Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kenan, ka dubi irin abinda kake sha kamar baka san illansaba


Haba Daddy dawanne danji ne da irin kashemun rayuwa da kuke qoqarinyi ko kuma da wadannann sarautan naka


Wanne irin kashe maka rayuwa kuma?
Ah waccar qazamiyan yarinyan da na kusa haifata ma dakuke wani cewa wai ita zan aura, to wlh ni dana auri wannan yarinyan gara na mutu ba aure dan ni mata basa gabana


Daddy yace kashe rayuwa ya fice wanda kake ma kanka, ka sha wannan kasha wancan kamar ba Dr ba, ko so kake kace bakasan illansaba, toh wlh kashiga hankalinsa da wannan shaye2n naka, inba haka ba ranka zai mummunan baci kodan kaga na zura maka idanu ina kallonka shiyasa kullum kake qoqarin zubarmun da mutunci


Daddy nifa banfa nemi dogon maganaba kawai kasan abinyi, inkuma ka matsa wlh sai kunji dama baku somaba dan bata yanda zan fara rayuwa da wannan jsririyar


To idan naqifa sai yaya ko zagina zakayi tinda ka girma


No, nifa gaskiyace kawai fa I can't marry that villager atow


Toh tinda ka girma har ka iya sa insa dani zangani nida kai waya haifi wani, ka kuma bud'e kunnenka da kyau kaji wlh kaji na rantse aure babu fashi, saanka 1 fauziyyah har yanzu yarinyace da acikin satinnan zaa daura auren inyaso idan aka kawo ta ka ratayeta, kuma ko Bayan raina banyafe makaba matuqar baka auri fauziyyah ba shashasha yana fad'in haka ya juya ya fita ransa a b'ace
Daddy yana fita papa ya kira momcy awaya, aiko tana dagawa ya fashe da kuka


Momcy hankali tashe tace papa lfy mene yafaru? Da kyar yayi shiru yafada mata yadda sukayi da Daddy


Rarrashinsa tayi tace kayi Haquri zuwa kudawo ba gobe daku dawoba, yace eh


Toh kaje kabawa Daddy Haquri inyaso idan kundawo dansan abinyi tunda baka so aiba dole


Yawwa momcy pls help me out, kada kadamu son ammafa kaje kabasa Haquri


Gaskiya nifa momcy bawani Haquri dazan basa kawai rabu dashi, ganin zai tsiyar mata rikici yasa tace shikenan sai kundawo din




Washegarin dawowarsu momcy tasamu Daddy akan maganar fauziyyah, nan yamata ba Daddy yace kuma kada tasake sa bakinta aciki tinda goyon bayan danta take


******
Watanni papa uku da dawowa Daddy yace toh papa ya shirya next week zai fara fita office


Ransa dai bai soba haka ya amince


Watan papa biyu da fara fita aiki amma har ansanshi acikin asibitin dan kwarewansa akan aikisa dik wata lalura indai yashafi harkan qashi, da ikon Allah bata gagararsa


Hakan yasa kowa Dr Alamin, sai dai miskilanci yasa bai kula kowa, cleaners kuwa basa barin ya kamasu da laifi dan yanzun yaci mutuncin mutum baqaramin aikinsa bane


Ahakanma yanzun sai ya gadama yake fita aikin, acewarsa baison stress, Daddy dai ya zuba masa idanu tsakaninsu sai adduar shiriya






Pls ku managy da wannan, battery na yayi low




✍🏻Faty Mmn Faty
[10:39PM, 8/6/2017] β€ͺ+234 703 448 8635‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾






Budurwar Qauye πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€


Written by Faty Mmn Faty


July, 2017






0⃣5⃣
Haka rayuwa take tafiya, inda kullum alamarin papa qarauwa yake, tun su momcy suna damuwa har sun dawo yimasa addu'a kawai


Afannin aikinsa da kyar Daddy ya shawo kansa ya amince yana fita kullum, gashi teaching hospital ma sun nemeshi yazo ya masu aiki


Yacema Daddy shifa barai iyaba, aiki dai masa yawa, Daddy yace masa ai hakan ba laifi bane inkuma bazaiyiba shiya sani


Ganin ran Daddy ya baci yasa ya amince
Kafin wani lokaci, kamar wasa sunan Dr Alamin yabazu


Sannan hanyar shigan kudi ya qaru masa, sai iskancinsa ya fi nada


Wani gida flat mai kyau sosai yasaya a sokoto road, wanda ko su Daddy basu san yasayaba


inya taso daga wajen aiki can yake wucewa ya sha shagalinsa


Amma dik abinda zaiyi da mace sai dai ya romancing d'inta ya barta dan baqaramun kyankyami yake da ba


Sau da dama TJ kan ce masa anya kuwa Ameen kana da lfy


Yace me kagani, haba abokina dik irin lokacin da kake b'atawa da mace amma baka iya....


Dariya kawai yayi yace umm kawai banson qazanta da jaqwali shiyasa tinda mutum baisan suwane suka.......


TJ ya jinjina ma abokinsa yace tab wlh nikam sai naci kudina tsaf dana bari


Papa yace kadafa watarana kaci wahala


TJ yace ina nimahaukacine da zanyi ba condom


Papa yace kabi dai ahankali


Yanzu gidama bai komawa sai 12 wani tym har 1pm, idan yadawo da wuri kuma to irin 11pm ne


Yanzun hankalinsa akwance yake ganin lokaci yana tafiya bai kuma jin Daddy ya sake maganar waccar *BUDURWAR QAUYE* ba


Inda shikuma har yau baiga macen data burgesa amatsayin matar aureba






************
*Bayan wasu Shekaru*


Yan makarantar secondary ne sun taso amakaranta misalin 12:30pm


Wata kyakykyawar yarinya, yar matashiyar budurwa wadda shekarunta bazasu fice 15 ba


Tana da dogon fiska mai dauke da dara2n idanuwa, dogon hanci had'i da d'an mitsi2n bakinta, Allah ya mata yalwar gashin gira


Fara ce tass wadda idan kaganta zaka fahimci ba algus acikin farin ta


Fauziyyah Usman, daga bayanta wata ta kwala mata kira


Juyawa tayi ba tare da ta amsa ba, ganin mai kiranta yasa ta gyara tsayuwarta dan jiran isowarta


Tana isowa tace, ashe kinfito inatakan dubaki bangankiba sai Aisha salman tacemun kintafi


Fauziyyah tace wlh saurinake yau suna zamuje da mama


Kai Fauziyyah ba kya girma bikin suna kuma


Tsaki tayi gami d juya manyan idanuwanta amasifance tace eh d'in, ni kina b'atamun lokaci mene yasa kika tsaidani


Sanin halin Fauziyyah na fad'a yasa tace haba qawata ba nufina kiyi fushiba amma Allah ya baki haquri, dama note d'in Basic science nakeso ki aramun


Tabd'ijam, kinajifa abinda uncle bala ya fad'a d'azu, kada kowa yayi wasa da note d'insa saura mana term 1 daga wannan mu fara JSSCE
Kuma dik sai antambayemu abinda aka mana tin daga first term


Marairaice murya tayi haba qawata gobefa zan dawo maki dashi


Toh indai kinyi alqawari shikenan, barin nabaki


Yawwa nagode


Bud'e jakarta tayi ta lalimo mata, gashi ta miqa mata saura kuma kibari qannenki su shafamin miya


Uwar masifa ta fad'a aranta, amma afili sai tace haba dai yadda kika bani haka zandawo maki da kayanki


Sallama sukayi kowa ya wuce, tanashan kwana taji horn d'in mota abayanta


Juyawa tayi ganin wadda ke cikin motar yasa ta murmushi da yaqawata fiskanta


Parking yayi ya fito, dogon saurayi choculate colour, kyakykyawa dashi


Da murmushi ya qaraso wajenta, shine kika tafi abinki ko beauty na, abinda ya fad'a kenan


Sunkuyar da kanta qasa tayi, kayi haquri uncle yasir sauri nake kada mama ta tafi ta barni


Yar mama kenan kinfa girma yanzun kam, kibar mama take zuwa unguwa ita kad'anta


Shagwab'e fiska tayi, bikin sunafa damuje a can gongola


Toh shikenan kada na tsaidaki amma amshi wannan nagaji da rashin jin muryarki ko yaushe


Duban tsaleliyar wayar daya miqo mata tayi, shiru tayi bata amsa ba


Amshi mana beauty yace da ita


Gaskiya ina tsoron mama tamun fad'a


Haba my fauzee pls ki amsa kinji inyaso kada kibari mama ta gani


Amsa tayi tace nagode


Aa nine da godia


Ahuta gajiya ko baby na saina kiraki


Toh amsa sannan ta wuce


Juyawa yayi ya koma mota, wanda yasan koda yamata tayin zai maida ta gida bayadda datayiba


*Wanene Yasir?*
Yasir Mukhtar shine ainahin sunansa, asalinsa haifaffen garin Gombe ne, shine d'an fari a gidansu, iyayensa suna zaune a unguwar Buba Shango, kuma balaifi suna da hali


Bautar qasa ya kaishi dambam, inda aka turashi makarantar su Fauziyyah, shine malaminsu na Mathematics


Tin lokacin da yaga Fauziyyah yaji yana tsananin sonta, kuma da aure yake sonta


Da kyar ya shawo kan Fauziyyah har takarbi tayin soyauyarsa, inda yanzu suke tsananin son junansu


Kuma Fauziyyah ta amince masa da zarar sungama JSSCE shima dai dai da gama service d'insa zai turo magabatansa maganar aure


Inyaso taci gaba agidansa, dan jiyake bazai iya haqura har ta qare secondary ba, wannan kenan




✍🏻Faty Mmn Faty
[10:39PM, 8/6/2017] β€ͺ+234 703 448 8635‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾






Budurwar Qauye πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€


Written by Faty Mmn Faty


July, 2017






0⃣6⃣
Tana shigowa gida, sallama tayi tana mai cire hijabin wuyanta


Daga cikin d'aki mama ta amsa mata


Wurgar da hijab da d'ankwalinta tayi atsakar d'aki, jakarma firo tayi da ita sannan tayi super kan gado tana cewa wash Allah na


Mama ta miqe tana tsintar kayan data watsar tana fad'a


Aifa kindawo kenan, Komai haka zaki watsar mun kamar haka kikaga nakeyi


Haba mama zafifa na d'ebo wlh nagaji


Bawani nan dama haka kike kullum, aiko a ruwan sama kika dawo haka zaki hejjefar da kayanki


To mama nabari shikenan


Aikam daya fi maki, inkuma haka zaki keyi ad'akin mijinki to kinada aiki ja


Wuwwurga qafafu tafara haba mama nikuma nawa ma nake, kullum kice gidan mijina


Sai kiyi kuma mama tace tana fita waje


Yanda tabarta haka tasameta akwance, toh kitashi kici abinci gashinnan, kishirya mutafi inkuma bazaki ba toh kada kibata mun lokaci


Tashi tayi zaune ta bude plate din, lafiyayyar shinkafa da miya da maccaroni, yaji naman rago


Nan tafara ci hankali kwance dan mama badai iya girki ba


Nan da nan taci ta shirya suka tafi gidan suna


Gafda magriba suka dawo, basu jimaba Abba yadawo


Bayan sallan ishai, suka hadu sukaci abincin dare atare kamar yadda suka saba ko yaushe


Fauziyyah ta miqe tamasu saida safe, ta wuce d'akinta, sai data kulle qofarta tayi adduan kwanciya sannan ta jawo wayar da yasir ya bata


Nan ta kunna aiko ba tafi 2mins sai call ya shigo


Assalamu alaikum ta fada lokacin data daga wayar


Lumshe idanunsa yayi, yace waalaikumussalam beauty na


Dftn ka yini lfy


Lfy lau my baby n u


Tace umm nima haka lfy lau


That's good, dayaushe kuka dawo?


Umm tin kafin sallan magriba


Ayyah ina ta trying wayarki bai shigaba sai yanzun


Umm yanzun na kunna dftn habiby baiyi fushi ba


Haba dai waneni, nifa yanzun burina bai fice kuyi JSSCE nanba, su dad suzo kodan sami natsuwa


Kai uncle yasir yan....
Katseta yayi nifa banson uncle dinnan, gaskiya


Dariya tayi toh habiby naji barin sakeba


Yawwa ko kefa, nan suka sha hiransu sosai na masoya daga bisani sukayi sallama akan sai sun hadu gobe a school


Rayuwa tana tafiya ma Fauziyyah da yasir yadda suke so, ana haka suka fara exams na second term, kuma idan anyi hutu yasir zai tafi gombe shima


Ranan da suka gama exams, aranan yasir ya tafi amma da kyar suka rabu da Fauziyyah, tasha kuka kam shima ba qaramun daure zuciyarsa yayi ba


Bayan tafiyan yasir Fauziyyah tayi kewarsa shima haka amma saukin suna waya


Ana gobe hutunsu zai qare yasir ya dawo, Allah Allah yake gari ya waye yaga abin qaunarsa


Haka Fauziyyah itama dokin wayewar gari take dan yanzun ta tabbatar yasir yazama wani bangare na rayuwarta


Wanda batajin akwai abinda zai iya rabasu (toh fa lalle akwai chakwakiya inji Mmn Faty)






*********
Daddy ne zaune da Abba wanda ya kawo masa ziyara


Suna harabar gidan Daddy sai hira suke kasancewar saturday ne


Papa ne ya fito cikin shiga ta alfarma kamar kada ya yaushe, rigace navy blue da ash troser, yasha wasu bufolino shoes, gashin kansa sai kyalli yake alamun yasha gyara kuma ankashe kudi


Qarasowa yayi wajensu, da faraa yagaida Abba, Abba ya amsa cikin sakin fiska




Miqewa yayi Daddy barinje wajen TJ


Toh saika dawo yace dashi, wajen motarsa ya nufa wadda tasha wanki sai kyalli take


Mai gadi na ganin haka dasauri ya bude qofa gudun yin laifi


Sai daya fice sannan Abba ya dubi Daddy yace Alhaji inaga lokaci yayi Da zamuyi Wa yaranna aure, badan mamana ba aa sabida Alamin, bazaiyiwu muna kallonsa har fice munzalin aure ba gaskiya sabida wani dalili nadaban


Daddy yayi shiru yana sauraronsa, sai daya qare sannan Daddy yaja dogon numfashi yace


Gaskiyane Alhaji amma tin bayauba nakeson muyi maganar nan sai dai bansan ta inda zan somo makaba, nayi shiru ne danaga Fauziyyah ma yanzun take kan karatunta


Abba yace ai karatu bazai hana aureba, tinda yanzun nan da watanni uku masu zuwa zasu zana jarabarsu ta JSSCE to ya isa haka agidana, sai kuma ta ci gaba agidan mijinta, kuma ko Alamin yace bai aminta da ci gaba ba to balaifi matarsace, baranma shima ai yasan dadin karatun


Daddy cikin damuwa yace aiko da idan hakan ya faru danafi kowa farin ciki, sai dai hakan bazaiyiwu ba




Abba yace bazai yiwuba kuma, yana kallon Daddy dan yamasa qarin bayani




Daddy yace kwarai sabida Fauziyyah bata dace da miji irin papa ba, aurensu bawani abu sai tauye mata rayuwa da zaiyi, tana yarinya qarama


Cikin rashin fahimta Abba yace kafahimtar dani Alhaji




Daddy yace Alamin yacanza daga Alamin d'in daka sani, Alamin yadauko wasu halaye nadaban yamaidasu abokan rayuwarsa nan ya zayyanema Abba halin papa tas sannan yace kaga fitan da yayi yanzun toh shida yadawo sai 12am ko 1am


Shiyasa nace maka sam Fauziyyah bata dace dashiba, sai yaje can ya nemo abokiyar shashancinsa ya aura


Abba kuwa zufa kawai ke tsatstsafo masa ta ko ina


Nisawa yayi sannan yace tabbas wannan alamarine babba kuma abin dubawa.....






✍🏻Faty Mmn Faty
[10:39PM, 8/6/2017] β€ͺ+234 703 448 8635‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾




Budurwar Qauye πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€


Written by Faty Mmn Faty


July, 2017






0⃣7⃣
Amma wannan bazai hana komaiba, Fauziyyah matar Alamin ce


Muyi fatan Allah ubangiji yasa sanadin auren yazama shiriyarsa kuma muci gaba da addua Allahu ya shiryeshi


Wani dadi Daddy yaji, rungume amininsa yayi yace nagode nagode Allah ya bar zumunci


Abba yace da Fauziyyah da Alamin dik 1 sike awajena, kamar yadda barin kyamaci Fauziyyah ba haka barin kyamaci Alamin ba


Daddy yace babu abinda zan cemaka kagama mun Komai arayuwa


Abba yace bakomai inaga kawai nan da watanni 4 masu zuwa sai ayi bikin ko kuwa


Daddy yace dik yadda ka tsara hakan zaayi, Allah ya kaimu ya nuna mana


Abba ya amsa da amin, Inyaso sai yazo su fahimci juna kafin lokacin biki


Daddy yace insha Allah next week zaizo Allah yasa Fauziyyah ta amince
Abba yace ai Fauziyyah bazataqi dan uwantaba sabida dan bawani saurayima take dashiba dan nahana babu wani wanda ke zuwa wajenta fatanmu Allah ya daidaita su


Washegari da safe Abba ya koma


Bayan tafiyar Abba Daddy yasamu momcy yamata bayanin yadda sukayi da Abba




Momcy taji farin ciki sosai, nan taji wani sabon son Fauziyyah har cikin zuciyarta






*********
Abba da mama suna zaune Bayan sun tattauna maganar biki, sai dai sam bai fada mata halayen papa ba




Mama tayi naam da hukuncin da suka yanke


Abba yace ta kira masa Fauziyyah


Tare suka shigo dakin Abba, durqusawa tayi gani Abba


Zauna da kyau mamana, gyara zamanta tayi


Fatima Abba ya kira sunanta


Dam zuciyarta ya buga dan Abba bai taba kiran sunanta haka direct ba sai yau


Naam ta amsa asanyaye


Abinda yasa na kiraki munyanke shawarin hada ki aure da dan uwanki Alamin dan gidan baffanki na bauchi


Dasauri ta dago kanta, dan jin maganar tayi kamar amafarki


Sannan ba shawarinki nake nemaba umarni nabaki, ina fata zaki amince masa dan kitayani cika alqawarin dana dauka shekara da shekaru




Kuma ina fatan yau kin fahimci dalilin dayasa, na haneki tsayawa da samari sabida gudun fadawa soyayyar wani bayan akwai mijin da muka tanada maki


Daga kanta kawai ta iyayi dan intace zatayi magana to tabbas kukane zai kubce mata




Abba yace Allah ya maki albarka, tashi kije


Tana fitowa da gudu ta nufi dakin ta, tana shiga ta fashe da wani irin kuka mai cin zuciya, dan bata taba tunanin haka zai kasance ba arayuwarta, fatanta Allahu yasa mafarki take kozata farka taga hakan bai faruba






*********
Ranan friday da daddare, Daddy da momcy da papa suna zaune afalon Daddy


Papa yace Daddy gani


Daddy ya gyara zama da kyau sannan ya dubi papa fiska ba walwala


Alamin inason ka bude kunnenka da kyau, kuma kasaurari abinda zan fada maka umarni ne ba shawaraba dafatan kanajina


Papa yayi shiru yace eh inaji




Daddy yace good, so abinda nake so dakai gobe idan Allah ya kaimu kaje dambam gidan baffanku Usman kasami yarsa Fauziyyah ku daidaita dan aurenku nan da watanni 4 masu zuwane


Dftn kufahimci magana ta kuma banson musu ko excuse dan aure babu fashi


Papa dake zaune sai daya miqe dan jin maganar yayi kamar saukan guduma atsakar kansa


Idanunsa nan take suka kada sukayi jajur, no no Daddy shine abinda yake fada yana girgiza kansa




Daddy yace ai nagama magana kuma zamu bata dakai matuqar ka tsallake maganata that's all


Juyawa yayi yana kallon momcy ko zata sa baki


Amma sai yaji tace ga wannan ka kaima Fauziyyah kuma koda wasa kada kace nina bata, kabata amatsayin tsarabarka


Karba yayi ya fice kawai


Dakinsa ya wuce kansa kawai ya dafe dan yarasa mafita




Washegari ba wanda yayi ma sallama ya wuce abinsa dan dik haushinsu yakeji




Bayan azahar ya isa, sai daya huta kafin ya sake wanka, shiryawa yayi cikin farar shirt mai layin baqi da black jins


Baqaqen bufalinos ya saka aqafarsa kallo daya zaka masa kagane akwai naira a hannunsa


Wayoyinsa ya dauka ya fice, danwareriyar motarsa ya shiga itama baqa sannan ya nufi gidan Abba


Fauziyyah ta fito daga wanka kenan tana kwalliya dan zataje gidansu Amina Ibrahim qawarta


Sai taji mama tana gaisawa da mutum, daga yanayin maganar ta fahimci baqon da Abba taji yace zaizone ya iso


Dogon tsaki taja yanzun dik saurina ya tashi a banza kenan, naso na fice kafin yazo ta fada afili


Mama ce ta shigo tace Fauziyyah ga Alamin yazo yana waje sai ki bude masa falon abbanki


Naji shine abinda tace


Takai 15mins kafin ta fito nanma sai da mama ta sake mata magana




Papa yagama quluwa kamarshi ace wata banza har ta ajiyeshi, duba time yayi nan da 5mins idan bata fito ba to zaiyi tafiyarsa




Sai gata ta fito, fiskanta fayau ba kwalliya tana sanye da atampa riga da zani, da farar hijab


Wani wawan tsuka yaja Dan gaba daya haushi ta bashi, ji qirjinta kamar na sauro to ma yaci me da ita


Ganin yayi shiru yasa tazargi kallonta yake ta cikin glass din idonsa


Kallo 1 tamasa ta kauda kanta, ina yini tace dashi


Qalau yar Qauye, Zaro ido tayi


Yace meye kike Zaro ido qaryane, dubeki wai Budurwar Qauye ko


Toh kisani nafarko banson raini dan nasan halinki ne


Sannan wannan auren hadin iyayenmune kada kiyi tinanin inasonki kozan soki, so kitsaya amatsayinki




Kada nakuma zuwa ki bata mun lokaci


Yana fadin haka ya bude mota, wani bag mai kyau ya miqo mata gashi inji momcy


Bata riqe ba yasake, jakar tafadi aqasa


Ko kulawa baiba ya wuce ya shiga mota yayi tafiyarsa


Fauziyyah kuwa rasa ma mai zatayi tayi, lalle wannan inna bashshi abinda zai mun kare bazaiciba


Amma zan gwada masa nafishi qin wannan auren


Sunkuyawa tayi ta dauki jakar tayi cikin gida da tunani kala2 aranta........




*Toh ina jiran raayoyinku shin Fauziyyah da Alamin ta dace koda Yasir*


Idan naga comment dayawa to zaa qara sambadowa




✍🏻Faty Mmn Faty
[10:39PM, 8/6/2017] β€ͺ+234 703 448 8635‬: 🌾🌾🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾🌾




🌾🌾🌾






Budurwar Qauye πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€πŸ€·πŸΌβ€β™€


Written by Faty Mmn Faty


July, 2017






0⃣8⃣
Dakin mama ta wuce, dangwarar da jakan tayi zata juya


Mama tace badai har ya tafi ba?


Eh kawai tace


Mama tace to wannan jakar dakika ajemun nayi me da ita


Turo baki tayi nima banaso


Mama ta qare mata kallo tace ni lfynki kuwa? Ba kwalliya nasameki kikeyiba amma yanzu naga fiskanki haka ba ko kwalli sai farin ido kamar na tsohuwar ba amurkiya


Dad'a turo baki tayi kai mama to mene aciki kawai bana raayin fita da kwalliyarne


Toh ya maki kyau, sai ki daga jakar kiwucemun dagani


Nifa mama nace maki banaso kuma mafa ni baimunba gaskiya


Wane ne bai makinba?


Alamin d'in tafada kai tsaye


Eh lalle aifa dama kallonki nake nafahimci take2nki, toh nikam baruwana sai kibari idan Abbanki ya dawo kifada masa


Amma ina baki shawarin kada ma kisoma wannan tunanin dan bamai goya maki baya atow


Kuka tafashe dashi ta juya ta nufi dakinta




******
Washegari papa ya dawo bh, direct sokoto road ya wuce
Can suka had'e da TJ sai wajen 11pm yadawo gida


Washegari da safe cikin shirin fita office ya fito, afalo ya sami momcy da Daddy suna break fast


Fiska daure yace morning Daddy morning momcy


Morning my son Daddy yace dashi, momcy tace lfy kake wani had'e fiska


Sake bata fiska yayi haba momcy yanzun ammun adalci kenan, ahadani da wata tarkacen yarinya kawai


Momcy tace au maganar bata wuce bane dama to nidai baruwana amma kanatsu kama kanka fada, jayayya da iyaye ba abine mai kyau ba


Daddy yace ai tarkacekam kaine ba na biyunka, kuma wlh Fauziyyah itace ta rufa maka asiri


Da wad'annan munanan halayen naka data aureka ahaka


Kai da kanada kunya har dakace baka sonta ai kodan hallaccin da mahaifinta yamaka sai ka haqura ka koyawa zuciyarka sonta


Miqewa papa yayi yace shikenan ai tinda kun dage na amince zan aureta dan kunaso Badan ni nakeso ba


Yana fadin haka ya fice


Direct asibiti ya wuce, excuse ya dauka akan baijin dadi


Fitowa yayi ya shiga motarsa a 360 ya figeta sai office din TJ


Sai da yayi parking sannan ya kirashi awaya, ringing biyu ya picking, ya kana office ne ya tambayesa, ok to ganinan zuwa


Yana shiga ya sami waje y zauna




TJ yana ganin yanayin abokinsa yasan ba lfy, rufe file din gabansa yayi


Cikin kulawa yace yadai man ar u alright?


Ahankali ya zare glass din idanunsa, duban TJ yayi Da jajayen idanuwansa am not ya amsa masa


TJ yace mene ne yake faruwa haka man


Rai bace yace wai aure Daddy zasumin in d next 4 months


Hhhhh TJ ya fashe da wata dariya yace kai mutumina ashe zaka kafaso gari


Papa yasake quluwa yace dan ubanka Ina fada maka damuwana kanamun iskanci


TJ yace ah ai nasan Daddy bazasu maka zaben wasa ba, wlh indai akan wannan ne har kake bata ranka gara kasake musha biki kawai malam


Papa dayaji kamar yashaqo TJ yace wai kai baka ganewane tinda abin naka iskancine kaga tafiyata


Dasauri yace yi haquri mutumina wasa nakema toh ina jinka a ina yarinyar take


Papa yace kaidai bari wata *BUDURWAR QAUYE* kawai Daddy ya jonamun


Nan yabawa TJ labari


TJ yace haba su kuwa su Daddy mene yasa zasuyi haka amma wani hukunci kayanke


Na amince zan aureta tinda naga dagaske Daddy fushi yake but sai ta gwammace bata aureniba dan wlh babu abunda zanci da wannan yarinyar


TJ yace hakan dakayi yayi sabida kasan iyaye sai ahankali amma yakamata muje naganta ko


Kai haba bana da ranan komawa amma idan naga zanje sai muje tare


To godia nake ango Allah yasamu adanshimku


Papa yakai masa duka akafad'a yace kai dai baqaramun dan iska bane, sai anan yaji yasamu relief a ransa


Gida ya dawo yayi kwanciyarsa bai sake fita ba sai Washegari ya fice office




********
Fauziyyah kuwa kwana biyu tanawa mama bore kan itafa atafam bata son Alamin


Mama tace toh kinsan Allah idanma amakaranta ake zugaki zugar qawaye yaukam bari Abbanki yadawo insanar masa kuma daga yau kinqare makarantar


Sanin halin Abba sarai yasa taita roqon mama tayi haquri bazata sakeba


Amma azuciyarta har yanzun bata yarda akwai abinda zai hanata auren yasirba


Shiyasa tayima mama likimo kafin tasamu mafita, takuma gagara sanarma yasir halin da ake ciki dan batason hankalinsa ya tashi


*3 weeks later*
Awannan week din ranar saturday papa da TJ suka shirya suka taho dambam


Inda Daddy ya kira Abba yasanar masa zuwan papa


Girki mai kyau yasa mama suka shirya, bayan sallan laasar Fauziyyah da qawarta yar qanwar mama mai suna khairy suka fasa wanka suka shirya suna zaman jiran isowar su papa


Mama kuwa ganin Fauziyyah tasake har da kwalliya yasa taji dadi sosai


Fauziyyah kuma tayi hakane sabida akwai wata manufa aranta


4:30pm
Su papa suka iso, tinda yayi parking sai wani ciccin magani yake, fiskannan kamar an aiko masa da saqon mutuwa


TJ ya dubesa haba mutumina kasake fiskan mana, irin wannan bonewa haka


Yamutsa fiska yayi yace

Please Login or Register in order to submit comment