Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da ya yiwa Abida.
Ya dube ta sosai tana ta kuka ya ce, “I’m warning you Abidah.... don’t repeat it! Don’t repeat it!! Don’t repeat it!!!”

Ta ce, “To Yaya Khalipha”. Ya mike ya fita ya ja musu kofar.

****

A yau duk gidan shiri suke yi domin halartar bikin kammala karatun su Ibrahim, karshen kure adaka ‘ya’yan Dr. Mansur sunyi. Duka sanye suke cikin English wears kowanne da design din sa, sunyi kyau kwarai. Aziza samfurin ‘george’ Abida da Rayha ‘Mclaren’, Jawahid kuma H&M ne duka riguna da wando domin zama da madaukin kanwa yau da gobe tilas ya koyar da Rahane saka wando. Don su a wurin su (casual wear) ne da babu inda bazasu iya shiga dashi ba. Dr. Mansur baya hana su shida kansa in ya fita waje yake sayo musu saidai ya kudure ya kusan dakatar da hakan da zarar sun shiga sakandire.
Kalar kayan kowanne daban, amma duka babu wadda ba yi kyau ba kamar ka lashe. Kai ka ce irin yaran nan ne dake rayuwa a Honolulu.
Rahane ta kara da farin hijabi, wanda ya sauka a kan kafadunta. A zahiri duka su Abida sun fita kyau, sun fita haske. Amma idan ka dubi Rahane a wannan lokacin sai ka kara marmarin maimaitawa, saboda kalar fatar jikinta baka mai duhu amma mai sulbi kamar Somali, da dirin jikinta da ya soma bayyana da wata irin kamala da nutsuwa hadi da kwarijini bayyananne daga indallahi.

Taron, wanda aka gudanar a dakin taron (Musa Abdullahi Auditorium) dake cikin sabuwar Jami’ar Bayero, ya samu halartar kusoshin ilimi na Najeriya da shuwagabanni, malamai da sarakuna. Farfesoshi da Dactoci, har da mataimakin shugaban kasa.
A jawabin mai girma V.C Proffesor Attahiru Jega, ya ce yau shekaru ashirin kenan da jami’ar ta ba da shaidar MBBS mai daraja ta daya, daga nan ba ta kara samu ba sai yau a kan Dr. Ibraheem Mansur Takai. Don haka ‘chevening scholarship’ dake tallafawa hazikan ‘graduates’ na kasashe masu tasowa dake karkashin majalisar Turai ta bashi zabin duk kasar da yake so ya yi specializing a duk fannin da ya zaba. V.Cn ya kare bayanin sa da cewa “Dr. Ibraheem congratulations!”
Ya fada tare da mika masa hannu suka gaisa, sannan ya mika masa kwalinsa, ya karkata masa hularsa. Sannan ya dafa kafadunsa yana girgizawa.
Sai da Nabila ta san yadda ta yi ta kutsa cikin jama’a tana daukar I.M da V.C hoto duk motsin da sukayi, daga karsh Baba Dacta ya rungumo suka jero tare suna sakkowa daga kan steps din zuwa wajen Mami, wadda ke tsaye harde da hannuwa a kirji, fuskarta ta kasa rabo da kayataccen murmushin dake tattausan bakinta. Itama ta rungume shi Nabilan na ta daukar su hoto.

Kwana biyu da taron Baba Dacta ya shiryawa I.M walima a nan reception din gidan. ‘yan’uwa ne na jiki, abokan arziki da abokan aiki na Baba Dacta da Mami, dangin Mami daga Jos, abokan Ibraheem da na Nabila, hatta Hakimin Takai ya zo da iyalansa.
Don haka Dacta ya kama musu daki a Tahir. Don duk girman gidan nan cika ya yi da ‘yan’uwa da abokan arziki.
Addu’o’i aka fara yi, sannan daya daga cikin malaman Ibraheem (Consultant Dr. Bello Sajoh) ya ba da tarihin Ya Himu, hazakarsa da determinations dinsa kan karatunsa.
Sannan ya ja hankalin iyaye kan su karfafi ‘ya’yansu da karatu a fannin kiwon lafiya don taimakon kasarmu da al’ummar mu. Ba wai bamu da masu hazaka bane a Arewa kamar ‘ya’yan Kudu da sauran kasashen da suka ci gaba, a’a, determination wato (kuduri) yaran Kudu dana sauran kasashen da suka cigaba suka fi namu da jajircewa kan goal attainment, sai kuma ZUCIYA.
Ya ce,
“har yanzu Najeriya tana sahun underdeveloped societis, bai yarda da cewa tana shaun developing ba, saboda rashin zuciya da lalaci irin namu, muyi ta diban miliyoyinmu muna kai wa Turawa don suyi mana magani muna kara bunkasa su alhalin ba a fimu da komai ba.
Maimakon masu kudinmu da shuwagabanninmu su yi amfani da miliyoyin wajen gyara asibitocinmu da kawo magunguna masu inganci da kayan aiki ko da a matsayin sadakatul jariya ne. A’a, sai suke kaiwa Turawa suna karawa mai karfi-karfi, kasarmu kuwa da marasa hali ko oho!
Ka je asibitin gwamnati irin su Murtala da asibitocin koyarwar mu ka ga yadda ake wulakanta talaka da masu haihuwa. Lafiya ita ce gaba da komai, karatun kiwon lafiya bai yi tsamarin da al’umma ke duban shi da shi ba, nutsuwa kawai yake bukata da jajircewa.
Masu hazakarmu sun tattare a (Social Science) maimakon (Physical Science) da Arewa ke bukata, ba don rashin kwakwalwa ba sai tsoro da muka sawa zuciyarmu a kan ilimin. Don haka ne ‘yan Kudu suka fi mu ci gaba a fannin, suka fi yawa a kasashen ketare domin neman ilimin Kimiyya.
Dr. Bello ya ci gaba da cewa,
“a yanzu sabuwar gwamnatin da muke ciki ta yi alkawura na daukar nauyin daliban Arewa a fannin kiwon lafiya, amma fa sai da hadin kan iyaye. Dutyn sune su ba wa ‘ya’yansu maza da mata kwarin gwiwa a kan ilimin kimiyya, musamman mata a kan (Gynaecology) wanda yake halastacce a addininmu.
Ya ba da misali da Ya Himu, kwata-kwata shekarunsa ashirin da bakwai amma saboda samun kulawa da iyaye tsayayyu a kan al’amarinshi da kwarin gwiwar da ya sanyawa ransa da zuciya yau ga shi a cikakken likita (General Practioner) da zai iya duba kowacce irin cuta ta yara ko ta manya ya yi (prescribing) ya fadi maganinta, da yadda za ayi a kauce mata da kuma yadda za a shawo kanta in ta yi qamari. Me ya fi wannan amfani ga al’umma? Me ya fi wannan zama abin alfahari a zuciyar iyaye?”
Jama’ar sun ji dadin tunasarwar Dr. Bello, iyaye da yawa sun dauki shawararsa. Ba irin cimar da ba a ci ba.
Ibraheem ya samu kyaututtuka na alfarma. Hakimi mukullin dalleliyar mota ne. Su su Rahane yawo kawai suke cikin mutane ita ba ta ma san taron me ake yi ba sai da Jawahir ta gaya mata.
Yaya Khalipha ya tafi jihar Sokoto inda aka tura shi bautar kasa. Mami na zaune a falo tana waya da Khalipha, Himu ya fito cikin shiri da alama fita zai yi.
Ta yi mishi alamar ya dakata ta karasa magana da Khalipha. Ta gama ta ajiye sannan ta dube shi ta ce, “Ya za ka fita ba ka karya ba?’
Ya yi dan tsaki ya ce, “Ban jin cin abincin yanzu, heart burn ke damuna”.
Ta mike ta isa ga table ta hada mishi shayi mai kauri tana firfitawa ta ce, “Atleast ka sha wannan, rashin cin abincinka ya fara damuna Ibrahim.
Wai me ke damun ka ne? Na lura tunda aka yi maganar auren nan duk ka bi ka rasa kuzari. Nabilan ce ba ka so ko ya ya ne? Idan ka san ba sonta kake ba don me za ka bata mata lokaci har zuwa yanzu kana yi mata yawo da hankali?
Yarinyar nan ta ki kowa sai kai, iyakar soyayya ta gaskiya ta nuna maka, ba ta cancanci rana daya ka juya mata baya ba”.
Ta dauko GESTID tana girgizawa, shi kuma ya soma kurbar tean a tsaye. Sai da ya shanye ta zuba gestid din a cokali ta ba shi da hannun ta cikin bakin sa. Fuskarsa da zuciyarsa cike da jin dadin kauna da kulawar da uwarsu ke musu, kamar wasu kananan yara.
Ita kwata-kwata bata ganin girman su, kullum yadda take treating su Jawahid haka take treating dinsu, wani zubin har sai Dr. Mansur ya ankarar da ita. Ya ce, “Mami nifa ba yanzu zan yi aure ba, don haka ki ajiye zancen Nabila aside. In ta samu miji ku rufawa kanku asiri ku aurar da ita. Ba zan taba auren macen da ta fara cewa tana sona ba!”.
Baki Mami ta saki, ta ce, “Mai sonka kuwa ai shine masoyinka. Bakin da ya furta SO, baya dawowa ya furta kiyayya”.
Murmushi ya yi, ya sumbaci goshinta ya yi gaba.
“Sai na dawo Mami ba nisa zan yi ba”.
Ta ce, “Nima rainin hankalin za ka yi mini Himu?”
Birki ya ja, sannan ya juyo. Cikin damuwa ya ce, “Mami ya ya za ayi na raina miki hankali? Cewa nake ra’ayin da ke zuciyata kika tambaye ni? Na gaya miki gaskiyar abin da zuciyata ta yarda da shi. Bayan wannan ma ba zan yi auren zumunci ba Mami”.
Ta ce, “Hujjah?”
Ya ce, (cikin bude ido kadan) “Hujjoji barkatai”.
“Kamar wanne da wanne?”
Komawa ya yi cikin kujera ya zauna, ita ma Mamin haka, dab da shi ta zauna.
“Idan ma’auratan suka samu kuskuren fahimtar juna, kowanne zai bi bayan bangarensa ne. Sai ki ga su ma’auratan har sun manta sun shirya a tsakanin su amma abin zai yi ta zama a zuciyar iyayen nasu, a dinga kallon juna da shi. Daga nan zumunci zai baci, kin ga garin hada zumunci an lalata shi.
Irin zumuncin da na taso na gani tsakanin Mai martaba Hakimi da Daddy ban taba ganin irin sa ba. Bazan yardain zamo sanadin da zai yi tuntube ba ko kankani. Ina son yadda suka faro shi suna yin sada gaskiya su cigaba da yin sa har karshen rayuwar sub a tareda mun samar da tangarda a cikin sa ba.
Idan na auri Nabila ko laifi tayi min bazan iya hukuntata ba, zan yi ta yi mata uzuri da Baba Hakimi, haka shima ko wacce irin cuta zan yi mata bazai tada kai ba balle ya kalla, nikuma yadda bana son a danne hakkina haka bana danne hakkin kowa. Don haka auren zumunta baya cikin tsarina, don a ganina auren mugunta ne kawai.”.
Murmushi ta yi ta ce, “Hujjarka is invalid. Kai dai kawai ka ce baka ra’ayin Nabila, don in kana sonta har zuciyarka ba za ka tsaya yin la’akari da wadannan kananan abubuwan ba”.
Ya ce, “To Mami maganin kada a ji, kada a yi”.
Ya mike ya fice ta bishi da idanuwa. Sannan ita ma ta mike ta soma shirin tafiya ofis.

****
Kwanaki ke juyawa a hankali su koma satittika, satittika su bada watanni, watanni su bada shekara. Kamar yadda rayuwa take a kullum kenan, komai ma juyawa yake. A haifa, a mutu, a girma, a tsufa.
To hakan ce ta faru da Rayhanah, shekarun girma sun soma juyata daga kwaila zuwa matashiyar budurwa. Mai dauke da wasu ilhamomi da dama.
A yau Rahane shekarunta goma sha hudu, sun kammala karamar sakandire a Darul-Arqam suna jiran fitowar jarrabawarsu (placement) don wucewa babbar makaranta.
Shekaru biyu kenan da wucewar Ibrahim Jami’ar Chicagon Amurka, inda yake fafutukar kwalin zama cikakken (nephrologist) likitan koda. Yayin da Khalipha tuni ya kammala bautar kasa ya fara aiki da Ministry of External Affairs dake Abuja.
A yanzu idan kika ga Rayhanah zai yi wuya ki shaidata farat daya. Ta saje da ‘ya’yan Baba Dacta, fari kawai suka fita, sai fatarta ta ba da wata irin kala ta wankan tarwada mai sheki, jikinta ya fara cikowa ya nuna ilimi da hutu zallah.
Lokacin da jarabawarsu ta fito, kowacce makaranta daban ta ci. Amma Baba Dacta sai ya tattarasu su duka ya kai su ULUL-ALBAAB (Science Secondary) dake Katsina. Azizah ce ta ci gaba da Darul Arqam.
Har zuwa inda yau ke motsi, Abida bata daina cuzgunawa Rahane ba, musamman da aka mai da su nesa da gida babu Baba Dacta balle Khalipha.
Jawahir kuwa dama ta riga ta rainata kamar ita ce babbar. Haka take fadawa ‘yan ajinsu da ‘yan hostel dinsu Rayha ‘yar matsiyata ce ta zo ta makale musu, Babanta na kauye ya asirce babansu ya lika musu ita.
Sannan a gaban Raihan take fada, don ba tsoron Jawahir take ba. Uffan ko daga ido Rayhanah ba ta yi balle ta yi magana. Son Abida take bilhaqqi, saboda darajar iyayenta da Yaya Khalipha.
Khalipha wani irin mutum ne mai matukar tasiri da alheri cikin rayuwar Rayhanah, ko kadan baya son ya ganta cikin rashin walwala. Duk da dai dama ba mai walwalwar ba ce. Abubuwa iri-iri na gilmawa a zuciyar Khalipha a kan Rayhanah, yarinya ce da ta iya takun rayuwarta matuka, ta kuma iya tafiyar da mutum da halinsa.

Abubuwa da yawa kan sa a so mutum, muhimmi shine halayensa ba kyan sura ba. Rahane mai aji ce (classique). Duk da tushenta shine kauye. Ba kyakkyawa ba ce, sannan ba ta da wani abu mai fizgar hankalin namiji banda halayenta. A fuska kam babu kyan, amma a halittar jiki sai an tona cikin dubu kamin a samu goma irin Rayhanah.
Ba ta damuwa da lallai cewa sai ta sanya hearing aid in ba lokacin daukar darasi ba. Sai ta yi kwanciyarta shiru a kan gadonta, ta yi ta tunanin makomar rayuwarta.
Wato yanzu da Rahane ta kara shekaru, sai ta kara sanin ciwon kanta. Baba Dacta da Mami ba jininta bane, ba ta da kowa da za ta bugi kirji ta ce nata ne banda Babanta. Wanda ke ta fama da kansa a halin yanzu, yau ciwo gobe lafiya ba a san hakikanin abin da ke damunsa ba.
Ranar da Baba Dacta da iyalinsa suka gaji da rikonta, ina za ta je? Tsufa ya soma cimma Malam Rashidu. A zahiri babbar matsalar ciwuwwukansa kenan, ta fahimci cewa ita din abin tausayi ce. Karatun nan da Baba Dacta ya tsaya mata take yi shine kadai madogararta sai Ubangijin Talikai.
Duniya ba matabbata ba ce, haka komai na cikinta yana da lokaci. Ta fahimci akwai ranar da dole za ta bar hannun Baba Dacta da Mami tunda ba su suka haife ta ba.
Ranar da hakan ta faru ina za ta? Takai?
Ai ko gida basu da shi a Takai. Babanta babu lafiya ga tsufa, ta kowanne bangare idan ta duba sai ta ga kawai Allah ne gatanta sai yadda ya ga dama zai shirya mata rayuwa.
Wani tunani ne ya fado zuciyar Rayhanah farat daya, zuciyar ta ce AURE! Rayhanah ki yi aure ki samu ki kafa naki iyalin ki yi tabbatacciyar rayuwar iyali. Ki haifi ‘ya’yan da za su rungumi rayuwarki wata rana.
Amma abin tambayar a nan shine, wa za ta AURA? Wane ne zai iya aurenta da LALURAR ta? Wane miji ne zai juri cewa sai matarshi ta saka inji kafin ta ji magana? Wane ne zai ba ta kwarin gwiwa irin wadda Khalipha ke ba ta? Wane ne mai kirki irin Khalipha?
A cewar Abida ita MUNAFUKA ce, son Yaya Khalipha take yi, shi yasa ta damu da shi fiye da kowa a gidan. Idan ita MUNAFUKA ce don tana son mai kyautata mata, ita kuma da take tozartata a bayan idon Khaliphan yaya sunata? They are all the same kenan ko?
Kwata-kwata ma ita ba ta san wane irin so Abida ke nufi ba, don ta kan ce ya fi karfin ki.....ba ajinki bane.....me zai ci dake? Ya yi kama da mai saran kofaton Doki ne? Da sauran maganganu irin wadannan wanda inda sabo, to RAYHANA ta saba jin ire-irensu daga bakin Abida.
Abida ta fi Jawahir power, ta fita baki, ga tsiwa, ga rainin wayau. In ta raina mutum ya shiga uku. ‘Abida Hukuma’. Sunanta kenan in ji Khalipa, domin duka baya karya mata zuciya sai dai ma ya kara tunzurata ga abin da ake dukan nata a kansa. Ya kara kangarar da zuciyarta a kansa.

****
Wani abu da ya kara ta da ma Abida hankali a kan Rayhanah shine, kokarin da ta zo ta fita sakamakon wasa da tsokanar da ta sawa ranta.
Sunyi jarrabawar shiga aji biyar, Rayhanah ta kwace 3rd position na ajin wanda Abida ke kai tun farkon shigarsu Ulul-Albaab, ita kuma ta kwaso na goma.
Sun zo gida hutu ranar Asabar, a yammacin ranar ne Khalipha ya iso, sanye yake da ‘yar ciki da wando har da babbar riga na wata danyar shadda (sheraton) kalarta coffee wato ruwan kasa. Ya dora hula damanga a kan goshinsa, daman dai Khalipha ba dai iya karya karin hula ba, ita ma ruwan kasa ce.
Takalmin fatar damisa ne a kafarshi budadde wanda kudinshi ya haura naira dubu ashirin, Dattijon, daure yake da agogon polo na fata a damtsen hannunsa launin kayan jikinsa. Shigarshi reception rataye da babbar rigarsa a kafudunshi da wata karamar bakar jaka mai dauke da komatsansa masu muhimmanci.
Da sassarfa ya soma taka steps don cimma falon sama, sai suka yi karo garam! Da goshinsu shi da Rayhanah.
Goshin nasa ya kama ya ce, “Kai-kai-kai! Rayhanah goshi za ki fasa min in rasa matar aure?”
Ita ma ta kama nata goshin cikin irin muryar zolayar da ya yi mata maganar da ita ta ce,
“Kai Yaya Khalipha, kai ne fa ka kara mini”.
Ya bita da idanu luuuu! Wani chemistry ya yi aiki cikin ‘yan dakikai. Ba ta taba ganin irin wannan kallon da Yaya Khalipha ke mata yanzu a idon kowa ba, ji ta yi ba za ta iya jurewa kallon ba don haka ta yi saurin dauke idonta ta rabe ta gefensa za ta wuce, sai ji ta yi ya riko hannunta ba tare da ya juyo ba.
Mintuna uku suka dauka a hakan, ta yi saurin zame hannunta da sassarfa ta karasa sauka daga matattakalar zuwa aiken da Mami ta yi mata wajen Mal. Dahiru maigadi.

Tun daga wannan ranar Rayhanah ta samu kanta da matsananciyar kunyar Khalipha, ba ta kara bari ya ganta ba, in ta jiyo muryarsa a falo ba ta fita. Shi kuma dama tuni ya daina shiga dakinsu, tunda suka dan tasa. Balle yanzu da suka zama ‘yammata ko yau aka yi musu aure gobe za su haihu.
Ya damu kwarai da ya ganta, don haka yake yawan zaman falon amma ko keyarta babu. Mami da Dacta sun je wata seminar likitoci a kan cutar Shan Inna a kasar Algeria, daga ita sai Abida ne a gidan, don Jawahir ma da Azizah suna Jos. Har ya kammala week end dinsa ya koma Rayhanah na mishi boyo.

Khalipha Mansur, zaune a ofishinsa yana shigar da wasu sakonni cikin kwamfuta zuwa Nigerian Embassy Accra (Ghana). A kan zuwan Ghanain President (Rawlings of Ghana), wanda zai zo Nigeria cikin satin ya haura Philippines daga Nigeria suka samu matsalar visa za su fito daga kasar Kenya.
Haka nan ya ji aikin ya gundireshi. A dan tsukin nan tunda ya dawo daga gida, ya rasa gane kansa, ya kasa gane me ke damunsa.
Gaba daya ya tattaro hankalinsa da tunaninsa wuri daya. Ya zubawa tafin hannunshi ido, a hankali kuma ya kai shi hancinsa, still kamshin Escada Sentiment yana nan bai gushe ba, domin ko da ya zo wanka bai yarda ya wanke hannun ba, kada ya daina kamshin turaren RAYHANAH.
Khalipha, duk da cewa yana kan gabar kuruciyarsa, kuma a kan matakin da babu macen da ba za ta so shi ba. To fa ba kowacce mace yake kallo da kima ba har ya taba yiwa kansa sha’awar aurenta, mata iri-iri kam ya yi mu’amala dasu tun zamanin yana karatu, anyi abokai cikinsu an kuma yi ‘yammata, sai dai kuma babu wacce mu’amalarsu ta kai labari tsahon shekara daya za ayi hannun riga, don shi bai yarda yana neman yarinya wani ma yana nemanta ba, daga ranar da ya gane hakan duk son da yake mata ya barta kenan har abada.
Hibba kuwa da Hakimi ke son ya aura, har ta gaji da jiransa ta kama dahir, yanzu haka har an sa mata rana. Saboda tamaula da hankalin da yake mata.
Da fari ya ce karatu, ta jira shi ya karasa, ya dawo ya ce Bautar Kasa. Nan ma ta jira shi. Sai kuma ya dawo ya ce sai ya fara aiki, ta jira shi har ya samu. To fa kuma tunda ya fara aikinsa, bai kara bi ta kanta ba, ita kuma ta ga ba rasa manema ta yi ba zai sa ta tsofe a gida alhalin kuma ba shi da niyyar auren ta. Don haka ta yiwa kanta ludufi ta dauki na damo, ta bar Nabilah da koshin wahala......
Yau shekara guda kenan da kammala karatunsu amma tana nan tana jiran Ya Himu, wanda tunda ya cilla kafa a Chicago ba a kara jin duriyarshi ba, ko waya ba sosai yake yi da jama’a ba, idan ya gaisa da Hakimi sai ya ce a gai da kowa.
Sannan ba shi da takamaimiyar lambar waya, wani zubin ma a bakin hanya zai tsaya ya sa (credit card) dinsa a commercial ya kira wanda ya ga dama ya zare abinsa.
Kowa na kokari a kan Nabilah ta yi hakuri da Ibraheem amma sai tasa musu kuka. Hajiya Karima kan ce, “Nabila ki yiwa kanki fada ki zabi daya cikin masu sonki ki aura tun tauraruwarki ba ta dishe ba.
Kuruciyar ‘ya mace ta dan lokaci ce, shekarunki ashirin da bakwai ga kwalin digiri ga na master, kina tunanin idan Ibrahim ya dawo yadda yake ji da kuruciyar nan zai aure ki? Wallahi shi a lokacin ne zai fara samartakarsa, Juma’ar da za ta yi kyau tun daga Laraba ake gane ta”.
Nabila sai dai ta hura hanci ta zumburi baki, ko me za a ce in dai a kan Himu ne ta bayan kunnenta yake wucewa.

Khalipha ya yi baya da lallausar kujerarsa, ya bi jikinta ya kwanta ya lumshe ido. Abubuwa da yawa ke sawa ya so mace, amma ba kyan fuska da kyale-kyale ba, dukiya ko zuzzurfan ilimi. Yana son mace wadda ta san kanta (mai tsare gida da rashin kula maza). Kuma yana son ta kasance mai aji ba kyakkyawar da kowanne karabiti zai biyota a dalleliyar mota ya ce yana sonta ba.
Yana son mace mai kunya, wadda ba ta iya hada ido da namiji in ba dole ba. Mai karancin magana, ba wadda za ta zauna cikin mutane ta yi ta zuba kamar ‘ya’yan kanya ba.
Baya son mai alfahari da son nuna iyawa, baya son mai gwalli da kwarkwasa, baya son wadda za ta cika fuska da jan baki, eye shadow da su maskara da hoda. Baya son wadda za ta rambada ‘yan kunnaye da sarkoki

Please Login or Register in order to submit comment