Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

karewa text din kallo, tana tunanin wace amsa zata bashi,
Nan taji dinn, karar text yakara shigowa, text dinshine kamar haka

Hmm "Naji kinyi shiru bakice ameen ba kobakya sonane"
Ameela tayi rau rau da ido kamar mai shirin yin kuka, ta daura hannunta akan kypat tana tunani mezata rubuta masa...

Na:-?Rabi'atu sk mash da Mr, Smiles??
[7:29PM, 5/7/2016] Mr, Smiles??: [9:28AM, 3/27/2016]
???? Amanar Aure ????
???????? www.gidannovels.blogspot.com
??13 and 14??

Via OHW???? www.gidannovels.blogspot.com

Sai 12pm na rana amrah tabar gidan, haka baki suka dinga zuwan gidan zuwa ganin amarya,

Ameela tarika tarbar bakin hannu bibbiyu,

Misalin karfe biyu narana bayan ameela tagama sallar azahar sannan tadaura indomi guda biyu, bada jimawaba tadafe indomi kan danni table ta daura indomi ta cinyeta tas sanna tatashi tashiga bandaki tayi wanka, tafito tasake sabon shiri, cikin atamfa dunkin yasha aiki, kuma yakama jikinta sosai tayi kyau abinta,

Kangado ta kwanta ta janyo wayarta ta kunna DATA tana jiran shigowar messages,

Cikin seconds messages suka fara shigowa,
Bayan sun gama shigowa ameela tadanna hannunta akan Facebook,
Text tafara gani na wani frd dinta wadda yace mata shi dan fim ne kuma yana online, da sauri tashiga wurinsa bayan tagama karanta text dinda yayi mata, wadda yayi mata jiya dadare bata gansaba wayarta tadauke,

Ameela "barka da warka"

Dan fim "barka dai mai kyau meyasa jiya muna cikin chart kika fita, kina fita sainaji duk chart din badadi, gaskiya nayi miss dinki beauty"

Ameela taja nunfashi tana kallon text dinsa kafin tace "hmm sory wlh wayatace tadauke, yau baku aikine, naganka online, da rana"

Dan fim "hmm muna aiki mana yanzu haka ina gurin shooting wani fim ALLURA DA ZARE, muna tare da rahama sadau da Adam zango"

Ameela ta dafe baki cike da jindadi tana masifar son rahama sadau saboda yadda take rawa, tana burgeta,

Ameeela "woow my rahama tana tare daku yanzu, wayyo jinake kamar nabiyo iska nazo naganta, dan Allah kace mata fan dinta tana gaidata"

Dan fim "hmm zataji, karki damu mai kyau aike tamusamman ce agurina, dama ace zakiyi fim, dasai kinfi rahama fans"

Ameela "hmm inada sha'awar yin fim"

Dan fim "ayya to kizo ai zaki samu shiga indai kinaxa kyau, da ilimi, kuma ina tare dake zanmiki hanya,
Baijira tayi reapply ba yasake turamata
"Sorry director yakirani, yanzu zamu koma aiki, muhadu 12:00am zamuyi magana sai anjima beauty"

Ameela "to shikenan saimun hadu" tafito daga cikin username dinsa sannan tashiga duba notification dinta da kuma frd reqst da aka turo mata kuma duk tayi accept duka mazane babu macce ko daya, a kalla kullum zata samu frd reqst kusan mutum ashirin kuma duk maza,
Hakadai takare da Facebook, sannan tafito tashiga Whtsapp,
Badama tafara duba texts dinta bakuwar numbers tagani har guda ukku, sai sauran messages na grp dakuma kawayenta da samarinta,
Bakuwar number tafarko tafara budewa sakone kamar haka "aslm, sunana ANISA daga gombe gaskiya pic dinnan dakika saka yamun kyau shine naji ina son kizamo kawata daga Sun shine grp"

Ameela tayi murmushi kafin tafara typing na reapply, "wslm, sannunki da zuwa kuma nagode, nikuma sunana Ameela"
Bayan tagama typing din tatura mata sannan tafito tashiga bakuwar number tabiyu, sallamace kawai akayi mata tayi reapply sannan tafito ta duba ta ukkun, sakone kamar haka "wow kyankyawan surar jiki kamar na bata, ga manyan boobs, gaskiya ta ko ina kin hadu"
Tsaki taja tafara typing "kai malam dakata nifa matar aurece"
Ta sender masa daidai dayana online,
Alamu tagani na tabbas yagani kuma yakaranta, a saman number aka rubuta is typing,
Ta mannawa number ido tana jiran zuwan sakon, bada nimawaba sakon yashigo ta danna cikin number tafara karantawa "?? wai matar aure, to ainima namijin aure ne, to koma daike mecece, nidai nagani inaso kuma, ina fatan zan more dake, sunana kamal"

Ameela jitayi kamar tayi block dinsa saikuma tafasa

Ameela "kafita harkata nagaya maka nifa matar aurece, kuma ni bayar iska bace"

Kamal "hmm kwantar da hankalinki yan mata nifa ba tabaki zanyiba kawai dai zamuna rikayin sex chart dakuma send pic din .... Kidai gane, gaskiya kinada kyau sosai domin ni harna sace pic dinki a dp dinki yanzu haka shinake kallo inasamun natsuwa"

Ameela cike dajin haushinsa tarubuta masa "dan banza, marar aikinyi tare tsaki sanann tayi block dinsa,
Sannan tafito taci gaba da sauran text dinta,
(Nace yayi kyau Yau Ameela ta hadu da gamonta, irin mazan nan masu lalata sakankun mata a chart, Allah ya shirya mu" ameen

Na:- ?Rabi'atu sk msh da Mr, Smiles??
[9:43AM, 3/27/2016]
???? Amanar Aure ????
???????? www.gidannovels.blogspot.com
??15 and 16??

Via OHW???? www.gidannovels.blogspot.com


Number data rubutawa HMM taduba baya online amma yabar mata sakon cewa yau su hadu karfe shabiyun dare, akwai magana, kuma yaga pic yagode"

Tagyara kwanciya tayi, tai ajiyar zuciya sannan taci gaba da chart dinta,
Tajima tanayi da samarinta, dakuma kawayenta,
Sannan taji ankira sallar la'asar, amma taki ajiye wayar haka taci gaba da chart har aka tayar da salla, aka gama kamar ba a kunnen akayiba, ko motsawa batayiba, balle tasa niyar tashi tayi sallah,

Saida tagaji sannan tatashi ta ajiye wayar akan gado tanufi bandaki tayi alwala, tun acikin bandaki takejin karar wayarta, amma taki fitowa saida tagama alwala sannan tafito,
Tataras anmata, 3miss call,

Zare ido tayi alokacin data duba number babu shakka number guy din nan ce wadda yayi mata maganar banza a Whtsapp chart tayi block dinsa, dafe baki tayi tana mamaki tace "nashiga ukku"

Dasauri tashiga blacklist tasaka number shi sanann tajiye wayar tajanyo sallaya tafara sallah,
Bayan tagama sallah, tadanyi adu oi sannan takara janyo wayarta tana kallon pic dinda sukayi dazu ita da kawarta amrah,

A hakali taji anturo kofar dakin anshigo,
Hilal ne rike da jakar aiki a hannunsa alamar gajiya ta bayya a fuskarsa karara, tashi tayi, tai masa sannu dazuwa, sannan takarbi jakarsa, cike dajindadi,
Hilal yakarasa bakin gado yazauna, bayan takai jakar a mazauninta,
Ameela tazo tazauna kusa dashi tana murmushi "Dee mezakayi wanka, ko bacci ka huta domin naga alamar kagaji."

Hilal yajuyo ya kalleta cike da kasala yaja tsaki, kamar mai rowar muryarsa yace " wanka zanyi, kuma idan nafito zanzo muyi fira kafin sallar magrib",

Ameela tace "to shikenan, bari na hada maka ruwan zafi" tana karasa maganar tatashi tanufi bandaki, bada jimawaba tafito tace "Dee evry thng is rdy"

Hilal yatashi yacire kayansa ya daura tawul yanufi bandaki,
Bayan yafito suka zauna sukayi fira irin ta mata da miji, har zuwa magriba, sannan hilal yafita yaje masallaci yayi sallah,
Bai dawo gida saida aka kira isha akayi sallar isha, bayan angama sannan yadawo gida, yatsaya yarufe kofofin gidan sannan yakaraso cikin gidan,
A kan kujera yasameta tana dannar wayarta, tanajin shigowarsa tayi sauri ta ajiye, tana murmushi,
Shima ya mayar mata da amsar murmushinta kafin yakaraso gurinta yasamu kujera yazauna, suka kara taba fira, sannan hilal yatashi yace "tashi muje mukwanta" bata musa masaba tatashi suka nufi daki,
(A lokacin harna shiga dakin nafara rubuto muku abinda zai wakana sai abdul yayi saurin janyoni baya, yace karnaje lekon asirin ma aurata bakyau, banshiga dakinba, nafito amma ina gani aka kashe wutar dakin), ... Toooh??

Na:- ?Rabi'atu sk msh da Mr, Smiles??
[10:20AM, 3/27/2016]
???? Amanar Aure ????
???????? www.gidannovels.blogspot.com
??17 and 18??

Via OHW???? www.gidannovels.blogspot.com

tunda sassafe natashi, naci gaba da rubutuna,
babu abinda yachanza game da chart dinda Ameela takeyi, amma dai jiya bata samu damar chart din dareba,

Ko yau hilal bai tsaya karyawa cikin gidan ba, wanka kawai yayi yadauki jakarsa yawuce gurin aikinsa,

Bayan fitar hilal ta dauki wayarta tayita chart domin bata aikin komai, sabuwar kawarta data samu wato anisa sunyi chart yau mai dadi kuma hartayi save din number ta domin taga anisa tana da kirki sosai, duk wadan da tacewa zasu hadu shabiyun dare jiya, tabashi hakuri tace musu baccine ya dauketa, bata farkaba sai safe... Kujimun karya irin ta Ameela,
*****
A WANI GIDA

Wata wainar ake toyawa,

A Falo suke zaune sunyi jugum jugum, suna jiran amsar daga bakin AFHAM,
Afham yayi shiru ya sunkuyar da kansa kasa, yakasa magana

kawu bello yace "magana muke maka Amma kayi mana shiru, shin kanason AMAL ko kanada wadda kakesone"

Afham ya girgiza kai "aa kawu babu wadda nakeso amma kuma kawu maganar amal dince.."

Abban afham dayake zaune a gefe haushin afham yakamashi yayi saurin cewa "maganar amal dince.. To fada mana, abban afham yajuya ya kalli kawu bello yace "nifa kaine kake masa ta laluma, mumuka haifesa koshine ya haifemu, kagafa saboda gudun irin wannan matsalar yasa naki barinsa yayi karatu anan naija, nakaisa cen waje saboda karya taso ya bijirewa umarninmu, nifa nafada wannan auren shida Amal saifa anyisa domin wannan burin mune tun muna yara"

Kawu bello yace "a a yaya karka yiwa yaron nan abinda bayaso, yanzu dai abarshi yaje yayi shawara, kawu bello yajuya gurin afham yace " tashi kaje kayi shawara zamu nemeka" Afham yatashi ransa abace, shiba macceba amma ace za'ai masa auren dole, shifa baya son Amal dinnan,
Haka dai yashiga dakinsa zuciyarsa cike da wasi2 kala2,
Ya zauna gefen gado yayi jim yana tunanin wani abu saikuma yatashi yafito, yanufi dakin kanwarsa ANISA wadda akoda yaushe itace abokiyar shawararsa,

Akwance yasameta saman gado, Tana dannar waya, yayi sallama sannan yashigo dakin,

Dago kanta tayi tana murmushi ta amsa masa sannan yanemi gure a gefen gado yazauna yadan saka murmushi " chart kike koh, bakida aiki sai chart,.sai ciwon chart yakamaki"

Anisa tayi dariya sosai "la yaya harda wani ciwon chart akwai ne"

Afham yace "sosai ma idan mutum ya nace akan chart to chart zaibi jikinsa mutukar baiyi saba to bazaiji dadi ba"

Anisa tace "toh wannan likitancin kane yaya, anisa tatashi zaune tace "ai nama gama chart din daman wata sabuwar kawace nasamu wallahi yaya karka ganta ta hadu kamar ita tayi kanta,

Anisa tashiga gallery cikin Whtsapp prfil pc takai ga photon ameela tatsaya "kaganta yaya, sunanta ameela, kamar baindiya" tamikawa afham wayar, yakarba, dam yaji gabansa yafadi a lokacin dayayi tozali da kyankywar fuska ameela, sak irin yadda yake neman macce dakyau da diri da kuma kyakkawar surar jiki,
Anisa tana gefe tana dariya ganin yadda afham yakurawa photon ido,
Kamar daga sama taji muryar ummanta tana kiranta, dasauri anisa ta karasa bakin gado tasaka takalminta, tayiwa afham alama da hannu "ina zuwa yaya,.bari nazo musa labule idan yarinyar taimaka," takarasa maganar cike da zolaya dakuma dariya,

Afham gabaki daya pic din yatafi da imaninsa, lumshe ido yayi sannan yasake budewa, tabbas yasamu irin maccen daya jima yana nema, wadda tajima tana zomasa a mafarki,

baimasan da fitar anisa ba yajuyo yayi yana waige waige ganin bata cikin dakin yasa yayi saurin fitowa da wayarsa yashiga xender yatura pic din, sannan yashiga Whtsapp yaga number da aka rubutawa ameela, da sauri yadauki number yayi save a wayarsa ya ruba mata ZABINA,
Sannan yajiyewa anisa wayarta a kan gado yafita yakoma dakinsa,
Akan kado yakwanta yakamo pic din ameela yana kallo yana maimaita sunan a bakinsa, yaa lumshe ido sunan da surar jikinta duk sun masa, tabbas ya yayi gamu da katar kuma yanzunne zai samu damar tunkarar su kawu bello da abbansa yafada musu cewa yasamu wadda yakeso, matukar wadda yake gani a pic dinnan ta aminta dashi, duk azuci yake fadan wadan nan maganganun, a fili kuwa tambayar kansa yake, to ta ina zaifara....

Hmm akwai chakwakiya kenan.. muje zuwa

Na:- ?Rabi'atu sk msh da Mr, Smiles??
[7:29PM, 5/7/2016] Mr, Smiles??: [9:14AM, 4/2/2016]
????Amanar Aure????
???????? www.gidannovels.blogspot.com
??23 and 24??

A hankali take typing, ba 'ason rantaba harta karasa rubuta masa" ina son sosae, har cikin zuciyata"

Hmm Yace "Amma naji dadi sosae Ameelanah??"

Suna cikin fira Afham yahau, yaga taga text dinshi harta karanta amma babu amsa,
gabanshi ya fadi a ranshi Yace "Ya Allah ka taimakeni akan soyayyatah! Ganinta online yasa ya shiga rubuta mata wani text din..

Afham "Sunana Afham, ina zaune a garin gombe, na ansa numbrki ne a wurin qanwatah Aneesha, Ameelah kinyi matuqar burgeni ne, saboda irin kyaun da Allah yamiki, lokaci daya naji zuciyatah ta kamu da sonki, ina fatan babu wanda ya rigani!"

Ameelah ta jima tana tunani akan text din kafin ta bashi amsa, kalamansa masu dadi sun ratsa zuciyarta,

Ameelah "gsky ngde sosae??"

Afham Yace "hka kawai zakice, kinko san yadda zuciyata ta kamu da sonki, dan Allah kibani cikankiyar amsa wadda zata gamsar da zuciyata"

Ameelah taja nunfashi tana nazarin kalamansa masu sanya zuciya shaukin so da kauna, sannan tayi murmushi,

Ameelah "??hmm tohm mezance??

Afham yace "inaso ne ki bani amsa, wlhy Ameelah daga jiya zuwa yanzu zuciyatah qara cika take da zazzafar qaunarki, idanuwana basa muradin kallon komai bayan kyankyawar fuskarki, ki aminta dani namiki Alkawarin bazan barkiba"

Murmushi take tana kara maimaita kalaman a kwakwalwarta, kanta yadau zafi, tana zaune ta kurawa text din ido,
TaRasa abinyi gashi bangare guda HMM text dinshi sai shigowa suke shima da irin nashi rigimar, ga messages na Facebook sai shigowa suke,
rufe datar kawai tayi ta zauna ta dafe kai tana tunanin Afham,
( Ameelah tabani tausayi, irin zaman danaga tayi saikace shege agurin rabon gado, saikuma wata zuciyar tace meye abin tausayi a tattare da wannan bayan nema take taci AMANAR AURE, ai Allah bazai taba barinta tasamu kwanciyar hankali ba)
*** ***
Batasan iyakar mintocin data bata tana tunani ba sai dai qarar wayarta ne daya katseta, number Aneesah ne da tayi saving da 'qawah' sai data kusan katsewa kafin ta dauka ta sanya a kunne cikin rashin kuzari.

Tun kafin tayi magana Aneesah cikin barkwanci ta fara cewa "haba qawah, gsky banji dadiba yanda kika saka yayanah cikin damuwah, Allah yana sonki da yawah ba yabon kai ba yen mata da yawa na sonshi amma ban taba ganin wadda yakeso kamanki ba! Don Allah ki amince mishi, kinji qawata"

Ajiyar zuciyah Ameelah tayi kafin tace "bazaki gane bane qawah matsalan kawai itace inada...."
katseta Aneesah tayi dacewa "kina dame nidai karkicemun kinada saurayi, kuma basaina gane ba kawai ki fitar da yayana dga cikin damuwah, kinga yadda yashigo dakina kuwa, a gigice wai ameelah taki aminta dashi"

Murmushi ameelah tayi sannan tace "shikanan zamuyi magana dashi anjima"

Dariyar jin dadi Aneesah tayi kafin tace "ngde sosae qawah bari na mishi Albishir"

Ameelah tayi saurin cewa "kenifa bacewa nayi na amint.... kafin Ameelah tayi magana aneesah ta kashe wayan, Shirun da ameela taji yasa tarinka fadan Hello, hello, a lokacin tafahimci cewa takashe wayar, tayi ajiyar zuciya, zuciyarta cike da tunani kala kala..

Na:-? Rabiatu sk msh da Mr, Smiles??
[9:14AM, 4/2/2016]
????Amanar Aure????
???????? www.gidannovels.blogspot.com
??25 and 26??

Ameelah ta dafe kanta kafin ta yarfar da hannu tace "tohm miye ma A cikin Soyayyar? Soyayyah ne pa kawai shi da yake gombe ma ina xai ganni?" A zuci tayi maganar sannan ta buda datar ta taci gaba da charting dinta, amma a lokacin afham baya online, batama shiga Whtsapp ba Facebook tashiga tayi chart da dan fim..

Akayi sallar laasar duk tana zaune, charting yahau kanta,
(Wa'iyazubillah, wannan jarabar chart da masifa take, yanzu Ameelah ko tunanin mutuwa batayi, hmm Allah yakara karemu da kariyarsa, wai kaga mutum ana sallah shiyana zaune yana charting, wai bayason sauka, to idan baisauka anan duniyaba ai ya sauka kiyoma, Allah ya kyauta)
*** ***
Har lokacin dawowar hilal yayi babu Abinda tayi tana kwance falo saman kujera ya shigo da sallamarshi da sauri ta ajiye wayar tana kallonshi kamar marar gaskiya sannan ta mishi sannu da zuwa..

Ya amsa a gajiye, ganin yanayinta yasa baikara maganaba ya shige dakinsa, dasauri ta janyo wayarta ta rufe data, tayi ajiyar zuciya, tana zaune ya fito ya zauna saman kujera ya kishingida, Yace "wlhy yau na gaji da yawa, ga yunwa da nakeji"

Ameela ta dubesa tayi murmushi Tace "ayyah sannu"

Hilal yace "sannu bazata gamsar da yunwar danakejiba ki daukomin Abncinah inci"

cike da mamaki ameelah Tace "Yau kuma?

Hilal Yace "ban gane yau kuma ba?

Ameela takara yin murmushi Tace "naga ko breakfast baka tambayana ne, Yau kuma harda tambyar Abncin rana ko ka manta satin daya daka bani, baifa cikaba saura kwana biyu??

Girgiza kanshi yayi cikin takaici yaja tsaki, sannan ya daure ya danne damuwarshi ya tashi tsaye ya koma daki, ciki minti biyar ya fito ya canja shiga da mukullin motah a hannunshi, Yanufi kofar fita, tana zaune tana kallonsa,

Har yakai bakin kofa bai ce matah komi ba,
sai itace tace "ina kuma zakaje?

Hilal Yace "zan fita ne inciyo abincin waje, tunda nayi aurenma bazan huta ba"

Muryarta a shagwabe kamar zatayi kukah tace "ayni daman baka damu da cin abincinah ba"

murmushi hilal yayi yace "hmm ki fadi Abnda kike bukatah zan zo miki dashi, domin nasan kema yunwar kikeji"

Mikewah tayi tsaye sannan tace "ni sai dai ka tafi dani"

cikin mamaki yake kallonta kafin yace "ina zakije ko sati bakiyi da aure ba? Ina zanbarki ki fita wani ya kallemunke, Kiyi zamanki ki huta, kinji"

sororo tayi a tsaye don tasan maganace ya gaya matah, tana tsaye har yayi ficewarshi.

Ta tabe baki ta zauna taci gaba da chating dinta, kusan minti biyar tana jiran Afham har a lokacin bai hau ba, ta kagara suyi chart, ta rufe datar domin duk taji chart din ba dadi, ta ajiye wayar akan kujera, "Allah tadani naje nayi sallah" tafada sannan tatshi tanufi dakinta tashiga bandaki, tayi alwala sannan tafito tafara sallah, tayi raka'a biyu, tana cikin tahiya, taji karar wayarta a falo, a dai dai lokacin Hilal yashigo falo, da ledojin abinci a hannunsa, Ya dallawa Ameelah kira, saida ta zabura duk da sallah take, gabanta yayi mummunan faduwa,
Yau kam asirina ya tonu" tafada a zuci...

Na:-? Rabiatu sk msh da Mr, Smiles??
[7:06PM, 5/23/2016] Mr, Smiles??: [8:11PM, 5/3/2016] Mr, Smiles??: [6:16PM, 4/2/2016]
???? Amanar Aure ????
???????? www.gidannovels.blogspot.com
??27 and 28??

Via OHW???? www.gidannovels.blogspot.com

Jitayi anturo kofar dakin da karfi, duk inda ilahirin jikinta yake yadau rawa, tayi matukar tsorata,
Hilal yashigo yatsaya yana kallonta tana sallah, ya girgiza kai ransa a bace yaja tsaki yafita ya koma falo,

Jitakeyi kamar takarawa sallar gudu, shaf2 ta gama sallar ko adu'a bata tsaya yiba tafito falo a gigice,
Wayarta tagani a hannun hilal, ta zare ido ta zabura kamar anmata sock, tayi matukar razana, taku takeyi cikin sanda ta sunkuyar da kanta kasa,
Jin tafiyarta yasa hilal yajuyo sukayi ido hudu taga yanayinsa ya chanza, ta tsaya cak guri daya tana jiran taji mezaice
A zuci take fadan nashiga ukku yau ruwa yakarewa dan kada"
Ameela ! Hilal ya kirata,
Cike da fargaba murya na rawa ta amsa,

hilal yace "karaso nan" ya nuna mata kujera da hannunsa,
Kafafuwanta har wani rawa suke dakyar takarasa bakin kujera tazauna, ta sunkuyar da kai tana wasa da dan yatsan, gabanta naduka shida shida,

Hilal yadubeta cike mamaki " ameelah kinbata wayonki a banza wlh, kin zalunci kanki, wane irin rudine shedan yamiki dahar...." Ameela ta katse masa magana da shakankiyar muryarta, kamar mai shirin yin kuka tace " dan Allah dee kayi hkr wlh..."
Hilal yadaga mata hannu, idanuwansa sunyi jajir yace "banason naji komai daga bakinki, wannan laifin da kikeyi bani kika yiwaba Allah subhanahu wata'ala kike sabawa, hilal yalura da irin tashin hankalin da ameelah take ciki, hawaye suka soma sauka kan kumatunta, yadan tsayar da maganar sa yana kallonta kafin yaci gaba dacewa "meya hanaki sallah da wuriii"

Dasauri ameelah tadago kai tallesa, zuciyarta harwani sanyi tayi, tace
Dee wlh bacci nake, koda natashi time ya wuce, amma kayi hkr bazan karaba"

Ajiyar zuciya yayi ya tashi tsaye, sukayi ido hudu yace " laifinki biyu kenan kinyi karya a yanzu kuma kinkiyin sallah da wuri, ameelah matukar kinason muzauna lfy dake a cikin gidan nan to karna kara ganin kinyi late din sallah", mika mata wayarta yayi kafin yaci gaba da cewa "karbi wayarki naxo naga ana kira, kafin nakarasa gurin wayar kiran ya tsinke, wata number mai suna Hmm"
Cike da firgita ameelah tace " ehhhm"

hilal yakara kallonta "eh amma bansamu daukaba koda na naxo ta tsinke"

ya mika mata wayar sannan yajuya yanufi dakinsa,

Wata irin babbar ajiyar zuciya tayi, ta share hawayen dake edonta, yana shigewa daki tadaga hannu sama "Allah nagodema "
Tana gama fadan hakan ta sauka daga kankujera ta zauna kasa. Ta janyo ledar abinci tafara budewa...

Na:- ? Rabi'atu sk msh da Mr, Smiles??
[6:31PM, 4/2/2016]
, ???? Amanar Aure ????
???????? www.gidannovels.blogspot.com
??29 and 30??

Via OHW???? www.gidannovels.blogspot.com

Favorite food dinta yasaya mata tuwon amala da miyar yakuwa,
Zauna tayi ta gyara cikinta, taci saida ta koshi sannan tatashi, taje kichin ta wanke hannayenta tayi drooping din ledojin a dustbin,
Ta wuce dakinshi kai tsaye,

tatura kofar dakin tashiga sannan tayi sallama, a kwance tasamesa saman gado, dagashi sai singlet sai gajeren wando yayi shirin bacci,

Batare daya ko motsa daga kwanciyar dayakeba ya amsa mata sallamar.

Sum2 ameelah takarasa bakin gadon ta zauna tana facing dinshi,
Tayi gyaran murya tace " fushi kake dani mijina"

Baikulata ba hasalima juya mata baya yayi,

Sai abin yasoma bawa ameelah dariya domin tasan hilal bazai taba fushi da ita,.ba. ( a zuci nace "oooh shiyasa takecin Amanarsa. Dan taga yana sonta, da karfi naji an firgi biro daga hannuna, "idan kingaji da rubutun kibani naci gaba" Bro abdul yafada ransa a bace, na shagwabe masa fuska kamar zanyi kuka nace " haba dan Allah nina cemaka nagajine. Tunanin wani abu kawai nake" sai yace "to naji karbi amma karki sake" nayi murmushj na karbi biron naci gaba da rubutu" ...
*** ***
Ameelah takara matsawa kusa

Please Login or Register in order to submit comment