Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gaban baƙuwar, ta juya tana mamakin wannan ziyarar haka.

Bayan Kulu ta ci ta yi nak, Hasina ta ce "To ina ga yanzu ke yi ƙwarinda zaki iya kallon dramar da kyau, bari in kira shi."

Miƙewa ta yi zuwa ciki, jimawa kaɗan sai ga su sun fito a tare tana gaba yana biye.

Dinning Area ya nufa kai tsaye, don ko bai ma san da zaman wata baƙuwa a gun ba, ko da Hasina ta shiga ciki bata gaya masa ba,cewa kawai ta yi ya fito su karya.

Sai bayan ya zauna ya fara cin abincin sannan ya lura da wanzuwar Kulu a kan kujerar da yake fuskanta.

"Alhaji ina kwana." Kulu ta faɗa tana sunne kai saboda kwarjinin da ya mata.

"Lahiya lau." Ya amsa, sannan ya maida kallonsa ga Hasina da alamar mamaki a fuskarsa.

"Abukkiyata ta Kulu ai kasanta." Hasina ta faɗa.

Shi dai bai kuma cewa komai ba ya ci gaba da cin abincinsa har zuwa lokacin da ya kammala.

Miƙewa ya yi da zimmar shiga ɗaki, dama tuni Hasina ta gama cin abincin ta dawo kan kujera kusa da ƙawarta ta zauna.

"Alhaji taho nan ka zauna." Ta faɗa cikin bada umurni.

Juyowa ya yi ya kalle ta, sosai ya ke mamakin sauyawar hajiyar daga jiya zuwa yau, amma bai musa mata ba ya je ya zauna kusa da ita, a tunaninsa ko akwai abinda take son gaya masa ne.

Murmushi ta jefe shi da shi tana kallon Kulu ta wutsiyar ido.

"Gani Hajjiya mi halam?" Ya tambaya.

"babu komi kiranka ɗai niyyi."

"Ko da yake danna min ƙahwahuna, yau na tashi suna min ciwo." Cike da izza take maganar, wai ita a dole ta asirce shi.

Wani shegen kallo ya watsa mata, wanda ya saka ta shiga ruɗani gami da al'ajabi.

Amma duk da haka bata karaya ba, ta kalle shi a ɗage ta ce "Ka danna min ƙahwahuna nicce, mi kat tsaya kallo?"

Kulu dai na daga gefe tana kallon show sai ƙunshe dariya take, ba abinda take jira sai ta ga yanda alhaji sai durƙusa yana matsar ƙafa.

Shi ko Alhajin ɗaga mata hannu yayi cikin tsawa ya ce "Ya ishe ki haka Hasina! Wai mi ka damunki ne? tsakanin jiya da yau na kasa gane miki, sai hauka kikai iri-iri, in ke samu taɓin ƙwaƙwalwa na ki hwaɗamin in kai ki asibiti ya hi ki tsaya kina karanta min shirme."

Har ya juya zai tafi kuma ya ci birki yana cewa "Kuma daga yau sai yau, kakki ƙara yimin maganar banza irin wagga ko da gani sai ke, balle gaban wata ƙazamar mata, sannan ki tabbatar ke maisammin takardar gona ta kahin dare, in ba haka ba....."
Bai samu damar ƙarasawa ba tsabar taƙaici da ya turniƙe shi kawai sai ya wuce fuu! Zuwa cikin ɗaki.

Dukkansu suka saki baki sototo! Kamar garkar wawa, suka bi shi da kallo.

Kulu ta ci haushin kiranta Ƙazama da ya yi, don ko kalmar nan ta caki zuciyarta sosai.

Hasina ta sha kunya, ji ta yi tamkar ƙasa ta tsage ta shige ciki, wai ita zai ciwa zarafi a gaban macen dake ƙasa da ita? Ko da yaushe Kulu na girmamata da jin shakkarta amma yau Alhaji Munir ya zubar mata da mutunci da darajar ta, tabbas ba zata taɓa barin shi ya ci bulus ba, dole ta ɗauki mummunan mataki a kansa.

Hasina ta manta cewa shi ta so ta wulaƙanta sai reshe ya juye da mujiya.

Kulu ce ta katse mata tunanin da take ta hanyar faɗar "Hmm! Tofah! Meka hwaruwa nan wurin ga? Ko dai ke yi kure wurin anhwani da maganin?"

Dogon numfashi ta ja ta sauke sannan ta ce "Tabbas akwai matsala, ni dai na san na bi komi bisa tsari, amma yanzu ki tahi gida zan binciki inda matsalat take."

Kulu ta ɗauki jakarta ta fice daga gidan tana yiwa Hasina dariya a ranta ta ce "Yau fa rana ta ɓaci ga mata, su Hasina an shiga hannun kwalawa, ai na so ace ya zabga mata mari wallahi da na ci dariya, amma bakomai randa rana ta kuma ɓaci inda rabo na gani."

¥¥¥¥¥¥¥¥¥¥¥¥¥¥¥¥

Ina labarin yaro Abdul?

Yaro Abdul dai ya nausa a cikin jeji sai tafiya yake, tun yana ƙirgen kwanaki idan ya ga dare ya yi gari ya waye ya ce ɗaya, gobe ya ce biyu, har a ka kai lokacin da lissafi ya ƙwace masa.

Zuwa lokacin shanyayyiyar ƙafarsa ta ɗage sosai, da ba don Albarkacin sandunan da yake tare da su ba, tabbas da ba zai iya matsawa ko daga nan zuwa can ba.

Tun yana damuwa tare da licin ciwukan dake jikinsa har ya daina damuwa dasu, ya yanke ƙauna, hawayensa ko tuni sun ƙafe, ya kuma fitar da rai ga samun mataimaka.

Ba abinda yake sai roƙon Allah a zuci da sarari domin ya kawo masa ɗauki.

Allah ma ji roƙon bawa.

A wata rana daga cikin ranaku a ka kwana a na tsala ruwan sama kama da bakin ƙwarya, Abdul bai samu mafaka ba, don haka a kansa ruwan suka ƙare.

Da safe ruwan ya tsaya cak kamar ba a yi ba, can zuwa rana tsaka rana ta ƙwalle sosai, tamkar ba jiyan nan aka tsala ruwa ba, ikon Allah kenan.

A daren ranar Abdul ya kwana da wani irin zazzaɓi mai zafi, don haka ya kasa tashi ya ci gaba da tafiya yana nan kwance a'inda ya kwana, zuwa can da ya ji rana ta yi zafi sosai ya yunƙura daƙyar ya kwashi sandunansa ya ci gaba da gangarawa cikin jejin jikinsa sai kyarma yake.

Tun daga nesa yake jiyo busa mai daɗin gaske ta na kawowa kunnensa ziyara.

Cike da tsananin murna ya ci gaba da bin sautin busar ya na jin nishaɗi.

Ba komai ne ya saka shi farinciki ba, sai don tunanin cewa zai samu mataimaki, ko ba komai dai ya san zai samu abinda zai sakawa bakinsa idan mutumin dake tafe mai jinƙai ne.

Can bayan wasu daƙiƙu ya iso gun wata bishiya mai girma da inuwa sassanya, a ƙasan bishiyar ya hango mabushin zaune, sai dai bayan mutumin kawai yake iya gani, domin daga bayansa Abdul ɗin ya ɓullo.

Nan ya ci gaba da nufar mutumin da zimmar ya kewaya ta gabansa su haɗu.


Shi ko wannan mutumin jin motsi a bayansa ya saka shi miƙewa cikin hanzari tare da saita bindonsa da wani mulmullen dutsi mai ɗan girma, ya juyo a fusace ya na jiran ƙarasowar mai kawo harin.......


Hmmmm! Tofah! Shin mutuminan wanene shi? Me yake a jeji? Zai harbi Abdul kuwa?

Ba wannan ba, anyah zai taimaki yaro Abdul idan ya yi arba da halittarsa?🤔🤔🤔



Don jin ya zata kaya sai ku biyo NI a pages na gaba.


More comment more typing.....

Follow me on Wattpad @Ruky_I_Lawal.



Vote share and comment.





RUKY I LAWAL CE🌹🌹🌹🌹


Follow me on wattpad @Ruky_i_lawal.





RUKY I LAWAL🌹🌹🌹🌹🌹

*HALITTAR ALLAH CE*
👨🏻‍🦼👨🏻‍🦼👨🏻‍🦼👨🏻‍🦼👨🏻‍🦼

*(Labari mai taɓa zuciya, da sanya imani da tsoron Allah a zuciyar mai karatu)*

*ALƘAMIN: RUKAYYA IBRAHIM LAWAL (UMMU INTEESAR)*

*MARUBUCIYAR: SOYAYYAR MEERAH*
*Y'AR GANTALI*
*RIKICIN MASOYA*
*A SANADIN KAMA*
*RASHIN GATA*
*WATA ƘAWA*

*AND NOW*
*HALLITAR ALLAH CE*

15Rabiul awwal/1 November.
1442hjr/2020.



Wannan page SADAUKARWA ne ga masoya wannan book ɗin, iya wuya ana jone🥰🥰




________________________________


*AREWA WRITER'S ASSOCIATION*
_________________________________
*💦{Arewa ginshiƙin al'ummah}💦*
_________________________________
https://www.facebook.com/104534761033461/posts
arewawritersassociation@gmail.com

*BISMILLAHIR RAHMANIR-RAHIM*



PAGE 37-38

Ganin haka yasa antar Abdul kaɗawa, a take ya tsaya cak a gun, tare da runtse idonsa da ƙarfi, domin a tunaninsa ba abinda zai hana mutumin nan ya same shi a dai irin wannan saitin da ya yi.

Shi kuwa mutumin har yanzu bai sauke bindonsa ba, sannan bai yi yunƙurin matsowa kusa ba, domin halittar yaron ta saka shi al'ajabi, sai dai bai ji ko ɗigon tsoro ba, kasancewarsa maharfi da ya saba yawo a dazuka, ba irin abinda baya cin karo da shi a yayin da ya shiga jeji, don haka ganin wannan ma bai saka shi tsorata ba.

Jin shiru ya saka Abdul ya buɗe idonsa, ganin mutumin bai yi ko gezau ba, ya saka shi fara takawa don zuwa gun shi.

"Dakata yaro!."

Maharbin ya faɗa cikin ɗaga murya.

Tsayawa ya yi cak a inda yake, kamar yanda aka umurce shi.

"Mutum ko aljan?"
Ya jefo masa tambaya.

"Mutum na." Ya bada amsa.

"Yaro meke tafe da kai?"

Cikin raunanniyar murya ya ce "Taimako nika biɗa, ka temake ni, ba ni da lahiya kuma ina jin kishirwa da yunwa."

Da ganin yanayinsa ka san yana jin jiki.

Sai a lokacin Maharbin ya mayar da bindonsa, sannan ya matso kusa da Abdul ɗin.

Hannunsa ya saka a jakar bayansa ya fito da shantalin ruwansa ya miƙa wa yaron ya sha, sa'annan ya ja shi zuwa gindin bishiyar da yake zaune, ya ɗauko ragowar gasasshiyar tsuntsuwar da ya ci ɗazu ya miƙa masa.

Da sauri ya ƙarba ya cinye, duk da naman ba yawa kuma bai masa maganin yunwa ba, amma ya toshe masa wata kafa, don kuwa ya ji damar yunwar da ta addabe shi.

Bayan ya yiwa yaron duk taimakon da ya kamata sai ya miƙe ya cigaba da zagayawa a jejin ko ya samu wani naman da zai kai gida.

Abdul ya bi bayan shi, har ya fara nisa a tafiyarsa ya ji motsin mutum a bayansa, juyowar da zai yi haka sai ya ga wannan yaron ne da ya taimaka 'yan mintinan da suka wuce.

"Yaro lafiya dai?" Ya tambaya cike da mamaki.

"Babu komi, dama cewa niyyi zan bika mutahi." Abdul ya faɗa cikin rawar murya.

"Ni fa ba na gane wannan Hausar taka, wai ina zaka bi ni?" Ya kuma tambayarsa.

"Ni ko ma ina na mu tahi ɗai." Ya faɗa.

Zuwa lokacin Maharbin ya fara ƙuluwa, ga haushin rashin samun abun farauta tun safe da ya fito, ga shi baya gane Hausar yaron, saboda haka ya ce "Kai yaro saurare ni da kyau, na riga na maka taimakon da zan iya, ko kai aljani ne ya kamata ka bar ni haka."

Ya na gama faɗa ya yi gaba abinsa, Abdul ya fashe da kuka ya kuma binsa a baya tamkar jela.

Da Maharbin nan ya ga abun ba na ƙare ba ne, sai ya tsaya ya yiwa Abdul gargaɗi da babbar murya tare da tsoratar da shi, a kan idan ya yarda ya biyo shi sai ya yanka shi ya kai namansa gida a madadin naman tsuntsaye.

Bisa ga tilas Abdul ya haƙura, ya yasu a gun ya na kuka, Maharbin kuma ya ci gaba da nausawa jeji ran shi wasai, yana neman abun farauta.

¥¥¥¥¥¥¥¥¥¥

A can gidan Alhaji Munir kuwa, hankalin Hajiya Hasina ya kai ƙoluluwar tashi da ta fahimci cewa maganinta bai ci ba, sai zarya take a falon ta na ƙoƙarin tuna inda ta yi kuskure a cikin aikin.

Ta yi iya yinta amma ta kasa gano inda matsalar take, haka ta ci gaba da zarya, ranta sai tuƙuƙi yake mata, ko ta halin ƙaƙa tana so ta nunawa Alhaji Munir cewa ruwa fa ba sa'an kwando ba ne.

Ta na cikin wannan halin Alhajin ya fito da shirin zuwa kasuwa, ya zo zai gifta ta gabanta ya wuce ta kira sunansa.
"Alhaji!"
Ko kallonta bai yi ba ya ci gaba da tafiya.

Har ya je ƙofa ya tsinto muryarta tana faɗar "A dawo lafiya mai gida."

Wani uban tsaki ya ja ya fita, cike da ƙunar zuciya.

Haƙiƙa yana daf da kamuwa da ciwon zuciya, ga damuwar ɓatan tilon ɗansa, ga wannan matar da take so ta ƙara mishi damuwa a kan wadda yake ciki.

Haka ya bar gidan da kuntaccen kai.

Tafe yake a mota shi kaɗai ya na tunanin rayuwa, damuwa ce cunkushe a ƙasan ransa, har ya zama na cewa tuƙin kawai yake amma hankalinsa baya kan titin.

Ikon Allah ne kaɗai ya kai shi Marna police station, ya je don ganawa da officern da ke riƙe da case ɗin ɓatan Abdul.

Bayan sun gaisa officern yake tambayarsa, "Alhaji hay-yanzu dai shiru a ɓangarenku babu labarin komi? Ba wani wanda kaka zargi da aikata wanga laihin?"

Shiru ya yi kamar mai nazarin wani abu, can ya ɗago kai ya ce "A'a officer ba na zargin kowa, yanzu dai abinda nika so gare ku, don Allah ku ƙara tsaurara bincike wallahi ina cikin damuwa, ku yi ƙoƙari ku gano min maƙiyina da ya raba ni da tilon ɗana, ya sani cikin zullumi da tunanin halin da rayuwar ɗana za ta kasance a lokacin da ya nisanta da gida."

Shiru ya yi na ɗan lokaci, yayin da ɗan sandan ke faɗar "Insha'allah! Alhaji zamu ƙara ƙoƙari akan wanda mu kai, da yardar Allah sai mun kama mai wannan laifin mun tabbatar da an yanke mai hukuncin da yaddace da shi."

Nisawa Alhajin ya yi sannan ya ce "Ina ji a jikina cewa Abdul ya na cikin matsala, ko barcin kirki ba na iya yi, ina yawan mafarki da shi ya zo yana kiran 'Abbu ka temake ni, ina cikin matsananciyar matsala' shiyassa ka ga hankali yana kasa kwanciya Officer."

"Dole hankalinka ya tashi Alhaji, ɓacewar ɗan mutum ba wasa ba na, yanzu dai ka koma insha'allah za mu zo nan gida domin akwai wadda muka zargi a cikin ahalin gidan." Cewar ɗan sandan.

Zaro ido Alhaji ya yi ya ce "Wa kuke zargi?"


"Matarka Hajiya Hasina." Ya ba shi amsa.

Ya so ya musa, amma shi kansa yanzu ya fara zargin ta don haka bai ce komai ba ya yiwa officern sallama ya ƙara gaba.

¥¥¥¥¥¥¥¥¥¥¥¥¥¥¥

Hasina kuwa bayan fitar Alhaji ta kuma faɗawa dogon nazari, can ta yanke hukuncin cewa za ta ƙara amfani da maganin wankan, domin a nan kokontonta yake, don kuwa ba ko shakka a gabanta ya ci abincin da ta sakawa maganin, wankan ne dai bai yi da kyau ba.

Da yamma bayan dawowar Alhaji gida Hasina ta same shi a ɗaki ta durƙusa a gabansa.
"Don Allah Alhaji ka yi hanƙuri ka yafe min, na tuba ban ƙarawa, kuma ma na mai samma takardun gonakka ka yi hanƙuri mijina."

Banza ya mata kamar ta na yi da bangon ɗakin.

Ganin hakan yasa ta fashe da kukan makirci ta na ƙara roƙarsa.

"Don girman Allah Alhaji ka yi hanƙuri na tuba, ni kaina ban san mi ya hau kaina ba nit aikata abubuwan da niyyi, ka yahe min."

Kuka take kashirɓan kamar gaske, a zahiri za ka rantse ta yi nadama, amma a cikin ranta ba haka ba ne, zuciyarta cike da son ganin ta mallake shi.

Sai a lokacin ya ɗago zuciyarsa cike da tausayinta, ya lallashe ta ka na ya yafe mata, tare da tabbatar mata da cewa komai ya wuce a gunsa.

Take a gun suka shirya suka dawo kamar da.

Ganin ta samu wannan nasarar ya saka ta shiga shirya yanda za ta yaudare shi ya yi wankan ruwan maganin.

Kashegari kamar waccan ranar, ta kuma zuba magani a ruwan wankansa, sa'annan ta tsaya a ƙofar banɗakin ta yanda za ta iya jiyo duk motsinsa.

Bai kawo komai a ransa ba ya shiga wankan, sai dai kamar waccen ranar, ƙaiƙayi ya ta so masa, da kamar zai ɗibi wasu ruwan ya wanke sai kuma ya tuna ya na sauri ne, da yake ba sosai yake jin ƙaiƙayin ba, kawai sai ya ɗora towel ɗinsa ya fito.

¥¥¥¥¥¥¥¥¥¥¥¥

Wasa-wasa sai da Maharbin nan ya share sama da sa'o'i biyar amma ko tsuntsu ɗaya bai haɗu da shi ba, har ya sare ya cire rai ga samun wani naman.

Gwuiwoyi a sanyaye ya juya don komawa gida, sai dai ya na cike da zullumi da tunanin yanda zai tunkari iyalinsa hannu rabbana.

Har ya ci rabin tafiya, kamar daga sama ya ji an ce "Ka manta da yaron da ka wulaƙanta ɗazun nan, da dai ka koma gare shi wataƙil da ka dace."

Nan fa ya hau waige-waige ya na neman mai maganar, amma bai ga kowa ba.

Sai a lokacin ya tuna da wancan yaron da suka haɗu, har ga Allah shi ya ma manta da rayuwar yaron shaf, sai yanzu da aka tuna masa....








RUKY I LAWAL CE🌹🌹🌹

*HALITTAR ALLAH CE*
👨🏻‍🦼👨🏻‍🦼👨🏻‍🦼👨🏻‍🦼👨🏻‍🦼

*(Labari mai taɓa zuciya, da sanya imani da tsoron Allah a zuciyar mai karatu)*

*ALƘAMIN: RUKAYYA IBRAHIM LAWAL (UMMU INTEESAR)*

*MARUBUCIYAR: SOYAYYAR MEERAH*
*Y'AR GANTALI*
*RIKICIN MASOYA*
*A SANADIN KAMA*
*RASHIN GATA*
*WATA ƘAWA*

*AND NOW*
*HALLITAR ALLAH CE*

21 Rabiul awwal/7 November, 2020.
1442hjr/2020.

DEDICATED TO: ANTY HAUWA (MAMAN USWAN)








________________________________


*AREWA WRITER'S ASSOCIATION*
_________________________________
*💦{Arewa ginshiƙin al'ummah}💦*
_________________________________
https://www.facebook.com/104534761033461/posts
arewawritersassociation@gmail.com

*BISMILLAHIR RAHMANIR-RAHIM*


PAGE 39-40

Cikin hanzari ya juya ya nufi inda suka haɗu da yaron ɗazu.

Sai da ya iso bakin bishiyar da suka zauna ɗazu, nan fa ya hau dube-dube ko'ina ya na neman yaron, amma bai gan shi ba sam, nan fa hankalinsa ya dugunzuma, ya bazama a cikin jejin yana neman yaron, sai da ya shafe tsawon lokaci ya na nemansa, amma ba amo ba labari.

Zuwa lokacin gajiya ta gama riskar dukkan gaɓɓan jikinsa, gun bishiyar ya dawo ya zauna don ya huta, sa'annan ya nufi gida.

¥¥¥™™™

Yaro Abdul kuwa, tun lokacin da ya fahimci cewa Maharbin nan ba zai taimaka masa ba, kawai sai ya miƙe daga inda ya yasu, ya ci gaba da tafiya yana sharar ƙwalla, zuwa lokacin zazzaɓin dake jikinsa ya tsananta, amma saboda kafiya da ƙarfin hali irin na shi ya ci gaba da tafiya, cikinsa tamkar ba na shi ba saboda yunwa....

Komai rashin imanin mutum idan ya haɗu da Abdul a cikin wannan yanayin, tilas ya tausaya masa, saboda yanda ya ƙwarjame ya yi duhu sosai, dauɗa ta gama samun muhalli a jikinsa, tufafinsa kuwa har sun canza launi saboda datti.

Da yake lokacin da zai baro gidan Kande tufafin da ya baro gida dasu ne ajikinsa, tun barinsa gida sau ɗaya aka wanke su, lokacin da Basiru zai yi wanki ya haɗa dasu, nan ma ba don sun fita ba, tunda yaron bawai ya iya wankin ba ne sosai...

Wandon jins kalar blue black ne a jikinsa da riga light blue, amma wandon har ya fara dafewa saboda datti, rigar kuma ta fara zama brown.

Yau kusan kwana goma kenan rabonsa da gidan Kande.

Haka ya ci gaba da gangarawa, yana cikin tafiya kawai sai ya yi tuntuɓe da wata baƙar leda.

Cikin rawar jiki ya durƙusa tare da ajiye sandarsa, ya zauna.

Janyo ledar ya yi ya buɗe ta, sai ga lafiyayyar shinkafa da wake a ciki, dama ledar kusan a cike take.

Cikin tsananin murna mara misaltuwa Abdul ya ɗaga hannu sama ya ce, "Allah na gode ma."

Nan da nan ya fara afa shinkafar nan, tamkar mayunwacin zakin da ya jima bai yi kalaci ba.

Duk da cewa baya da lafiya sai da ya cinye shinkafar tas sa'annan ya miƙe don neman ruwa.

Abun mamaki, sai ya ji rabin ciwon ya tafi, har wani irin ƙarfi ya ji ya zo masa.

A bayyane ya ce "Kai! Dama ashe yunwa ta nika ji, ita at rabin ciyon." Hahaha, ya bushe da dariya shi kaɗai cike da nishaɗi ya matsa gaba.

Can zuwa rabin sa'a yana tafiya, idonsa ya sauka kan wata kwalba cike da ruwa, murmushi ya bayyana a fuskarsa, ya je ya ɗauko ta, ya buɗe ya kwankwaɗa sai da ya sha fiye da rabi sannan ya wanke hannunsa ya tafi da sauran.

Abinda Abdul bai sani ba shine, duk abin nan da ke faruwa aljani Barkuza ya na tare da shi, kuma shine asalin aljanin da ke tare da shi ya na gadinsa tun yana gida, shine ya ƙwace alewar hannun Abdul ya yar, lokacin da yaya Sunusi ya kawo masa alewa mai guba.

Haka a lokacin da su Gumush suka sace Abdul ya ɗan ɗaga zuwa wani guri, da ya dawo ya tarar ba yaron shi ne ya ba zama nemansa, har ya taddo inda yake.

Tun lokacin ya na tare da shi, har zamansa a gidan Kande, ya bar yaron ne ya ɗanɗana wahalar rayuwa, domin ya san zafi da ɗacin rashin iyaye da kuma wahalar nema saboda rayuwarsa ta gaba ta inganta.

Shi ne ya ajiyewa Abdul wannan shinkafar da ruwa da siyo a kasuwar wani ƙauye dake kusa da su, ya ajiye masa a fakaice yanda ba zai tsorata ba.

Shi kuwa Aljani Mazkud shi ne ya shiga jikin Abdul a kwanaki uku na farkon zamansa a jeji, haka zalika shi ne wanda ya je gidan Kande ya tsorata ta, shine kuma wanda ya bi Maharbi a baya ya tuna masa da yaro Abdul.

¥¥¥¥¥¥™™™™™™

A Sokoto kuwa, labari ya sha bam-bam da na baya, domin ko a cikin satin nan biyu abubuwa da dama sun faru marasa daɗi, domin kuwa Hasina ta yi nasarar mallake Alhaji Munir, yanzu fa sai abinda take so yake yi, bayan kwana uku da zuwansa station 'yan sandan suka zo gida domin sake gudanar da bincike, buɗar bakin Alhaji sai cewa ya yi "Ku tahi ɗai ofisa ni ba ni da wani ɗa da ya ɓace don kuwa ban ma taɓa haihuwa ba, ga matata nan ku tanbaye ta."

Ƙwalalo ido waje suka yi su duka, suka cika da tsananin mamaki, to miya ke damunsa? Shekaranjiyan nan fa ya je da buƙatar a tsananta bincike a kan ɗansa yanzu kuma ya ce baya da wani ɗa.

Ofisan ya shanye mamakinsa ya ce "Alhaji ko dai ka sha'afa ne? Nina hwa Asp Bello Yahaya, wanda case ɗin ɓacewar ɗanka Abdul yake hannuna."

Alhaji Munir ya kalle shi a ɗage cikin wata irin murya ya ce "Na ce maka ni ban taɓa haihuwa ba... Hajjiya ko na taɓa haihuwa?" Ya ƙarashe zancen ya na kallon Hasina.

Cike da izza da isa ta ce "Har sai ka tambaya Munir? Ni ce dai matarka kuma ban haihu ba."

Maida dubanta ta yi ga tawagar 'yan sandan ta ce "Ofisa kuna iya tahiya mu ba mu da wani yaro da yat ɓace."

Har ogansu zai buɗi baki ya yi magana, Hasina ta ɗaga mishi hannu cikin tsawa ta ce "Kuna hita ko sena jissat muku kwandon rashin mutunci?"

Kallon inda Alhaji ke tsaye suka yi, ya na nan a gun baya da niyyar motsawa bare ya yi yunƙurin dakatar da ita, tsaye kawai yake kamar wani soko.

Ganin hakan ya saka ta ce a ranta "Bari na nuna muku ƙarfin ikona."

Kallon Alhaji ta yi cikin isa da bada umurni ta ce "Munir shiga cikin gida."

Ba musu ya juya zuwa ciki, tamkar yaron da uwarsa ta masa umurni.

Nan take idon ogansu ya fara tara ƙwallar tausayi, "Tabbas ta na ƙasa tana dabo." Ya faɗa a ransa tare da juyawa bai ce komai ba ya yi gaba, sauran tawagarsa suka bi sa a baya, yayinda Hasina ta raka su da harara...















RUKY I LAWAL CE🌹🌹🌹

*HALITTAR ALLAH CE*

👨🏻‍🦼👨🏻‍🦼👨🏻‍🦼👨🏻‍🦼👨🏻‍🦼


________________________________


*AREWA WRITER'S ASSOCIATION*
_________________________________
*💦{Arewa ginshiƙin al'ummah}💦*
_________________________________
https://www.facebook.com/104534761033461/posts
arewawritersassociation@gmail.com


*(Labari mai taɓa zuciya, da sanya imani da tsoron Allah a zuciyar mai karatu)*

*ALƘAMIN: RUƘAYYA IBRAHIM LAWAL (UMMU INTEESAR)*

*MARUCIYAR: SOYAYYAR MEERAH*
*Y'AR GANTALI*
*RIKICIN MASOYA*
*A SANADIN KAMA*
*RASHIN GATA*
*WATA ƘAWA*

*AND NOW*
*HALITTAR ALLAH CE*

PAGE 41-42

Abdul kuwa ya cigaba da nausawa cikin jeji ba tare da gajiyawa ba, duk da cewa ita kanta sandar hannunsa ta ɗanɗana kuɗarta, don zuwa wannan ranar har rufin sandar na ƙasa ya guntule, duk ta moƙaɗe a wasu gurare, tsabar faɗi tashin da yake a cikin duwarwatsu.

Ƙafarsa kuwa, tun yana damuwa da zogin da take masa, har ya zo ya daina damuwa, tuni ma ƙafar ta ɗage sama, saboda rashin kulawa.

A haka ya cigaba har bayan shuɗewar wasu kwanaki.
Watarana yana cikin tafiya ya hango alamar wani gari a gabansa.

Farinciki ne ya cika zuciyar Abdul, sai sauri yake zubawa cike da zumuɗin ganin ya isa garin.

Tafiya kawai yake bai yi aune ba sai ji ya yi ya yi tuntuɓe da wani murgujejen dutse, kansa ya bugu da dutsen, wata uwar hantsilawa ya yi, har sai da ya tsallake dutsen, ba shiri ya baje a ƙasa magashiyan, jini kuwa sai tsartuwa yake daga goshinsa.

Daga nan bai kuma sanin inda kansa yake ba.

**************

Wata tsaleliyar mota ce ke tafe, sai sharara gudu take tana nufo gun, da dukkan alama matuƙin motar yana sauri ne.

Saura kaɗan ya taka yaron,ba shiri ya taka burki yana sakin ajiyar zuciya da alama ya firgita.

"Innalillahi wa inna ilaihir raji'un!" Shi ne kaɗai abinda mutumin ke maimaitawa.

Buɗe motar ya yi tare da fitowa ya yo kan yaron.

Hannu ya saka ya birkito shi da nufin ya taimaka masa.

Ba shiri ya janye hannunsa, don yin arba, da mummunar halittar yaron, ja da baya kaɗan ya yi, haƙiƙa ya kaɗu matuƙa da ganin wannan yaron.

A ransa ya ce "Ko dai aljani ne?" Ras! Ƙirjinsa ya buga, tsayawa ya yi jim, kafin ya maida dubansa ga yaron, ganin goshin yaron nata zubar da jini ya saka ya kai hannu ya ɗauki yaron bakinsa na furta duk addu'ar da ta zo mashi.

Ya yanke a ransa zai tafi da wannan yaron zuwa cikin gari don kai shi asibiti, ko da kuwa aljani ne, yasan Allah zai kare shi daga sharrinsa, don shi ya yi ne saboda Allah.

Motarsa ya nufa ya saka yaron a gidan baya, ba tare da ya lura da ƙafar yaron ba, bare har ya fahimci cewa gurgu

Please Login or Register in order to submit comment