Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Safiya ce ta shigo da sauri ta ƙarasa gun ta, ta na faɗar "Oyoyo oyoyo!! Sannu da zuwa yaya."

Jan ta ta yi suka shige cikin ɗakinta domin su tattauna a sirrance.

Ba su jima da shigewa ba, Baba direba ya shigo da Abdul falon ya na sallama, dawowarsu kenan daga makaranta, jin shirun ya yi yawa yasa ya dubi yaron ya ce "Abdul yaron kirki mamakka bata kusa ƙoƙarta ka ida shiga ciki."

Da to yaron ya amsa, sannan ya yunƙura ya tattara dukkan ƙarfinsa ya isa gaban 2sitter dake falon, ganin ba kowa gashi tun a makaranta cikinsa ke murɗa masa, kawai sai ya yi dabara ya haye kujerar ya kwanta ya na sauraren cikinsa dake masa ciwo sosai, sai hawaye ke fita a idonsa.

Lafewa ya yi luf, ya na tunanin da ya saba, domin tun ba yanzu ba tunani ya auri ƙwaƙwalwarsa, Ga shi dai yaro ne mai ƙarancin shekaru, amma matsalar da yake fuskanta koda yaushe ta haddasa masa yawan tunane-tunane.

A ransa yake tunanin Mammansa bata sonsa ko kaɗan, domin bata kula da shi, ko don ya na gurgu ko makaho ne take masa haka?, Ko da yake ba ita kaɗai ce ba ta sonsa ba, ya lura har makaranta yara tsokanarsa suke, wasu ma tsaronsa suke, ba mai son zuwa kusa da shi idan ba nakasasshi 'yan uwansa ba, sauran duk ƙyamarsa suke, Abbunsa ne kaɗai ke sonsa, shi kaɗai ne yake rungumarsa har ma ya lallashe shi idan ya na kuka.

Tuna wannan da ya yi ya saka ya ce a ransa "In Abbuna ya dawo zance ya cire ni daga makarantar ban son karatun na gaji."

Haka ya cigaba da rirriƙe ciki ya na kuka har bayan shuɗewar wasu mintuna masu yawa, sai ga Hajiya Haseena ta fito yayarta Safiya na biye da ita a baya sai dariya suke ƙyalƙyalawa da gani kasan ta mugunta ce, wannan na nuna kenan wata munakisar suka ƙulla a cikin ɗakin.

Dai-dai lokacin da suka zo tsakiyar falon, idon Safiya ya sauka akan Abdul da sauri ta runtse idonta ta na faɗar "Innahu min sulaimanu wa Innahu bismillahir-rahmanir rahiim, ku ka ganinmu ba mu mu ka ganinku ba."

Shi dai Abdul bai ce uffan ba, sai ƙuri da ya yi mata da idonsa ɗaya.

Hajiya Haseena ce ta ƙaraso gabansa ta saka hannu ta murɗe masa kunne ɗaya ta na faɗar "To baƙin maye, kallon ya isa haka, kurwar yayata kur, ka ci kanka ka sha baƙin ruwa."

Ta na gama faɗa ta sake masa kunne suka nufi hanyar fita falon Safiyar na faɗar "Tab! Lallai Haseena kina ƙoƙari, haka kika zama da wanga yaro? Ke bai ma baki tsoro da dare?"

Dariya Haseena ta ƙyalƙyale da ita ta ce "Yayata ke cika tsoro, ni ai ban ma yadda mu haɗu da shi da dare sai bisa dole, ke san ko in Babanai na nan har ga jikina nake ja nai ina mai wasa?"

"Uhmm! Lallai iyawa kikai, ni dai sai an jima bari In tahi, kafin nakasasshen ɗan ga naku ya samin hawan jini."

Ta na gama faɗa ta yi gaba abinta.

Shi kuwa bawan Allah Abdul ya na nan inda suka bar shi, sai matsar ƙwalla yake, zafin ya haɗe masa biyu, ga ciwon ciki ga wannan zaluncin da matar babansa ta masa.......



Follow me on Wattpad @ ummu inteesar




RUKY I LAWAL CE🌹🌹🌹🌹🌹
*HALLITAR ALLAH CE*
👨🏻‍🦼👨🏻‍🦼👨🏻‍🦼👨🏻‍🦼👨🏻‍🦼

*(Labari mai taɓa zuciya, da sanya imani da tsoron Allah a zuciyar mai karatu)*

*ALƘAMIN: RUKAYYA IBRAHIM LAWAL (UMMU INTEESAR)*

*MARUBUCIYAR: SOYAYYAR MEERAH*
*Y'AR GANTALI*
*RIKICIN MASOYA*
*A SANADIN KAMA*
*RASHIN GATA*

*AND NOW*
*HALLITAR ALLAH CE*



________________________________


*AREWA WRITER'S ASSOCIATION*
_________________________________
*💦{Arewa ginshiƙin al'ummah}💦*
_________________________________
https://www.facebook.com/104534761033461/posts
arewawritersassociation@gmail.com

*BISMILLAHIR RAHMANIR-RAHIM*



PAGE 7-8


Ko da ta dawo ma wucewa ta yi abinta, ko kallon inda yaron yake bata yi ba, bare ta ji dalilin kukansa.

Sai can wuraren ƙarfe huɗu da rabi na yamma sannan ta fito jiki na rawa, ta turawa Abdul kekensa zuwa ciki ta kira Lami 'yar aikinsu ta ce "Lami ki yima yaronga wanka, ke ga Babanai ya kusa dawowa."

Ta na gama faɗa ta juyowa ta koma inda ta fito.

Lami ce ta masa wankansa tsaf a bathroom ɗin dake ɗakinsa, bayan ta kammala ta shirya shi cikin ƙananun kaya.

Ganin yanayin yaron ya sauya daga yanda ta saba ganinsa, ya sa ta dube shi ta ce "Abdul mika damunka?"

"Yunwa nika ji anty, kuma cikina ka ciwo." Ya bata amsa.

Cikin alamun tausayawa da mamaki ta juya ta nufi kitchen don nemo masa abinci, mamaki take ya aka yi Hajiya ta bar yaronta da yunwa haka? Kuma baya da lafiya amma da alama bata ma sani ba.

A haka har ta ƙarasa kitchen, ta samu su Ladi masu aiki a kitchen sun gama girki ta ce Su zubowa yaro Abdul zai ci.

Jiki na ɓari Ladi ta ɗauki lafiyayyen filet ɗan madai-daici ta shaƙe masa shi da cous-cous da miya haɗe da naman rago akai, ta miƙawa Lami.

Ƙarba ta yi ta juyo ta nufi ɗakin Abdul, an yi Sa'a Hajiya bata falo don haka ba a samu wata matsala ba.

Sauke shi ta yi ƙasa kan carfet, sannan ta miƙa masa kwanon, sai ta ga har hannunsa na kyarma gun amsawa, hakan ya nuna tsananin buƙatarsa ga abincin, nan take ya fara ci hannu baka hannu ƙwarya.

Jinjina kai ta yi cikin tausayawa, ta juya zuwa boys quaters da yake can ne mazaunin 'yan aikin gidan, ta ɗauko masa maganin ciwon ciki ta kawo masa.

Bayan ya gama cin abincin ta ba shi ya sha sannan ta kwantar da shi, nan da nan barci ɓarawo ya yi awon gaba da shi.

A haka Abdul ya ci gaba da rayuwa cikin tsana da tsangwamar matar uba da ƙiyayyar yayyen uba.

¥¥¥¥¥¥¥¥¥¥
Waye Alhaji Munir?

Sunansa na asali shine Munir Abbas.
Mahaifinsa Alhaji Abbas tsohon ɗan kasuwa ne, yana da yara Goma sha uku.

Matansa biyu, Saratu da Sa'adatu, Saratu ce uwar gida tana da yara Goma, maza biyar mata biyar.

Bilya shine babba sai Sani, Sunusi, Bello sai Mizbahu.

Acikin ƴaƴanta mata kuwa uku sun mutu saura biyu Hajara da Halima suke nan suka rage mata.

Yayinda Sa'adatu take da ƴaƴa Uku, namiji ɗaya mata biyu, Munir shine babban ɗanta sai Hadiza da Fatima.

Alhaji Abbas ya aurar da duka ƴaƴansa mata, yayin da ya aurar da wasu daga cikin mazan, ya na zaune da iyalinsa a unguwar ƙofar kaɗe can cikin gari.

Yaransa sun taso cikin haɗin kai da ƙaunar junansu, da kuma kyakkyawar tarbiya da suka samu daga iyayensu.

Lokacin da Alhaji Abbas ya fuskanci tsufa ya taso masa, sai ya ɗauki ƴaƴansa maza ya saka su a harkar kasuwancinsa, manyan su ke kula masa da shagunansa, ƙananan kuwa ya rarraba su a shagunan abokansa suna masu jiran shago, daga cikin waɗanda ke shagunan abokansa akwai Munir, mai gidansa ya na sonsa sosai saboda gaskiya da riƙon amanarsa, bayan wani dogon lokaci Munir ya bunƙasa har ya tsayu da ƙafafunsa ya buɗe shaguna guda biyu inda yake siyar da yaduka da atamfofin mata, a dai-dai lokacin ne kuma ya samu aikin gwamnati, bayan kammala digirinsa.

Lokacin yana da shekaru ashirin da bakwai a rayuwarsa.

Ya samu aiki a asibitin amanawa na jihar Sokoto, inda yake bangaren gwaje-gwajen jini.

Ya ji daɗi sosai, duk da albashinsa a lokacin ba wani mai yawa ba ne, a haka ya daure, domin da babu gwara ba daɗi, wannan aikin da yake bai hana masa yin kasuwancinsa ba, da ya dawo daga gun aiki yake wucewa kasuwa.

A lokacin ne kuma ya haɗu da wata budurwa mai suna Zulaiha ta waya, sai dai Zulaiha ba mazauniyar jihar Sokoto ba ce 'yar jihar Taraba ce, da farko bai san ko ita wacece ba, daga ta yi kuskuren number ta Kira shi, shikenan ya kamu da ƙaunarta, su na gaisawa a waya matsayin abokai lokaci zuwa lokaci, sai daga baya ya bayyanar mata da soyayyarsa, ba musu ta karɓa da yake ita ma tun ranar farko da suka fara waya ta ji ya kwanta mata a rai.

Shi a tunaninsa duk 'yar gari ce sai da tafiya ta yi nisa, sannan ya tambaye ta wace unguwa take anan Sokoto ya na so zai zo su haɗu.

A lokacin ne take shaida masa ita ba 'yar nan ba ce, ta na zaune a jalingo ne ta jihar Taraba.

Lokacin da ya ji wannan labarin sai jikinsa ya yi sanyi laƙwas, har ya fara sarewa da soyayyarta, sanin a yanzu ba zai iya tafiya har can ba, idan ma ya je ba lallai iyayensa su amince masa auren wacce ba 'yar gari ba.

Amma saboda tsananin ƙaunarta da yake haka suka cigaba da soyayyarsu, tare da alƙawarin cewa watarana zai zo jihar Taraba su yi zancen aure.

Watarana Munir ya shirya ya je Taraba ya gano Zulaiharsa bayan kwana biyu ya dawo gida cike da murna.

Bayan shekara biyu iyayensa suka shirya zuwa Jalingo don nema masa auren Zulaiha, duk da sai da aka kai ruwa rana, kafin iyayensa su amince masa da batun auren.

Sun isa jalingo lafiya, sannan sun samu tarba iya tarba, da karammawa daga fulanin Jalingo, kasancewar garin da nisa dole sai da suka kwana biyu a ranar na uku suka juyo cike da murna, su na ji a ransu haƙiƙa ɗan su ya yi mata, ya samu natsattsiya mai tarbiyya, daga can aka sako ranar aure nan da shekara ɗaya.

Murna ce fal ran Munir da Zulaiha, ganin suna daf da cika burinsu na zama ma'aurata.

Bayan shekara ɗaya aka sha shagalin bikin auren Munir da Zulaiha.

'Yan uwan Zulaiha suka yo tattaki har jihar Sokoto, don rako amaryarsu ɗakinta.

Bayan amarya ta tare a gidanta dake unguwar Nakasari bayan school of nursing, suka ci gaba da shimfiɗa ƙauna da soyayyarsu, zaman lafiya suke sosai ba hayaniya bare tashin hankali kasancewarsu masu haƙuri da juna.

Kwanci tashi asarar mai rai, su na nan a haka, har aka share shekaru biyar ko ɓatan wata Zulaiha bata taɓa yi ba, nan fa abin duniya ya dame ta, Munir ɗin ne ma mai lallashinta da lallaɓa ta, yana kwantar mata hankali da cewa ai haihuwa nufin Allah ce, wata rana za su samu.

Da ire-iren waɗannan maganganu yake samu ya na ciwo kanta a duk lokacin da ta tashi hankalinta akan wannan maganar.

A dai-dai lokacin ne kuma arziƙin Munir ya bunƙasa, domin yanzu ya na da babban shago a tsohuwar kasuwa inda yake bada sarin atamfofi, da wasu shaguna guda huɗu a sabuwar kasuwa ya zuba yara a ciki, inda suke sayar da kayan kitchen saura kuwa, suke siyar da yadukan maza.

Haka rayuwa ta cigaba da gudanar masu, suna cikin sukuni sosai, a shekara ta bakwai ne Munir ya canza gida daga Nakasari suka koma sama road commissioner quarters, domin zuwa lokacin Allah ya tarfawa garinsa nono, ya zama hamshaƙin ɗan kasuwa har ya fara siyar da motoci ga kuma aikinsa da yake, an ƙara masa matsayi a shekarar da ta gabata.

A lokacin ne kuma 'yan uwansa suka ƙullace shi a ransu, suka fara yi mi shi hassada da baƙin ciki, domin duk ya fi su nasibi a harkar kasuwanci saboda riƙe, gaskiya su ko da suka saka zamba sai abin nasu ya lalace, har aka kore su daga shagunan, sai shine ya ɗora su akan dukiyarsa su na kular masa da ita.

Da yake ba masu amana ba ne, sai suke yin yanda suka ga dama da dukiyar, har ta kai wata rana suka haɗa kansu akan cewa kawai za su kashe ɗan uwan ne ta hanyar da ba wanda zai gane, domin su ci dukiyarsa tun kafin matarsa ta haihu.

Akan wannan tsarin suka ci gaba da tafiya, kullum su na cikin ƙulla masa gadar zare, da ya ƙetare wannan sai su shirya wata, yayin da shi kuma yake zaune da su da zuciya ɗaya.

Duk a cikin yayyensa Mizbahu ne kaɗai ba shi da burin cutar da ɗan uwansa, ganin haka ya saka su huɗu suka haɗe kansu tare da ware mizbahun daga cikinsu kullum ce masa suke "Kai dai wallahi ka yadda zucciyarka kare ya ɗauka, ɗan uba ai ba abin so na ba."

Shi ko sai ya ba su amsa da cewa "Na ji dai, ni ina da imani, sannan ban taɓa yarda a haɗa kai da ni a zalunci ɗan uwana ba, ku dai da kuka ga kuna iyawa sai ku yi, amma ina mai maku nasiha da ku ji tsoron Allah."

Cikin wannan lokacin ne kuma wataranar Alhamis Alhaji Abbas ya tashi da wata zazzafar rashin lafiya, akan haka ya saka aka tattaro masa kan ƴaƴansa ya masu nasiha tare da gargaɗi akan riƙe amanar junansu da haɗin kai ko bayan ransa.

Bayan ya sallame su kowa ya watse washe gari ya cika, sai saƙon mutuwarsa suka ji, Munir da Mizbahu da ƙannensu mata sun sha kukan wannan rashin da suka yi, yayin da su kuwa su yaya Bilya ko a kwalar rigarsu, a ransu ma cewa suke tafi nono fari, ai gwanda ya mutu tunda dama ba sonsu yake ba ya fi son Munir, shiyasa ya ɗauke shi ya kai shi inda zai yi arziƙi.

Bayan an yi bakwan mutuwar Alhaji Abbas, iyayensu mata suka tattaro su tare da ƙara jadadda masu wasiyar mahaifinsu da ya bari.

Amma su kam su Sani, inda suka ji maganar anan suka bar ta, ba ɗaya da ta shiga kunnensu, sai ma wutar hassadar da ta ruru a ransu, sai dai sun danne hakan a can ƙasan ransu.

Bayan kamar wata uku da mutuwar uban, suka takura akan a raba gado a bawa kowa nasa, ba don iyayensu mata sun so ba, haka aka kira malamai suka raba musu gadon saboda sun takura.

Da aka zo rabon gadon Munir ya kawo shawarar me zai hana a bar wannan gidan da iyayensu suke ciki don su ci gaba da zama, ko ba komai bai kamata don Babansu ya mutu a siyar da gidan ba, amma fafur su Sani su ka ƙi suka ce sai dai a siyar.

Ganin hakan ya saka Munir ya siyawa iyayensa gida a unguwar Miyatti Allah domin su koma can da zama, bayan siyar da wannan, haka kuwa aka yi.


Bayan rasuwar mahaifiyarsu da kamar shekara ɗaya Mamansa ta rasu ita ma, ya shiga damuwa da alhinin mutuwarta ba kaɗan ba, shikenan fa shi yanzu ba shi da kowa sai matarsa Zulaiha, ya yi kuka har ya gaji, da ya ga ba mafita dole ya ɗauki na annabawa wato haƙuri.

Bangaren matarsa kuwa har yanzu bata sake zani ba, domin har zuwa lokacin bata samu haihuwa ba, don haka suka duƙufa da addu'a ba dare ba rana, ya kuma rarrabawa malamai abin sadaka domin su taya su da addu'a har saukar Alqur'ani aka yi.

¥¥¥¥¥¥¥¥¥¥¥¥¥
Allah maji roƙon bawansa.

Bayan shekara ɗaya da mutuwar Mamansa ciki ya bayyana a jikin Zulaiha, farin cikinsu ya kasa ɓoyuwa.

Bayan wata tara Zulaiha ta haifi ɗanta namiji, ya kama shekara goma cif kenan kafin su samu haihuwar.

Wannan haihuwar ta zo masu da yanayi biyu, farin ciki da kuma damuwa, domin yaron ya zo duniya a cikin wata irin siffa mai ban al'ajabi da sanya imani da tsoron Allah a cikin zuciyar duk wanda ya gansa.

Yaron ya kasance baƙi ne a kalar fata, rabin fuskarsa a shafe yake sumul ba alamar yankan halitta a gun, komai nasa rabi ne, kunne ɗaya, ido ɗaya, rabin hanci da rabin baki.

Duk da wannan irin siffar da yaron ya zo da ita, hakan bai saka Alhaji Munir ko Hajiya Zulaiha sun ƙyamaci ɗan su ba suna matuƙar sonsa, kuma sun yi godiya da wannan kyautar da Allah ya masu..........



Follow me on wattpad @ummu inteesar






ÜMMÜ INTEESAR CE🌹🌹🌹🌹🌹
*HALLITAR ALLAH CE*
👨🏻‍🦼👨🏻‍🦼👨🏻‍🦼👨🏻‍🦼👨🏻‍🦼

*(Labari mai taɓa zuciya, da sanya imani da tsoron Allah a zuciyar mai karatu)*

*ALƘAMIN: RUKAYYA IBRAHIM LAWAL (UMMU INTEESAR)*

*MARUBUCIYAR: SOYAYYAR MEERAH*
*Y'AR GANTALI*
*RIKICIN MASOYA*
*A SANADIN KAMA*
*RASHIN GATA*

*AND NOW*
*HALLITAR ALLAH CE*



________________________________


*AREWA WRITER'S ASSOCIATION*
_________________________________
*💦{Arewa ginshiƙin al'ummah}💦*
_________________________________
https://www.facebook.com/104534761033461/posts
arewawritersassociation@gmail.com

*BISMILLAHIR RAHMANIR-RAHIM*


PAGE 9-10

A lokacin da 'yan uwansa suka ji labarin haihuwar tuni sun yi nisa a shirin su na kashe shi da suke, domin a gobe ne ma suke so a kaddamar da shirin, sai ga labarin haihuwar ya zo masu.

Sun yi matuƙar baƙin ciki da haihuwar, amma ba yanda suka iya bisa ga dole suka dakatar da shirinsu, sanin cewa zasu yi 'aikin banza yiwa kare wanka' domin ko da ya mutu basu da gado saboda wannan ɗan da aka haifa masa shi zai gaje komai, kenan ya zama dole su yi sabon shiri domin ba'a fafe gora ranar tafiya.

A ranar ba a kwana ba sai da yayyen Alhaji Munir suka shirya su dukansu da dare suka je ganin jinjirin da aka haifa masa.

Haƙiƙanin gaskiya ba sun tafi ne don taya shi murna ba, sai don su ga wanda ya ɓata masu shiri domin su san irin matakin da zasu ɗauka a kansa.

Bayan shigarsu gidan a babban falo suka yi masauki suka zauna, suka yi zuru-zuru sai rarraba ido suke, kallo ɗaya zaka masu ka gano cewa suna cikin tashin hankali, Mizbahu ne kaɗai ya ke cikin farin ciki.

Bayan Alhaji Munir ya zo sun gaisa ne, suka nemi da a fito masu da Jariri su gani, saboda har zuwa lokacin ba wanda Hajiya Zulaiha ta bari ya ga ɗan, domin tsoron gulmar mutane.

Shiga ɗakin Zulaiha ya yi ya tarad da ita rungume da ɗan nata tana sharar ƙwalla, abu biyu ne ya haɗe mata ga zafin ciwon da take fama da shi tun bayan haihuwar, ga kuma damuwar wannan halittar ta ɗan nata.

Ƙarasawa ya yi, ya zauna bakin gado ya na faɗar "Zulaiha me ka damunki?"

Share hawayenta ta yi tace "Bakomai Alhaji."

Gyara zamansa ya yi ya dube ta cike da tausayawa da alhini, domin yasan yanda take ji, don kuwa shi ma yana jin irin wannan yanayin, amma ba yanda zasu yi, kyautar Allah ce, haka ya ga dama ya basu wannan kyautar cikin iyawarsa da hikimarsa, domin ya zame musu wa'azi su da sauran al'umma.

Daƙyar ya buɗi bakinsa yace "Ki yi haƙuri Zulaiha, ki jure mu samu mu cinye ƙaddararmu, ki tuna shekara goma muka share ba haihuwa, yau kuma Allah ya dube mu da idon rahama ya mana wannan babbar kyautar bai kamata mu butulce masa ba."

Nisawa ya yi sannan ya ci gaba da cewa "Allah maɗaukakin sarki yace Inna khalaqnal insana min nuɗufatin amshajin nabtalihi, faja'alnahu sami'an basiraà." Ma'ana

"Lallai mu muka halicci ɗan adam, daga ɗigon maniyyi garwayayye, muna jarabta shi, muka sanya shi mai ji, kuma mai gani."

A cikin wata ayar kuwa cewa ya yi
"Inna hadainahus-sabila imma shakiran, wa imma kafuraà."
Ma'ana

"Lallai mu muka shiryar da shi (Ɗan Adam) hanya guda biyu, ko dai ya zama mai godewa Allah, ko kuma ya zamo mai butulcewa Ubangiji."

"Duba da wadannan ayoyin guda biyu, ya kamata mu ɗauki haƙuri mu rungumi kaddara domin kada mu kasance cikin masu butulcewa ni'imar Allah."

Ya na gama faɗa ya saka hannu ya ɗauki yaron dake kwance a gabanta, cikin sanyi jiki ya nufi hanyar fita yana faɗar "Su yaya Bilya ne suka zo ganinsa."

Bai jira amsarta ba ya fice abinsa.

Tafiya yake kamar wanda ƙwai ya fashewa a ciki har ya ƙaraso gabansu, ya miƙawa yaya Bilya yaron yana cewa "Ga yaron."

Karɓarsa ya yi ba tare da ya lura ba, sai bayan ya saka yaron a cinyarsa ya kai dubansa a kan fuskar yaron, a razane ya kauda kai gefe yana faɗar "Subhanallah! Miye wannan Munir? Ina ka samo wannan dodon?"

Wannan zancen da ya yi ne ya karkato da hankalin sauran, suka kalli fuskar yaron da kyau, nan take suka razana jikinsu ya dinga kyarma, domin ko a mafarki ba su taɓa ganin mummunar halitta irin wannan ba."

Cikin dakiya Mizbahu ya matso kusa ya saka hannu ya ɗauke yaron daga kan cinyar yaya Bilya yana faɗar "Kai masha'allah! Allah abun godiya, Allah mun gode maka da wannan kyautar da ka mana."

Sauran suka tada kai suka kalli Alhaji Munir sai suka ga kamar bai ji daɗi ba, ganin hakan ya saka Sani ya yi saurin cewa "Masha'allah! Allah ya raya mana, mu zamu tafi."

Kamar masu jira, yana rufe bakinsa duk suka miƙe suna faɗar "Allah ya raya." suka yi gaba, Mizbahu ne kaɗai ya ɗan tsaya, har zuwa lokacin da Alhaji Munir ya harhaɗo kalmomi daƙyar ya ce "Yaya sun tafi fa, kada su barka a nan, mun gode sosai."

Da gama faɗa ya karɓi ɗansa tare da juyawa ya shige ciki rai a jagule, domin wannan ƙyamar da 'yan uwansa suka nunawa ɗansa bai ji daɗinta ba ko kaɗan, ko ba komai wannan yaron jininsu ne bai cancanci haka daga gare su ba.

Bayan kwana uku dangin Zulaiha suka zo daga Jalingo, su da suka zo taya murna sai abin ya rikiɗe zuwa taya juna alhini, sun matuƙar razana da ganin halittar wannan yaron.

'Yan Barka kuwa duk wanda ya zo ba a bari ya ga yaron, sai 'yan uwan Hajiya su kawo uzurin cewa ana yiwa yaron wanka ne, wani zubin su ce yana gun Babansa ne, domin sun lura da biyu mutane ke zuwa barkar ma'ana dai gulma ce kawai ke kawo su.

Ranar suna yaro ya ci sunan Abdulrazzaƙ(Bawan mai azurtawa) wanda mahaifinsa ya raɗa masa, ba don komai ya raɗa masa wannan sunan ba, sai don tuna shekarun da suka shafe kafin samunsa.

Je ka ga yanda gidan Alhaji Munir ya cika a ranar suna, 'yan shan miya da magulmata duk sun zo, a cewarsu dole ai a fitar da yaron ran suna kowa ya gani, amma sai suka ga saɓanin haka, domin sun ta bulala ido amma ba su ga jinjirin ba, da alama a ranar ma ɓoye yaron a ka yi.

Wuni cur, aka yi ana shagalin ciye-ciye da shaye-shaye, duk da ba shagalin suna ne irin wanda aka saba gani ba.

®®®®®®®

Bayan watse taron suna dangin Zulaiha suka koma gida, dama sun ƙagu a yi sunan su tafi, saboda tsakani da Allah basa iya jure kallon wannan halittar kowa ƙyamar zuwa kusa da shi yake.

Zulaiha ta yi kuka mai yawa har hawayenta suka ƙafe, ganin yanda 'yan uwan nata ke ta zumuɗi da murnar tafiya gida, ta gane nufinsu sarai, nan take ta tuno da Margayiyar mahaifiyarta da kuma mahaifinta, ta san da suna raye, ba za'a mata irin wannan cin kashin ba ko don albarkar idonsu.

Ga baki ɗayansu suka watse, ba wacce ta tsaya har zuwa lokacin da za'a fita jego.

Bayan komawarsu Jalingo da kamar kwana uku sai ciwon Hajiya Zulaiha ya motsa, ta dinga fisge-fisge kumfa na fita a bakinta, cikin kiɗima 'yan aikinta suka kira Alhaji suka shaida masa.

Ko cikakken minti talatin ba a yi ba, sai gashi ya shigo a kiɗime hankali tashe ya kinkime ta zuwa asibitin koyarwa ta Usmanu danfodiyo dake jihar Sokoto.

Bayan yin gwaje-gwaje aka tabbatar masa ta kamu da cutar convortion ne, galibi masu ɗanyar haihuwa sukan haɗu da shi, mafi yawa daga cikin matan da lalura ta sama mutuwa suke, sai mai nisan kwana ce zata rayu, wasu ma haukacewa suke.

Gado aka bata a asibitin, sai da ta shafe kwanaki masu yawa tana jinya ƙarƙashin kulawar likitoci da 'yan aikinta, sai shi kansa mijin nata.

Bayan doguwar jinya aka dawo da ita gida, ta cigaba da kula da ɗanta cikin nuna soyayya da kulawa, domin ta sa hannu biyu ta rungumi ƙaddararta.

A ranar da ta cika kwana arba'in da haihuwar Abdul, bayan fitar Alhaji Munir daga gida zuwa wurin aikinsa, tana kwance a ɗaki ita kaɗai sai yaronta da yake manne da ita ko-da-yaushe, kawai sai ciwon nata ya motsa ba tare da sanin kowa ba, ta dinga fisge-fisge gumfa na fita a bakinta, ta kwashi kusan awa a haka, kafin shigowar Ladi ɗakin, domin ta tambaye ta kalar abincin da za'a dafa.

Ganin yanayin da hajiyar ke ciki ya saka ta ratsa ihu, ta nufi boys quaters da sauri, ta lalubo wayarta har hannunta na kyarma, ta kira Alhaji ta sanar masa.

A gigice ya ƙara so ya sure ta sai Asibiti, ko tsayawa ɗaukar Abdul bai yi ba, sai Ladi ce ta yi ƙarfin halin ɗauke yaron zuwa sashen su domin ta kula da shi kafin dawowar iyayensa, domin kuwa tana matuƙar son Hajiya Zulaiha saboda yawan alkhairan da take mata.

Da isarsu asibitin, kai tsaye Emergency ya nufa da ita, cikin hanzari a ka karɓe ta zuwa ciki don bata agajin gaggawa, bayan likitoci sun yi iya ƙoƙarin su aka samu ta dawo hayyacinta, sai dai a matuƙar galabai ce ta ke, anan ta roƙi nurses ɗin dake kula da ita da su kira mata mijinta don su yi bankwana.

Bayan ya shiga ɗakin ya nufi gaban gadonta, cikin murya mai sarƙewa haɗe da kakari ta

Please Login or Register in order to submit comment