Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

za'afara_


So
More
Comments more
typing and pls share it
๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ
๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ
๐ŸŽ๐ŸŽ
๐ŸŽ


๐ŸŽ *_ZAUJUN -MAJNUN_*๐ŸŽ
_(miji mahaukaci)_


๐ŸŽ
๐ŸŽ๐ŸŽ
๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ
๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ




Page5๏ธโƒฃto6๏ธโƒฃ


WRITTEN
By


๐ŸŽ *AMEENA UMAR FARUQ*๐ŸŽ


OR


๐ŸŽ *MEENAT*๐ŸŽ




Marubuciyar
*_DA SANNU_*
*_ZUCIYATA CE_*
*_AFSANA_*
*_KYAUTAR ALLAH CE_*
and now๐Ÿ‘‡๐Ÿฝ
*_ZAUJEE-MAJNUN_*


SADAUKARWA GA


*_My lovely blood sisters ๐Ÿ‘ฉโ€โคโ€๐Ÿ‘ฉHadiza (aunty)and Nana Firdausi out last bornnn, do u know what? sisters humm l really love love love yous irin babu adadin nan fa so muchhhhh love๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹._*




Littafin nan na kudi ne duk me bukata zaya iya turo katin mtn ko airtel na 200 a wannan layin 08161850024, idan kuma tresfa zakuyi duk zaku iya tuntuban layin sai abaku acc no nagode.




_____________________________
ยฎ _PEN : WRITERS ASSOCIATION_
_______________________________
~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~




https://www.facebook.com/groups/1061983803858837/






_FREE PAGE_




โœ๐Ÿผ




_*Bismilahirrahamaniraheem!!!*_






"Ai babu abinda Baba yabari ko kudin dayake kasuwanci dasu duk na mutane ne, kuma tuni yabashi ya mayar masu da abinsu,




Cikin tsananin tsoro! Ammu ta kalle shi! haka malaman gurin mamaki yarufe su dajin wannan magana me kamada almara, domin dai ansan "Alh Sule yanada dukiya me tarin yawa,




Wanda kuma tabbas tashi ce bata wani ba amma taya d'an sa zayace wai batasa bace to me yake nufi?....yayinda Haj Hajara ta goyi bayan shi domin kuwa da daya daga ciki malaman dazasu raba gadon ya tambaye ta, meye gaskiyar lamarin?..




Sai tace ai gaskiyar kenan domin itama kusan kodaya yaushe yanafad'a mata ba dukiyar shi bace, abu kamar wasa yazama gaskiya don haka malaman da suka tsaya akan rabon gadon suka bar gidan,




Bayan sun tabbatar ma Alh Muda da mahaifiyar sa cewa muddun sukaci kwayar zarra na hakkin wannan baiwar Allah zasu biyata gobe kiyama, sannan suka fita.




Yayinda akabar shi daga shi sai Ammu da Haj Haraja cikin mutuwar jiki Ammu tace yaya Muda kaji tsoron Allah, taya zakace duk dukiyar nan bata "Baba bace?.




Dariyar mugunta yayi yace ah! dukiya kam ta duk ta "Baba ce kece dai bazan bawa ko sisin kobo aciki ba, wanda kukaci keda mijinki da y'ay'aki ya'isa haka wannan tawace nida y'ay'ana da zan haifa,




tace to don Allah kabada kudin ayiwa Abbun su aiki cikin masifa yace wlh ko sisi bazaya bayar ba aiba kudin ubansa bane, kai su tashi ma subar masa gidan shi,




Wasa-wasa Alh Muda yamursashe idonsa yahana ma Ammu gadon ta, kusan kullun taje don yabata tabiya wa yara kudin school, akuma yiwa Abbu aikin kafar sa wanda akace naira miliyan biyar za'ayi Amma Dan talikin nan har yau kusan shekara uku kenan,




Amma yaki bata ba tun yana garin kaduna har yakoma Abuja dazama cikin daya daga gidajen Alh sule, kasan cewar dama yanada gidaje a Abuja, aduk lokacin dataje saidai yaimata walakanci idan kuma tacinma yan arzikin yace mata tazo yawan maularta ko?...




To shine sai kaga wata rana yabata wasu yan kudi shine zata hau mota sauran suci abinci, idan kuma yanaji tsiya kosisin baya bata saidai Safara'u matarsa tabata kudin motar dawowa, shiyasa komai duk yacab'e masu rayuwa tayi masu zafi hatta da abinci dazasuci yana kokarin yafi karfinsu,




School kuwa tun sunayi masu hakuri har sungaji yanzu kusan kullun sai ankoresu, Abbu yasha ce" Ammu tayi hakuri ta kyale "shi tunda yaki bata Amma takiya kasan cewar Ammu akwai kafiya.




Ahankali ta sauke ajiyar zuciya sannan tamike cikin nutsuwa tashiga toilet din cikin dakin, *Beenazeer* kenan tanada matukar nutsuwa da kunya ga ladabi da biyayya musamman ga iyayenta tanada ilimin addini sosai,




Domin kuwa ta sauke alqur'an da hadda takuma an wasu littafai addini sosai, yanzu haka tana koyarwa a islamiyar su idan wata yayi abiyata wanda dashi ne suke dan samun abinda sukeci, amakarantar boko kuma tana S S 3 sune ma zasu rubuta jarabawa wannan time din, batada yawan magana domin kuwa miskilace tabugawa ajarida saidai tanada hakuri sosai amma kuma akwai matukar zuciya duk haka kuma tana da tsoro uwa uba ga kafiya wanda da alama Ammu su tabiyo,๐Ÿ˜€




Sannan tana matukar kaunar iyaye ta da yan'uwanta fiye da yadda take kaunar rayuwarta zata iyayin komai domin sama masu farin ciki, wanda hakan yasa iyayen ta suke kaunarta fiye da tunanin me karatu wanda suka dayai suka san adadisa aransu,




Ko bakomai itadin me shiga raice ga duk wanda ya zauna da'ita sai yaji tashiga ransa yaji yana Sonta, hakan nan suma yan'uwan nata suke kaunar ta ko dayake hakan yanada nasaba da yadda iyayen nasu suka koya masu kaunar junan su.




Bata dad'e atoile din ba tafito daure da tawul dai-dai lokacin da *Banafsha* tashigo dakin da sallama, tace Aunty *Beena* "Ammu ta tafi Abuja gidan "kawu Muda ne?..kai ta gyad'a mata cikin sanyi murya tace Aunty *Beena* Allah yasa kawu "Muda yaba Ammun mu kudin ta,




Ahankali tace ameen my *Banaf* kicire uniform kisa wasu kayan mutafi gidan maman Abdul tare kinji?..cike da murna tace to.




Cikin kankani lokaci *Bana* tashirya wanda kusan tare suka gama da *Beena,* sanye suke cikin riga da zani na wata blue atamfa bayan ta murza man kwalacca sai tafeshe jikinta da turaren humra da maman Abdul ta bata sannan su kasa hijab fari sannan suka fita,




Dai-dai lokacin da *Bassam* da *Bash* suka dawo raka Ammu, *Beena* tace su shirya su tafi gurin inda suke zuwa koyon dinki sukace to, dinki mata *Bassam* yakeyi yayinda *Bashir* yake koyan na maza *Bassam* tuni ya'iya dinki wanda har dashi suke samun kudin sayen abincin,




Sannan su *Beena* suka shiga dakin Abbu suka sallame shi sannan suka fito suka tafi gidan maman Abdul.




Maman Abdul makociyarsu ce, tana zaune da mijinta da yaran su biyu Abdullah da Anisa tanada kekunan saka Wanda take koyawa yammata aciki har da *Beena* da *Banaf*, maman Abdul tana matukar kaunar *Beena* saboda tanada basira sosai gata dasaurin dauka abu wannan kenan.

*Cigaba*


*ASIBITIN SHIKA*


****""""*****
Koda suka isa cikin sauri aka tarbe su kasan cewar Dad babban Dr ne acikin asibitin don haka akazo da gadon daukar marasa lafiya aka dauki *Blue,* wanda yaketa faman ihu tareda fisge fisge direct emagency room aka nufa dashi,


likitoci sunfi biyar akasa aciki
har da Dad sosai suka dukufa akansa yayinda yaketa fisge fisge tareda wani irin ihu,



Likitoci sunyi iya kokarisu akan *Blue* amma abun yaci tura domin kuwa be daina fisge fisgen da ihun dayake ba, tareda ture duk wanda yai yin kurin rikeshi,




Don haka dole suka taru kusan mutum goma aka danne shi sukayi masa alluran barci me matukar karfi, sannan suka fito kowa sai sharan gumi yake yayinda zuciyoyin suke cike da mamakin abinda yasa meshi haka...?
Musamman Dad.




Direct wani babban daki suka shiga inda suke tattaunawa especially idan irin haka tafaru, sosai ake tattaunawa akan wannan lalura da tasamu Dan abokin aikinsu, nan Dad yake fadama su yanda abun yafaru, sai daya daga cikin likitoci yace niko sai nake gani kamar aljanu ne suka shafe s....




Zumbur Dad yamike cikin bacin rai yace haba Dr lbrahim wannan wace irin magana ce....? D'an nawa ne aljanu suka shafa?...to kasani ni 'Dana ba buwasu aljanu dasuka shafe "sa, asalima ni mabansan akwai wasu aljanu aduniya ba,




Sannan yafita rai bace daga dakin daya daga cikin likitoci yace humm! Dr I b kenan kaima kasan cewa "Dr L U be yarda da duk wani abu daya shafi gargajiya ba,




Amma tabbas ciwon "yaron sa yayi kama da shafar aljanu, Dr I b yace "uhumm kaima kafad'a yanzu dai mubari yatashi musake ganin yanayin sa tukun ko?..suka amsa da eh haka za'ayi sannan suka fito kowa yanufi office dinsa zuciyar sa cike da tunani halinda *Blue* yake ciki.




Dad ma koda yafita direct office dinsa yanufa da sauri *Barrister* tareda *Bulama* suka bishi, alokaci daya suka zazzauna cikin tashin hankali *Bulama* yace Dad meye samu my *Blue?...* *Barr* ma irin tmbyr yayiwa Dad,




Shuru Dad yayi kafin cikin bacin rai yace kai kaji "Dr I b wai aljanu suka shafi my "boy da sauri cikin harshen turanci *Bulama* yace Dad
meye kuma haka..?wai evil, tsaki yayi yace karya ne Dad me I don't believe this wooo! Dr yace me to my boy,




Shikam *Barr* shuru yayi yana nazari lamarin can sai yace Dr lamarin fa akwai kamshi gaskiya, da sauri Dad yace haba *Barr* kamar ya fa?...




yace naga yanda yake irin yadda aljan...dasauri Dr yace enough! enough!! enough!!! *Barr* banaso kana alakanta "boy da wayan nan shirmen da ni kwata-kwata banyi believe dasu ba, yace sorry bawai nace sudin bane amh! to yanzu dai ya jikin nasa"?...




Cikin had'e buska Dad yace him in bad condition, yanzu ma saida mukayi masa alluran barci me karfi wanda zata iya kaiwa gobe so idan har yafarka banga wani cigaba ba zanfitar dashi waje, *Barr* yace to Allah yabashi lfy,




Dad yamike tare da cewa Amin mujen ku gida inason nad'anyi wani bincike akan ciwon boy, *Barr* yace ok *Bulama* yace Dad ni zan tsaya gurin my *Blue* murmurshi yayi tare da dafa kafad'ar shi yace karka damu my boy akwai masu kulashi so muje ka huta kaji..?




Yace yes Dad, Sannan Dad yafara fita sai *Bulama* da sauri *Barr* yakama kunnan shi aikam yasaki yar kara kadan cikin shagwaba yace ahhh! papa akwai zafi fa,




Kasa-kasa yayi da murya yanda Dad bazaya jiba, yace l know meyasa bakaji ina rabaka da wannan akida kana ko karin yiko?..yace papa me nayi?..yace gidan ku, cewa fa kayi bakayi believe da aljanu ba, yace gaskiya papa ni ban yarda da wasu aljanu ba, yace to dan ubanka ko ka yarda kokar ka yarda akwai aljanu,




Yace to papa ni ban taba ganin su bafa taya zan yarda akwai su?..,da sauri yace Dan ubanka karkayi fatan ganinsu domin ganinsu arayuwa ba alkhairi ba ne,




Kai! tsaya ma tukun kanayin addu'a kuwa?..yace papa inayi shimafa my *"Blue* yanayi sosai har yafini yifa, yace kaidai shashasha ne to wlh gara kadage dayin azkhar domin suna tsare mutum daga bad evil kaji ko?..




Yace to dai-dai lokacin da suka karasa gurin mota escorts suka bude masu, suka shiga
kasan cewar tuni Dad yashiga don haka sukaja suka tafi......




*WAI WANENE BLUE*?........






_Muje zuwa yanzu za'afara_


So
More
Comments more
typing pls share
it


*_LUFHAT CE_*


โœ๏ธโœ๏ธโœ๏ธโœ๏ธโœ๏ธโœ๏ธโœ๏ธโœ๏ธโœ๏ธโœ๏ธโœ๏ธ
*ยฎ _PEN: WRITER'S ASSOCIATION_*


*~_Only the exquisite_~* *~__and whizkid_ _writers_~* ~*_are_* *_opportune to_* *_be__*~
*~_pen writers_~*
โœ๏ธโœ๏ธโœ๏ธโœ๏ธโœ๏ธโœ๏ธโœ๏ธโœ๏ธโœ๏ธโœ๏ธโœ๏ธ
__________________
https://www.facebook.com/groups/1533639276725285/
๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ
๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ
๐ŸŽ๐ŸŽ
๐ŸŽ


๐ŸŽ *_ZAUJUN MAJNUN_*๐ŸŽ
( _Miji mahaukaci_)


๐ŸŽ
๐ŸŽ๐ŸŽ
๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ
๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ


Page7๏ธโƒฃto8๏ธโƒฃ

WRITTEN
By
๐ŸŽ *AMEENA UMAR FARUQ*๐ŸŽ


OR
๐ŸŽ *Meenat*๐ŸŽ


Marubuciyar
*DA SANNU*
*ZUCIYATA CE*
*AFSANA*
*KYAUTAR ALLAH CE*๐Ÿ‘‡๐Ÿผ
and now
*ZAUJUN MAJNUN*


SADAUKARWA GA


*_My lovely blood sisters๐Ÿ‘ฉโ€โค๏ธโ€๐Ÿ‘ฉHadiza (Aunty) and Nana firdausi our Last born do u know what...? sisters humm l really love love love yours irin babu adadin nan fa irin so muchhh love_*.๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹




Littafin nan na kudi ne duk me bukata zaya iya turo katin mtn k airtel 200 a wannan 08161850024, idan kuma tresfa zakuyi duk zaku iya tuntuban layin sai abaku acc no ba nagode.


*_FREE PAGE_*


โœ๐Ÿผ


*_Bismillahirrahamanirraheem!!!_*






*BILAL LAWAL USMAN* shine cikakken sunan sa sai abokan sa suna kiransa" *BLUE*, yakasan ce d'a ne ga Alh Lawal Usman kona ce Dr wato Dad asalin sa mutumin kano ne aiki ne yakawo shi zaria, gaba daya zuri'ar su Dad yan'boko ne na bugawa ajarida irin masu komai dabi'ar su ta bature ce




Kuma asalinsu fulani ne mahaifin Dad prof Lawal Bilai yarike mukamai sosai akasa najeriya yana daya daga cikin mutanen dasuke fad'a aji kasar nan, don haka zuri'ar su manyan mutane ne kuma masu kudi ne sosai Dad su uku ne kawai agurin iyayen su kuma duk kansu manyan ne acikin gwamnati, Kabeer shine babba wanda yake zaune a Lagos da iyalan sa matarsa daya da yaran sa biyu duk maza kuma shi din babban Lawyer ne,




Sai me bimasa macece me suna Sadeeya itama babbar Dr ce tana zaune abuja da mijinta da yaranta uku maza biyu mace daya, sai Dad Wanda shima babban Dr ne acikin asibitin shika da kuma Abuja Dad yaran sa biyu Aunty Aseeya itace babba wacce suke kira da Bebe kasan cewar sunan mahaifiyar Dad taci,




yanzu haka tana abuja tana auran wani babban Lawyer gwanati tanada yaranta hudu duk mata tana aiki ababban asibitin Abuja,




Sai *Bilal* amma ba maman su daya ba domin Aunty Bebe tanada shekara 8 aduniya ciwon kansar mahaifa yakashe mahaifiyar ta me suna Hafsatu, bayan shekara daya da rasuwar ta sai Dad ya auri mahaifiyar *Bilal* me suna Hauwa wacce take shuwa arab ce kyakkawa ce, suma asalin su yan boko ne sosai sannan sunada kudi.




Dad yana matukar son Hauwa domin tanayi masa biyayya sosai kusan duk, abinda yakeso tanaso saidai ra'ayin su yasha bambam kad'an,




Dad yanada akidar boko sosai komai nasa na boko ne itama tanada shi saidai shi yafita, amma kuma duk da haka basa fad'a akan bambamcin ra'ayi, saidan kaji fadan su akan *Bilal* domin tun da aka haife shi bata sake haihuwa ba hakan be damu Dad ba tunda dama shi bayada ra'ayin tara yara dayawa,




don haka yadauki so da kaunar duniya yad'ora akan *Bilal* sosai yake matukar son shi bayason abinda zaya bata masa rai ko kad'an, hakan yasa duk abinda *Bilal* yakeso shi yakeyi shiyasa yatashi shagwababb'e domin Dad yabashi gata sosai,




wanda hakan shike hadasu fad'a da Mom dinsa kuma idan tana koya masa akidar gargajiya tareda ta addini sam Dad bayaso amma duk da haka saida ta matsa ya sauke al'qur'an yakuma sannan wasu littafain addini,




Tun *Bilal* yana yaro suke rigima akan haka har ya girma ba adaina ba wanda shine dalilin rabuwar su,




Saidai tunda suka rabu ba wanda yayi aure cikin su har yanzu, tun *Bilal* yana secondary har yayi digren nafarko akan pharmacy wanda ra'ayin Dad ne, inda yaje chana yayi digren sa na biyu akan business administration Wanda ra'ayin sa ne wannan dawowar su kenan, wannan bakon al'amari yafaru dashi wanda bamusan komene ba amma dai bari mubisu asannun muji.




*BUHARI TAHIR BULAMA* shine cikkakken sunan shi sai abokan suna kiran shi *Bulama* kawai,
D'a ne ga papa wato *Barrister* Tahir Bulama asalin su mutanen barno ne tajahar meduguri aiki ne yakawo sa zaria,




Shidin kuma babban Lawyer ne me zaman kanshi shima d'an boko ne sosai saidai bashida ra'ayi irin na Dad,




Aminaine sosai shida Dad tun suna makaranta har yanzu, papa d'an sa kenan kwara daya wato *Buhari* wanda suka haifa tare da matar sa me suna Falmata.




*Blue* da *Bulama* suma aminan juna ne sosai tun suna yara tare sukai karatu tun daga primary har degree saidai shi *Bulama* law yayi a degree farko Wanda shima ya'ayin papa ne, domin duk suna San yaransu su gajesu sai degree na biyu shine yayi business administration shima ra'ayin sakenan,




Don haka kusan ra'ayinsu daya nason akidar boko shida *Blue* saidai halinsu yasha bambam, *Blue* ya kasance dan gaye miskili ne sosai ya'iya daukar wanka don haka yanada mutukar tsabta ga masifar kyankyami bakomai keyi masa ba,




yanada mugun high test yana kuma matukar kyamar zina shiyasa yake gudun yanmata don gudun afka mata, yayinda su kuma suke mugun son shi sosai suke bibiyar sa amma baya kulasu ko kad'an basa gaban sa.




Shima *Bulama* yana da tsabta sosai Dan gaye ne ya'iya daukar wanka kamar *Blue,* saidai shikam mutun ne me barkwanci sannan yana kula yanmata sosai shima yana kyamar zina saidai yana buga soyayyar shan minti da su, wannan kenan.



*Cigaba*
******
Su Dad kam basu tsaya ko'ina ba sai anguwar tudun jukum duk dacewa Dad shima yanada gida anguwar amma beyi nufin shigaba saidai kawai aka sauke su *Bulama* ,




Sannan yanufi gidan shi dake anguwar kwarbai suka nufa wani tsararran gida suka shiga bayan me gadi yabude masu get, bayan driver yabude masa kofa yafito direct yanufi cikin gidan yayinda escorts din sa sukabi shi abaya dauke da tarkacen *Blue*.




Masha'allah wani tsararran falo suka shiga wanda yasha blue and white din labule, gawasu manya manya set din kushin masu asalin kyau dasuka zagaye falon suma blue and white ne kai gaskiya falon ya tsaru wanda tsayawa fadin tsaruwasa bata lokacine,




Bayan escorts sun ajiye kayan sai suka fita yayinda Dad yashiga bedroom be dad'e ba yafiti sanye da jallabiya fara hannun sa dauke da wayoyi, wani table yanufa me dauke da manya manyan littafain,




zama yayi akan kujeran dake gaban talble din tare da ajiye wayoyi sannan yabude wani babban littafi,




Dai-dai lokacin da wani me aiki yashigo cikin girmamawa yaduk'a yace wlcm Sir....yace yauwa peter yace Sir u need something?..




yace no peter I want to be alone ok Sir" yajuya yafita dai-dai lokacin da daya daga cikin wayoyin sa tayi kara, ganin sunan daya bayyana akan wayar ne yasa yai murmurshi be dauka ba saidai yayi receive tare da bud'e kara,




Ajiyar zuciya akayi tukun kafin ace thank God Dad me yake faruwa ne tun d'azu nake kiran layin *Bil boy* be dauka ba kaima haka I hope dai lafiya?.




yace hum! Bebe ba lafiya, cikin tashin hankali tace oh! God Dad me yafaru?....nan yafad'a Mata abinda yafaru da *Blue*.




Kuka tasaki cikin tashin hankali tace Dad meya same shi haka?... yace I don't know saidai wata maganar banza inji Dr I B wai yana gani kamar aljanu ne suka "shafe sa, da sauri takatse shi dafad'in na Lia Dad don't trust, tsaki yayi yace is big lia makuwa so how can't I trust?..




cikin kuka sosai tace Dad yanzu meye abinyi?...yace sai "yafarka tukun munga yanayi jikin nasa tukun if bawani cigaba zanfita dashi waje, yanzuma zand'anyi wani bincike ne so karki damu ki kwantar da hankaliki everything will be ok,




tace ok Dad I will come tomorrow morning zanbiyo jirgi, ok sannan takashe waya shima ya'aji tasa tare da fara reseach.




*Abuja*
******
Ammu kam ta'isa Abuja lafiya cikin yardan Ubangiji direct gidan Kawu Muda tanufa dake garki, bayabo ba fallasa Safara'u ta tarbeta bayan sun gaisa sai tasa aka kawo mata ruwa da abinci saidai ba taciba saboda bakinta dauke yake da azumi,




Sannan Aunty Safara'u yaya Muda yana nan kuwa?....cikin had'e fuska tace lafiya murmurshi Ammu tayi tare da cewa lafiyar nazo ne akan maganar gadona, tsaki tayi tare dacewa wai ke Fatima meyasa bakigane karatun ne?....




tace aibazan taba ganewa ba muddun ba'abani hakkina ba, tace to yace bazaya bayar ba don haka sai kiyi hakuri amma kinnace sai kace maiyya, gaskiya kin takura wa rayuwar mu eheee! ta karesa fad'i tare da girgiza jiki,




Still murmushi Ammu ta sakeyi tace aikune kuka takurawa rayuwata dai-dai, lokacin da Kawu Muda yafito yanacin magani, zama yayi kuda Safara'u yana me ballawa Ammu harara cikin masifa yace wai hardama abinci ki kabata?..fuska tayamutse tare da fad'in eh badan halinta ba,




harara yasake watsama Ammu sannan yace malama lafiya?...tace lafiyar kenan nazone karban gadona don Allah yaya Muda kayiwa girman Allah kabani hakkina, wlh inacikin wani hali kasani "mijina bayada lafiya yau kimani shekara uku kenan, yarana sai sai korosu ake daga makaranta,
Yaud'in nanma suje ankoro su.




Cike da masifa yace to Ina ruwana da halin da ku keciki kuma mutu mana ba abinda yadameni, gado ne nace bazan bayar ba, don haka kitashi maza kibarmun gidana konayi maki mummuna rashin mutunci kinji ko?....




kuma kika sake tako kafarki ciki gidan nan narantse sai yani maki abinda harki mutu bazaki manta ba,




cikin tsananin mamaki ta kalle sa tare da cewa.....






Muje zuwa


*LUFHAT CE*โœ๐Ÿผ


๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ
๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ
๐ŸŽ๐ŸŽ
๐ŸŽ


๐ŸŽ *_ZAUJUN-MAJNUN_*๐ŸŽ
_(miji mahaukaci)_


๐ŸŽ
๐ŸŽ๐ŸŽ
๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ
๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ๐ŸŽ




Page9๏ธโƒฃto๐Ÿ”Ÿ


WRITTEN
By


๐ŸŽ *AMEENA UMAR FARUQ*๐ŸŽ


OR


๐ŸŽ *MEENAT*๐ŸŽ




Marubuciyar
*_DA SANNU_*
*_ZUCIYATA CE_*
*_AFSANA_*
*_KYAUTAR ALLAH CE_*
and now๐Ÿ‘‡๐Ÿฝ
*_ZAUJUN-MAJNUN_*




SADAUKARWA GA


*_My lovely blood sisters ๐Ÿ‘ฉโ€โคโ€๐Ÿ‘ฉHadiza (aunty)and Nana Firdausi out last bornnn, do u know what? sisters humm l really love love love yous irin babu adadin nan fa so muchhhhh love๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹๐Ÿ’‹._*




Littafin nan na kudi ne duk me bukatar zaya iya turo katin MTN ko AIRTEL na 200 a wannan 08161850024, idan kuma tresfa zakuyi duk zaku iya tuntuban layin sai abaku account no ba nagode.


_____________________________
ยฎ _PEN : WRITERS ASSOCIATION_
_______________________________
~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~




https://www.facebook.com/groups/1061983803858837/




*_FREE PAGE_*




โœ๐Ÿผ


_*Bismilahirrahamaniraheem!!!*_






Rarashin mutuncin ka kam aiba bakon abune agurina ba, kuma kasani bazan daina zuwa gidan ba har sai kabani hakkina,




Cike da masifa yace haka kikace ko?...eh ke! wai bakizuwa ki kwaci hakkin naki eye?..tace aidan kasan bazan iya kwata bane shiyasa kake kokarin danne mani hakkina Oho! to aisaiki kyale ni dashi, wlh bazan kyale kaba sai kabani hakkina.... to kira akwatar maki mana,




Murmushi tayi wanda yafi kuka ciwo sannan tace babu wanda zankira ya kwatar mani sai Allah wanda kullun nake kai masa kuka na, kuma nasan inshallah zaya sharemun hawaye ya kwatar mun.




Tsaki yayi tare da mikewa cikin b'acin rai me had'e da masifa kamar zaya rufeta da duka yace tashi ki barmun gida, konayi maki dukan tsiya yanzu na cike da mamaki tace dukafa kace yaya Muda?...eh ko kinfi karfin dukan ne ko kuma kina ganin bazan iya dukan ki ba?....




kaita girgiza yayinda idonta yacika da hawaye zuciyar ta cike da bakin ciki tace tabbas, ayanzu kam nawuce duka saidai agurin azzalumi irinka banwuce ba, cikin tsananin bala'i yace ke! Dan ubanki nine azzalumi?....




Itama cikin tsananin b'acin rai tamike tare da fad'in eh kaine azzalumi mugu macuc.....bata karasa ba yadauke ta da lafiyayyan mari, dasauri tarike kumatu tana me kallon shi cike da mamaki yayinda shi kuma sai hura hanci yake.




Yace wlh idan baki fita harkata ba sai nayi maki fiyeda haka, ke! abinda zanyi maki nan gabama sai
kinsha mamaki sai kinyi danasani sanina arayuwar ki, don haka fitarmun agida ko yanzu nasa afitar dake dakarfin tsiya....




Cikin kuka tadauki Jakarta sannan tace aiko bakace ba zanfita ne kuma Allah saiya saka mani akan zalunta tadakai, kuma wlh saina nadawo kabani hakkina kozaka kasheni oh! Ko ?..eh tafadi taname karasa kaiwa bakin kofar fita,




yace ok to muzuba dani da ke shege kafasa kisake dawowa din kiga abinda zanyi maki, sannan yanufi ciki rai b'ace yayinda Safara'u ta tashi tabishi tana cewa yauwa kayi mana magani me shegen nacin tsiya Mata saikace mayya.




******
Ammu kam datafita saida ta tsaya bakin get taci kuka takoshi wanda dama tasaba yin haka aduk lokacin da taje gurin Kawun Muda suka rabu baranbaran, yayinda dattijo Baba megadi yakeba ta hakuri cikin tausaya mata kamar koda yaushe idan tazo,




murmushi tayi me cike da bakin ciki sannan tamike tana goge hawaye da bayan hijab dinta, tare da cewa nagode Baba nizan tafi dasauri yace y'ata sake dawowa zakiyi?...tace eh Baba dole saina dawo, yace to ga wannan yafadi yanasa hannu acikin aljihun gabar rigar sa yaciro kudi nara dubu guda yace to yata karbi kikara kiyi kudin mota kinji?...




yakarasa cikin tausaya mata, shuru tayi tana kallon kudin tsawon lokaci tana tunanin itada yakamata tabashi sai shine zaya bata kai! yaya Muda yazalince ta kuma sai Allah yasaka mata yakwatar mata hakkin ta, cikin katse mata tunani yace karbi mana yata,




Murmushi tayi tare da duk'awa takarba tana fad'in nagode Baba Allah yasaka da alkhairi yabani ikon saka makada abinda kayi mun, yace bakomai Allah yayi maki albarka yashige maki gaba adukkan al'amuran ki yakuma albarkaci zuri'ar tace amin ki sauka lafiya to Sannan ta tafi taxi ta tare tare da fada mashi yakaita tasha.




Sai da yamma lis Ammu ta'isa zaria duk tagaji saboda azumin datake fauke dashi ga kuma gajiyar tafiyar mota, don haka agajiye tashiga gida duk su *Beena* suna tsakiyar falon zazzaune dasauri suka mike suna fad'i sannun dazuwa Ammu tace yauwa *Bash* yakarbi jakarta yayinda *Banu* taje ta rungumeta tare da fad'in Ammu danatashi bacci banganki ba,




Murmushi karfin hali tayi tare da fad'in gani nadawo my *Banu* kije gurin su Aunty kijirani bari naga "Abbun ku kinji?..kaita gyada tare da

Please Login or Register in order to submit comment