Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Kishin yarinyar nan yayi yawa, daga *Hugging?*...... Kai na gamu da gamona ni madaki, problem din ta gama gane na mutu kanta,
Ya tashi zaune, kaii..... Lallai , in ba umaimah ba wace yar iskar yarinya zan ringa bi tana mun wannan wulakancin, wai ni madaki nake ba mace hakuri tana mun tsawa a kai.
Mtseww *I hate this condition* ya dafe kansa.
Ta tsaneni ko ganina bata son yi? Ga mamee na sane ta zuba ido?
Ya kara tsoki, wallahi zuwa zanyi ayita ta Kare na gaji, ita bata da tausayi ne?
Ya sauko sai kawai ya hangota ashe mamee ta aiko ta,
Tana hangoshi ta juya zata koma ya karaso da gudu ya tari gabanta, ki dubi girman Allah ki saurareni umaimah .....zatayi magana ya katseta, ,,... *Girman Allah na ce*
Tayi shiru. Haba umaimah wannan kiyayya haka ko lokacin da muke tsahin hankalin ma bakiyi mun haka ba ballatana yanzu da muke son juna kawai dan kuskure ne da za a iya gyarawa..... Ta kalleshi *Dan kuskure*
Yayi saurin daga hannu sama, *Babbar matsala* ce afuwan.
Wallahi samira babu wani abu tsakanina da ita, kinji na miki rantsuwa ...... Ni na ga haka tunda ka mance dani ka mamuke ta,... Kamar zaiyi dariya ya dai tsuke, shin ai don na hugging din ta ko?
To wallahi bazan kara ba, yanzu haka na rantse da Allah ko clerks dina tsoransu nakeyi.
Tayi mishi banza, ya nuna mata kujera don tsoron tabata yakeyi ki zauna ba don ni ba don Allah...... Ta zauna kanta gefe tasha mur,
Ya ce kut, cikin rai.
Ya fiddo waya duba ki gani text din da tayi mun ko a ranar sannan tabar mun note office hada zagi na rantse da Allah baki bina bashin rantsuwa umaimah ban kulata ba har yau.
Ko kirana akayi yanzu naji muryar mace gabana faduwa yakeyi . ya kamata ki sassauta man saboda akwai huldodin da dole dasu nakeyi........ Na fika sanin haka, don yanda ka saba taba jikin mace bazaka iya ko wace hulda bata ba........
Innalillahi sharrin da zakiyi man kenan? ..... Ni na gani da ido na.
Ta taba wayar gari nan gidan baka dankeni ba?
Haka idan kaje office ka dunga rungumar mata sannan ka dawo nan ka dosa dani ...ta kalleshi na maka kama da *Yar iska?*
Ya zaro ido umaimah ki fahimceni.....wallahi ban fahimtar ka, ni bakai man ba.
Ta mike tsaye ina rokon ka ka ajiye maganar so mu ringa mutunta juna. Wallahi bani iya auren namiji mai hali irin na ka....... Ya tari gabanta idan na taba rike wata diya mace bayan ke Allah ya tsine mun, sai kuwa samira tun yarinta idan mun hadu zamu........ Zaku kadaddabe juna.
Ya langabar da kai, *Kiyi hakuri* in shaa Allah na miki alkawari hakan bazai kara faruwa ba.
Zatayi magana ya hada hannuwa *Na tuba* kiyi hakuri na kai karshe wallahi na horu, ba zan kuma na please........
Ta kawar da kai *Ya wuce*... Ya saki wata sanyayyar ajiyar zuciya har sai da ta waigo ta kalleshi ya sakar mata murmushi...ta kara tsuke fuska.
Ya zauna taimaka ki kawo mun ko tea ne inyi buda baki, ta kalleshi da sauri......
Kina mamakine?
Wallahi bana sahur bana buda baki kullum daga dabino sai madara nake sha.
Ya langwabe ai na ga *Bone* kwanakin nan..... Ta wuce shi kawai.
Shiru shiru mamee ta fita taga lafiya kawai taji maganar su falo sai kawai ta sadada ta koma,
Ta zubo mishi farfesun kaji da fruits salad nan da nan soyayya ta tashi, da ya kawo hannu zai kamota sai ya tuna ya basar .......
Ana tsoron mu nida iya, inji diyar mayya......πŸ˜ƒπŸ˜ƒπŸ˜ƒπŸ˜ƒ
Suna nan sai dai kawai sukaji liman ya kwala kiran sallah....Allahu akhbar....

*Maman Abdallah*
😘😘😘😘😘😘😘😘

Na gode da addu'o'in Ku.

Aunty rabi na godiya matuka🀝🏼😘
[1/27, 7:42 AM] β€ͺ+234 806 091 7227‬: πŸ’‘ *AUREN FARI* πŸ’‘

0⃣2⃣7⃣

*Abincin wani gubar wani ina rokon duk Wanda labarin nan bai mishi ba don girman Allah kada a karanta don Anyi shi ne kawai don ilimantarwa da nishadantar wa, duk wani marubuci mai hikima yana kokarin fiddo abinda ya zama ruwan dare a rayuwa ya misaltashi kafin ya nuna illar sa. Maganar runguma da akeyi ai gashi nan a universities 'yayan hausawan mu suna chudanya da maza rike hannu da rungumar basu daukeshi bakin komai ba, mafi yawa kuma sakacin iyaye ne, saboda haka ina sane da abinda nake rubutawa a daina sauri ana zarbabi, masoyana kuma ku sani labarin AUREN FARI wallahi na rubuta shi don girman SOYAYYA saboda haka ni bani raina masoyina duk in da yake kuma ko yaya yake. Ku sani nafi kaunar ku fiye da yanda kuke son labarin AUREN FARI wallahi, Allah yabar so da yarda. Kada a manta don HAJIYA RABI BADAWI MAMAN IBRAHIM DA NURY na rubuta AUREN FARI da duk daukacin masoyana.*

...... Ya kalleta ta kalleshi, suka kwashe da dariya, ni ban taba kwanan zaune ba yau gashi ka janyo mun,
Mamee ta fito, me zatayi ba salati ba, anan kuke zaune har assalatu?
Umaimah ta buga hamma,
Ya kalli mamee to tunda kin sa mun ido zanyi mussai a cikin gida ba dole ni in shawo kan abata ba,
Ta wurga mishi harara, mamee tayi yar dariya au ka bayar da hakurin?
Dole na ma,
Kuma shine ka tsare mun 'ya har assalatu, duk kuna cewa me?
Ohh yauni na shigesu da mamee fira mukeyi da begen juna ko bakiga kwanakin da muka kwashe ba tana gudu na,
Ya mike samira zata janyo mun ko ma in ce ta janyo mun bala'i.
Au wai duk fitinar akan samira ce?
Dai dai ya zauna bisa dining wallahi mamee ita ce daga *Hugging* yarinyar nan ta birkice mun,
Da kyau......mameee ta fada itama lokacin tana zama.
Uwani taso muyi sahur kike ta hamma daga zaune,
Da kyau fa kika ce mamee,
Eh mana, ta mun dai dai kaga yanzu sai ka fahimci abinda kake aikatawa bashi da kyau lokacin da nake fada ma dariya ma na baka irin ban waye ba to yanzu kaga wayewa zata bi da kai don da alama uwani ba sakarkarun matan nan bane...
Ya bata fuska, mamee ban tunanin gidan nan zaki taba ganin laifin yarinyar nan, maimakon kiyi mata fada ta sanyawa ranta hakuri ki kwatanta mata yanayin huldodina da mutanena shine zaki kara zuga ta?
Akan me?, ko kadan wallahi, huldodin banza sai aka ce hulda dole da mata za ayi ka kamo hannun waccen ka riko waccen.?
Mameee......... Haba wannan wace irin shaidata ce kin mayar dani magnet.
Ai na daina ko sunan mace bana son ji yanzu,
Ta tuntsure da dariya, da sauranka yaro.
Umaimah na gama hada musu ta dauki nata tayi ciki yayi kiran duniya ko waige, da basu yi haka ba kamota zaiyi ya bita da kallon takaici, duba kiga abinda takeyi man mamee tana jina tayi shiru in rikota yau in wuni cikin azaba........ Kaii ni *madaki* naga ta kaina.
Me mamee zatayi ba dariya ba. Ai uwani na birgeni wallahi ka sami mata dai dai da halinka. Saboda duk wacce ka aura tana jin tsoronka ko tana binka saboda dukiyar ka bazata taba fada ma gaskiya ba, bazaka taba gane kayi kuskure ba haka zalika baza ka taba gane rayuwar aure ba har abada.
Amma a yanzu uwani ta fara bi dakai hanya.......haba mamee,
Tayi yar dariya na yi karya ne?
Zaiyi magana canza zancen, jiya *Yaya ta kirani*
Watan babbar yayarsu ta Kaduna,
Ya bata fuska su Aunty jamila sun kai mata gulma ko?
Madaki..... Ka dubi girman Allah ka daratta yan uwana bana son kana nuna masu ko ka shiga maganar da ba taka ba. Ya ajiye spoon shi kenan na daina in shaa Allah.
Me ta ce miki?
Tambayata takeyi da gaske ka sami mata cikin yan aiki?
Na ce mata eh amma ba yar aiki ba ce.
Kika bata bakin ki? Sai ki bita da eh,tana da abinyi ne?
Mamee na fama da yan uwanta, yaya ta kaduna ita ce babba sai ita mamee din sannan anty jamila da aunty murja, Aunty jamila ita ce munafuka duk wani motsi da mamee zatayi ita ce ke kwarmata wa sauran.
Mijin yaya yafi madaki kudi nesa ba kusa ba. Amma idan sabga ta tashi mamee ce dawainiyar su da komai, basa tausayin ta ko kadan, yaya bata wata bata fita wata kasa ba, amma ko sabulu bata taba kawo wa mamee ba da sunan tsaraba.
Mamee kuwa da yake tafiye tafiyen bai dameta ba sai kamar ko umara daga can su biya kasa daya ko biyu, haka zata bi su da kayayyaki designers su da ya'yen su, idan sallah ta tashi haka zata dunke 'yayansu da tsadaddun kaya. Ta aika mota a dauko su tela ya auna su.
Amma sai yayar ta ce ana ma yaranta dunkin banza a ringa kawo mata suna badawa dunki.
Kullum dadi sukeji madaki yaki aure har suna gulmar koda kudi ba sai da farin jini ba?
Jin ya sami mata yar aiki kuma yanzu surutu ya karu.
Ya riko hannunta, mamee ki kwantar da hankalinki kada duk abinda zasuyi ya dameki.
Ko kadan kawai ina takaicin uwa daya uba daya amma bakinciki ya shiga zumunci da jin zafi.
Cuta ce mamee, hassada sukeyi miki kuma sune a kasa kada ki fasa kyautata masu, kullum ina fada miki daga naira daya zuwa miliyan dubu mamee kada kiji shakkar tambayata koda kina sha'awar kawai in baki kisa masu wuta.
Tayi yar dariya Allah yayi Maka albarka umar, Allah ya kara maka arziki mai amfani kaima ya baka yaran da zasu ji kanka su tausaya maka su kula ka kamar yanda kayi mani.
Aamminnnn mamee, amin.
Ina so daman muyi magana,
Tsakanin ki da Allah mamee Umaimah ta miki? I mean uwani,
Tayi murmushi, kwarai kuwa, hasali ma ni uwani tayi wa kafin tayi maka......ya kyalkyace da dariya na sani.
Ina maganar fa AURE. Ta daga kai tabbas kuwa ta yi mani wallahi bani da matsala ko kadan da uwani, yarinya ce mai hankali, barkwanci, girmama na gaba da ita, tausayi, bata da kwadayi uwani bata sata, na auna yarinyar nan yafi sau dari amma wallahi daga baya ma sai da na ji kunya,
Yanda duk baka tunani ina son uwani ummaru.
Ya fadada fara'ar sa to ina son kiyi man alfarma in je in nemo auren ta a daura mana aure ranar sallah.
Ta zaro ido baiyi sauri ba? Karatun ta fa?
Duk ina sane dashi wallahi wallahi bazan taba hanata karatu ba mamee ko PHD take son yi zan kyaleta amma aiki ne bazatayi ba.
Maganar sauri kuma zanje Abuja muyi magana da baba Lawal da baba Nura sune zasu sanar da sauran.
Zan biya Kaduna da kaina na fadawa...... A a ita dai ka bari na fada masu.
Amma ka fara tuntubar uwanin kuyi shawara sannn.....mamee rigimar yarinyar nan nake tsoro kada ta birkice mun kuma,
Dariya mamee keyi hada kwalla wai yau *Madaki* ke Shakkar wani abu a rayuwar sa,
Yayi murmushi, Allah kuwa rigimammiya ce.
To kasan abinda za ayi?
Ka je kuyi magana da mahaifin ta komi ya ce shi kenan...... Haka za ayi ya fiddo waya,
Kai bani son hauka.....amma ina har ta fara ringing, ya ce to ai yanzu yana sallame sallah zai fita gara in fada mishi ya jira in zo.
Hakan kuwa akayi.
Yana dawowa sallah ya shirya kawai ya fi ce,
Umaimah kuwa tana sallame sallah itama ta kudundune a bargo, mamee na shigowa ta tarar da ita, sai kawai ta rage mata A.C ta ja mata dakin ta koma falo.
Malam bawa ya share zaure da kansa ya shinfida tabar ma yana jiran Madaki.
Shi kadai yazo, bayan sun gaisa yana ta tsumayen yau kuma da me yazo?
Ya dan yi jimm, baba adaiyi hakuri don Allah...
Haba haba wallahi babu komai in ce dai lafiya?
To kusan lafiyar dai zance, wallahi wata alfarma na zo nema da kuma shawarar ka,
Ya kalleshi a mamaki yallabai tami kuma?
A gaskiya baba ina son umaimah kuma so na aure hasali ma idan za a taimaka man baba ina son auren kada ya wuce sallar nan idan muna da rabon kaiwa.
Yadan yi shiru, jin malam bawa bai ce komai ba ya ci gaba da cewa,
Wallahi bana son ko tsinke naku na yafe ita kadai nake so ku bani sannan zan dauki duk wata dawainiya ta bangaren ku.
Wannan ita ce alfarmar da nake nema, shawara kuma,
Ina zullumin kada umaimar taki amincewa don yanzu haka na sanya ta karatu tanayi kuma na yi alkawarin wallahi zan barta ta karasa duk inda take son kaiwa a matakin karatu. Shin in sanar da ita ko inyi shiru?
Ya dan yi shiruuuu!!....
Ya langabe baba don Girman Allah ka taimaka man.
Haba yallabai, babu abinda zaka roka in hanaka, matsalar ina da yan uwa kauye zan so na sahawar...... Idan har kana ganin babu damuwa na amince mu je yau ka gabatar dani. Kafin iyayena su koma.
Ya danyi murmushi yallabai hakanan zaka wahalar da kanka in shaa Allah zan je da kaina.
Baba kayi hakuri don Allah ..... To shi kenan bari na shiga na fito kada rana tayi mana hanyar bata da kyau.
To baba maganar umaimah fa in fada mata?
Rabu da ja'ira ni zan mata magana da kaina don kada ta ga laifin ka tunda har kana da tabbacin zata iya birkicewa.... Ya shige gida in ba iyeshe na yaran yanzu ba ita har tana da abinda yafi auren a wannan maraicin nata?
Sai biyu da rabi suka dawo, Madaki na ta murna yanda aka tarbeshi kai wadannan mutane da mutunci suke,
Shima malam bawa yana ta jin dadin yanda madakin ya saki jiki kuma ya girmama yan uwansa ba tare da raini ko nuna kyama ma.
Suna zaune falo ita da mamee ya shigo yayi lilis don gajiya, mamee ta kalleshi yanda ya zauna da kyar,
Wash wallahi na gaji mistake daya nayi da na tuka mota yau.
Ke baki iya cewa sannu da zuwa darling?
Mamee ta harareshi ka dawo zaka sa miyon bakina kafewa ina ka tafi yau wayar ka ma bata samuwa?
Bari mamee wallahi mutanen nan na dade ban ga masu mutuncin su ba, mota ta nacen cike da buhunnan wake da aka bani.
Nan da nan mamee ta dago shi ta kalli umaimah uwani jeki karasa man gyaran durowar kinji....... Kiyi sauri danayi sallah zamuyi zance.
Ta yi ciki tana dariya mamee ta bishi da harara, ina sauraron ka ni ra sa kunya.....
Ya kwashe duk yanda akayi ya fada mata.
To amma kai yanzu ga azumi ya zakayi da wadannan tafiye tafiye ga hada kayan aure, ....ya mike tabbb ni kuwa nasan yanda zanyi mamee ya haye sama
.......

Kuyi hakuri wallahi yau school naje.
Afuwan πŸ‘πŸΌπŸ‘πŸΌπŸ‘πŸΌπŸ‘πŸΌπŸ˜ƒ

*Maman Abdallah*😘😘😘😘😘😘
[1/27, 7:42 AM] β€ͺ+234 806 091 7227‬: πŸ’‘ *AUREN FARI* πŸ’‘

0⃣2⃣8⃣

........ Daga masallaci ya wuce shi da driver gidan su umaimah, lokacin da suka isa malam bawa ya gama shinfida zaure,
Ya tare shi cikin girmamawa amma Madaki sai sumsumkewa akeyi alamar nauyi da kunya.
Bayan sun zauna malam bawa ya mika mishi hannu alamar su gaisa Madaki ya zukunna har kasa abinda ya kara daure kan sa kenan.
Bayan sun dan zauna jimm, malam bawa ya kalleshi wallahi ranka ya dade tunda naji wayar ka na kasa natsuwa ina ta zullumi da fargabar ko lafiya?
Ya danyi murmushi lafiya qalau baba daman ina son rokon wata alfarma ce kuma da neman shawarar ka.
Alfarma? Wallahi kafi karfin komai a wurina yallabai. A yanda nake jin labarin ka a gari ban taba tabbatar wa ba sai da naga zahiri. Ka cika *Da* na halas! Na ji dadin yanda ka mun duk mai son ka a rayuwa shi ke fada ma gaskiya...... Baba mubar maganar nan ta wuce!
Abinda ya kawo ni ina neman Alfarmar *Auren umaimah*...... Ya dago kai da sauri....... Kada in ce daman furucin ka na farko da gaske kakeyi ko kuwa har yanzu kana da tunanin...... Wallahi baba bani da tunanin komai sai alkhairi.
Ina son umaimah saboda Allah kuma ina son ta zamo *Uwar 'ya'ya na* Alfarmar da na ke ka taimaka man da auren ta karamar sallar nan mai zuwa.
Baba amincewar ka kawai nake bukata wallahi tsinke bana so daga gareku sai ita kadai. Maganar hidima zan dauke muku komai.
Yayi shiruuu...... Kafin yace, Alhamdulillah.
Na ji dadi sosai da wannan albishir domin a gareni albishir ne, gareni baka da matsala, amma ka sani ina da yan uwa a kauye wadanda suma suna da hakki akan yarinyar kuma muma muna da iyaye zan so ka bani lokaci.......
Baba banyi gaggawa ba amma ina rokon ka da idan babu damuwa yau zan kasance tare dakai matukar zaka jagorance ni garesu in gabatar da kaina kafin in aiko da magabatana.
Yayi murmushi wallahi babu wata damuwa sai mu tafi.
Sai maganar shawarar ka, agaskiya ina tsoron fadawa umaimah kada ta birkice mun....... Au daman bata amince maka ba?
.....wallahi tana so na baba, na sanya ta makaranta ne, to bata son katse karatun nata....... Yayi dan murmushi *Au*,
Kuma zan barta ta karasa karartun ta sannan idan ma tana son karawa gaba na amince *Aiki* daine bazan amince ba. Shine na ce in sanar da ita din ko kuwa ana zaku mata bayani?
Malam bawa ya mike tsaye kaima ka zama yaron kenan, kyale ja'ira kada Wanda ya ce mata qala, tunda har kana tunanin zata ki amincewa. Bari na sako babbar riga kada muyi rana yayi ciki.
Goggo hansatu ce ta fara tarar sa malam kai da wa ye haka tunda safe?
Ya fadada murmushin fuskar sa, maneman auran umaimah ne yanzu haka zamuje kauye....... Ta daki kirji *Aure?*
Suna fitowa Abba yazo zai wuce fangan fangan... Malam bawa ya daka mishi tsawa ganin zai ingije bako.
Yayi yar dariya babu damuwa baba.
Kayi hakuri ba natsuwa a hanya yake fada mishi ko waye Abban, ya tausaya masa tare da alkawarin da sun dawo zai daukeshi yakaishi *Rehabilitation*
Yayi mishi bayani sosai ya kuma gamsu yana ta godiya.
Kauye ne mai cunkusassun gidaje,Abinda yaba malam bawa mamaki shine yanda *Madaki* ya saki jiki bai nuna wata kyama ba ko shimfida akayi mishi sai ya yaye ya zauna yanda kowa ya zauna, babu Wanda baiba girma ba. Wannan abu ya wa malam bawa dadi a rai. Hatta kananan yara sai da ya raba musu kudi.
Shi kuma duk gidan da suka je sai an basu ko gero ko wake, haka suka dawo da tumbaye ransa sayau, Yayi yayi malam bawa yabar tumbayen abincin nan amma yakiya.
Hakan ya kara sanyaya zuciyar Madaki kaunar umaimah da tausayin iyayenta ya karu cikin ransa.
Karfe biyu da rabi ya isa gida suna zaune falo mamee taga ana shigowa da yan buhunna , ya shigo mamee ta kalleshi duk ya gaji..... Daga ina haka?
Ya zauna wash!
Sannu da zuwa, umaimah ta ce dashi tana satar kallon mamee.
Yawwa my dear ya gida?
Sannu da gida mamee love.... Kai ban son iyashege kaji ko.
Ya tuntsure da dariya umaimah dai tayi ciki.
Ya bita da kallo *Ke dawo*....... Amma ina ta shige.
Ya kalli mamee yarinyar can dole inyi maganin ta ta raina ni,
Naji, ina ka tafi ko wayar ka ba a samu ka shigo da wasu yan buhunna kamar Wanda yaci kasuwar kauye..... Kin canko dai dai.
Kauye naje mamee.... Kauye?
Wallahi kuwa ya bata labari kaf!
Ta rike baki Allah sarki, wayyo Allah kai masha Allah wadannan mutane sunyi bazata..
Kwarai kuwa.
Gobe zan tafi Abuja zamuyi magana dasu baba Ibrahim muji me zasu ce. Sai in biya Kaduna ...... A a ka bari zan fa da ma su yaya.
Ya dauki waya yawwa kaga missed call dina ko?,......okay ka ganshi? To passport nake so latest jibi don na gama magana da embassy..... Ya kashe.
Me zakayi da passport?
Na umaimah ne umara zaku tafi kuyo mana addu'a kafin ku dawo na gama wasu gyare gyare.
Don Allah? Kai masha Allah.
Amma naso ka bari sai karshe...... Mamee kuyi hakuri bana so kuyi sallah can saboda daurin aure ya mike. A ajiye mun kayana kada a taba mun,
Ka fada mata?
Kiyi shiru sai zaku tafi.... Kai ban son shirme komai ayi shiru komai ayi shiru to sai na fada mata.
Ya haye sama kunfi kusa..
Sallah kawai yayi ya kwanta barci.
A saman yasha ruwa cook din sa ya hada mishi tea da sandwich.
Umaimah taji shiru har ta dawo asham amma bai sauko ba ga mamee zaune tana kunyar ta kirashi sai kawai ta tura mishi text.
*I know for sure that you are my life, Since the time you have left today ,i feel so blue and nothing interests me, i think you have taken a part of me ,And I really can't survive without you ..I love you and I miss you , You should know that I truly do ,Please come down soon!* Ya maida mata amsa *When I say thank you, I mean it from my heart, Dear you helped me achieve so much, You were there from the start, A heartfelt thank you to you, am coming dearest*
Bata karasa karantawa ba ta hango shi yana saukowa, ya sha wanka cikin kana nan kaya *Kai madaki nada kyau* suka hada ido ya sakar mata wani narkakken murmushi ta mayar mishi tare da sunkuyar da kai.
Mamee na lura da ita, sai tayi kamar bata ganshi ba ta mike uwani idan kin gama kallon kya kashe ni kam na gaji...... Mamee barka da shan ruwa ina zuwa kuma?
Au ka sauko? Barkan mu juna, zan dan kwanta ne na gaji.
Yayi murmushi kawai.
Tana wucewa ya ce matso malama ki fassara mun text din ki.
Ta danyi murmushi kawai, ansha ruwa lafiya?
Qalau,
Me kika rage mun?
Kosai.....
Ya kyalkyace da dariya wallahi banci, sai me?
Dan na rogo....
Ya fara dariya.
Ta tashi ta dauko mishi yanballs da samosa, sai dan juice din ta na kwakwa da fresh Ginger, mamee ta ce kafi son mai dan nama nama gashi idan zaka iya ci don kai nayi.
Ki ce Allah!
Allah kuwa,
Ya janyo cooler iyye yarinyar nan fa zatayi *Caring*
Ta ce hmmmm
Ya fara ci yana Santi
Cewa zakiyi nabar banza na tsaya cin sandwich saboda kiwa.
Gaskiya.
Ya dan zaro wani abu gaban aljihun sa kawo hannun ki in baki tukuici.
Ta mika mishi, ya zo zai kama tayi baya dashi da sauri tare da 6ata rai, wallahi kaga abinda na tsana a tare dakai.
Ohh am sorry please. Ya kamata ka fidda wannan muguwa tabi'ar a ranka gaskiya domin wallahi haramun ne,...... I said sorry woo..
Yeah I know but let me tell you, ka fidda fashion a maganar nan ka sanya addini, taba mace baliga haramun ne , me yasa namiji baligi ko baliga idan sukayi alwala akace shafa ko babu sha'awa alwalar ta warware?
Addini fa sauki gareshi wallahi ko musulman mu dake zuwa kasashen turawa suna gaisawa dasu bala'i suke daukar ma Kansu.
Haka ma khausar a school sai da na mata magana ita da kawayen ta kawai kana zaune kato zaizo ya kai hannu ya dafa ka ko ya kai duka wai abobota.
Ya kamata ka daina bana so na fada ma da arziki, na fada ma cikin fushi to yanzu na fada ma a addinance wallahi next bazatayi mana kyau ba.
Wallahi na daina kiyi hakuri ungo zobe ne zan saka miki amma saka da kanki Allah ya bada hakuri ustaziya ta.
Ta yi murmushi.
Shi yasa na ce wa mamee kuje umara

Please Login or Register in order to submit comment