Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Kirarin sa kenan a gari. *madaki nada kyau* shi ba fari ne ba amma saboda hutu, kudi da kuma jin dadi yasa farat daya baka iya gane hakan. Irin kalar nan gareshi ta bakake mai kyau watan mai haske kamar chakuleti. Amma yana da sumar kai mai laushi da tsawo. Kullum tana kwance luf luf tana sheki da kamshi.
Dan gayu ne na karshe kuma miskili na kin karawa.
Ya kasa yin budurwa saboda mugun miskilancin sa ya ce babu macen da zai yi wa bauta ko ya bita yana lallashi bare uwa uba har ya mata laifi ya bata hakuri. Duk Wanda ke tare dashi yasan haka,
Mamee ta kalleshi cikin ido. Gaban sa yayi mugun faduwa yasan doka ce zata saka mishi ko umarni ko kuma wani gargadi mai amfani.
Kaga yara falo? Kaje ciki ka ga wacce tayi ma duk na san halin ko wace ciki da mahaifanta, tunda ka ce baka son auren zumunci. Sannan na baka dama har kishi uku kana *failing*
Ya kalleta namee ....wallahi bazan kuma sauraron ka ba, kaje kayi abinda nace kada ka hadu da fushi na. Haba madaki ya zaka maidani sakarai kana nufin baka aure ko me? Ko kuwa matan banza kake bi namiji cikakke kamar ka bai yiwuwa ace har yau bakaji son ko wace mace ba........ai kinyi sauri ne mamee.
Ta daka mishi tsawa nayi saurin don iyayenka, kaje kayi abinda na umarceka kada ranka ya 6aci.......
Ba kince kin san halin ko wace ba? Kije duk wacce tayi miki cikin su shi kenan......yasa kai ya fice kamar ya kurma ihu don takaici.
Tayi kasakΓ©...!!! Wannan taurin kai na madaki ya zanyi dashi?
Ransa ya gama kara jagulewa, tayi wayar duniya ya sauko yaci abinci yace ya koshi. Haka ya kwanta ga azababben tunani ta ko'ina ga yunwa.
Haka ya kwanta har safe ga cook din sa baya nan yayi tafiya,
Karfe takwas ta iso, mamee tayi kiran duniya yazo ya yi kalaci amma yaki daga waya,
Duk tunanin ta fushi yakeyi, har karfe goma bai sauko ba,
Ta kwala ma umaimah kira, tazo.
Hau sama ki kira man umar.
Hmmm kawai ta fada ta juya. Don bata san me zata fadawa namee ba.
Shin ai duk masifar sa bazai dauki raina ba ko? Wata rana sai labari. Ita kadai ke sabbatu, tana tafiya, gabanta na dada faduwa.
Ta kwankwasa har kusan sau shida ba ayi magana ba. Tayi tsaye tana tunani kada ta shiga a kara yar gidan jiya, har zata juya sai taji wani irin kakari daga ciki. Ta saurara da kunne tabbas shine. To lafiya? kakarin amai taji ta Murza kofar taji ta a datse, ta sauka da gudu ta nufi dakin mamee tana kwala mata kira mamah! Mamah!! Mansura ta tareta ta zagaya baya fa.
Tana jin haka ta yi hanzarin zuwa ta dauko mukulli ta kara hawa saman da gudu.
Kwance yake saman kafet cikin amai ko in ce kumallo, gashi yana fama da ulcer. Ya duke yana ta murkususu ya dafe cikinsa.
Ta doka salati ta nufi inda yake ta dago shi *baka lafiya?* da kyar ya daga kai *Bani wani abu in ci please*
Ta sakeshi da sauri ta kara yin kasa, duk an shirya kalaci a table ta hado tea da madara ta zubo farfesun koda ta hanzarta.
Yana inda ta barshi. Ta ajiye kayan ta kamashi zaka iya tashi? Ya girgiza kai alamar a'a. Ya hakuri ka daure bana iya dagaka ta yaya zakaci abinci cikin amai?
Ya daddage ya dafata zai mike ta durkushe duk suka fadi gefe. Ta ce wash!
Ungo sha tea din. Ya kasa motsawa. Ta lura tabbas ya gama galabaita sai kawai ta ringa diba tana bashi.
Yaushe rabon da ya sha tea da madara?
Ta dunga dura mishi da spoon yana sha yaji dadin da ya rabu da ji a rayuwar sa.
Tana bashi tana faman sannu.
Ya shanye duka, ta dauko naman shima ta fara bashi, ganin ya fara farfadowa ta kalleshi kamar hada yunwa ma ciwon.
Ita ce ma ba ( kamar ). Jiya banci komai ba gashi ina da ulcer.....ulcer? Ai wannan wauta ce ta fara bambami, gashi ka garkame daki ai da kayi mussai yau.
Ya kalleta sai ta bashi dariya, yayi murmushi kawai.
Wai me ma ya kawo ki dakina?
Ta dalla mishi harara nazo *ceton ka* ya dan tureta zai tashi yayi luuuu ta taroshi da sauri ya fizge ta bishi da kallo. Me ya kawoki dakina?
Mamee ke kiranka.... Kada ki fada mata abinda ya faru.
Naji ta fada tare da mikewa. Ya tashi da kyar ya dauko magani yasha.
Ta tafi ta mayar da kayan . ya sauko ya nufi dakin mamee yaji kiran.
Umaimah kuwa tana kai kayan ta koma saman ta goge aman ta gyara mishi dakin tasanya mishi freshener ta canza mishi bedsheet sannan ta shiga kewaye ta wanke mishi.
Tana gamawa ta tabe baki. Allah yasa yau ya zame mishi ishara ya rage zafin rai.
Tana sauka shi kuma yana hawowa, ya kalleta sama da kasa, ina kuma kika je? Me kike mun a sama.
Ta kalleshi ci ke da takaici, abar hali aci me? Gama rasa me zata ce mishi kawai ta raba shi ya fincikota ya hada da bango.
Bana hanaki ina magana ki gudu ba?
Ta kalleshi kai wane irin mutum ne?
Irin ki ne.
Ta girgiza kai ni ba haka nake ba........ Ke bakinki bai mutuwa ko?
Ikon Allah, ta fada.
Saboda bana son maganar zan tafi ka dawo dani shin me kake so?
Jiya kin mayar dani sakarai kin pretending na shiga ciki kin gudu ko?
Kin gwammace in rike albashin naki da ki dauki jakar can ko?
Kwarai kuwa na hakura da albashin. Don haka bani wuri in wuce.... Ta ingijeshi ya daki karfen bene ta baya.
Tana yin step daya ya murdo hannunta ya maidota da karfi jikin sa ya maida hannuwan sa duka bayanta.
Wani takaici ya diran mata sai kawai ta dora kanta a kirjinsa tana kuka.
Jikin sa yayi mugun sanyi, yayi shiru!!!... Tayi mai isarta tukun, ta dago, yayi saurin sakin ta, ta kalleshi idanu jawur, na rasa yanda zanyi da masifar ka, munzo na baka hakuri na daina shiga sha'anin ka, kullum da abinda kake tokalowa.
Bana son hadaka da mahaifiyar ka amma ka kasa ganewa. Kwallah suka shatato mata.
Na gaji na gaji. Wallahi zakayi dana sanin wulakancin da kayi man yanzu. Bani kwadayin kudin ku. Ina yiwa mutuncin mahaifiyar ka ne.... Kuka yaci karfinta da gudu ta sauka. Ya bita da kallo kaman ya kamota ya bata hakuri amma baya iyawa.
A sanyaye ya hau sama, turus yayi ganin yanda dakin ya koma, ya zaro ido innalillahi yarinyar nan ashe gyarawa tazo tayi. Ya dafe kai *ohhhh my God* jikin sa ya kara yin sanyi,
Umaimah kuwa tana baya ta lafe tana ruzgar kuka, tayi mai isarta, sannan ta goge fuska, *In shaa Allah bazai kara ganina ba* ko mamah ta aikeni zan San dabara amma wallahi bazan yarda ya kara sanya ni a ido ba. Kuma na rantse da Allah sai ya bani hakuri akan wannan wulakancin.............. Turkashi.

*MAMAN ABDALLAH*

MU KWAN LAFIYA😘😘😘
[1/25, 8:02 AM] Bahajatu: πŸ’‘ *AUREN FARI* πŸ’‘

0⃣1⃣2⃣

Gabanta yayi wani mugun faduwa, ya kura mata ido ta bala'in canza mishi, ya fara taku zuwa inda take tsaye tana yar kyarma,
Ta fara yin baya baya yana biyota har sai da ta kure ma bango, ya sa hannuwan sa duka ya dafa bangon yayi mata katanga tare da sunkuyo wa dai dai fuskarsa fuskarsa murtuk..... Ke baki iya gaisuwa ba? Ko kinfi karfin kiyi man sannu da zuwa?
Ta dago kai aiken ka nayi?
Me yasa kake da neman dalili?
Ta ingijeshi ai fa ka dawo,....ya fizgota da karfi ya buga bayanta a bango. Ai fa na dawo? Ni da gidana kike fadan aifa na dawo watan baki so na dawo ba ko?
Kwarai ban.....wata muguwar matsa yayi mata tayi shiru sai kawai ta fara kwalla...ya kura mata ido sannan ya saketa a hankali ya dan ja baya ta kwasa da gudu ya bita da kallo.
Kafin ta sauka kasa tayi saurin gyara fuskar ta, mamee na ganin ta ta ce yawwa je kikai man wadannan fridge, waccen ledar kuma ki juye mana a tray kizo da wuka,
Suna ci ya sauko janye da jaka....
Wai mamee keda yar nan taki baku da aiki sai ci?
Dariya tayi, barakallah da lafiya akeci ai,
Yayi murmushi Allah yarinyar nan ta koya miki ci duk gashi nan kunyi yan kumatu..... Kai bani son sa ido, Apple din ne ci? Uwani ma da ta tsani abinci kullum nan cikin mata fada nake,
Ta mike zata bar wurin duk ta hade rai, ya daka mata tsawa ke! Wallahi kika bar wurin nan bazan biyaki albashi ba wannan watan,
To azabau ka dawo zaka hana ta shan ruwa ,hada wallahi? Uwani zo ki zauna,
yasha mur kawai.
Ta bishi da harara ta zauna.
Yarinyar nan ta gama rainani mamee ita tafi karfin ta gaisheni ne?
Ko sannu da zuwa fa.
Kana mata wannan hayagagar zata gaisheka?
Ya kamata ki ringa nuna mata kuskurenta zata sha wahala tamm..
Ta kalleshi kai wane irin yaro ne mai taurin kan tsiya?
Shin nayi shiru, ya fada yana watsa hannu, ga tsarabar ki sauran na sama.
A a a uwani buda mu gani, mazga mazgan riguna ne irin wadanda mamin ke sawa da mayafai .
Ta kalleshi banga abinda zaiyi wa uwani anan ba,
Ai daman naki ne, ya mike kawai yayi sama abinsa,
Ta kalleta ke bishi kice yaban sauran wata kila acan ciki kya samu,
Gabanta ya fadi, in dai don ni wallahi na yafe mama haba.....ni ban yafe ba, ko dan turare ai kya samu gasu mansura can kowa da ledar sa danaji babu taki a ciki nayi tunanin tare zai hado man.
Jeki maza ki karbo ta fada tare da shigewa ciki.
Tayi tsayeeee!!! Allah gani gareka, me kuma zan tarar?
Kamar wacce kwai ya fashewa take tafiya, zan bi duk wata dokar sa in shaa Allah.
Sai da ta hadiye wani tsinkakken miyau tare da sakin ajiyar zuciya sannan ta kwankwasa,
*come in*... Ya ce daga ciki,
Ta murda a hankali *Assalamu alaikum,*.....
Allah kasa amsa sallamar yayi *he wasn't expect her now* ya tashi zumbur dama ya dan kishin gida ne,
Ta dan sati kallon sa, kwanciya dai kwanciya mtseww kamar mace, amma a fili sai ta ce,
Hajiya ce ta aiko wai ka bata sauran kayan. Ya mayar da kai kawai ya runtse ido, yafi mintuna biyu, ta dai yi tsaye tana wasa da hannunta cikin hijab kanta kasa,
Ya dago ga su can a Leda.... Ba bata lokaci ta dauka tayi hanyar fita........ Tsaya! Yace,
Gabanta ya fadi tayi chak tare da runtse ido, *to wace masifar ce kuma?*
Ta kasa juyowa,
Ki miko mun jaka gata can...lokacin ta juyo da sauri, tayi hanyar inda yake nunawa,
Ta ajiye mishi kawai zata juya, *idan kina so ki dauka idan kuma bakya so kibarta nan*......sai kawai ta juya abinta ya daka mata tsawa cikinta ya murda ya dirko gabanta *bakiji me na fada ba?*
Ta kalleshi a wulakance ni kuwa na jika, ka ce idan ina so in dauka idan kuma bana so in barsu nan, haka ne? Ta bukata tana hararar sa sama da kasa tayi kicin kicin da rai, shine kaga na barsu din *domin bani bukata*......ya yi mata wata irin chafka har zaiyi magana kuma sai ya fasa ya bankada ta tayi baya baya taga taga zata fadi.
Ko kallon sa batayi ba tayi fice warta,
Dan rainin wayo wannan uwar jakar zaice in dauka to duk meye aciki watan in dauka ya gana man wata azabar, kai *madaki ya shiga uku da masifa* INA dalili.
Ledar magungunan mamee din ne da take sha na hawan jini tare da sauran maganin da take shafawa a kafafu.
Mtseww ta buga tsaki, kyaleshi uwani ai zan tafi umara nima tsaraba sai kin ture.
Ta yi yar dariya kwarai kuwa mama.
Wai tana nufin zanyi asara ne? Tabb ya zabura sai wayarsa tayi kara.
*Yeah Ku shigo ina sama* ya kashe
Abokansa ne wadanda ke kula da wasu kamfanonin sa zasuyi meeting.
Ya kira mamee, a kawo mana abincin mutum goma .
Yayi ta zuba ido yaga umaimah amma bata ciki, abinci ma baici ba don takaici, da la'asar ya sauko, tana ta faman gyara wasu duwatsu kaman na sarka,
Ya kura mata ido yana kallo, babu abinda yake kwantar masa da hankali yanzu irin kallon ta,
Ta dago kai kawai taga ita yake kallo ya sakar mata murmushi ta balla mishi harara kawai taci gaba da aikin ta.
Kai ni kike harara?
Yarinyar nan kin rainani ko?
Tayi mishi banza
Kije ki dauko jakar nan ko kuma wannan watan baki da albashi......ta dago zatayi magana yace wallahi zan hanaki kudinki kin San zan iya ko?
Ta mike ta shiga ciki, sallama tayo wa mamee kawai ta fito tayi hanyar waje,
Ya yunkuro ya kamota da karfi *me yasa kin fiye taurin kai?* ta lumshe ido tare da dafe kanta tana magagi kamar me shirin somewa, ya kara matsarta ya daga murya, kina ganin zaki iya ja dani........luuu ta tafi ya tareta a kirjinsa tare da zaro ido *UMAIMAH*...Ya firgice ya rikice ya waiga ya waiga ba kowa, ya sungumeta yayi bisa kujera ya kwantar yayi ciki da gudu ya dauko ruwa..... Ta bude ido a hankali koda taga ya shige sai ta mike tare da kwasawa da gudu.
Ya fito da kofin ruwa a rude.....kawai yaga wayam. Ya kwala kira umaimah...garam yaji anja kofa. Nan da nan ya fahimci me tayi ya yi wurgi da kofin da ruwa ji kakeyi ratsatsatsa..............

*Maman Abdallah*

Good morning to you all😘😘
[1/25, 8:02 AM] Bahajatu: πŸ’‘ *AUREN FARI* πŸ’‘

0⃣1⃣4⃣
*A rubutu na idan kuka ga MZ to ina nufin MOTHER a hausan ce ina cewa MOZA*
*Ba kowa ke da sunan ba sai Babbar masoyiyata SALAMATU DAHIRU wasu na kiranta SALAME DAHIRU kamar yanda kuke son wannan labarin to tabbatas ita ce jagoran siya mun data ba tare da tayi shawara da kowa ba don in muku rubutun AUREN FARI ku nishadantu ku kuma ilimantar. Zata sami addu'a daga gareku? To ina bara domin nima na ce ALLAH YA KARA DAUKAKA SANA'AR TA YA SHIRYA MATA ZURI'A YA RABATA DA IYAYE DA DUNIYA LAFIYA SANNAN YA KARA FAHIMTA ITA DA MAI GIDA AMIN.* KE MI KIKA CE???😊

....Yayi tagumi, anya ba nine ke rikita yarinyar nan ba? Ya dunga tariyo yanayin da ta shiga ganin sa a galabaice.
Mtseww, talaka ba abinda bazaiyi ba idan yana son abinka.
Washe gari tana zuwa tabi ta baya, ko mamee bata ga shigowarta ba, taci gaba da aikinta, ya gama zamansa falo har kusan sha daya baiga tazo ba dole ya hakura ya tafi office, umaimah ta gama lakantar gidan duk inda tasan CCTV zata hasko ta sai ta daina zama wurin,
Tana daki zaune ta fiddo mamee kaf tana kara gyarawa mameen ta shigo,
Au kina nan wai?
Ke bakya gajiya da shirya kaya a durowa? Ga gidan kawu can ana cigiyar ki zaki taya su shirye shirye baffa ke birthday jibi.
Ta yi zumbur ashe zamu sha shagali bari in hanzarta ai ina son bazide din nan saboda kek din nan mai yar madara madara.
Mamee ta kwashe da dariya, ai nan kika fi auki in da kwadayi to karki yamutsan kaya wurin sauri.
Koda ta gama tabi ta baya tayi can.
Tana zuwa ta tarar ana ta hura balloons ita ma ta hau yi.
Aunty kune ke hadawa da kanku? Ta tambaya
Wannan karon daine zamu hada saboda a saman benen *madaki* zayayi kin San baffa da iyaye gashi na gaban goshi ne baya laifi. To sanin ka'ida irin ta madaki gara muyi da kanmu kar ayi mishi ba dai dai ba.
Uhumm, kawai ta ce jikin ta yayi sanyi lallai bata ciki.
A kulla wannan a kwance wancen haka sukayi tayi sai shidda ta tafi gida. Ko sallama sai dai ta waya tayi wa mamee.
Tun biyar ya dawo yana falon mamee a zaune ya latsa wannan tasha ya maida wannan, daya ji motsi sai yayi firgigi, wasa wasa har akayi magrib ya kira cikin yan aikin ke ina uwani? Ta kame hannu tana yar kyarma, ta tafi gida.......sai kawai ya mike yayi sama,
Washe gari ma haka tana gaisawa da mamee ta ce ta tafi gidan su kawu aikin birthday. A dawo lafiya kai uwani akwai son shagali ta bita da dariya.
Ya fito yana yan dube dube bai ganta ba, kawai ya nufi dakin mamee tana bi ta baya yana shigowa, ya fara dube dube ta kalleshi me kake nema? Ya kara kallon dakin ba komi ya fice,
Aiki ya rikeshi office shidda ya iso gida yana ta hanzari yana shiga ya tarar mamee da baki a falon sama sama ya gaishesu yayi cikin dakin mamee yana zuwa wayam! Ya fito ya leka kitchen ke ina uwani? Ta tafi........mtseww ya buga tsaki ya juya.
Wai meke tsakanin Alhaji da uwani? Mansura ta bukata, laraba ta ce ya tsaneta ne ita kuma ta nace yarinyar ta fiye shisshigi ke gaki 'yar aiki amma kina acting kamar diyar gida?
Hajiya ce take lalata yarinyar.
Bilkisu ta dago kai amma bata da raini duk tana bamu girma..... Tabb billahil azim ta raina oga bata tsoron sa ko Kadan....duk suka zaro ido bakin ki aka ji kowa ya watse.
Umaimah kuwa tana can ana shagalin toye toye da soye soye abin na matukar bata mamaki birthday kamar shagalin biki?
Kai masu kudi na yarda suke so. Ta zage ta dunga aiki tana kwasar ilimi duk abinda akayi gabanta to ba sai an maimaita ba, kowa yaba mata yakeyi yanda ta nuna rashin son jiki kuma komi akace tayi bata gardama ko bata fuska,
Sai karfe tara tabar gidan aka dibar mata naman kaji, snacks da lemuka ta tafi gida ko mamee tayi tunanin tun marece ta tafi. Wasu na can sashen mamee da saman madaki ana kulla balloons da kayan kwalliya Sam taki zuwa aikin ta manne wurin abinci duk don ta gujewa haduwa dashi.
Hankali madaki ya gama tashi ya sami mamee na lazimi bayan isha'i.
Yarinyar nan bata aikin ta yanda yakamata ko? Kwana biyu bana ganin ta...... To fitina'u kwana biyun nan ma tafi aiki bana son neman rigima, yaushe zaka basu kudin su ne?
Gobe ya fada da Sauri kowa yaje sama da safe ya karbo don zan danyi aiki bazan sauko ba.
Allah ya kaimu, amma kasan gobe ne shagalin baffa nasan kuma ire iren wadannan shiriritun kamar yanda kake fada gidan kake bari tunda wuri gashi a saman zasuyi komai eh zan fita zuwa goma ina nufin suje kafin lokacin.
Oho to na gane,
Ya fito yana cewa ai shegen son kudi gareta gobe na ganta ba shiri.
Zata manta duk wani laifi da akayi mata akan kudi.
Murna tsalle gida ya rikice ana lashe lashe da tande tande.
Goggo hansatu ta lumba wata tsoka ta cika mata baki, to gobe kwana zakiyi kenan saboda shagalin ko?
Ta dago kai da sauri kwana goggo? Eh mana kya taho ba a gama ba?
Tayi murmushin takaici. A a dawo wa gida zanyi komin dare.
Suka ci gaba da ci.
Tunda safe mamee ta tafi Kaduna an aiko ciwon babbar yayar su ya tashi na ciwon sugar. Ta kira umaimah ta shaida mata don haka koda tazo bata iske ta ba,
Kawai sai ta wuce sashen su kawu, babu Wanda yaga zuwanta. Ko wace ta karbo kudin ta amma bai ganta ba, ta karshen na zuwa yace ke ina uwani?
Wallahi ban ganta ba amma bari in nemo ta, ta karba ta fita da hanzari, ya dauki waya, hello mamee ya mai jikin? Da yake a jirgi ta tafi,
Ta ce gata da sauki amma ina tunanin sai na kai gobe gaskiya, asshha zan shigo anjima a gaishe ta. Yarinyar nan taki zuwa ta karbi kudin fa ya kamata ki kirata a waya ko ki turon number ta. Tayi murmushi uwani sarkin hidima kiri kiri taki zama tunda taji za ayi party.
Bari in kirata,
Eh kirata amma still mamee nima turo man number ta please. Ta ce to ta kashe wayar.
Ashe kina nan? Kizo inji Alhaji ki karbi kudin ki..... Na ji. Ta fada a takaice. Zata kara magana wayar umaimar tayi kara,
Hello mama kun isa lafiya ya mai jikin?
Da sauki uwani, kije ki karbo kudin ki zai fita ke kadai yake jira. To mamah ta fada kamar da gaske.
Tana kashewa wayar ta kuma yin kara, ta dauka mamah yanzu fa zanje......... Sai kin gama bata man loka...... Tayi saurin dauke wayar daga kunnen ta, tana ganin number tayi saurin lace wayar sannan ta kashe ta gaba daya.
Kutumeee..... Dai dai shigowar nafisa yallabai gata nan zuwa.
Umaimah ta bata fuska, Wallahi na yafe kudin, ai shi da ganina sai dai wani tsautsayin wallahi.
Ke da wa kike sabbatu? Aunty ta gani gabanta tana dariya.
Ta danyi murmushi kawai.
Uwani tunda mun gama hada jakun kunan da take away kije gida ki shiryo ki dawo da ke da nafisa, mansura da kuma bilkisu ku ba baki abinci da rabon kayan kuma.
Ta ce to, ta tafi amma azuciyarta bata da niyyar dawowa.sai da taje gida tukun ta kunna waya ya kirata yafi sau goma bata daga ba.
Ya sauko a harzuke ya gamu da bilkisu ke ina uwani?
Tana sashen kawu babba bari na kira..... Ban aikeki ba ya wuce fuuu.....
Kamar daga sama Aunty ta Ganshi bai taba shigowa sashen ba ko sau daya, ko haihuwa tayi sai dai akai mishi yaron .
Ina *uwani*? Abinda ya ce kenan da shigar sa.
Yanzu kuwa ta tafi gida..... *what*???? Ya juya kamar mahaukaci, wai laifi nayi sosai ne?
Lallai na gane fushi takeyi yarinyar nan.
Mtsewww yeah I know ban kyauta ba but at least won't she give me a little bit chance? I regret and ready to show my appreciation..... Ohh my God ya dafe kai.
Tana zaune daki tana gyara jakar kayanta wurin karfe biyar mamee tayi kiranta,
Ta dauka tana fargabar ko ya fada mata bata karbi kudin ba.
Hello, mamee ina wuni,
Lafiya lau uwani kada ki manta ki ringa barmun daki a kulle kinga gidan yau Allah kadai yasan wa zasu shigo gashi bani gari.......gabanta ya fadi ta ce toh.
Tana ajiye wayar ta mike na shiga uku, tabar gidan a gaje.
Tana rufo dakin ta fito kenan tayi kucibis da baffa, yawwa uwani ungo muje sama, ya tasa keyar ta.
Kowa gidan yana can an kawata wurin swimming pool ana ta shagali, nan da nan umaimah ta sake aka fara hada

Please Login or Register in order to submit comment