Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

baya ta debo uban *klin* ta zuba a katuwar roba tana ta gurzar jaka, mamee ta kwala mata kira,
Ta antayo da gudu hannun ta duk kumfa,
Ya bita da kallo duk ta jike hijab dinta,
Naga hannunki kumfa me kikeyi agogo? Mamee ta bukata tana kallon ta cike da kulawa.
Tadan murza hannun kumfan ya fado kasa tana satar kallon sa, jaka nake wankewa...... Ya dago *what a ruwa kika saka ta?*
Mamee yar nan taki wallahi duk abinda nayi mata kar kiyi magana.
*Da tayi maka me?*
Ki tambayeta gata nan, ya nuna ta da yatsa,
Uwani me kika mishi?
Ta dan kara kame jikin ta tana dan in ina....... Uwani matso nan saki jikin ki. Ta kalleshi wallahi bani son takurawa yarinyar nan da kake yi madaki tsoron ka takeyi kamar me dubi yanda jikin ta duk ya rikice da kyarma ina dalilin wannan azaba?
Ta kamota me kikayi mishi?
Jiya ne ya ban jaka ban san cewar mai tsada bace shine....... Ki faro mata daga farko.... Ya katseta.
Kai bana son shiga uku kai ka fada man mana.
Mamee yarinyar jiya zan tafi stadium na hadu da ita hanya zata je gida na taimaka mata na rage mata hanya na ganta da kudi a hannu na ce bata sawa jaka ta ce bata da ita, na biya na siya mata mai tsada shine yau ta yo cefane da ita duk kifi da karikitan data siyo ciki ta zubo shine......... Shine me?
Ina ruwanka idan wuta ta saka ta Ina ce kai dai ka bata ko?, zai yi magana ta daga mishi hannu kai bani son rashin gaskiya, daman ka siya ne don ka uzzura mata, duk tsadar ta ina ita zata san haka?
Ta kalleta kin rage dan faten? A a duka na juyo shi sai Wanda na diba a plate...... Sai ki ajiye mun shi kar ki taba.
Mamee ta bishi da kallon takaici,
Ko bakiji ba? Ta ce to zata juya, mamee ta kamota je ki ci fita batun sa,..... Haba mamee ....... Zakayi mata kurulla ne?
Sai kawai ya mike ya nufi kitchen din ya dauko. Wai madaki meke damunka?
Ai mamee idan na zauna gidan nan wata rana ma cewa zakiyi ba ki haifeni ba sai uwani ya wuce sama da plate din.
Ungo wannan je karasa cinyewa kyaleshi. Kullum ganin kansa yakeyi yaro karami shi yasa nake burin yayi *Aure* gaban umaimah ya fadi *wai ya zanyi naga madaki da wata?*
Tayi ciki tana karasa wanke jakar,
Ta ringa jiyo hayaniyar mutane, ta sami mamee daki ta ce, kamar baki nakeji falo.
Wannan fitinannen ke meeting ai shirin zuwan su ne jiya na wuni baya ina gargadin su mansurah, manya manyan manajojin sa ne,
Au, ta fada a takaice.
Firatan ya ki hawa sama duk ya takura kowa.
Madaki kuwa yasan yau wuni zaiyi tare dasu gashi baya son umaimah ta tafi bai sani akwai maganar da zaiyi da ita.
Karfe uku aka fara shirya musu abinci kamar yanda ya tsara, umaimah an dage aiki baji ba gani, magana yakeyi amma hankalin sa na gunta idan ya hangota ta fito.
Ashe shima cikin manajojin shi daya ya hangota nan da nan hanakalin sa ya dauku. Ya dan juyo yana sosa keya,
'Yallabai ni fa na hango iri.
Ya maida hankalin sa gareshi sosai saboda shine babban manager da yake ji dashi a Lagos yake,
Iri na me?
Dai dai ta fito ya ce waccen yarinyar....... Ya sha mur *Bana son maganar banza* abinda ya kawo ka kenan?
Nan da nan ya kame kansa saboda suna bala'in tsoron sa.
Suka tafi zuwa dining, Sun fara cin abinci kenan sai gata da tray an nado kaji gasassu. Rashin sani ta ajiye gaban manager ya dago kai tare da dan murmushi ita ma ta mayar mishi, ya ce sannu....... Wata fizga yayi mata sukayi ciki ya kaita har kofar dakin mamee ya ingizata *wallahi kika kara fitowa sai na bata miki rai* ya juya.
Ta bishi da kallon takaici, su manager na ganin haka jikin kowa yayi la'asar ya dawo yanata mazurai ya nuna ma kowa plate *serve your self*
Kowa sukuku ana ci ana tattaunawa. Yana sauraron kowa yana kurbar lemu yaki cin komai.
Umaimah kuwa tana shiga ta ce mamah mun gama bari na dan huta , suka fara fira,
Bayan sunyi sallah suka dauko gyada mai bawo soyayya data siyo kasuwa ta juyo ta a tray suna ci.
Gashi an rufe kofar baya ya ce kada Wanda ya bude, ga shidda ta wuce tana son tafiya gida, ta rasa yanda zatayi. Kamar mamee ta karance ta, Uwani yau ko fira za a mun naga baki fara wannan saurin naki ba gudu gudu.
Ta danyi murmushi, na ga har yanzu suna falo kada ya ce ina mishi sintiri.... Ke kama hanya ki tafi gida kinji gobe kin san akwai lesson kuma na safe.
Taji wani kwarin guywa ta fito simi simi *ya daka mata tsawa bana ce karki fito*.......tayi baya guje
Mamee ta ganta kamar an jefo ta. Ke lafiya waya biyoki?
Tayi shiru tana kallon kofa.
Ya mike tsaye, kowa na iya tafiya gobe ma karasa by 8:00am. Yana gama fada ya haye sama da sauri.
Mamee ta ce muje ta taso ta a gaba. Ba kowa falon umaimah tayi turus.
Kama hanya ki tafi gida yanzu kyaji kiran sallah.
Ta ringa hada kafafu don sauri gudu gudu ta fito tana rufo kofa taga mutum tsaye.
Ya figeta sukayi wata hanya, me yasa ke kullum kin fi so kiga ina miki hayagaga?
Ta sunkuyar da kai.
Ya bita da kallo wai yarinyar nan yanzu bata biye mun?
Da ke nake magana . tayi shiru, idan kika kara fitowa nayi baki sai ranki ya baci daga yau.
Ta ce toh a hankali. Ya kalleta sosai, ko bakiji ba?
Naji, ta ce kanta a kasa.
Ya dan saketa ga jakar ki can da kika ki karba ta tsaraba na ce maikudi ya kaiki gida kije yana jiranki...... Ta kalleshi da sauri maikudi drivern sa da baya tuka kowa?
Ta girgiza kai bana shiga.
Dalili?
Haka nan,
Idan na ce dole fa?
Malam bafa zan shiga motar ka ba, kawai sai aga cewar waccen motar ta ajiyeni wane kallo za ayi mani?
Zai kara magana ta hada hannuwa don Allah ka kyaleni haka nan na kai makura..... Har jakar bazaki dauka ba?
Ko na karba zan raba ka da su ne ba tare da nima na amfana dasu ba to meye amfamin amsar?
Ya kalleta har zaiyi magana ya ingijeta ya wuce....
Ta bishi da kallo ohh wannan akwai bahagon mutum ta wuce tana yan tunane tunane.
Ya wuce masallaci yana magana kasa kasa cikin fada, gidan nasu zan je in kyare masu warning duk shegen da ya yi amfani da kayan inci uwashi. Ai na karanci matsiyata tun jiya.......

*Mukwana lafiya*

😘😘😘😘😘😘😘😘
[1/26, 9:18 AM] ‪+234 813 180 9991‬: 💑 *AUREN FARI* 💑

0⃣2⃣0⃣

....... Tana shiga ko zama batayi ba goggo jummai ta nuna mata tulin kayan wankin ta ita da yara,
Ko sallar magriba batayi ba ta shiga yi don ko hijabi ta nufi cirewa ta tabbatar sai ta daketa,
Karfe takwas da rabi taci dunin wankin sosai, duk suna bisa tabarma ana ta shewa ita ta basu baya.
Tsit taji gidan yayi kamar wuta ta dauke ta juyo da sauri, katti ta gani ko wane da bakaken kaya tadan ware ido nan da nan ta gane ko su waye, ta mike zumbur dai dai shi ma ya shigo wasu na binsa a baya.
Duk su goggo suka makure sun kasa ko motsi ganin ko wane da bindiga,
*Sannu da zuwa*..... Ta fada hannunta jage jage da kumfa, ya kalleta Tun daga sama har kasa sannan ya fara waiwaye ya hango tulun wankin da ke ajiye da kuma Wanda ke a robobi manya.
Ya sha mur *Zuwa na yi in miki gargadi na karshe*
Tunda mamee ta na ce sai kin mata aiki to babu yanda zanyi domin duk abinda takeso bana kin sa matsalar bazan taba daukar *Kazanta ba* duk yan aikin gidana babu kazama irin ki, ya nufeta kamar zai shaketa tayi baya ya dan bita, *Kinga wannan jakar?* kaya ne a ciki Su zaki ringa sakawa kina zuwa aiki na san ko kala nawa ne don ni na siyo, ko wane turare, sabulu, mai da duk abinda ke ciki nasan kamshin sa da adadin da zaiyi.
Ya fizgota na sanki da *Taurin kai* ki bada ko toothpaste ne kiga yanda zan *halaka ki da Wanda kika ba din*
Su goggo kowane ya zaro ido tare da hadiye wani dunkulallen miyau.
Ya kalli lubabatu dake bakin tabar ma *Ina ne take kwana?* ya daka mata tsawa. Ta tsira hannu *Gashi can*!
Ba tare da yayi magana ba cikin kattin wani ya yi ciki da jakar.
Ta kalleshi cike da takaici wannan mutum akwai wulakantacce ni zai kira *kazama*? Ji yanda yazo yana mun hayagaga har gidan mu ban tsira ba. Kai ohh ni umaimah na jefa kaina a jafa'i.
Ya kalleta sosai *Ki rufawa kanki asiri ki bi doka ta* ya juya kawai duk suka bi bayansa.
Ta bishi da harara ta wuce wurin wankin ta.
Lubabatu ta saki ajiyar zuciya, goggo jummai ta ce yau naga masifa, wannan matsiyaciyar yarinya zata janyo mana bala'i.
Kowa na tofa albarkacin bakin sa amma goggo hansatu ko motsi sai da luba ta lura sannan ta tabo ta *inna*..... Tayi firgigi ta ce *Wayyo mun shiga uku*....... Duk aka kwashe da dariya ta mike da gudu ta suri buta tayi kewaye.
Umaimah me zatayi ba dariya ba. Ta ce su goggo manya wannan 'yar barazanar ta firgitata da sune yake ma wujijjigawar da nakesha wataran mussai zasuyi. Ta kara tuntsirewa da dariya sai kawai ta ganta tsaye gabanta tana nishi idanu duk sun fito, kyayi dariya don ubanki hankalin ki ya kwanta ki kawo mana ajalinmu har gida.
Ta shiga bambami kowa ya dunga zagin umaimah.
Ta waigo goggo haka fa yake da wannan masifar ta babu gaira, saboda Allah luba bana tsafta idan zan tafi?
Duk suka kwalalo ido *Anya yarinyar nan bata tare da aljannu?* firar yau batayi tsawo ba kowa ya shige daki.
Sai goma saura ta gama tayi salloli, ta kura ma jakar ido gabanta ya fadi *Ohh ni umaimah*
Ta juya luba kinyi barci?
A a ido na biyu.
Au, kuma kikayi lamo? Tashi mu danyi fira bana jin barci wallahi.
Ta janyo jakar ta bude sai kawai ta dafe kirji *Na shiga uku* wasu irin kayana ta gani ta ce luba zo ki gani.
Mi? Tabb um um , sai kawai ta bata baya kada ma ta hango wani abin ya birgeta. Tayi murmushi ta dauka wasa takeyi sai ma tayi mata banza.
Duk sai taji babu dadi *wannan ai mugun hali ne* ta fada a hankali. Kiri kiri yazo ya firgita jama'a. Dogayen riguna masu kyau wasu matsattsu wasu budaddu, turaruka, Mayan shafa wani abin ma bata San ya ake amfani dashi ba,Gyaluluwa kai kaya barkatai , kunya ta kamata ganin brezias mtsew ta buga tsoki ta rufe jakar.
Luba dai na jinta tayi lamo.
*Madaki* kuwa suna fita yaji kamar ya koma ya dauko umaimah su tafi gida. Yarinyar nan tana wahala gidan can. Wanki hada na yara?
Amma mutanen nan akwai matsiyata, zasuci ubansu, ya kuta.
Sai na gama ci masu uwa sannan in dauketa in mayar da ita gidana zan fara nemo waye uban tukun shima dayan *shashashan*
Yayi dan murmushi Matsoratan banza duk sun rikice ganin bindiga. Sai na mayar dasu ma'aikatan ta a gidan *nasu wasa ne*
Da safe ta fito da shirin ta normal zata tafi , tayi karo da goggo lami, ta kalleta sama da kasa Sai kawai ta fizgota ta fara bugu, duk mutanen gidan suka fito lafiya?
Ta kallesu tana nishi Ku dubi duk gargadin da yarinyar nan tasha jiya a haka zata tafi. Kowa ya dauki salati nan suka yo kanta mai kulli nayi mai kwanya nayi, suka tasa ta a gaba tana ta kwalla har gaban jakar , goggo tasa hannu ta fiddo wata bakar riga tasha ado da duwatsu rigar ta yi kyau matuka da dan gyalenta karami, suka tsareta ta saka, sanan suka dauko turaruka suna feffesawa suna ci gaba da dankwasar ta *Shegiya mai kunnen kashi* baki gudun wahala baki gudar ma wani.
Ta kalli kanta ta kallesu tana kuka goggo haka zan fita da wannan dan mayafin in ratsa gari?........ Gam goggo hansatu ta buge bakin , wannan shegen bakin zai yi shiru ne? Idan ba da shi da uwaki zaki tafi?
Ta jefa mata wasu golden brown din takalma maza kisa ki tafi suka rufe jakar, duk tulin kayan babu wanda ma yabi ta kansu har su birgesu.
Karfe bakwai da rabi ta shigo tayi sama da gudu cikin bacin rai don kagare take ta iso gidan, yana kwance daki bisa gado yana ta sharar barci, haka kawai yau yaji barci kamar me,
Ta dunga bugun kofar da karfi ya tashi firgigi da jallabiya tunda ya dawo sallar asubah.
Ya kasa magana ya taso da sauri ya bude a hasale, yana ganin ta yayi turus yaja baya tayo kansa tana bala'i, me kake nufi dani ne, ya dunga baya baya tana binshi, ka firgita man iyaye ka rikitatsu ka kara jefa ni masifa, *Why are u increasing my problems?* ya zaro ido jin tayi turanci, yana kaiwa ta bango Sai ya daga hannuwan sa sama *am sorry* ta daki kirjin sa bazan yi ba wallahi na gaji da halayen ka ...... Ya ce, Ammmmm.... Ta kura mishi ido.
Kayan nan sun miki kyau. Ya bita da kallo tun daga sama har kasa yana dan murmushi, taja tsaki tare da juyawa ya fincikota ya maida ga bangon fuskarsa daf da tata ya sunkuyo, ya zaki tayar dani barci ki gudu ai yau muna nan.
Ta zaro ido..... Ya balla mata harara kilibabba an kwana tunanina zaki wani taho a 360 kina wani borin kunya.... Ya buge bakin zatayi magana naji ba haka bane kwalliya aka zo nuna mun in yaba ko?
Ta ture shi da karfi zata gudu ya maidota tabaya a jikin sa ya leko da kansa ta wuyanta, *Ke bakya godiya idan an miki abin arziki ko?* tsikar jikin ta ya tashi ta rasa in da zata sa kanta, ya lumshe ido yana shakar kamshin jikin ta.
Duk sukayi shiruuu kowa najin abin da yakeji a zuciya.
Shine mai karfin hali ya dan saketa amma Sai ya ruko hannunwan ta muje can kasan ya dan fizgeta..... Ta jiyo muryar mamee ta yi saurin turjewa ya kalleta *ya dai?*
Kai ni dai sakeni don Allah.
Ya kara fizgarta bazan saki ba haka zamu sauka sai kawai ta zukunne *Na tuba wallahi ga mamee can*!!!! ...... Shi ma ya zukunna kina jin kunyar ta ne?..........
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/8RrbAeADj5FLV7LZ24rBDH

💑 *AUREN FARI* 💑

0⃣2⃣1⃣

https://chat.whatsapp.com/8RrbAeADj5FLV7LZ24rBDH

....... Ya kyalkyace da dariya ta bishi da wani irin kallo. Mamaki ya baibayeta wai meke damun *madaki sometimes?*
Ta langabe don girman Allah kayi hakuri ba don ni ba wallahi bazan kara ba...
Baza ki kara me ba?
Ta yi shiru, kinji?
Don Allah ni dai kayi hakuri.
Okay naji zanyi amma da sharadi kullum da kinzo zaki wuce sama ki fara gayar dani kafin ki shiga inda mamee take kin amince?
Eh na amince duk ta kagara ta sauka,
Ya kalleta idan kika saba menene hukuncin ki?....ka rike albashina na amince,
No! Banda wannan... Ta kalleshi cikin kosawa duk abinda kaga dama na amince kayi man.... Ko menene? Ta daga kai eh na amince bama zan saba maka ba kayi hakuri ,
Kiyi man alkawari duk abinda nayi miki zaki rama. Ta kalleshi ya daga kai *yes*! Idan na mareki kema zaki dalla man mari. Ta sunkuyar da kai na amince, no! Kiyi rantsuwa Kice wallahi zan rama. Ta dan kalleshi kaikaice *wallahi zan rama*
Ya danyi yar dariya *Good girl* ya maida hannuwan sa baya yadan kishingida kin ce ko menene fa?
Haka na ce ta fada tare da yin hanyar falon mamee. Ya bita da kallo yana yar dariya.
Saukowa takeyi mamee ta bita da kallo har ta kusa karasowa kusa da ita, sai mamee ta dauki salati..... La'ilaha ilallahu mahammadu rasulullah tana tafa hannuwa *Uwani?* gabanta ya yi wani mummunan faduwa....
Kallon ki kawai nakeyi ina tunanin ina muka sami 'yar balarabiyar budurwa tun da sassafe kuma daga saman bene? Ta karasa maganar tana yar dariya.
Ta zumburo baki kai *Mamah* ta kyalkyace da dariya wallahi da gaske nake waya baki tsarabar makka ko kudin naki ne kika kwashe kika siyo..... Kai mamah wai ya akayi? Ta karasa gunta tana yar dariya.
Ta dago fuskar ta anya *Uwani na ce yau*? Kai wallahi kinyi kyau. Ko kefa don Allah ki ringa sauya shiga amma kullum cikin kodaddun kaya kamar almajira kina fama da hijabi balam balam kai kace matar liman. Duk suka kwashe da dariya.
Allah kullum ina son miki magana amma bana son kiji babu dadi tun da ban san tanadin naki ba.
Ta mike zuwa ciki tana yar dariya ta bita da kallo ohh uwani yarinya ce har yarinya talauci babu abinda baya boyewa kuma sai ta zamo tana da hakuri da rashin kwadayi.
Kamar kullum *Mr Samuel* yazo ta fita lesson. Yana bala'in jin dadin koya mata saboda bai taba tambayarta sau biyu ba, ya dade baiga mai kokarin umaimah ba.
Ya kalleta da yake bayajin hausa ko kadan wata biyu ta gama kwarewa da turancin sa tana ganewa kawai wajen maidawa ne wani lokacin take samun matsala amma yana gyara mata to an wuce wurin.
Ya kalleta yana murmushi *primary certificate din ki ya kammala* zan bawa oga shawara ya sanyaki js 3 kawai ina da tabbacin zaki iya. Kinga da kin je SS2 kawai kiyi WAEC.
Ta washe baki haba? Lallai naji dadi. To wane school zasu amince? Ta bukata , yayi murmushi *Madaki international school* ta zaro ido yana da makaranta?
Makarantu dai ai duk kasar nan babu inda baida branch.
Yanzu haka private university yake ginawa, kano, Kaduna, Abuja, Lagos da katsina. Zaiyi lunching a lokaci daya.
Tabb lallai ta fada.
Ya kalleta ke ai kilan anan cikin gida zakiyi ta ki.
Ta kyalkyace da dariya sai kawai taga mutum kamar an jefo shi ya kalleshi *koya mata kakeyi ko maganganun banza?*
Ya mike yana kyarma no sir is part of our lesson...... Shut up, ya kalleta 6ace man da gani kada in miki rauni...tayi ciki da gudu.
Ya nuna shi da yatsa *Ka shiga hankalinka*
Ya fara bashi hakuri. Lesson din da ba a kara ba ya hana.
Washe gari kamar yanda tayi alkawari ta wuce sama direct yau idonsa biyu, kwankwasawa daya tayi ya ce *Shigo*
Tana bude kofa ta durkusa ina kwana?
Ya dan harareta da Allah malama shigo ciki.
Ai kaji matsalar, nasan bazai taba amsa gaisuwa ta ba. Ta fada a zuci tare da shigewa ta rabe a bago.
Kinga leda can da jaka ki dauko, uniform din ki ne da school bag. Ta washe fuska ta nufi wurin da sauri.
Monday zaki fara zuwa idan kika saki kika kasa maida hankali sai na miki bugun kudina don bazan yi asara ba.
*Ta durkusa guywa biyu* na gode Allah ya saka da alkhairi ya kara arziki mai amfani.
Ya dade yana kallonta har ta ji ba dadi tunda kanta a kasa yake.
Ya ce amin.
Magana ta karshe makarantar *mix* ce wallahi kika kula wani namiji kin gama karatun daga ranar..... Ta banka mishi harara ya zaburo *Au baki dauka ba?*
Ta kwashi kayan tayi waje da gudu tana fadin *Nima so kake in tsofe irin ka ba aure*?
Ya biyota da gudu yana iyye yarinyar nan kin gama rainani ji kakeyi daf daf daf....da da da.... Karar gudu dai dai mamee na fitowa tayi bayanta wayyo mamah ..wayyo zai dakeni.
Ta tattare kai tsaya wallahi ka taba ta sai ranka ya baci. Me ta maka?
Umaimah daga bayanta ta ce uniform ya bani zan fara zuwa makaranta litinin wai idan na kula maza na gama daga ranar. Don na ce so yake in tsofe kamarshi ba aure shine ya biyoni zai daka......
Mamee ta zaro ido ta kalleshi sai wani mazuran borin kunya yakeyi. Sai kawai tayi murmushi, kayi hakuri toh bazata kara ba.
Mamee yarinyar nan fa ..... Na ce kayi hakuri *uwani shige ciki* ta ruga da gudu kuwa.
Ya bita da kallo kamar yanda mamee itama ta tsareshi da idanu.
Fakam fakam yayi sama.
Ta koma ta zauna bisa kujera *Haba wallahi koda naji* fitinar nan ta uwani da madaki ta isa watan *Son ta yakeyi shi ne yaketa wannan haukan*
Wani sanyi ya diri zuciyarta bani da matsala da uwani wallahi. Ta rike haba *ohh*....
Ta yi ciki ta tarar da ita zaune. Ta na ta nishi.
Ta kalleta taji ta kara sonta fiye da *da* wannan kauna da nakeyi ma uwani ta isa, ashe surukuta zanyi da ita.
Ta zauna kusa da ita, uwani?. Ta kalleta kawai, ki daina biye mishi kina wannan mugun gudun wata rana sai kinyi wa kanki rauni. Idan ya taso ki tsaya kiga zai kasheki?
Duk sharuddan da ya kindaya miki to kibi su babu kuskure matukar kina son Ku zauna lafiya ya daina wahalar da ke.
Ta ce toh, ta kalleta wai rigunan da yawa kika siya haka naga ta yau tafi ta jiya kyawu.
Ta yi murmushi mamah wadannan kayan fa *Madaki* ya kawo mun ta zaro ido *madaki* ta kwashe duk yanda akayi ta fada mata sai kawai ta hau dariya *Au har mutanen gidan naku ma basu tsira ba?*
Lallai abun nashi azimun ne. Shawara daya zan baki ki daina hawa sama idan yana nan in ba wani kwakkwaran dalili ba ko gyara idan zakiyi ki bari sai ya fita office ranar da duk bai fita ba to ki kyaleshi.
Ta ce toh.
Ranar litinin tunda safe ta iso a falo ta tarar da shi nan suka gaisa tayi ciki don shirin makaranta.
Ta dora hannu a kai *Na shiga uku* dan skirt ne bai karasa kai guywa ba hade da karamin wandon sa sai farar riga yar shirt mai karamin hannu tare da neck tie. Ta zaro ido wai makarantar su Khausar zanje? Irin kayan su ne ta shirya tsaf, da doguwar safa sai farin takalmi *camp bus* sai yar hula karama daman tayi sabuwar kalaba kanana amma duk ta hadeta wuri gida ta kulle, shiru shiru ta fito mamee ta shiga ta ganta tsaye. Ke fa kadai bus ke jira gasu can suna *oda*
Mamah haka zanje? Ta zaro ido babu ruwansu da ke makarantar duk turawa ke koyawa..... Kirjinta ya harba. Mamee ta kamo hannunta ta sagalo jakar sai rinjayarta takeyi saboda nauyin litattafai. Ya bita da kallo wani kishi ya turnukeshi ya daga murya.
Mamee.... Ta juyo da sauri
Sai kawai yasha mur ya kalli umaimah *Ke jeki sanyo doguwar hijabi idan kinje makarantar kya cire*
Mamee ta dankara mishi harara ke muje ta fizgeta.
Ya taso da sauri suna fita ya hango su baffa

Please Login or Register in order to submit comment