Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Ga number da za asame ni 08130269641 nagode Insha Allah*

Oum Muwaddah

3️⃣3️⃣

     "Ina binku dan ku nima mana mafita, amma kun gaza fahimtar haka. Idan nayi magana kuga kamar nafison kaina da ku, idan ta nine bazan damu na dawo k'asa ba, kune kuke da wutar fansa a ranki."
  
    "Afuwa Sultan."
   Bai kuma ce musu komai ba ya wuce inda wayar shi ke kara, d'aukar kiran yayi sannan ya zauna a kujeran da ya tashi, yace.
"Karki fara! Idan kuwa kika zo wallahi zan mugun sab'a miki, kiyi zamanki Ni zan zo nace miki"

    "Amma Ashuuu! "
  
"SAFINAH!!! Wallahi kar naga kafarki a jordan"
      Kashe wayar yayi cikin ɓacin rai, a ranshi yana fad'in.
*Su Mata Basu san damuwa ba, indai bata su bace*

     ★★★
Zuba mata ido suka yi har ta gama basu labarin abinda ya faru tsakanin Feener da Ashraf, dakatar da ita Malika tayi sannan ta nuna mata hanyar fita. Bin bayanta suka yi da idanun har tafi sannan suka kalli juna, tsuke fuska Malika tayi sannan tace.
"Wato baka jin maganata sai da na hanaka, shaye-shayen nan, amma kak'i ina gudun kar ka cutar da kanka sabida shi kuma duk ranar da aka gano haka sauke ka zasu yi, ka daina don Allah."

   Kwantar da kanshi yayi cikin sakalci yace.
"Ummana! Kiyi hakuri! Na daina"
 
Wato Bilal na mugun kaunar Mahaifiyarshi, sabida da ita ya Bud'e ido ya ganta, tasha wahalar rayuwa da shi, kuma shima ya sani. Idan akwai abinda ta tsana bai wucce yadda yake shaye-shaye ba, bata so bata kauna. Shi kuma ya gaggara rabuwa da haka.
"Bilal! Yau ma kasha wani abu."

         Girgiza kai yayi, dakyar ya bud'e bakin shi yace.
"Umma!!?"
   Dakatar da shi tayi cikin fusata tace.
"So kake zuciyata ta buga ko? Na hanaka shaye-shaye! Kaki ji ko? Toh shi kenan, ka cigaba idan kana ganin abinda nake gaya maka wasa ne."

   "Toh Umma na kiyi hakuri na daina daga yau"
 
    Fad'a tayi mishi sosai kamar zata rufe shi da duka, sannan ta mike tayi zata bar falon Jiri ya nemi kada ita, dole ta zauna shi kuma duk ya rikice.

           Dr Fu'ad ya sa aka dauko, yazo ya duba ta, sannan ya rubuta mata magani, sannan ya tafi.
     Tun bayan tafiyar likita Bilal ke ciki damuwa, taya zai daina shaye shaye, wanda a kuddin tsarin mulkin ƙasar, ya haramta wani basaraken shan abinda zai bugar dashi, sai gashi ya hau karagar kasar amma yafi kowa tu'ammali da miyagun kwayoyi, dan daga Mexico City, ake kawo min shi A sace.

          Lumshe idanun yayi cike da damuwa, mik'ewa yayi zuwa part d'in shi, hango bayanta yayi wanda yake bayyane sakamakon, rigar da tasaka, me budadd'yar  baya ce, gashinta kuwa har tsoro suka bashi, sabida tsayin su da kuma yawansu, dukda an kitse su, amma reton da jelar gashin keyi ya kara bashi mamaki, mutsika idanu yayi, yaga dagaske mutum ce, bai san lokacin da ya shiga bin bayanta ba, duk da mace bata gabanshi. Wannan me kama da aljanun tashiga cikin zuciyarshi, ta kuma rufe kofar bayan ta falffala d'an mukulin ta wurga a tekun dake kwarara, a birnin zuciyarshi. Ganin zata shiga wani lungu dake cikin masarautar yasa shi kara azama har ya cin mata, fincikota yayi.

         Suna fuskarta juna, saka hannunshi yayi ya cire kyalen da ta rufe fuskarta dashi, kura mata ido yayi ta kuma tafiya da imani shi, dukda shigar ta na gargajiya ce, amma haka bai hana Sandia kyau ba, karawa al'amarin armashi har da hujin hanci.
    Juyawa yayi zai bar gurin, cikin sauri tace.
"Ranka shi dad'e! Kana bukatar wani abu ne."

  Bai kulata ba yayi gaba abinshi dan yana cikin rud'ani, kuma yana son yin kodumo koda kwalba d'aya ce, dan ya same kwarin gwiwar tun karar wannan zukekiyar baiwarshi.

           ....... Yana shiga cikin part d'in shi, d'akin shi ya nufa inda ya rufe sannan ya ciro kwalaben kodumo,  yana gamawa ya ciro wayarshi a cikin aljuhun wandonshi, ya danna wasu number can yace.
"Turo min hoton shi da ita d'in."

        Cigaba yayi da shan giyarshi har wayarshi tayi kara. Dubawa yayi yaga abinda yake nima ya samu, jan laptop yayi sannan ya shiga tura sako, ta Tweet d'inshi bayan ya d'aura hoton Ashraf da SAFINAH, sannan ya rubuta da manyan harafi wanda yake da bak'in tawada yace.
*KUNCE MULKI NA, INA ZALIMCIN! SHI WANDA KUKE SO FASIKI NE! DAN KAN KARUWAR SHI YA AJIYE MUKU ƘASAR KU!*

          Sannan ya sake, cikin lokacin ƙalilan aka shiga yawo da sakon.
     Sake rubuta wasu kalman yayi wanda sukafi na farko muni.

*KAR MANTA ZUWA NA, AKA DAINA SAYO BAYI AKA DAINA CIN ZARAFIN SU, AMMA KUKE GANIN LAIFINA DAN NA HANA AYI RASHIN ADALCI, SANNAN MULKINA BAN KASHE MUTANE DA MULKIN ASHRAF YA KASHE BA, NI BAN KASANCE MAZINACINE BA! AMMA SHI FA!? WAYE YA BASHI DAMAR ZAMA DA MACE A CIKIN GIDAN SHI BA MUHARAMMAN JUNA BA, TABBAS IDANUNKU SUN RUFE DA MAKAHON SON, SHI DA AKA BASHI ZAB'E DA MULKIN DA MACE WANNE YA ZAB'E YACE MACE, MACE MA BAKA Y'AR AFRICAN, MARA DARAJA DA KIMA, SHINE KUKE KALUBLANTAR MULKINA, ZAN SAUKA NA BAR MUKU MUTUMIN BANZA DA KUKE SO*
   
   Sosai Bilal yayi magana tare da tare da nuna musu shi zai sauka baya jin komai a ranshi, amma suyiwa kansu adalci shi bai zalunci kowa ba, sai aikin gaskiyar da yayi niyyar aiwatarwa.
                 Yana gamawa ya rufe komai ya kwanta a gurin, yana jin shi a gajimare, tsabar iskanci yayi mishi karo.

         A cikin awa d'aya komai ya bazu a garin jordan, cikin da kewayen shi. Abinda ya haifar da cece kuce kenan. Take aka shiga muhawara me zafi da daukar hankali.

       Abu Zarri yakira Ashraf ya gaya mishi matsalar da ya kunno kai.
            Shiru yayi sannan yace.
"Ya samu nasara hakkarmu bata cima ruwa ba, kawai zan koma inda nafito."

"A'a Ashraf! D'azun na same wani labari me kyau kuma zai maka amfani dan Allah ne ya kawo mana mafita, sannan kai ma ka kara zage damtse, Insha Allah zamu yi nasara koda bazan kai labari ba, ina da yakinin kaine zaka kawo karshen komai, don Allah kayi mana wani abu, sannan."

              Karan harbi yaji wanda yasashi cewa.
"Abu Zarri!?"
Daga can yaji muryan Ukshe nacewa.
"Dama nasan kaine zaka kawo mana matsala, dan haka ku kashe min shi. Kai kuma Ashraf zan zo nasame ka har inda kake, duk wanda yake da saka hannu a dawowarks sai mun ga bayanshi."

           Kashe wayar Ashraf yayi yana kallon su Fahad, ya ce.
"Dole muyi wani abu, sun kashe Abu Zarri."

  Daga haka ya shige d'akin shi, suma zama suka yi zuciyarsu a dame.
          Wannan abinda Ashraf yake ba dan kanshi yake ba, sai dan dukkan su, amma sun gaza fahimtar haka, musamman Fahad. Amma yau da yaji yadda karan harbi yasa shi jin ba dad'i da bada goyon bayan akan aikin da Ashraf yake aiwatarwa. Ya kuma ji a ranshi tsayawa ka'in da na'in sai yaga abinda ya turewa buzu nad'i.

....
Wani sabon tashin hankalin shine watsa hoton Ashraf da laifin kisan Abu Zarri, abinda ya kuma d'aga hankalin mutane kenan, inda Bilal yayi rubutu kamar haka.

*Dama ba kunce ban iya ba! Toh gashi nan daga zuwan shi ya fara kashe manyan masu fad'a a ji, na masarautar. Wanda shi yake bashi goyan baya, toh ya kashe shi nima kuma yana niman tawa Rayuwar, duk wanda yayan shi ya sanar zai sami babban kyauta.*

A cikin kankanin lokaci, aka shiga niman Ashraf, cikin da Wajen kasar. Dole Ashraf ya cire layin shi, , domin sun fara bin diddigi shi, shima kuma tayu yana da hujjar shi na ajiye layin a gabaki daya, tunda abin kamar akwai makirci, oho.

★★★
Nigeria...

Ina cikin barci naji karan wayata, lallubar wayar nayi sannan na manna da kunne na, na fara magana.
"Waye."

Iska ya hura min, lumshe idanuna nayi, sannan na ware su akan Ablah. Nace,
"Ashu! Nifa zan zo.".
"A'ah Karki zo! Yanzun ma nakiraki ne, dan ki tayani da addu'a, sannan nima ina nan zuwa. Don Allah karki ce zaki zo."
Kashe kiran nayi dan muryanshi kawai ta tabbatar min da yana cikin damuwa, dan haka koda ya kuma kira ban d'aga ba na cigaba da barcina ina, dan wallahi ina d'agowa fad'a zamu yi sosai, zance zan zo shi zai hanani bayan kuma yana cikin damuwa, dan haka washi gari ban damu da na gayawa Ummi kudirin a ba, Passport d'ina na dauka tare da fidda jakata, Ummi tana part d'in Abba, na sulale na bar gidan. Daga Ni sai goyan baya na, na bar Aanih da Aamih, na fita daga gidan, sai da na hau Babban hanya sannan nasame motar da zata kai Ni, airport.

Duba kud'in cikin jakata nayi zata Isha Ni, har zuwa can murmushi nayi a raina nace.
"Zan zo naga halin da kake ciki ai"
★★★
Jordan.....

Yau ma ya fito gurin Mahaifiyarshi ya hangota, juyawa yayi yaga babu kowa a sha shin, cikin sauri ya cin mata, tare da riko hannunta suka wuce shashin sa, suna shiga yasaka hannun shi ya rungume ta, tare da lumshe idanunshi, can ƙasar makoshin sa, yace.
"Anjum!?"
A hanzarce ta kalle shi, sabida girman sunan da yakirata da shi, dukda bawani gama garin suna bane, amma lokaci d'aya ya kirata da Taurariyata!? Lallai Bilal ya fad'a tarko duk rashin yarda da kowa bai hana so ya mishi mugun kamu ba, kuma zata iya cewa ba so bane, sha'awa ce ta juya masa da tunani wata duniya na daban.
*Bayan daular Khalifanci da suka ja ragamar shugabancin Musulunci, na dogon lokaci. Kafin Daular Abbasiyya wanda suka kai da'awa har Spain, lokacin babu wata Daula me karfi a zamanin domin fitowar Abbasiyya daga dangi Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama, babu wata al'umma da tacisu yaki tayi nasara, dan haka sai yahudawa da Nasarawa suka dinga jin haushinsu, ganin haka sai suka shigo da mata cikin daular musulunci, musamman masarautun daulolin, inda aka shiga bad'ala, sosai har takai ana shagala a manta da addini ana aikata masha'a, da haka Kafirai suka samu damar karya karfin daulolin, sai ya zamana indai mace nada kyau toh da ita ake karya karfin duk wani wanda ya tsaya akan gaskiya, Zaku iya sauraron Kundin tarihi, fassarawa Malam Aminu Daurawa Kano, dan haka Akan yi amfani da mace dan karya karfin wani, ga misali akan Bilal cikin ruwan sanyin anyi amfani da kyan Sandia..... Hahaha wai India film na juya nake rubutawa,🤣😂🤭🙆🏽‍♀️ Allah na tuba ai ko basirar ta kare na nemo UmNass ta bani labari na rubuta,🤣 Wai ni book d'in da AMERICAN FILM KO INDIA NAKE KALLON YAYI KAMA, Yarinya zauna nan lokacin da muke hana idanunmu Barci kowa na barci, Ni ina makale a google ina bincike, akan jazziratul Arab, kina can kina zubda yawun barci 😂🤣 kai jama'a wai 150₦ ya yanke mana taulaci sorry dole sai anayi ana raha)

... Janye jikinta tayi daga nashi zata fita ya dawo da ita cikin, ya zaunar da ita, sannan ya rufe kofar part d'in, ya shiga cikin d'akin shi sai gashi dauke da kwalbar wine, zuwa yayi gaban ya ajiye, sannan ya koma ya dauko mata wani kwalba ya ajiye mata, tsabar bai yarda da kowa ba shi ko masu aiki yaki yarda a kawo mishi,(😂🤣 Shansha inji D'an gwari 😂😹🐪 Baban chinedu yace shansha shayin😹😂🤣)

Glass cup ya ajiye a kusada ita, da sauri ta mike, tana raba idanunta.
"Zauna mana Anjum!?"

Samun kanta tayi da zama, yaja cup ya zuba mata, juice d'in Grape, sannan ya mika mata. Ta sanin ba giya bane amma sabida ta nuna masa ita bata san komai akan kwalbar ba, tace.
"Ranka shi dad'e! Bana shan giya, kuma."

Mika mata yayi sannan yace.
"Ba giya bane! Taceccen ruwan inibi ne"
Amsa tayi cikin tsoro tasha taji babu komai, kad'an ta kara sannan ta ajiye, tare da mik'ewa.
"Haba!Anjum ki zauna mana ki min hira."

Zatayi magana wayar shi tayi kara ya tashi da sauri ya bar gurinta, tana ganin ya shige d'aki, cikin wani irin zafin nama, ta cilla wata kwaya a cikin kwalbar.
Sannan ta koma ta zauan tare da kallon kofar har ya fito, zama yayi kusada ita ya cigaba da kwankwad'ar barasar shi yana mata hira, har ya shanye tass. Sannan ya koma gefe ya kwanta akan cinyarta, yana cewa.
"A duniya ban yarda da kowa ba! Sai Ummata, sai ke kuma yau zan nuna miki yadda nake sonki."
A hankali yayita mata tambele, har yakai hannun shi cikin rigarta, tayi maza ta buge hannun shi tayi. Da sauri ya buɗe idanunshi, cike da mamaki shine yau mace ta bugewa hannu, ganin irin kallon da yake mata yasata fashewa da kuka tana cewa, kayi hakuri, bansan zaka ji haushi ba, bazan kuma ba.

Komawa yayi cikin shirme yace.
"Karki damu! Ni ba haushi nayi ba, nayi mamaki ne, ai ko me kika min bazan ji haushi ba, sabida ina kaunarki. Har cikin zuciyata, kuma zan Mallaka miki komai, idan kika amince da soyayyata."

Fari tayiwa Sha-sha-shan tuni ya sussuce, dama kuma giya na dawainiyya dashi, tuni ya gigice, ya shiga sumbatar fuskarta, dakyar tasamu ya bingire sai barci.

Nannah ta zaro wayata tashiga aikin da ya kawo ta.

(Har yanzun, U.S.A, CANADA, FRANCE,UNITED KINGDOM, suna aiki da mace domin kamo me laifi, ko kuma kashe wani fitacce, karamin misali Yasir Arfat. Shine shugaban Palastinu, wanda Yahudawa suka bada guba aka kashe shi a wani hotel, ta hanyar mace, na manta labarin but an tabbatar matar sa Bayahudiya itace ta ciyar da shi gubar.)

Dan haka karku yi mamaki da abinda Ashraf yasa Sandia ta mishi. Yana gamawa ta turawa Ashraf sakon video.

Tana tura mishi shi ta goge na kan wayar ta, ya rufe gidan. Yana zaune har ya tashi, kallon shi tayi cikin murmushi tace.
"Har ka tashi!"

Shima mai da mata martanin murmushin, sannan yace.
"Na barki kina ta gadina"

"Ai kafi ƙarfin komai a gurina, koda kuwa rayuwata kanima zan baka, amma ina Son komawa gidan."

Riko hannunta yayi sannan yace.
"Kina abu kamar wanda kike tare da dodo, saki jikinki babu abinda zan miki."

Gyad'a mishi kai tayi, sannan ya mik'e yana tangad'i ya wucce d'akin shi.

★★★

Mun fara biyawa ta Ehtophia ne, a babban birnin su Adis Ababa, sannan muka kuma ɗaukar hanya, sai jordan.

Mun isa da karfe daya na rana, sai jaraba layin shi nake ban samu ba.

Wasu mutane naga sunata kallona, wani ya dauki wayar shi ya duba sannan ya kare min kallo.
Can ina cikin jaraba layin shi, sai ga wasu mutane, sun zo kallo d'aya na musu zuciyata ta kusan bugawa.

"Kinzo gurin Sultan Ashraf ne!?"

"Eh! Shi ya aikoku!?"
Gyad'a min kai sukayi sannan d'aya ya ɗauki jakata, d'aya ya amshi Ablah.

★★★
Jikinshi ne yake ji wani iri, kamar wanda yake tare da ita, kallon Ghaniyu yayi cikin nutsuwa sannan yace.
"Jikina na bani, SAFINAH ta shigo Jordan kuma"

Bai kai karshen maganar ba wayar Ghaniyu tayi kara. Ɗauka yayi aka ce mishi.
"Ka bashi"
Mikawa Ashraf wayar yayi sannan aka ce.
"Ka mik'a kanka, ko kuma matar da Yar Me suna Ablah, a same gawarsu."

Kirjinshi ne yayi masa nauyi kamar wanda aka daurawa dutse akai idanun shi sukayi wani irin Jaa a hankali kwalla suka shiga tsatsafowa daga cikin idanunshi bakin ciki da takaici yasa shi sake murmushin dole yace.
"Ku tamb........




number da xaku mata magana idan kuna son Book ɗin Wanda yake a 500fs  +227 96 51 58 05 Maman Fareesah*
   *Ga masu son biyan Book 2-3 zasu iya turo kuɗinsu sai nasakasu a Paid grp idan ta bank ne 150₦ ne idan kuma Kati ne Transfer 200₦ ne, Mtn, ga number bankinaAcct: 0472282105...*
*Gtbnk Ramlat Abdulrahman Manga. Ga number da za asame ni 08130269641 nagode Insha Allah*

Oum Muwaddah

3️⃣4️⃣

"Ehtoh ta gaya maka gaskiya, Ni na jima da rabuwa da ita, sannan bani da wata alaƙa da ita, hmm toh bayan haka duk abinda kuka gadama ku mata."

           Yana gama fad'ar ya datse kiran tare da kashe wayar baki d'aya ya kalli su Ghaniyu.

"Fahad! Ka kira Sandia! Ka bata Passport d'inta, yau tabar jordan. Ta gama aikinta, Amma tasan yadda zata fito mana da katin gayyata, dan Yau Insha Allah zan fara aikina."

      Ganin yadda bai damu da halin da SAFINAH ke ciki bane yasa Ghaniyu yayi mishi magana, yace.
"Sultan! Kamanta jaririyar."

    Har ya isa bakin kofa ya tsaya cak, sannan yace.
"Domin samun Farin ciki wasu, dole ka sadaukar da taka farin cikin, dan haka idan ya kuma kira kace ya kashe su."

   "Sultan,!!"
Suka ambaci sunansa da karfi, ko a jikin shi, yayi tafiyar shi ya barsu da mamaki.
      Yana shiga d'akin ya zub'e a gado, zugi yake ji a ranshi. Shi kad'ai yasan yadda yake ji, domin kuwa ji yaƙe kamar ana  hura min shi wuta a ranshi.

     Duk kewarta da yake sai da yaji tafita kanshi dukda, yasan dole sai ta shigo cikin wasan amma tayi mishi shiga sauri, bai so haka ba. Yaso shi da kanshi zai dauko ta.
      
Jin muryan Sandia a gidan yashi mik'ewa da sauri ya fita.

Yana fitowa ya buɗe mata hannu, da gudu ta shiga tana dariya.
"Alhamdulillah! Sultan komai ya tafi yadda ka shirya min, kuma ya baki katin gayyatar, sai dai don Allah kar a cutar da shi, dan bayan umman shi nice mutum na biyu da ya yarda da ita, idan aka  cutar dashi zai zama bashi da wanda ya yarda dashi."

  "Sandia!"
Fahad ya daka mata tsawa, cikin Kishi. Juyawa tayi tare da isa gare shi. Tana murmushi sannan tace.
"Fahad! Tabbas nice nake sonka! Amma ko sau d'aya baka tab'a bud'e min zuciyarka ba, ka gashi kuwa daga gani na, ya bud'e min zuciyarshi. Kasan me yasa saboda shi yake sona, kai kuma nice nake sonka. Namijin da zai gaya maka gaskiyar shi, ba tare da yayi tunanin waye kai ba shine abokin rayuwa, duk da nasan Sultan Bilal yana gab da rasa mulkin shi, a shirye nake na karasa rayuwata dashi, don Allah kayi hakuri, bai Fika da komai ba sai da kulawar da ya nuna mine, Nagode sosai, Sultan ga katin bazan je ko ina ba, zan zauna a tare dashi. Har me faru ya faru,"

              Kura mata ido Ashraf yayi, cikin damuwa yace.
"Idan kuma aka kashe shi fa"

   A sanyayye ta isa gaban shi, cikin tsantsar kaskantar da kai tace.
"Sultan d'in mu! Mutumin kirki ne me rama Alkhairi a bayan sharri, mutum ne da yasan darajar soyayya, sannan masani ne. Akan hakkin al'ummar shi, idan ya kyaleshi yayi tafiyar shi har abada Sultan Bilal ba zai daina d'aga darajar shi ba, ko halin da ake ciki wasu ne suke kaiwa da komowa, da kuma rashin abokiyar hira, shawara da abokiyar rayuwa, ya taso bai san kowa ba, sai Mahaifiyarshi, dole yayi rayuwa irinta wanda bai san meye yake ba, idan Sultan bai manta ba shima yayi dogon rayuwa babu iyayen! Afuwa."

   Daga haka ta juya tare da barin gidan, sai a lokacin ta samu kwalla ya zubo mata, tabbas ta fad'a son Bilal ba tare da ta ankara ba, tayi dana sanin zuwa wannan aikin, koda ta isa gida zama tayi a d'akinta tayi, ta fashe da kuka, sai da tayi me isarta sannan ta tashiga wanka dan yau Masarautar zasu yi bikin zagayowar ranar haihuwa Bilal d'in.
           ★★★
Watsa min ruwan sanyi suka yi wanda ya sani sake ajiyar zuciya, me mugun ƙarfi, a hankali na fara tuno abinda ya faru.

Bayan mun fita daga tashar jirgin saman, abinda na sani, na shiga motar da aka kawo, daga nan ban kuma sanin abinda ya faru ba, sai yanzun. 

  Kallon kartin dake kaina nayi cikin tsoro tare da fargaban abinda zai iya faruwa ba dan yadda na gansu suna muzurai da ido nayi imani cinye Ni zasu.

      Ƙarar bud'e kofa muka ji, na d'ago kaina. Turo keken akayi suka shigo su biyu.
  
Had'iye yawun tsoro nayi, cikin tashin hankali, sunkuyar da kaina nayi sabida irin kallon da Ukshe ke min ta k'iyayya ce, da tsana.
        Cikowa kwalla sukayi ban san zan fad'a cikin wannan tashin hankalin ba da ban zo ba, gashi na kawo kaina cikin tashin hankali da Bala'i, kuka ne ya kwace min, kauuuuu naji kunne da gefen fuskana sun daina aiki na hucin gadi. Sake kifa min wani marin suka yi na fad'i daga kujeran, Ukshe ya ce.

"Bilal! Kasata tayi magana, dan wancan mara mutuncin ba bayyana zai yi ta dad'i ba."

     D'ago ni Bilal yasa aka yi, sannan ya koma inda Ablah keta sharar barci, ya d'auketa. Kyau tayi mishi cikin kaya dark purple.

          Duk na firgita da juya yarinyar da yaƙe.
"Ku kira min shi."
    Har suka kira shi da abinda suka yi da shi ina jinsi, kuka nake sosai dan nasan na kad'e har buzuna.

       Mika musu yarinyar yayi sannan ya dawo gaba na ya zauna.
"Kin daiji da kunnenki! Yace kun jima da rabuwa, shin da gaske ne."

Kallonshi nayi idanuna cike da kwalla nace.
"Eh!"
Nayi haka ne dan kare kimarta shi, dan ba dad'i na karyata shi.

     "Yana gana kana mata sanya ne!?"

Ukshe ya tambayi Bilal, d'aga mishi hannu yayi, sannan yace.
"Ku shigo min da dr Fu'ad"

        Can ya shigo, ya kalleni sannan ya min allura, tattara kayan shi yayi. Sannan ya yi wa bilal bayani, yana gama mishi bayani ya fita.

            Bayan wasu mintina, marin fuskana Bilal yayi sannan.
"Meye alakar dake tsakanin ku da Ashraf!?"
  A buge na d'ago kaina, dakyar nace.
"Mijina!?"

     Shiru duk wajen ya dauka, sake Mari na yayi sannan yace.
"Kafin aure kun tab'a wani mu'amala!?"

    Girgiza kai nayi, sannan na fara magana.
"Shekarun baya mun sami Y'ar matsala, a lokacin yana fama da lalurar hauka."
   Nan na gaya mishi yadda komai ya faru, sannan na cigaba da cewa.
"Lokacin da Alhaji Nuhu yazo zai aureni, Ni kuma bana son shi, shine Ashraf ya bani shawarar na zo gurin shi, a d'aura mana aure,  Ghaniyu ya wakilci shi, Ni kuma Imam d'in masallacin ya wakilci iyayena, kuma aka d'aura auren dan haka bana tunani, Ashraf zai aikata mugu..."
  Daga nan dai na dauke wuta, na shiga barcin bugawa.
   
   "Bilal"

.         " Toh tunda yace basa tare mu kashe su mana."

    Wani irin kallon Bilal yayi mishi, sannan ya mike tare da barin, d'akin har ya isa bakin kofa.
"Kar wani abu yasame uwar da yar."

    "Toh."

Sai da Ukshe ya tabbatar da yaji karar motar Bilal sannan ya, yace.
"Ku saka ruwan kankara ku zuba mata har sai ta farka, sannan Yarinyar kuma, itama a tsomata cikin ruwan"

             "Toh"
   Suka amsa mishi sannan ya fita shima, sannan suka shiga aikinsu, akan jaririyar ce suka kasa yin komai, sai tausayinta ya kama su, Ni kuma suka shiga cin Ubana. Ƙamar Allah ya aiko su.

         ★★★
Jiki a mace Sandia take shiryawata, kayan da Bilal ya bata ne, mermaid gown tasaka kalar golder, sai Whiter gold wanda akayi mix d'inshi da diamon, light makeup tayi sannan ta fito daga gidan su, ta samu

Please Login or Register in order to submit comment