Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

babu irinsa a rayuwa. Rahane ta kasa kuka sai addu’a take cikin zuciyarta ita ma Allah ya dau ranta ta bi iyayenta da Iya ta huta.
Yanzu kam ta tabbata ta zama marainiyar gaba da baya. Da dai-dai da dai-dai Allah ya yi ikonsa a kan wadanda ya bata su zame mata garkuwa a rayuwa, kuma bango abin jingina.
Shi kenan kuma ita yanzu ba ta da kowa! Idan Baba Dacta da iyalinshi suka gaji da rikonta ina za ta je?
...........“Sai dai kuma da na yi wani tunani sai na ga cewa kina da Uba makwafi na, wato Likita Mansur.....”
Ta tuno kalaman Mal. Rashidu masu kama da wasiyya. Ashe hirar karshe ce Baba, kaicona da na katseka!!!
A wannan lokacin ne ta samu hawaye suka zubo, ba tare da ta san suna kwarara ba sai ta ji an sa tissue ana share mata.
Ta juyo kadan sai ta ga Jawahir, ita ma kukan take tayata. Ta ce, “Rayha ki yi hakuri, Baba kwananshi ne ya kare, kin sani ko muma zamu iya mutuwa a kowanne lokaci. Addu’a za ki yi mishi. Rayuwa yanzu kika fara ta Rayhanah, ko ba iyaye za ka rayu idan haka Allah ya tsara maka.
Belle ke kin rayu da Baba, ya yi miki tarbiyya, ya baki ilimi dai-dai karfinsa. Sannan bai barki a hannun da za ki wulakanta ba.
Rayha ki daure ki tashi mu ci gaba da fafutukar rayuwa, darussa za su wuce ki, alhalin Allah bai nufa rayuwarki ta zo karshe ba.
Ina miki ta’aziyyah Raihanah, Allah ya ji kan Baba, ya ji kansa ya yi masa rahama, yasa Aljannah ce makomarsa, ya sanya mana dangana”.

Kwanaki bakwai da suka biyo baya, aka yi sadakar bakwan Mal. Rashidu. A cikin wadannan kwanakin, kwana biyu kacal ta yi a gida, ragowar a gadon asibiti.
Tuni Khalipha ya koma bakin aikinshi cike da alhinin RAYUWAR RAYHANAH!. Ga nakasa ga hawan jini, sannan ga maraiaci na uwa da uba da rashin dangi. Tausayi ba zai barshi ya ci gaba da ganin Rayha cikin wannan halin ba.
Ta rame kwarai, ita dama shiru-shiru jiki ba jiki ba, yanzu abin ya koma daga eh, sai a’a. Sai da Baba Dacta yasa aka soma rubuce mata Alkur’ani tana sha tsayin sati biyu.
Hatta Abida ta rage rashin mutuncin ta don ganin Rayhan, a yanzu kam wani dan Adam bai da abin da zai bata mata rai da shi, ko yankata za ta yi ba za ta daga ido ta kalleta ba balle ta san tana yi. Tunda ta jure rabuwa da Iya da Baba, to mene ne ma ba za ta iya jure shi a rayuwar duniya ba? Duniya ta fita a kanta sai fatan cikawa da imani.
Sati biyu bayan nan suka koma makaranta suka soma shirin zana jarrabawar shiga aji shida. Rahane kam ba fus, sakamako bai yi kyau ba. Sun ba ta maimaicin shekara guda (repeating), yayin da su Abida suka shige aji shida suka barta a aji biyar.
Amma maimakon Baba Dacta ya yi fada kamar yadda suka zata, sai ya ce “Rayhanatu a hakan ma kin yi kokari, Allah ya yi miki mai kyau a duniya, mai kyau a lahira a dalilin juriyar ki kan kaddarorin ki da kyawawan halayenki”.
Sati biyu Khalipha bai zo gida ba, ba don komi ba sai don baya son abin da ke zuciyarshi a kan Rayhanah ya fito sarari. Ya zo wani limit da ba zai iya boye soyayyarta ba zuciyar ba za ta iya basarwa ba.
In kuma har ya yi kokari ya boye din, to za ka iya karantar hakan cikin kwayar idanunsa cewa yana so.........kuma yana tausayin Rayhanah.
Haka nan ya samu kansa da wani sabon tunani, wato ya kai Rahane waje, masu jajayen kunnuwa su duba lalurarta. Babu cutar da ba ta da magani. Likitocinmu ba finsu kwarewa aka yi ba, kayan aiki ne bamu dasu kamar sauran kasashen da suka ci gaba.
Daga fara aikin shi zuwa yanzu yasan yanada account mai nauyi don bashi da almubazzaranci kuma babu nauyin kowa a kansa. In ma ya kakare ya tabbata Baba Dacta zai agaza masa in ya gaya masa kudurin sa.
To amma Rayhah ta balaga, shekarunta goma sha shida ya za ayi Baba Dacta ya yarda su tafi wata uwa duniya tare? Duk da neman magani ne?
Wata zuciyar ta ce, “To ka fito fili mana ka sanar da Daddy kana sonta ya aura maka ka tallafi rayuwarta da taka? In ta zama matarka shikenan babu sauran shinge. To amma anya ba ta yi kankanta ba? Ya tabbata ko Daddy giyar wake ya sha ba zai aurar da Rayha a wadannan kananun shekarun ba. Don haka furtawar ma bata da amfani.
Da ya kwashi wata daya bai zo gida ba, kewarshi ta damu al’ummar gidan, kada Azizh ta ji labari. Duk sanda Mami ta kira wayarshi sai ta jita a kashe, haka in ta yi amfani da social network baya responding.
Zuciyar UWA! Ba irin tunanin da ba ta yi ba. A yau dai ta kasa daurewa ta samu Daddy da zancen.
Ya ce, “Lafiya ita ke buya Asma’u, amma ba rashinta ba”.
Duk da haka ta kasa sukuni, a ranar Alhamis Daddy ya daga kasar Ireland domin halartar taron “Old Students Alumni of Trinity University”. Kwananshi daya da tafiya ta dauki hanyar Abuja ita kadai a motarta, tana tafe tana zancen zuci.

Khalipha na kwance cikin leather seat din falonsa bakake, a gabansa ash-tray ne na silver wanda ke cike taf da guntattakin Marlboro, a wannan lokacin ma abin da yake ta yi kenan, wato gajimare da hayaki.
Ya yi baki ya bar kasumba ta cika masa fuska, wannan kwantaccen gashin nasa duk ya kanannade saboda rashin gyara. Falon kaca-kaca ga kuma kura da kayan wuta suka yi, don ya hana yaronsa Jibril shigo masa daki balle ya gyara masa sai idan shi ya kira shi a waya ya sayo masa abinci.
Kararrawar shigowa falon ta yi kara, ta yi ta sake yi yana kwance bai motsa ba. A zatonsa Jibril ne alhalin ya san ya hana shi zuwa inda yake in ba shi ya kira shi ba. Farar singilet ce a jikinshi da dogon bakin wandon DKNY.
A fusace ya mike ya bude don ya yi masa marin da uwarsa bata taba yi masa ba. Amma sai ya yi tozali da tashi uwar wacce ko cikin mafarkinsa bai zaci ganinta a nan ba.
Kallon shi kawai Mami ke yi, bayan mintuna uku ta bi gefenshi ta shige falon ba tare da ya bata damar hakan ba.
Sai ta fara kiran ‘Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un....... smoking ABDALLAH???”
Sai ta zube cikin kujera ta saka mishi kuka.
Jikinsa ya yi bala’in yin sanyi, ya zube a gabanta ya kwantar da kai a cinyoyinta cikin matsanancin tashin hankali; mahaifiyarsa na zub da hawaye a dalilinsa.
Ta kara dago ido ta dube shi, “Ashe addicted ka zama? Shi yasa baka nemanmu? Abdallah tun yaushe kake shaye-shaye ban sani ba? Me ya kawo ni ganin wannan bakin cikin? Me ya kawo ni, ni Asma’u???”
Sai ta mike za ta fice idanunta jage-jage da hawaye. Da hanzarin gaske ya cimmata ya rungume kafafunta.
“Wallahi Mami ki yarda dani, ban taba shan abin da zai fitar dani daga hankalina ba. Mami damuwa ce bana cikin sukunin da zan iya sarrafa kaina. Ina sha ne kurum don ta rage min damuwa. Marlboro ce kawai, wallahi Mami idan na taba shan wani abu bayan ita, Allah ya yi miki sakayya a kan tarbiyyar da kika bani”.
Ta tsaya da kukan, ta shiga nazarin falon baki dayansa cikin bakin-ciki marar misali, ta ce, “Mene ne haka? Me zan gani haka? Kazami kuma ka koma? Me kake yi yau a gida ranar aiki baka je office ba?”
Bai bata amsa ba, don bai san me zai ce mata ba.
Ta girgiza kai ta ce “ai Shi kenan, ni zan tafi, dama na zo in duba lafiyarka ne. Don na san haka kawai ba za ka ki gaishemu ba. To na gani lafiyarka kalau bamu isa bane kawai mu ji damuwar taka ka gwammace ka lalata rayuwarka”.
Da hanzari ta fita, bata barshi ya yi wani furuci ba. Kayan dake jikinsa kuwa ba za su barshi ya bita ba. Ko hutawa bata yi ba, ko ruwa ba ta sha ba ta dauko hanyar Kano.
Allah ne kawai ya kawo Mami gida, amma ba nutsuwar zuciya ba. Wai Dan da ta haifa ne yake shan taba bata taba sani ba. Ko tun tsahon yaushe yake sha?
Duk tsantseninta a kan ‘ya’yanta, duk jansu da take a jikinta don su zama abokan rayuwarta, a yau Khalipha ya nuna mata aikin banza take, ya nuna mata yana da wata damuwar da ba ta isa ya gaya mata ba, ya gwammace ya mutu a cikinta.
Da asubahin ranar ta ji Malam Dahiru ya bude get, ta daga labulen dakinta tana kallon shigowar motarshi, wannan ya tabbatar mata tafiyar dare yayo, sai ta ji tausayi ya tsirga a zuciyarta.
Har ya fito daga motar ya rufe ya ratayo bakar jakarshi ya shigo reception tana kallon shi. Ta koma bakin gadonta ta zauna, ko minti biyu ba ta yi da zama ba ta tsinkayi sassanyar sallamar sa a kofar dakinta. Babu kuzari sam a jikinta ta ce,
“Yes, come in”.
A yadda ya shigo din cikin kayan da ta baro shi ne, bakar rigar sanyi kawai ya dora a kai wadda ta iso har gwiwarsa, bakin glass da bakin cover takalmi.
Sai ta nuna mishi toilet dinta, tana daga zaune “Go take a wudu’ (alwala), a brush, a shave and a shower, then come to me….”. (Shiga ka yi wanka, ka yi brush, ka yi alwala, ka yi aski sannan ka zo gareni).
Maimakon ya shiga nata toilet din sai ya juya nashi dakin ya bi umarninta.

Ya idar da sallah ya yi addu’o’i masu yawa, yana rokon Allah yasa Mami ta fahimci ba shi ya dorawa kanshi damuwar ba, Allah ne ya dora mishi.
Sannan ba shi da karfin zuciyar da zai sarrafata ko ya boyeta. Su kuma ba za su iya yi masa maganinta a wannan lokacin ba. Don haka ba zai iya fada mata ba, don fadar bazata yi wani amfani ba.
Mami ta ji shiru-shiru Khalipha bai fito ba. Ta kasa hakuri ta biyo bayanshi har dakin nasu.
A lokacin shi yana shirya abin da zai gaya mata ne don ba zai iya gaya mata gaskiya yanzu ba. Ya san Mami da boko kamar Ibraheem, cewa za suyi Rayhanah ba ta isa aure ba ko su kushe zabin nasa. Ko suce ‘child abuse’.
Don haka tuni ya tattara abin da zai gaya mata. Dai-dai lokacin da ta zauna gefen ‘sofa’ dinsa. Ya shafa addu’a ya ce, “Mami kin zo lafiya?” Ta ce, “Da ban zo lafiyar ba za ka ganni ne har dakinka da kafafuna eyi?”
Ya yi murmushi, “Mami kin tayar min da hankali Allah, da baki tsaya kin ji uzirina ba balle damuwar dake damun nawa. Mami in kika yi fushi dani ina zan sa raina? Jahannama fa Mami, babu ni babu jin kamshin Aljannah. Mami don Allah kar ki kara yin fushi dani, kin ji Mami?”
Jikinta ya yi sanyi kalau, ta ce, “Mene ne ke damun naka?”
Ya ce, “Mami SOYAYYAH!”
Sai ta yi murmushi ta ce, “Alhakin Hibba ne, wace mai tsautsayin ce again?”
Ya ce, “Mami ban sameta ba, an kasa ni”.
Ta kara yin murmushin ta ce, “Ba ita kadai ce diya mace a duniya ba, Allah yasa hakan ya zama mafi alkhairi. Wani zubin in Allah ya tsara abu, sai ka ga na gaban ya fiye maka amfani. Ni tuni ai na yi maka mata Khalipha, jira nake ka zamo settled tukunna kafin in gabatar maka da zancen”.
Cikin Halifa ya karta ya bala’in kadawa. Da sauri ya ce, “Um-um Mami, bar zuciya da abin da take so. Har yau din dai da nake gaya miki ban fidda rai da samunta ba. Wani sanadi zai iya zuwa idan har matata ce Allah ya bani in aureta. Tunda an ce matar mutum kabarinsa”.
“Ya ya sunanta? A ina take Dattijo? Su waye iyayenta?”
Ya ce, “Mami tunda a yanzun bani da damar aurenta sanin wadannan amsoshin ba zai amfaneki da komai ba”.
Cikin rashin damuwa da lamarin ta mike tana fadin, “Toh! Allah ya maganta maka, ni na dauka wani muhimmin al’amari ne, zancen Radhiyyah kuwa na baka sati har biyu ka yi tunani a kai”.
A cunkushe da zancen ya ce, “Radhiyyah kuma? Gaskiya Mami bana son ki sa ranki ga abin da ba zai yiwu ba. Matakin iliminta ya wuce wanda nake so a macen da zan aura kafin in aure ta. Nafison duk wani ilmi da mace zata yi bayan sakandire tayi shi a gida na. Kuma da kadan na girmeta, in zan iya tunawa shekara uku na bata.
Haba Mami, ai an dena irin wannan hadin auren yanzu a kauye ma ba a birni ba, gaskiya ta min tsufa.
A perception dinki ban zaci akwai irin wannan tunanin ba, na abubuwan da aka yi a can wani karni can da ya shude. Na soyayyar ma yaya aka kare da shi balle na hadi?
Ki barni kawai in na samu wadda za ta maye min gurbinta da kaina zan gaya miki. Amma don Allah Mami kada ki kara daga maganar nan, kada zumuncin da ke tsakaninku da Mamanta ya lalace a kan abin da ba zai yiwu ba”.
Cikin mamaki Mami ta ce, “Ni kake cewa haka Dattijo?”
Da sauri ya gyara kuskurensa da cewa, “Ba nufina baki da iko a kai bane Mami, kawai ina gaya miki abin da zuciyata ke gaya min a kan maganar. Ki yi hakuri idan kalamaina sun bata miki rai, I’m sorry Mamee! Ki yi hakuri don Allah”.
Ta yi ajiyar zuciya sannan ta fita. Allah kadai ya san abin da take sakawa da warwarewa a zuciyar nan tata. Mami na son ‘ya’yanta matuka, tana kishinsu irin kishin nan mara amfani, wanda ya kimsa mata tunanin cewa da akidar cewa ba za ta bari su auri wadanda suke mutuwar so ba, sai wadanda ke son su, don kar su rabata da su.
Irin ‘yan’uwansu su Hibbah, Nabila da Radhiyyah diyar aminiyarta Dacta Halima wadda ta ki auren minister saboda mahaukaciyar soyayyar da take yiwa Khalipha.
Mami na da wannan kudurin cikin ranta tuni, wanda kuma take da yakinin ko za ta yi yawo tsirara ne sai ta cika shi. Saboda masifar son da take wa ‘ya’yanta.

****


ASabar, biyar ga watan Yuli, rana ce ta ziyarar ‘yan makarantar kwana. Khalipha na tsaka da aiki a Office kiran Mami ya shigo wayarsa. Ya dakatar da komai ya daga ya fara gaisheta.
A gurguje ta amsa tare da cewa, “An zabe ni zuwa karbar (Award of the best paediatrician of Africa) a kasar Djbouti zamu tafi har Daddy gobe insha Allahu, so ba zamu samu zuwa ma yara visiting Katsina ba, shine na ce ko za ka samu sararin lekasu can Katsina tunda ba ranar aiki ba ce?”
Khalipha ji ya yi kamar yana yawo a kan gajimare dan dadi. Ga dama ta samu ta ganin Rayhanah wadda yau sati shida kenan bai dora ido a kanta ba, ba da tsimi ko dabararsa ba.
Domin dai Mami ba ta taba cewa yaje musu visiting ba, shi bama ya sanin yaushe ake yi sai dai Mamin ta ba shi labarin cewa yara suna gaishe shi.
Amma sai ya dan danne farin cikinsa ya ce, “O,k, to ba matsala Mami zan yi kokari in gani ko zan samu zuwan in b azan je gida ba, Congratulations Mami! Safe journey........”
Suna murmushi dukkansu suka aje wayar lokaci guda.
Aikin da ke gabansa kasa karasashi ya yi, ya hada komai ya rufe ya aje ya mike ya nufi gida.
Washe gari ranar ta kama Juma’a, bayan ya fito daga sallar Juma’a ya nufi Sahad ya soma shopping. Ba kayan ci kadai ba, har da na amfani. Wani irin Shopping yake yi kamar ba sai ya yi losing energy dinsa da lokacinsa ake ba shi kudin ba.
Sai dai kuma kayan abinci ne ya sayi komai na mutum uku, sauran kayan amfani kuwa sitturu nena sanyawa a gida ko makaranta designers ‘yan gidan versace da channel hade da dogayen riguna kala-kala da tafi amfani dasu.
Kayan shafa na Avon da coesmetics, deo-sprays duka ‘yan gidan Avon. Ya ma manta a makaranta take. Shi kansa bai san adadin kudin da yake kashewa ba, burinsa kawai Rahane ta koma irin yadda yake son ganin matarsa.
Filin makarantar ya cika ya batse da motoci da jama’a. Ba tun yau ba, tsarin Ulul-Abaab ke burge Khalipha ba. Jama’a makil kowa nasa yake nema, sai manya-manyan coolers kawai ake saukewa da katan-katan na kayan abinci da abin sha.
Lokacin da Khalipha ya iso karfe goma sha biyu dai-dai, tunanin Khalipha shine cikin wannan bataliyar al’umma ina zai je ya nemo ‘yan kannen nashi?
Don haka ne kawai ya fito daga mota ya jingina jikin kofar direba ya harde hannayenshi a kirji, don bai san ma wa zai tambaya ya nemo mishi su ba.
Sanye yake da shaddah getzner baka kar da bakar hula kalar shaddar dinkin Mohammed. Khalipha fari ne sol mai wata irin fata jawur da ta fi kama da ta mutanen Hurghada (Middle East). Hasken fatarshi ne kadai yasa ake danganta shi da Mami amma ba kamanni ba, domin ya fita kyau nesa ba kusa ba, musamman kanannadaddiyar sumar kanshi. Haka yake kamar ruwa biyu.
Kamar an ce da Khalipha juya, ya karyar da kai ya juya wani sashe daban. Rayhanah ce zaune a gindin wata bishiyar lemon tsami mai karancin jama’a ta yi tagumi da hannuwanta biyu, ko me take tunani? Allah masani.
Sanye take cikin uniform dinsu na daliban Ulul-Albaab da gajeren farin hijabi iya kafadunta. A idanun Khalipha har tsayi da zati ta kara. Duk wasu alamu na cikar budurci sun bayyana a jikinta. Kirar jiki dirarre wanda bai da alaka da kiba, cin kitse (cholestrol) ko over-eating duka babu su a jikinta. Da ganinta ka ga rainon likitoci wadda ke cin komai moderately kuma cikin tsarin balance diet na Bature.
Ya kai kallonshi ga fuskarta, kalarta choculate (wankan tarwada), fatarta fresh kamar ta yaran goye. Ba ta da dogon karan hanci gashi nan dai dan matsakaici sai manyan idanu dake lumshewa da kansu. Mai gazar-gazar din gashin gira dana ido bakake wul.
Rayhanah na da lebba masu dan kauri da sulbi kuma zagayayyu (kissable). Bayan wannan, Rayhanah ba ta da wani mugun kyan da za a dorar.
Wannan ita ce irin matar da yake so, ya dade yana nema, yana lalube bai samu ba. Ashe tana nan cikin gidansu. Duka wadannan nazarce-nazarce da ya yi, ya yi su ne cikin dan lokaci da bai gaza mintuna biyar ba.
Zuciyarshi na bugu da sauri da sauri ya rintse idanunsa, kafin ya yi tattaki zuwa inda take zaune. A lokacin ta sadda kanta kasa ne don haka ba ta ga tahowarshi ba, har ya tsugunna a gabanta. Sassanyan kamshin Chrome Legend ya tsirga har cikin kanta.
Da sauri ta dago ido ta dube shi, “Yaya Khalipha!” Ta fada cike da al’ajabi da farin cikin da ta gagara boyewa.
Murmushi ya yi, “Yaya Rahane”. Dariya ya bata sosai, don rabon da ta ji wani ya kira ta da wanann sunan, tun ranar da Babanta ya bar duniya.

A rayuwarta kuma ba sunan da take so irin Rahanen. Suna ne na mahaifiyarta da bata taba gani a duniya ba. Suna ne da Babanta ya zabar mata don kar ya manta da Yalwatinsa. Suna ne da ake kiranta da shi a Takai da intonation daban-daban.
Muskutawa ta yi ta soma share masa kura da dan hankicin dake hannunta kan dan kututturen itacen bishiyar da ta ke zaune.
“Sannu da zuwa Yaya Khalipha, yi maneji da nan ka ga duk an kwashe kujerun”.
Murmushi yake sosai, ya kwaikwayi ‘yar muryarta “Yi maneji da nan Yaya Khalipha”.
Kunya ce ta kama ta, ta rufe fuskarta da zara-zaran yatsunta.
“Ka sha hanya”.
Ta fada ba tare da ta daina murmushin da ke like a tattausar fatar bakinta ba.
“To ya za ayi? Ai ko bangon duniya Rahane ke karatu ba zan yi kasa a gwiwa wajen zuwa ziyararta ba, balle Katsina”.
A zuci yake fadi, bai san a fili yake yi ba saboda azabar son da ke kara ruruwa a zuciyarsa.
Sai ta yi dan jim tana nazarin kalamansa don sun dan yi mata tsaurin fahimta.
Ya ankara da katobarar da ya yi, ya yi saurin gyarawa da cewa, “Ina su Abida kike zaune a nan ke daya?”
Ta sadda kai ta ce, “Ni tun safe yau ban ga Abida ba, Jawahir muna zaune nan tare kawarta Teemoh ta zo ta yi kiranta su gaisa da ‘yan gidansu”.
Ta fadi haka ne don ta kare Abida, a zahiri kuma Abidar mari ta zabga mata cikin (domitory) a bainar jama’a, kan wai ta shafa vasiline dinta don nata ya kare. Jawahir kuma ba ta shafa vasilne sai lotion, abin da ya kaita ga shafa na Abida kenan.
Wannan wulakancin da Abida ta yi mata shine dalilinta na kadaicewa, tana tunanin rayuwa, canje-canjenta da juyinta, kamar rawar ‘yammata wai na gaba ya koma baya, da abebaden ban tsoro dake faruwa a cikinta.
Abin nufi, kowa baya tunanin gaba, wato me gobe za ta haifar? Mutuwa na iya zuwar wa bawa kowanne lokaci amma ta kasa gane me mutane masu irin halin Abida ke daukar duniya.
Da suke tozarta dan Adam don baya da shi, shi ba kowa ne ba. Sun manta da darajar da Allah ya yiwa dan Adam, har ya fadi da kansa cikin Alkur’ani mai girma cewa, ‘Ya karrama dan Adam…..’.
Da wannan tunanin da ta yi ne cikin ‘yan

Please Login or Register in order to submit comment