Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

aiba saika harbeta ba domin kuwa tuni naji numfashin ta yad'auke alamar ta mutu yace ok mutafi kawai cikin sauru suka shiga mota suka tafi.




*******


Koda su *Beena* suka dawo basu iske ammu ba sanin indata tafi yasa basu damu ba, saidai itakam *Beena* tarasa meyasa kirjinta yake bugawa sosai gawani irin fargaba datakeji,




Misalin karfe 4:20pm suka shirya suwa Islamiya bayan sun sallami Abbu sannan suka tafi, ko a islamiya *Beena* takasa samun natsuwa har tayiwa yara karatu kamar yanda tasaba saidai abokin koyarwar wanta ne yaimasu, domin gabadaya jitayi zazzabi yana neman rufeta,




suna cikin karatu sai tace don Allah malam saminu idan kanada kudi acikin wayarka kad'an aramun zankira "ammun mu, najiko tadawo ko kuma tana hanya yace Ammun tayi tafiya ne?...eh wlh, Allah sarki Allah yadawo da'ita lafiya amin to gashi karba tayi tare da fad'in yauwa nagode, koda tasa lambar ammu takira saita jita akashe tanata kira amsa daya ake bata hakan yasa taji wani matsananci fad'uwar gaba,



Cikin Dan firgici tace ah! kaji wayar wai akashe yace to ko babu chaji ne?...tace a ah akwai chaji to kila tana gurin da babu sabis ne, eh to kila nan dai tamika masa wayar shi tunda tayi takira baije ba.




Bayan antashi suna cikin tafiya *Bass* yace kila yanzu "ammu tadawo, *Beena* tace eh kilan ko tana hanya eh cike da yarinta *Banu* tace yeeee! ammu na zatadawo dariya sukayi mata ahaka har suka isa anguwarsu,




Saidai koda suka shiga gida basu iske ammu tadawo ba hakan yasa kirjin *Beena* cigaba da bugawa domin dai idan har taje bata" kwana, *Bass* yace ah! kinga bata dawoba to koyau lafiya?...aishi ne to Allah dai yasa lafiya to ameen.




Bayan sun cire kayan islamiya sun sawasu sai itada *Bana* suka d'ora girkin tuwo har suka gama akayi sallah magrib akayi isha'i ammu bata isoba, bayan sun gama cin tuwo suna zazzaune sai *Beena* tace abbu kilan bayau ammu zata dawoba,




"eh to da'alama amma kuma batace mun zata kwana ba eh nima bata fad'amun ba, amma bari naje gurin maman abdul tabani aron wayarta" nakirata naji ko tana hanya ne kilan bata taso dawuri bane ko?...




yace eh hakan zaya iya faruwa ko motar tasamu matsala ahanya ba, eh shidin ne bari naje to sai kindawo *Banu* tace aunty *Beena* zan rakaki tace to zo muje,




koda sukaje takira amsar kenan guda daya wato akashe wayar take hakan yasake fad'ar matada gaba sosai, gashi ita ko kad'an bata tab'a tunanin rike lambar "kawu muda ba balle takirasa domin yana d'aya daga cikin mutanan data tsana arayuwar ta,




haka nan takoma gida tafad'a ma abbu shikansa saida yaji fad'uwar gaba amma bai nuna masuba saidai yace duk yanda akayi kilan sai gobe zata dawo,




shuru *Beena* tayi tsawon wani lokaci sannan tace to Allah yadawo da'ita" goben lafiya, amin suka amsa amma dai haka suka kwana zuciyar su cike dakewar ammun da kuma fargaba musamman *Beena* da abbu, domin wannan shine kara nafarko arayuwar su dazasu kwana batare da'ita ba.




*******
Kamar koda yaushe atsakiyar katafarin falon tulin toys ne watse, sanye yake da riga t-shirt fara me hoton zuciya da wando jeams blue crazy lallausan suma kanshi yasha gyara kamshi sai tashi yake ajikinsa, fatar nan tashi sai sheki take alamar tana samun kulawa yanda yadace,




fuskar nan tashi fayau wanda yake nuna alamar bayada cikkakken lafiya, kwance yake k'asan kafet yayi ruf da ciki kafafunsa asama sai wasa yakeda su hannun sa duka biyu ya tallabe da kyakkyawar fuskarsa me cike da lafiyayyen sajen dayake shan gyara agurin masu kula dashi, yayinda ya kurama t-v ido yana kallon catoon din tony da Jerry sai kyalkyatan dariya yake abinsa *Blue* kenan,




"Gefensa masu kulada shi ne sai kallon sa suke cike da tausayin halin dayake ciki musamman peter, gashi ba musulmi ba amma yanada matukar tausayi tunda d'azu ya gama abincin dare yake fama dashi yazo yaci yakiya, kuma yana jin yinwa tunda rabonsa da abinci tunda rana amma saboda kallon catoon yadauke masa hankali shiyasa,




Daya daga cikin su yace idan bamu kashe catoon din nan bafa bazaya tsaya yaci abincin ba, kuma kusan me gida yakusa dawowa kuma kunsan fad'a zayayi mana yace" mun barmasa yaro dayinwa, daya yace haka ne to idan muka kashe kuma damun mu zayayi da kuka peter yace dole akashe yaci abinci haka akayi,




Aikam ana kashewa yamike zumbur yafara ihu yana shura kafafu saikace yaron da'aka anshe masa mama daga bakinsa, cikin lallashi peter yace yi hakuri me gidana idan kagama cin abinci zan kunna maka kaji?...




shuru yayi yana kallonsu, sai kuma ya makye kafad'ar shi alamar bai yarda ba kai peter ya gyad'a masa tare da cewa nayi maka alkawari dakyar dai suka samu yaci abincin sannan suka kunna masa catoon din yacigaba da kallon sa,




yana cikin kallon sai ga *Bulama* yashigo da sallama hannunsa rikeda jakar aiki da leda, zumbur *Blue* yamike cike da murna yanufe shi yana tsalle kasan cewar tuni yasaba dashi sosai, da sauri *Bulama* ya ajiye kayan hannun sa ya rungume shi suna ta kyalkyata dariya.




Kasan cewar tun bayan da *Bulama* yafara zuwa aiki duk lokacin da yataso daga aikin sai yafara biyowa tanan gidan su *Blue* yakawo masa tarkacen ciye-ciye, sannan yaciro takardu yana nuna masa yace kaga my _guy_ yau anyi kaza munyo odar kaza ansiyar mun kuma samu ribar kaza, anraba nasamaka naka acikin akawun dinka kaji my _guy_




shidai baya fahimtar abinda yake cewa saidai yayi dariya ko yace kai abokina ne ko?....sai *Bulama* yakai gyad'a masa kai wani lokaci kuma sai yafashe da kuka, yayinda shima *Blue* sai yafeshe da kuka dazaran yaga haka sai yayi shuru.




Kamar yanzuma zama sukayi suna kallon juna suna daariya bayan sun nutsu sai *Bulama* yadauko tarkacen daya siyo masa yamika masa, karba yayi yana dariya yabud'e yaciro pizza yafara ci yana kallon sa can kuma sai yadauko jakarsa yaciro takardu yafara nuna masa, saidai yauma ko kallon sa beyi ba,




asalima dariya yake tare da nuna masa t-v wai yakalli catoon wasu hawaye ne masu zafi suka taru acikin idonsa, don haka da sauri yamayar da takardu tare da daukar jakarsa zaya fita da sauri *Blue* yarike masa hannu batare da yakalle saba yace zandawo anjima kaji my _guy_?....




kai ya gyad'a masa sannan yasaki hannu tare da yimasa bye bye, sannan yafita da sauri zuciyar sa cike da tausayi halinda amininsa yake ciki.




"Aban garan mom kuwa duk bayan kwana biyu tana zuwa tagansa, saidai rabanta da gidan tun wani rana datazo ta'iske masu kula da *Blue* sunata damben rikesa saboda wani irin ihu dayake yana rikeda kansa alamar shike damunsa,




Dakyar suka rikesa tayi masa addu'a har yasamu barci sannan ta tafi gida tana kuka wanda tun ranan ne batasake zuwa ganinsa ba, domin bayan kwana biyu da komawar ta sai zazzabi yarufeta yanzu haka sai ankwantar sai antayar abin zan mamaki domin kuwa magani ake kamar ba'ayi,




Itama aunty bebe duk bayan kwana biyu sai tazo ganin *Blue* duk lokacin dazata tafi da kuka haka dai abin yaketa tafiya.




*_Bayan kwana biyu_*


*****
Su *Beena* kam hankalin su yagama tashi ganin har yau kwana biyu ammu bata dawoba don haka suka yanke shawarar *Beena* tabita tagani ko lafiya, tunda ko ankira layin ta baya zuwa don haka sai taje gurin maman abdul tabata aron dubu biyu dama akwai dari biyar da akabata kudin wata, *Bass* ma yabata dari biyar da ogansa yabashi saita had'a dashi takama hanyar abuja.




"koda ta'isa batasha wahala ba tunda dama tasan anguwan don haka ta hau tasi yakaita, bayan tabiya shi kudinsa sai tanufi get din gidan tana turawa taji kofar arufe don haka sai tafara kwankwasa wa,




sabon me gadi ne yazo yabud'e fuska had'e yace lafiya ke wacece?...saida tagaida shi sannan tace sunana *Beenazeer* nazo daga zariya ne ni d'iyar kanwar me "gidan na ce ba tare da yace komai ba yabud'e mata tashiga,




"Da sallama tashiga falon kirjinta yana bugawa cikin sa'a ta'iske kawu muda zaune shida Safara'u suna ganinta suka kalli juna cike da munafurci tace a ah lale maraba yau *Beenazeer* ce agidan namu?...,




murmushin karfin hali tayi tare da zaunawa kirjita yana cigaba da matsananci bugawa tace eh nice aunty Ina wuni lafiya lau, kawu Ina wuni yace lafiya lau ya mutanan gida?.. tace lafiya lau, yauwa ya'akayi ne?...tace umh! kawu dama munji Ammu shuru ne shine abbu yace" nabiyo ta ko lafiya yace kina nufin Fatima?.tace eh yayinda kirjita yake masifar bukawa yace tun yausheta wuto nan din?..




cikin fargaba tace tun shekaran jiya, kai! aiko batazo ba Safara'u ko kinganta"?...a ah banganta ba ido *Beena* tazaro cike da matsananci tsoro tace.....






Muje zuwa




โœ๐Ÿผ



Alkalamin


โœ๐Ÿผ


*_LUFHAT_*
๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ
๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ
๐ŸŽ๐ŸŽ
๐ŸŽ


๐ŸŽ *_ZAUJUN-MAJNUN_*๐ŸŽ
_(miji mahaukaci)_


๐ŸŽ
๐ŸŽ๐ŸŽ
๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ
๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ




Page1๏ธโƒฃ9๏ธโƒฃto2๏ธโƒฃ0๏ธโƒฃ


WRITTEN
By


๐ŸŽ *AMEENA UMAR FARUQ*๐ŸŽ


OR


๐ŸŽ *MEENAT*๐ŸŽ




Marubuciyar
*_DA SANNU_*
*_ZUCIYATA CE_*
*_AFSANA_*
*_KYAUTAR ALLAH CE_*
and now๐Ÿ‘‡๐Ÿฝ
*_ZAUJUN-MAJNUN_*




SADAUKARWA GA


*_My lovely blood sisters ๐Ÿ‘ฉโ€โคโ€๐Ÿ‘ฉHadiza (aunty)and Nana Firdausi out last bornnn, do u know what? sisters humm l really love love love yous irin babu adadin nan fa so muchhhhh love๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹._*




Littafin nan na kudi ne duk me bukatar zaya iya turo katin MTN ko AIRTEL na 200 a wannan 08161850024, idan kuma tresfa zakuyi duk zaku iya tuntuban layin sai abaku account no ba nagode.


_____________________________
ยฎ _PEN : WRITERS ASSOCIATION_
_______________________________
~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~




https://www.facebook.com/groups/1061983803858837/




*_FREE PAGE_*




โœ๐Ÿผ


_*Bismilahirrahamaniraheem!!!*_






Kawu batazo bafa kuka ce?...eh mana yo karya zamuyi maki?... hannu ta yarfar tare dafa kirji ta furta innalillahi! wlh kawu ammun mu tun shekaran jiya tabaro gida kuma nan tace zatazo, don Allah kawu idan wasa kake kabari wlh kirjina zaya iya tar watsewa dajin wannan wasan,




Cikin tsawa yace ke! nataba wasa dake ne koni abokin wasanki ne dazanyi maki wasa eye?...ance maki batazo ba batazo ba ko idan tazo zamu boye tane eye?...,kai ta girgiza yayinda jikinta yake mugun rawa bugun kirjin ta yatsanan ta wanda bayada misali, cikin rawar murya tace yanzu kawu da gaske kake ammun mu bata zo nan ba?...




Wani lafiyayyen mari yasakar mata akan kyakkyawar fuskar ta ido tarinte, ciki masifa yace ke! dan uwarki da ubanki karya zanyi maki nace karya zan maki eye?...,ke! Dan ubanki tashi kibar mun gida "uwarki kikazo nema ko?..to batazo ba, don haka tashi ko nayi mugun saba maki kinji ko?...




Ahankali ta bud'e idon wani irin duhu tagani amma haka ta mikewa jikinta sai karma yake, tadauki jakarta taku daya ana biyu ta zube kasa sume.




Zumbur Safara'u tamike tare dafadin mun shiga uku Alh kar yarinyar nan tamutu mana agidafa...tsaki yayi mtw! tare da fad'in ko ta mutu babu abinda za'ayi, cike da tsoro tace a ah alh garadai karta mutu mana anan ta kareshe fadi tare da fara girgiza *Beena* tana cewa ke! *Beenazeer!* ke! *Beenazeer!!*




shuru bata motsa ba hakan yasa tace Alh mun shiga uku tamutu fa, tsaki yasake tare da fad'in suma tayi ki dauko ruwa kizuba mata ta tashi tabar mana gida kinaji ko?...to, Da sauri taje ta dauko ruwa afirj in ta yayyafa mata ta dauki lokaci kafin ta farfad'o bakinta dauke da salati,




"Ahankali tamike zaune tare da dafa kai tayi shuru kawu yace ke! da sauri tad'aga kai ta kalle sa yace tashi ki koma inda kikafito domin dai "uwarki batazo nan ba kinji ko?.. kuka ta fashe dashi tare dafadin don Allah kawu kanemo mana "Ammun mu wlh bata gida, cikin tsawa yace ke! Dan ubanki nizan nemo maki ita nasan inda takene?...




cikin rawar murya tace a..a...h! Ina nufin kasa anemo mana ita don Allah, yace bazan saba tunda batazo nan ba idan kuma tazo to bansan gidan ubanda ta tafi ba balle nasa anemo ta, don haka tashi kitafi ga kudin mota kije kifad'ama wannan nakasheshsa "ubanki batazo ba,




yakareshe fad'i tare da ciro kudi acikin aljihun wandon sa yak'irga dubu biyar yamika mata bata karba ba sai kuka take tamkar zata shid'e, cikin tsawa yace dalla gafara karba kitashi kitafi nagaji dajin wannan shegen kukan naki da sauri takarb'a,




domin dai batada zab'in da yawuce takarb'a din tunda dai batada kudin motar komawa gida, ahankali tamike tare da daukar Jakarta jikinta sai rawa yake zuciyar ta tana cigaba da matsananci bugawa aranta kuma tunani take ina ammun su tashiga?....




******
"Ahaka ta tari taxi yakaita tasha tashiga mota sai kuka take gwanin tausayi acikin mota kuwa sai tambayar ta ake lafiya?...




bata iyabada amsa ba domin itadin ba ma'abociya magana bace, sai kuka kawai take wata mata tace ke kodai yammata anata tambayar ki meyasa meki amma kin kyale mutane, cikin tsanani kuka tafad'a masu abinda yasata kuka aikam take suka saki salati matar tace aikam dole kiyi kuka,




domin dakyar idan batafad'a hannun yan garkuwa da mutane ba, wata tace ai idanma yan garkuwa da mutane ne dasauki, suce akai masu kudi su bada ita idan tafad'a hannun yan yankan kai kam saidai wata ba'ita bakam domin kuwa ta halaka eh fa wlh,




aikam take kukan *Beena* yakaru tsoro yasake kamata wani d'an dattijo yace haba don Allah ku kam wani irin abune haka eye?...maimakon kutayata addu'ar Allah yabayyar mata da mahaifiyar ta sai kudinga irin wanyan nan maganganu dazasu sake firgitata saboda Allah fa?...




shuru sukai sai yakalli *Beena* wacce keta kuka yace kiyi shuru y'ata ki daina kuka haka inshallah zakiga mahaifiyar ki, kedai kiyi addu'a Allah yakareta dafad'awa mugun hannun kinji ko?...kai ta gyad'a alamar to, ahaka dai aka cigaba da tafiya sai yamma lis suka iso zariya don anama shirin Kiran sallar magriba, koda aka sauketa saita tari adai-daita zuwa anguwarsu dake fadaman sarki.




******
Zata shiga gida kenan saiga *Bass* da *Bash* sunfito zasu tafi masallaci, ganinta ita kad'ai yasa *Bass* jin fad'uwar gaba don haka da sauri yace Aunty *Beena* Ina "Ammun mu?...
kuka tasaki tare da shigewa cikin gida da sauri,




cikin tsanani tashin hankali yabi bayanta, yana kira d'akin Abbu tashiga dai-dai lokacin da yake kokarin tada kabbaran sallah azaune kamar koda yaushe, shigarta yasa yatsaya yayinda yaji wani irin fad'uwar gaba me tsanani, zubewa tayi agabansa tana cigaba da matsananci kuka,




Dai-dai lokacin da su *Bass* suka shigo cikin tashin hankali suma suka zube gaban Abbun, sai ga *Bana* itada *Banu* sunfito daki dasauri suma suka zube gaban Abbun sai ya kasance sun sashi tsakiya, sai kallon *Beena* suke itakam sai kuka take wanda har yasa *Bana* da *Banu* suma fara kukan, cikin tashin hankali *Bass* yace Aunty *Beena* wai me yafaru ne?...



Nace Ina "Ammun mu kinyi shuru sai kuka kike gashi har su *Banu* sun fara, shuru bata bashi amsa ba, sai kuka take hakan yasa shima *Bass* jin kukan yana shirin kufce masa da sauri yadukar dakai domin shidin ba ma'abocin saurin kuka bane ko don shi namiji ne?...oho.




Shikam Abbu kura mata ido yayi yayinda yakejin kukan ta har cikin ransa domin itadin y'ace mafi soyuwa agurinsa, ido ya lumshe acikin ransa yafurta yah Allah kasaba wani mummunan abune yasamu "Fatima ta ba?...




ahankali yabud'e ido yasake zubasu akan *Beena* wacce tsabar kuka har yasa tafara jinkanta yana sarawa, cike da fargaba yace *Beenazeer* abbu dasauri tad'ago kai fuska sharkaf da hawaye ta kalle shi yace bari kukan nan haka ki fad'amun Ina fatima ta take?..




Cikin kuka tace abbu bansan inda "ammu take ba...da sauri yace ban fahimce kiba?... kawu yace" bataje gurin su ba...cike da tashin hankali yace innalillahi! bataje gurin suba to Ina take?...bansani abbu bansaรฑ kowa'ina acikin abuja balle na nemeta, kuma nace kawu yasa anemo ta yace" bazaya saba, abbu ina ammun mu take?..




wani irin gumi ne yatsatsufo masa agoshi hannu yasa yashare tare da fad'in allahumma'ajirni'fimusibatiwa'akifliminhairinminar! yah ubangiji kabamu ikon cin wannan jarabawa amin, abbu Ina zamuga ammu Ina ammun mu tashiga?..




Cike da tashin hankali yace Allah shine masani inda take kuma shizaya bayyana mana ita, yanzu kutashi kuje kuyi sallah muroki Allah yabayyar mana da ita, sukace to tare da mikewa jikinsu asanyaye *Beena* kam har wani jiri ke d'ibarta gwanin tausayi gabad'a tafisu shiga tashin hankali rashin ammu.




****"****
Abu kamar wasa wai karamar magana tazama babba ba domin kuwa ba ammu ba labarin ta wanda hakan yasake tayar masu *Beena* hankali, sunyi kuka har sun gajin duk sun rame musamman *Beena* da abbu tun suna saran ganin ta har sungaji sun zubawa hukuncin Allah Ido addu'a kam sosai suke yinta.




*_Bayan wata uku_*
*******
Haka rayuwa tamika yau kimanin wata ku kenan da batan ammu abubuwa da dama sunfaru aciki harda rashin lafiyar abbu, wanda tun ranan dayaji labarin rashin inda "ammun take yakefama darashin lafiyar da sai ankwantar sai antayar,




Sosai yakejin jiki garashin lafiyar kafa gata jiki da zuciya wanda idan akacire rashin lafiyar kafa sรกuran duk suna da nasaba da rashin "ammu, wanda ba karamin nakasu yasake yiwa rayuwar su *Beena* ba domin yanzu *Beena* da *Bass* sun daina zuwa gurin koyan d'inki da saka har da islamiya ma, saboda sune manya sukeda karfin kula da abbu
Saidai *Bana* da *Bash* ne kawai suke zuwa.




haka dai rayuwa ta mika to sannun ahankali abbu yake samun sauki da taimakon Allah dana baban Abdul, wanda yake kuladasu dai-dai karfinsa domin hatta da abinci yanzu gada gidansa ake basu tunda basu dakomai wata rana kuma sai yayomasu chefane su girka dakansu, don haka suke matukar girmama shi da iyalinsa.




******


"Abangare ammu kuwa saida ta kwana tawuni sannan tafarfad'o misalin karfe 8:00pm na dare bakinta dauke da salati, da kyar ta'iya bud'e idanun ta sakamakon nauyi dasukai mata duhu yamamaye ma ganinta hakan ne yasata sake murza idon ta,




donta tabbatar saidai kuma me?...duhun tasake ganin hakan yasa tajin fad'uwar gaba me tsanani, dasauri tamike zaune tafara kallon inda take shuru tayi na d'an wani lokacin tana tunani tuno abinda yafaru ne yasata mikewa zumbur,




Cikin tsanani tashin hankali tace subhallahi! Ina ne Nan nake?...ba amsa koda yake amsar kenan acikin daji take wanda tuni ta fahimci hakan, kuka tafashe dashi tare dafadin oh! ni fatima yanzu kiyayyar da yaya muda yakemun hartakai yasa asalwantar da rayuwata, saboda kawai na tambayi hakkina?...




tafiya tafarayi tana kuka sosai saboda tuno halinda iyalinta suke ciki ba tare da ta tsaya daukar jakarta da tarkacen kanta ba wanda ba lallaine tagansu ba saboda duhun gurin, cike da tsoro take tafiya wanda jefa kafafuta kawai take wanda ba takalmi yayinda bakinta yake dauke da duk wata addu'ar neman tsarin da tasani,




Tayi tafiyar da akalla yakai ta awad'aya da rabi kafin ta'isa bakin titi gabad'aya ta galabaita har ba ta'iya ganin gabanta sosai hakan yasa tahau kantiti batare da tasani ba, adai-dai lokacin da wata bakar mota dalleliya tashararo da gudu aikam take tadauke ammu saida tayi sama sannan tadawo kanta yabugi motar tafadi kasa take jini yafara zuba,




Dai-dai lokacin da direban yataka matsiyacin birki da sauri yafito yanufe ta yana fad'in subhallahi!, sannan wani dattijo yafito da sauri wanda akalla zayakai shekara sittin aduniya duk da duhun da garin yayi hakan behana agane farine shi ba,




sanye yakeda farar shadda dinkin manyan kaya ne wato riga da wanda da babbar rida harda nad'in farin rawani akasa fuskar sa manne da farin gilas, dasauri yakarasa gurinsu dai-dai lokacin da direban yadago kan ammu daketa malalar jini tamkar anyanka dabba,




yace subhallahi! mlm yakubu wa muka bige?...cike tsoro yace yallabai wlh wata matace bata ko motsi balle numfashi, innalillahi! yallabai Ina ganinfa ta mutu cike da tashin hankali yace....










_*Wannan page din shine free page na karshe don haka duk wanda yake son cigaban labarin kodaga farko zaya tuntubar wannan layin 08161850024 ko ya turo katin MTN 200 ko yai tresfa ta wannan acc no 0047769671 Abdullahi Amina gt bank ne nagode*_




Muje zuwa




*_Yanzu za'afara labarin ZAUJUN MAJNUN!_*
miji mahaukaci shin ya abin zaya kasance?.....






Tareda


โœ๐Ÿผ
*_LUFHAT CE_*




๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ
๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ
๐ŸŽ๐ŸŽ
๐ŸŽ


๐ŸŽ *_ZAUJUN-MAJNUN_*๐ŸŽ
_(miji mahaukaci)_


๐ŸŽ
๐ŸŽ๐ŸŽ
๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ
๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ




Page2๏ธโƒฃ1๏ธโƒฃ


WRITTEN
By


๐ŸŽ *AMEENA UMAR FARUQ*๐ŸŽ


OR


๐ŸŽ *MEENAT*๐ŸŽ




Marubuciyar
*_DA SANNU_*
*_ZUCIYATA CE_*
*_AFSANA_*
*_KYAUTAR ALLAH CE_*
and now๐Ÿ‘‡๐Ÿฝ
*_ZAUJUN-MAJNUN_*




SADAUKARWA GA


*_My lovely blood sisters ๐Ÿ‘ฉโ€โคโ€๐Ÿ‘ฉHadiza (aunty)and Nana Firdausi out last bornnn, do u know what? sisters humm l really love love love yous irin babu adadin nan fa so muchhhhh love๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹._*




Littafin nan na kudi ne duk me bukatar zaya iya turo katin MTN ko AIRTEL na 200 a wannan layin 08161850024, idan kuma tresfa zakuyi duk zaku iya tuntuban layin sai abaku account no ba nagode.


_____________________________
ยฎ _PEN : WRITERS ASSOCIATION_
_______________________________
~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~




https://www.facebook.com/groups/1061983803858837/










โœ๐Ÿผ


_*Bismilahirrahamaniraheem!!!*_






Innalillahi! kai! mlm yakubu kaifa haka kake taya kasan ta mutu?...to yallabai ko motsawa batayi ba gashi jini sai zuba yake, cikin tashin hankali yace to nidai yanzu dauko ta kasata amota mukaita asibiti su dubata,




to yallabai da sauri yad'auke ta yayinda dattijo yabud'e masa kofar baya yasata sannan yarufe, sukaje suka shiga mlm yakubu yaja suka tafi.




"Wani babban asibitin kudi suka kaita da sauri akazo da gadon d'aukar marasa lafiya aka dauketa d'akin taimakon gaggawa aka nufa da'ita,




sosai likitocin suka bawa ammu taimakon gaggawa sunyi nasaran tsayar da jinin saidai bata farfad'oba, amma numfashin ta yana tafiya yanda yadace sannan sun kafito.




Da sauri dattijon nan yatari babban
likitan yana tambayar sa likita ya me jikin?...cikin girmamawa yace ranka yadad'e dasauki amma muje ofis inason magana dakai yace to muje mana,




ayan sun zauna blikitan yace ranka yadad'e Allah yabamu ikon tsayar "mata da jinin don haka inshallah akoda yaushe taza iya farfad'owa...., saidai kanta yad'an bugu kad'an da sauri yace likita akwai matsala ko?..




"eh to yanzu dai bamuda tabbacin hakan harsai "ta farka munga yanayin ta tukun, ajiyar zuciya yayi tare da fad'in to likita nagode ita kuma Allah yabata" lafiya yace amin don Allah inason kasa akula mun da'ita" dakyau nizan tafi gida domin nasar da iyalina halinda ake ciki,




saboda basu saniba kasan cewar mun fito minna ne akan haryamu ta dawowa ne sai wannan baiwar allah ta gitta mana muka bigeta, yace Allah sarki kar kadamu yallabai inshallah za'a kula da "ita yanda yadace,




yauwa nagode sai ka lissafa kudin ka idan nadawo sai na rubuta maka cak to yallabai sai kadawo, sannan yatashi yafita direban sa mlm yakubu yatarbe sa yana tamayar sa yame jiki?...yace da sauki tare fad'a masa abinda likita yace ahaka har suka karasa mgurin mota yabud'e masa sannan shima yashiga yaja suka tafi,




"Anguwarsu dake maitama wani tabkeken gida suka nufa bayan yayi hon me gadi yabud'e masa kofa yashiga masha'allah, gaskiya gidan yahadu matuka kota'ina hasken kwan lantarki ne gefe daya kuma wasu yan' sanda ne tsayayaye kimanin su shida,




bayan direba yabude masa kofa yafito sai yan sandan nan suka gaidashi ta hanyar saramasa hannu yad'aga masu sannan yanufi cikin gida, wani hadadd'en falo yashiga wanda yaji kayan more rayuwar duniya.




Sallamar sace tasa matar shi da yaransa biyu tashi da sauri sukaje suka rungume shi cike da shagwab'a macen tace Abba muna takiranka baka dauka ba duk mundamu, kanta

Please Login or Register in order to submit comment