safe,kuma ke ba makaranta kike zuwaba,yansu surayyah kina nan da halinki na yawo da rashin kamun kai koh?"
"Iyah Gidan kawata fah naje,ni ba wajen wasu najeba yau din"
Jijjiga kai yayi kawai ya wuce shima cikin gidan,itama binsa tayi a baya har ta wuce dakinta,tanajin kowa yana fadar abinda takeyi ita kuwa tura dan kwali tayi tana bubble din chewing gum.
Sallamar yah Mahmoud ce ta fito da itah daga cikin dakin tana lekawa ta window,
"Miye kike lekoni kizo ki karba abinda kikace na baki"
Fitowa tayi kanta a sunkuye kamar wata wanda kwai yah fashe mata a ciki.
Mahmoud ne ya mikawa kaninnasa takardar tareda cewa gashi kaima kayi sign tunda kazo,
Har zai tambayi ta mecece amma Mahmoud ya hanshi,hakan yasa yah karba shima yayi sign din.
Mikawa surayyah takardar yayi kafin yace,
"Abinda kika tambayeni sati daya daya wuce ne,wanda nace miki saikinyi hankali shine kika dauki yin aiki na karyah ga ummah,ganin ban baki ba kika tafi wayo inda zan ganki koh?wato koma menene nayi din,shikenan na cika miki sharadinki,gashinan mun amince kiyi aiki da sameemah jar wuyah komai yah faru da amincewarmu"
Ba iyah surayyah ba har su ummah su da suke wajen saida sukayi Mamakin abinda yake faruwa,itah kuwa karbar takrdar tayi tareda komawa dakinta tana Murmushin jin dadi,kaman anyi mata albishir da kujerar makkah.
Uwar ce takasa hakuri tace,
"Amma mahmuda wannan wane irin danyen hujunci kayi,yarinyar da ake nema ta shiryu"
Saida yayi murmushi da alamun shi ya hango mai yah faru tukunna yace,
"Ummah karki damu babu abinda zai faru sai shiriyah,dan ina mai tabbatar miki kwananna surayyah zata shiryu a wajen seemah,dan nayi bincike nagano cewa duk yaranta yanzu ta hanasu shaye shaye da kuma aikin banza,dalilim da yasa tayi kidnap din surayyah dan na yi mata sign din takrdar neman izinine na zama shugabar yan vigilantee,kuma duk yaranta tace zata sakasu aiki,wanda zasuyimata iyah itah kadai,kaman yamda kuke ganinta ba haka takeba,tana kula da duk wanda yake karkashinta sannan yanda kikasan uwa akan yayanta haka take akan duk wanda ya yadda yah zama acikin kungiyarta,zata iyah bada ranta akansu.
Yamzu haka idan wani abu yasamu surayyah,ko bamuyi komaiba zatasan yadda zatayi ta tabbatar ta kubutar da itah,kuma ina mai tabbatar miki zata hanata yawon dare da kuma shaye shayen da take ganin tanayi,kuma dole ta daina dan dole,saboda zataji maganarta fiye da yanda takejin taku.
Kudai kuzuba idon ku gani,itah bata san yah sameemah takeba shiyasa take rawar kafar shiga kungiyarta ai,kudai ku zama yan kallo,sannan ku kwantar da hankalinku kaman kun kaitah gidan horo................mai zakuje zai faru tsakanin surayyah da seemah😂😂😂😂😂😂.


*Please wanda basayin comment sai dai thank koh liking,ku dunga yin comment mai kyau,musamman Facebook da telegram,naga yan wattpad sun dan fara dagewa.
Amma WhatsApp kune akan gama ina ji daku sosai*


*+______________________+*
*ABIN YABO BOOKSHOP*
Kasuwar Rimi Kano
Tel:📞 *07038339244*


❤❤SADY-SAKHNACEH❤❤

Kar ku manta da

#comment
#share
#like
#follow.

____** *GIDAN GANDU* **____
❤❤By sadi-sakhana❤❤


Wattpad username:SAKHNA03


❤26❤

Kwanaki sunja sameemah ana ta shiryen zama yar damara,duk wani abinda take bukata ta gama hadawa,dan yanzu koh lokacin yan gidannasu bata da shi bare kuma akai ga tsayawa ana saida dan hali.
Suma yan gidan nasu bidirin sukeyi an kawo goron tambayar auren Zainab,wannan jarabbabbeb saurayinnata da suke kaiwa dare a wake,sukuwa manyan gidan wato sameerah salma da su sameemah kaman anyimusu asiri babu wacce tayi aure har yanzu,dan gwara ma sameerah ta tabayi ta fito.
Su inna ramatu sai kafafa akeyi y'a zatayi aure,su guzuma ana zaune wato su salma.
Babu laifi yayi mata kaya masu kyau dadai karfin sa,inda aka saka bikin nan da wata biyu.
Duk abinda akeyi sameemah batasan anayi ba dan idan ta fita bata dawowa sai dare,sai shirye shiye sukeyI.
Yau ma da sassafe tah tashi kaman abin arziki akayi su wanka da shigar mutunci tafito,babu kowa a tsakar gidan dayake safiyah ce amma rana ta fito,manjo ta samu yana alwala a bakin kofarsa ko kuma nace wanke ido,hada ido sukayi koh eh bata cemasa ba haka shima bai kulata ba,yan miskilancin suna kusa.
Gidan su burgu ta fara zuwa tah daukeshi suka tafi ainihin babban office din dayake birini,dauke da takaddar da Mahmoud yayi mata sign da kuma ta Alhaji bala.
Saida ta dauki lawyer tah saboda tsaro kafin suka dauki hanyar tafiyar.
Zainab ce a zaune tana shafa kurkur a fuskarta tana wakar habaici saboda taga yayan kawu shehu mata a wajen da kuma sauran yan matan gidan,
"Lokacinki ne yayi amarya yar amana sai kize ki zauna da miji aure ibada ne............"
"Hee amaryah manya,amaryah da yin kurkur,kir ayi mai na kanti mana,kuma a wane shegen saurayin kowa yasan halinsa da bin yaran mutane"
Wata ce itama ta sake cafkewa bayan salma ta yi shiru,
"Ke ma kya fada,dan dai an rasa wani ne sai shi,in ba hakaba mai za'ayi da Uzairu a rayuwa"
"Eh haushin rashine makaho yace ido da wari,inma mai danne iyayene wata ta fito da nata mana,aurene nima zanyi na bar gidan gandu nafara girka nawa abinci wanda nakeso na barku da tuwon masara miyar lami"
"Dan ma tuwon masara kikaci kika girma ,kuma shi uwarki zata shigaba da ci har kasa ta binne idonta"
Salmace cikin yatsina fuska tace,
"Ke zainab ya isheki haka kuma,bamuson raini,a wane shegen saurayinaki naga saida nace bana sonsa kafin yah dawo wajenki,kuma shi banzan bazarane a cikin masoyana wallahi"
"Eh naji banzan bazarane shiyasa naga baki auri wannan tula tulan alhazan nakiba ai kika makale da soyayyar yah sameer har kike zagin matarsa,kuma duk jarabarki ma zaki barshi ki auri daya daga cikin tsofinnaki,dan anty saleemah ba sa'arki bace ehhe"
Cikin rashin daurewa da zancen salma tah kaiwa zainab wani uban naushi a bakinta,abinka da brush bai ishi bakinba sai jini yace yah samu wajen fita shikuwa.
Kururuwa ta hada itama ta kamata suka fara fada sai ga sameerah ta shigo da leda a hannunta da alama daga wani waje take,wajen su tayi tana rabasu tareda cewa,
"Ku hakan menene mai kuma yah faru kuke wannan kokuwar,ke salma bakiga aure zatayiba kike dukan ta a fuska?"
"Ke sameerah kema banason iskanci,auren yaci kundun ubansa,haukane auren dan zatayi ta dunga yadawa mutane magana,toh gobema ta kara saina zubar mata dukkan hakoranta,saidai inna ramatu ta akaita a saka mata na roba"
Tana gama fadan hakan ta bar dakin tana huci,sukuwa binta sukayi kawai da kallo.
Ita kuwa sameemah tun safe suke bakin kofar shugaban amma basu samu shiga ba schedule dinsu bai zoba har dare yafarayi,tun suna saka rai har suka hakura suka dawo,gashi sai wani satin su koma kuma.
In ran sameemah yayi dubu toh yah baci a wajen dan ko magana batayi sosai,haka ga gajiyah ga komai tah tuko motar suka taho.
Saida ta fara sauke barr.Kamal kafin ta sauke burgu shima a gidansu,yana mata godiyah da huta gajiyah ko kulashi batayi ba saima kara hade fuska da tayi.
Tun da ta shigo layin gidansu takejin muryar yan gidannasu gashi darene dan 9:30pm ta kusa,takaicine ya isheta tasan ba lallai ta shige Kalau na.
Ai kuwa hakance tah faru dan inna karimane da inna larai suke fada akan marar tuwo guda biyu.
Babu wanda yah kulada da itah a wajen dan manya da yara an tsatstsaya kowa wasuma hadda torchlight a hannunsu saboda su gani da kayau dayake an dauke nepa.
Baba umarune ya dawo ana tsaramasa yanda akayi,tun kafin su gama tsarawa sameemah tah fisge kwanon tuwon ta wullawa su bingo wanda suke biye da itah sunga ta shigo.
Kowa mamaki yayi tareda yin shiru amma banda inna larai dan masifah ta farayi kaman makogaranta zai fashe,
"Kinsan allah inna larai ko kiyiwa mutane shiru da darennan ko kuma na tura karennan yah ciromin mamanki na hagun idan kina bacci,kinsan sarai zan aikata yanda kofar dakinki kuwa ta baci babu sakata,dan haka saiki zaba yanzunan"
Kowa inna larai yake kallo da jin wanne zata zaba maganar sameemah,aikuwa cikin sauri tayi kofarsu tsitt kakeji kaman ruwa ya cinyeta.
Kowama dayaga hakan kofarsu ya nufa yana dariyah da tsoron inna larai,ga tsokana ga fada dakuma rashin gaskiya, aka bar filin wajen,sai gobe kuma.😂
Yanzu dakinnasu iyahsu kadaine babu zainab saboda tah koma dakin iyah mai kalwa(kakarsu da ta rasu )ana mata al'ada na aure,kaman su tsimi na tsugunne da sauransu,hakanma sai yafi musu,domin indai zasu zauna da itah da salma toh fadane zai biyo baya tsakninsu da itah,ita kuwa dama sameemah babu wanda take shiga shirginsa saidai idan ka shiga nata shirgin ku kwashi yan kallo.
Misalin karfe 12;00pm rana tayi ga kuma zafin rana saboda yanayin lokaci na rani,surayyah ce ta shigo gida da sauri sai hada gumi takeyi,babu ko sallama bare ta kula mutanen gidan ta dau buta tayi bandaki da gudu,saida ta fito ta sha ruwa kafin ta zube a tabarma a tsakar gidan nasu wanda take karkashin bishiyah.
Saida ta gama hakin da fifita kafin ummansu ta tambayeta,
"Mai Sunan uwata ya na ganki haka kaman wanda aka zefoki daga sama"
"Hmm ai bari kawai ummah,muna kan tsallaka siradi ne,da yawanmu shugaba ta saka a training kuma duk wanda bai fito da matakin nasara ba sallamarsa zatayi,gashi bata afuwa,idan tana yimana training dinannan kaman fah soja haka takeyi,gwanda ma ogah burgu yana mana da sauki.
"Ahh kikce aiki kukeyi babu kama hannun yaro"
"Hmm ni ummah kuwa anya kungiyar yan daba ce kuwa?"
"Me kika gani?"
"Naga an Hana shaye shaye,an hana yawon dare sannan ba'a yin shagali,kullum ana cikin training da kuma fita aiki,ni gaskiya gani nakeyi kaman ba kungiyar dana ke jin labari bace"
Dariyah ce ta kama ummah amma haka ta kunsheta kar surayyah ta gane,kwata kwata satinta daya tana zuwa wajen sameemah amma har ta fara sanjawa,babu shegen wayon club,babu shigar rashin mutumnci sannan babu wannan baccin safen har zuwa azahar.
"Uhm ummah bani abinci naci,nayi wanka dan in anjima shugaba tana neman mu akwai abinda za'ayi,naji tace wai zata sakamu a wajen koyon computer wasu kuma a turasu wajen training na police da yan sojoji,nikam kungiyar tamu har ta fara bani tsoro,yanzu ko samarina nagani tsoton kulani sukeyi wai tunda na shiga kungiyar seemah"
Narai narai tayi da ido kaman zatayi kuka,amma tunanin abinda zai faru idan bata koma ba yasa ta mike tana wani lankwashewa kaman wanda ta fito daga labor room,itadai ummah bata kara cewa komaiba sai dariyah da takeyi ciki ciki tareda fadin madallah.
Aikuwa la'asar nayi tun kafin tagama cin abinci saiga kiran burgu,da sauri ta tura sauran lomar da cokali ta mike zuwatt,badan tsoron burgu ba saidan tsoron wanda tasa burgu ya kirasu.
Da gudu gudu tayiwa ummah bye bey ta fita,sai a wajema ta karisa saka gyalen a wuyanta.
Tun da sameemah ta dawo gida sanda su inna larai suke fada da daddarenan take ta bacci har bayan azahar,su kansu yan gidan su zata ta mike ta can zuwa makwancinta na gaskiya,wanda da hakan yah faru da sunfi kowa farin ciki,saidai kash!!! Daidai wani lokaci ta bude idonta tareda yin wata mika irin ta wanda babu abinda yah dameshi.
Fitowa tayi tsakar gidan tana rarraba idon neman yaro dan ya debo mata ruwa,ita wannan rashin ruwa da suke fama dashi yana ci mata tuwo a kwaryah ba kadan ba.
Dan Gidan manjo ne yah yazo wucewa zai fita waje,sai sameemah ta kirashi,da sauri yah taho wanda koh uwarsa ce albarka,saboda yasan bata wasa dasu ko kadan.
Bayan ya tafi debo ruwanne tah koma dakin jin wayarta tana ta ringing,gashi dama bata saka volume kadan,kuma da saninta takeyin hakan.
Ganin number ummaruje saida tayi jimm kafin

Please Login or Register in order to submit comment