Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ji kake shuuuuuuuuuuuuu kamar kana cikin Mak'abarta nan, kai gaba d'aya ma garin haka ya koma.

A hankali Farida ke tsallake Gawar mutane tana ware idonta waje, zuciyarta na bugawa wasu hawaye na tsananin tausayin kanta dama wa'inda suke tare dasu, duk da tasan sune suka ja masu wannan shiga masifar.
A haka kuma idan ka ce zakai magana su ce zasu rufe ka da fad'a, sufa ta lura ma wasu daga cikinsu har yanzu ba nadama a tare dasu.

Kamar jira ake Farida ta tsallake wata Gawar mace dake yashe a k'asa.
Budurwar Al'ameen ce a bayanta, ta zo tsallaka gawar da Farida ta tsallake kawai kamar saukar aradu gawar nan ta tashi tana rarumo k'afar budurwar tana k'ok'arin kai mata cizo.

Wani uba-uban ihu ta saki wadda yasa gaba d'ayansu toshe kunnuwansu, domin ihun da mugun k'arfi ta sake sa, wani irin ihu take tana kiran sunan Al'ameen.

Duk ya gama rud'ewa ya rasa ta inda zai fara kawo mata d'auki shima.

Su Jasmin ko da Hanan k'ara matsawa suke daga inda suke suna dafe da k'irjinsu dake bugawa sosai na tsallar tsoro da wata irin razana da sukai.

Wata k'arar ta kuma kwalawa a sadda taji saukar hak'oran matar akan k'afarta, wani shegen zafi da rad'ad'i ne yayi ma Kwakwalwar kanta dirar mikiya, ta saki wata k'arar tana kiran.

"Wayyo Allah na shikenan ta kashe ni wallahi, shikenan nima na koma irinsu, na shiga uku wannan wacce irin masifa ce, Allah ya isa tsanina dakai Faruk duk kaine silar shigowarmu wajan nan, ashe ajalina na cikin wannan company nin, wayyo Allah na, wayyo wayyo wayyo".

Matar ce ta mik'e tana gunji kamar Mage ta samu b'era tana niyar sake kai mata wani cizon suka ji k'arar saukar wani k'arfe da Al'ameen yayi nasarar samu a wajan basu lura ba ya kwad'a mata shi a a tsakiyar bayanta, tana sake juyowa garesa tana niyar kamosa shima tana son kai masa cizo had'e da d'an wani ihu da gunji irin nasu na Zombies idan suka ji azaba.
Ya d'aga abunda ya kwad'a mata ya sake kwad'a mata shi a tsakiyar kanta, sai a lokacin ta zube a sume.

Kamo hannun Budurwar tashi yayi yana mik'ar da ita.
Sai aikin kuka take domin ita kam tasan nan da wani lokaci zata koma Zombies.

Wani kallo Jasmin take binta dashi batai wani nauyin baki ba wajan cewa.

"Tsakani da Allah Al'ameen asan yadda za'ai da wannan budurwar taka, Fisbilillahi wallahi bazata zauna damu ba, haka kawai bamu ankara ba ta zama irinsu ta zo ta ce zata farmaki wani daga cikinmu, nifa gaskiya a yanzu ban yarda da kowa ba, tunda k'anwarku ta mutu, to ya kamata kowa ma aka ciza to ku kyale shi kawai wallahi".

Rushewa da kuka budurwar tayi tana bak'in cikin abunda Jasmin ke fad'a.

A zuciye ta nufi inda Jasmin take tsaye tana cin kwalar rigarta tana cewa.

"Ashe Jasmin kece mutum ta farko da zaki fara gudu na?".

Wani d'an iskan kallo Jasmin ta jefa mata, tana saka hannunta ta yakice ta daga jikinta, tana nunata da yatsa ta ce.

"Karki sake wannan jikin naki ya ce zai sake tab'a jikina, kuma baki ji miye na ce tun muna a cikin mota a hanyarmu ta zuwa wannan wajan bane?, ke ko uwata ce ke na rantse da Allah yau sai mun raba hanya dake, bare babu uwar da muka had'a dake".

Cike da tsananin mamakin Jasmin Farida ke kallonta, tana zare ido waje, uwafa?, anya Jasmin nada hankali kuwa?, bata gudun itama gobe a cije ta?, amma ta manta da hakan, sai wani tayar da jijiyoyin wuya take, sai ka ce tana da tabbas d'in ita Zombies d'in Allah ba zai basu sa'ar su cije ta ba.

Cike da bak'in ciki da jin zafin Jasmin budurwar ta wanke ta da wani Mari, wadda Jasmin ta zabura a kid'ime domin Marin yazo mata a bazata ne, bata lura da lokacin data d'aga hannu ta kai mata marin ba.

Dafe k'uncinta tayi tana fiddo idonta waje bata tsaya b'ata lokaci ba wajan d'aga hannunta itama tana sauke mata wani gigitaccan mari har biyu wadda ya ci uwar nata zafi wadda tayi mata.

Ganin suna son had'a jiki suyi dambe yasa Al'ameen shiga tsakiyarsu ransa a mugun b'ace yake cewa.

"Wai mi yasa ku mata k'aramin tunani ne da ku?, miye abun fad'a muna cikin wannan halin?".

Nunata Jasmin take da yatsa a yadda take magana zaka san lokaci d'aya ta tsani budurwar Al'ameen d'in, fad'i take.


"An gaya miki ni sakarya ce dolowa irinki, da zan tsaya ki mare ni ban rama ba, ai ko ko uwar data haifeki tayi kad'an ta ce zata mari Jasmin bata mara ba, ki kiyaye a nan gaba".

Abu biyu ya taru yayi ma Budurwar nan yawa ga zafin cizon da aka danna mata, ga bak'in cikin ta kusa komawa Zombie, ga kuma tsanar Jasmin da take ji idan batayi sanadiyar zamowar Jasmin Zombie ba, ko tayi sanadiyar mutuwarta, to gaskiya bata haifo ba, hankalinta bazai tab'a kwanciya ba.

Wani kukan kura Budurwar tayi, Jasmin bata ankara ba Budurwar ta kamo wuyan Jasmin dai-dai fatar wuyanta tasa farce ta yakoshi Jasmin d'in, wacce bata lura da yakoshinta tayi ba, dama gashi tana tara farce zak'o-zak'o a hannunta.
Kuma dama tasan tunda yanzu jinin jikinta ya gama kamuwa da cutar, to tana da tabbacin idan ta yakoshi mutum a yanzu zai iya zama Zombies shima a ko wanne lokaci.

Jasmin zata kai mata duka a baki Faruk ya hankade Jasmin daga wajan, har yanzu Jasmin bata ji wani zafi ko rad'ad'in ciwon da Budurwar ta ji mata ba.

Fahimtar hakan da budurwar tayi ta saki wata shegiyar dariya, wacce tasa su Farida mamakinta, kai har Jasmin d'in, batayi gigin nuna mata wata illa da tayi mata ba, sai ma nunata da take da yatsa tana dariyar tsananin mugunta.
Gaba d'aya Jasmin sai taji ta tsargu, ta kama duba jikinta, amma babu abunda ta gani a jikin nata.

Kamar jira ake kawai sukaga budurwar an fyad'ata da k'asa, jaa da baya suka kama yi gaba d'ayansu, suna kallon yadda take komawa lokaci d'aya, jikinta ya kama sauyawa yana komawa color blue, jijiyoyin jikinta sun fito rud'u-rud'u, fatar jikinta ta koma ruwan toka.
Farida tana kallon yadda take wage baki tana ihu lokacin da k'asusuwan jikinta ke kakkaryewa, hak'oranta sunyi wani masifar tsini, na gaban bakinta.
Wata irin mik'ewa tsaye tayi tana layi, kanta ya jirkice kafafuwanta ma haka.
Da gudu suka fara ficewa daga company nin, kusan zan iya cewa Jasmin ce farkon arta na kare.
Sauran suka take mata baya.
Kamar jira ake su fara fita, suka fara ganin Zombies masu yawa suna fitowa daga wasu sassa na company nin, kota ina kamar zaro su ake suna fitowa suna niyar fitowa daga cikin company nin.
Faruk ne yayi azamar idasa ficewa kusan shine k'arshe, yasa iya k'arfinsa yana son rufe k'ofar company nin, domin idan wa'innan Zombies d'in suka fito da suke gani suna b'allowa daga cikinsa, to komai na iya faruwa.
Al'ameen ma ya taimaka masa da kyar suka datse k'ofar Zombies na gaf k'arasowa wajan k'ofar.
Suna jin lokacin da suka iso bakin k'ofar suna bubbuga k'ofar a hankali suna suna girgiza k'ofar da son b'allata.
Kamar ance Faruk ya waiga yaga wani k'aton duram mai cike da fetur a cikinsa.

Da sauri ya k'arasa inda yake yana ma Al'ameen alamar ya taimaka masa.

Bai san abunda yake nufi ba, sai da yaga Faruk d'in yasa inda duram d'in yake iya k'arfinsa ya jirkitar da Duram d'in fetur d'in da ke ciki ya fara malale k'ofar Company nin.
Ja da baya suka soma yi sosai Faruk ya d'akko wani dutse na k'ank'ara iya k'arfinsa ya irink'a had'e dutsen da d'an uwansa, suna bada wani sauti, can saiga wuta suna kawowa, idan ya had'esu waje d'aya.

Suna bada wutar yayi tsalle ya jefar dasu a cikin fetur d'in daya malale a k'asa.

Ai ko nan take wuta ta fara ci a wajan, kamar wutar daji ta fara kamawa da yawa tana nufar cikin company nin.

Suna tsaye nesa da wajan suna gani a sadda wutar ke k'ara ci sosai harta kama cikin company da yawa suna iya jiyo ihun Zombies dake ciki, had'e da kururuwarsu.

Wutar har wani tashe take sama, saboda zuwa lokacin ta gama kama gaba d'aya wajan, har sai da su Faruk d'in suka had'a da d'an gudu suna son barin wajan................


*GAWA TAFE, NA KUD'I NE AKAN NAIRA D'ARI HUD'U KACAL #400, DAGA EPISODE 9TO10, ZAI TSAYA FREE PAGES D'IN, KARKU BARI A BAKU LABARI, SALON LABARIN NA DABAN NE, BA SAI NA TSAYA INA MAKU DOGON SHIRHI BA, KUMA KUN RIGA DA KUN SAN AL'K'ALAMINA BAYA RUBUTUN BANZA*


*Zaka iya turo kud'inka ta wannan number d'in*👇
8130479973 Fatima Rabi'u Opay bank

Saika turo shaidar biya ta wannan number d'in 👇
08130479973

*GAWA TAFE*
(Zombies story)
On2025


*©Zahra Royal Star*



*ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION*


*EPISODE 9TO10*
*END OF FREE PAGES*



*G.R.A. Estate Residential Area, Katsina State Nigeria*


*ANAM POV*


Da mugun gudu Anam ta sakko k'asa tana duban Mom dake tsaye hankali a tashe rik'e da waya a hannunta, sai kiran waya take amma ana cewa wayar a kashe.


"Mom wallahi nima sai kiran wayar Hanan nake ita da su Faruk amma a kashe, ya za'ai su bi su kashe wayoyinsu wannan wane irin hauka ne haka Mom?".

Mom dake cikin halin rud'ani itama ta sake gwada kiran nasu again a kashe, sauke wayar tayi kawai tana dafe kanta ta kalli Anam tana cewa.

"Please Anam ina cikin rud'ani, ki barni da abunda nake ji, gaba na fad'uwa yake amma kinzo kaina sai hayaniya kike min".

"Haba Mom nima fa hankali a tashe yake, ya kamata ace tun sadda suka isa su kira mu ko?, amma har yanzu shuru"


D'aga kanta Mom tayi ganin Dad ya shigo Parlon a rud'e yana kallon Anam duk ya rud'e yana cewa.

"Maza-maza Anam kunna min Tv, an kira ni waya wai na kalli Labarin duniya na yanzu da ake haskawa akwai matsala da alama".

Gaba d'ayansu gabansu ne ya yanke ya fad'i bare Mom ido a waje take bin Dad da kallo ta kasa cewa komai.


Hannun Anam na rawa ta d'akko romot tana kunna Tv had'e da kamo tashar labarin duniyar.

Muryar mai labaran ce ta karad'e parlon a inda yake cewa.

"A labaran namu na yau zaku ji cewa a K'asar Goa wata muguwar annoba ta kunne kai a gabashin k'asar gaba d'aya, a inda yanzu haka cutar na dad'a yad'uwa kamar wutar daji, a inda shugabannin K'asar ke bada labarin cewa suna buk'atar taimakon K'asashen dake kusa dasu, kai harma da K'asashen duniya baki d'aya, a inda suke buk'atar kwararrun Likitoci wa'inda suka kware ta fannin aikinsu, domin suna son gano maganin da zai warkar da wannan Cuta, sai kuma buk'atar Sojoji wa'inda suka kware ta fannin yak'i domin yak'in wa'inda suka riga da sun gama kamuwa da ita wannan annobar, wacce idan mutum ya kamu da ita cutar yake cin naman mutum d'an uwansa. To sai dai muce Allah ya kyauta, kuma Allah yasa K'asashen duniyar suji Koken K'asar Goa domin tallafa mata wajan iyakance wannan annoba data riske su in.......
Kamin ma su idasa jin k'arshen labarin Mom ta sulale a k'asa a sume.
Anam dake kusa ta lura da ita ce ta saki wata gigitacciyar k'ara had'e da bazawa da gudu tana tarbo Mom a jikinta.

Kuka ta rushe dashi tana jijjiga Mom.

Dad kansa ya d'auki zafi yama rasa miye ya kamata ya farayi, dole su zauna da Gwamna da kuma, shuban K'asa, asan yadda za'ai suma su tura Sojojinsu had'e da Doctors domin cuto Y'ay'ansu dake a K'asar Goa.

Zufa kawai ke yanko ma Dad ba shiri ya cire babbar rigarsa, ya nufi inda Mom take da hannunsa ya kinkimeta sai waje.

Mutanan dake cikin gidan, ganin Dad ya fito da Mom a hannunsa bata motsi, yasa gaba d'ayansu rud'ewa ga Anam dake biye a bayansa sai rusa uban kuka take kamar wacce aka ce Mom d'in ta mutu.

Da kansa yaja Motar, bayan yasa Mom a baya sai Anam data shiga tana rungume da Mom, da gudu yaja Motar suka fice suka bar y'an aikin gidan da zullimin abunda ke faruwa.

_____________________
*HARUN POV*

Babban d'akin taro ne na Hukumar Sojan K'asar Nigeria, gaba d'ayansu ne zaune a wani k'aton Table kowanne mutum dake zaune an aje masa ruwa a gabansa. Gaba d'ayansu sun mai da hankalinsu ne ga Shugaban Sojojin da yake masu wani mahimmin jawabi kamar haka.


"Mun had'a wannan mintin d'in ne, a bisa shugabannin K'asar nan da suka bada umarnin tura wasu daga cikinmu zuwa K'asar Goa".

Sai kuma yayi shuru yana sake kallonsu, wata Tv ce a gabansu tana tsaye yana nuna jikin Tv d'in yana sake kallonsu yana sake cewa.

"Wata annoba ce ta riski K'asar Goa, a yadda muka samu labarin cewa cutar ta gama ma K'asar Goa babbar illar da har suke neman taimako a k'asashen duniya, wa'inda suke da halin taimaka masu k'ofa a bud'e take, suna buk'atar Likitoci wa'inda suka san aikinsu, sai kuma Sojoji wa'inda suka kware ta fannin yak'i. To shugaban K'asar nan ya bada Umarnin mu tura Sojojinmu na nan k'asa Nigeria domin kai masu d'auki, had'e da Likitoci manya na K'asar nan. A labarin da naji cewa akwai Y'ay'an Manyan K'asar nan da suka tafi Goa bada dad'ewa ba, shi yasa abun ya shafi Manyan K'asar yasa har suka bada umarnin ayi gaggawar kai masu d'auki".
Ya sake d'an yin shuru yana dubansu gaba d'aya sun bada hankalinsu suna sauraran abunda yake cewa, sai d'aga kai suke alamar suna fahimtarsa sosai.

Ya sake nuna jikin Tv d'in dake a gabansu yasa wani manuni yana nuna yadda K'asar Goa ta fara komawa kamar Mak'abarta yana cewa.


"A nan zaku ga irin illar da cutar ke yi a jikin D'an Adam, cutar dai tana kama mutum ne idan mai cutar ya cije ka ko kuma yasa farcensa ya yakusheka, cutar tana sa ka rink'a cin naman mutum, akwai had'ari sosai a wannan tafiyar da muke shirin turawa wasu daga cikinmu.
Kai Captain Harun kai zamu tura had'e da Y'an group naku, domin Hukumar Soja ta yarda da kai da y'an term d'inka, tana da tabbacin baza ku bamu kunya ba, shi yasa ma kai tsaye muka yanke kune zakuyi wannan tafiyar".

D'aga kansa kawai Harun yayi alamar tabbatarwa, da amsawa Kuma.
Taron ya tashi a inda aka ware y'an group d'in Captain Harun ciki harda Abbakar da kuma Captain Joha, sai wasu kusan su goma Sha harda mace Maza sunfi yawa a ciki.

_____________________
Momma dake zaune sai rusa uban kuka take har jikinta na rawa tsabar tashin hankali, a rud'e Abbie ke mata magana yana cewa.

"Haba ya kamata ki daina kukan nan haka nan, nasa fa za'a tura Sojojinmu na K'asar nan had'e da Doctors domin cuto Y'ay'anmu, insha Allah babu abunda zai faru dasu ki kwantar da hankalinki kinji?".

Kuka ta sake rushewa da shi, tana kuka tana cewa.
"Wallahi hankali na bazai tab'a kwanciya ba, baccin gaba d'aya Y'ay'ana suna K'asar da wannan cutar ta b'arke da ita, ya za'ai na iya kwantar da hankalina?, kana fa gani aka nuno yadda idan mutum ya kamu da cutar yake cin naman D'an uwansa, wannan wacce irin cuta ce haka, ni ban tab'a ji ko gani ko labari akwai irinta ba, Innallihi wa'inna alaihir raju'on, nikam da nasan hakane bazan tab'a bari suyi wannan k'addarar tafiyar ba, dan......
Toshe mata baki yayi ganin yadda take magana cikin kuka har tana shid'ewa, cikin kwantar da murya Abbie ya ce.

"Mu dukanmu bamu da sani da abunda Allah ya hukunta faruwarsa ai, addu'a ya kamata mu bisu dashi, dan Allah kibar kukan nan haka nan karki sama kanki wata cuta daban Kuma".

Cikinsa kawai ta shige tana sake rushewa da kuka, domin tashin hankalinta gaba d'aya Y'ay'anta suna Goa.
Taji labarin an kwantar da Mom a asibiti kwata-kwata bata da kwarin gwaiwar zuwa asibitin dubo ta, ji take dama ita ce ta suma ko ta samu sassaucin abunda take ji a ranta, dan ita sadda ta riski labarin komawa tayi kamar wata zararra, da kyar aka samu ta hawaye suka fara subo mata, daga nan ne kuma ta rink'a kuka mai sauti kamar ba gobe.

_____________________
*ANAM POV*

Rik'e take da hannunsa Mom da farkawarta kenan Anam sai kuka take tana kiran.

"Dan Allah Mom karki sake suma, kina bani tsoro, kuma nima dani za'aje domin ceto y'an uwa na, yanzu nake samun kira da Hospital namu ana son ganinmu gaba d'aya, kuma ana ji dani a asibitin da nake aiki, nasan zaiyi wuya ba'a ce za'ayi tafiyar dani ba".

Rik'e hannunta Mom tayi da k'arfi tana girgiza kanta, Dad na kusa ya d'an rik'e d'ayan hannun nata yana dubanta jin tana cewa.

"A'a a'a ban yarda kije K'asar nan ba, kema so kike na rasa ki?, ban amince kije ba, itama Hanan nayi danasanin barinta zuwa, ashe dama abunda kike ji a jikinki kenan?, shi yasa kike ta k'ok'arin nuna min kar na bar Hanan taje, amma nak'i, bazan barki kije ba Anam bazan iya ba, idan na bari kika tafi kamar banyi adalci ba".

Hawaye take tana maganar, Anam ma wasu hawaye ne suka sake wanke mata fuska ta girgiza kanta tana cewa.

"A'a Mom dan Allah karki ce karna je, ina son nima nayi taimakon bayin Allah, ko Allah zai ji tausayinmu ya k'are Y'an uwana dake cikin k'asar da annobar take, please Mom ki gane abunda nake nufi, ba abunda zai faru dani Mom please".

Mom zata sake magana wayar Anam ta sake d'aukar k'ara, cirota tayi ganin Doctor Halisa ke kira yasa ta kalli Mom tana cewa.

"Ki gani ko Mom?, kirana ake daga Asibitin da nake aiki mitin ne na gaggawa zamu shiga, please Mom ki barni naje dan Allah"


Dad ne ya katse hanzairin Mom dake son sake turjewa ya ce.

"Please ki barta taje nima na barta taje insha Allahu zata dawo lafiya ita da Y'an uwanta".

Ba dan Mom taso ba ta d'aga masu kai kawai hawaye na sake zubo mata akan fuskarta.
D'auke idonta tayi daga Anam d'in tana zare hannunta daga na cikin Anam d'in.
Dad ne yayi ma Anam alamar ta tafi kawai zaiji da Mom d'in, dan sun lura Mom bata gama amincewa da Anam d'in taje Goa ba.

____________________
Gaba d'ayan Doctors ne a zaune a wani d'akin taro a asibitin da Doctor Anam ke aiki, kusan ita d'aya ake jiran isowarta wasu har sun fara jin zafin ta, ciki harda wata Doctor Asiya sai cika take tana batsewa, a inda har ta fara surutu ita da wata K'awarta Doctor Sa'adha tana kallon k'ofar d'akin turon da suke tana cewa.

"Wai ya za'ai anzo an wani aje mu akan wata can bata k'araso ba, mi yasa baza'ai mana jawabin abunda ya taramu ba?, ko kuwa dole sai shafaffiya da mai d'in can Anam ta zo za'a fara?, dan wallahi na tsane ta, ta cika iyayen tsiya da son asani".

D'an tab'e baki Doctor Sa'adha tayi tana gyara zaman gilashin idonta, tana d'an yin magana k'asa-k'asa yadda ita da Doctor Asiyar ne kad'ai zasu ji ta ce.

"Ai ko zaman jiranta ake yi yanzu, danni nima fa wallahi haushi take bani, ashe ba ni kad'ai ce ke jin kwata-kwata batai min ba".
Asiya zatai magana Anam ta fad'o d'akin, kamar an jefota.

Doctor Fahat ne ya kalleta kusan shine shugaban asibitin, dan shine ma zaiyi bayani akan abunda ya tarasu.

"Mi ya tsayar dake ne Anam?, kin bar mutane a zaune".

"Am sorry Doctor Fahat, wallahi an kwantar da Mom d'ina ce a asibiti, ga abubuwa da suka cakud'e mana a family namu, amma yanzu na iso zamu iya fara abunda ya taramu".

Nuna mata wajan zama yayi ta zauna ya d'an kallonta cike da sonta da birgewar da take masa.

Su Doctor Asiya dake gefe kusan a tare suka tab'e baki.
Tana zama Doctor Halisa dake kusa da ita ta d'an mata rad'a a kunne wadda yasa Anam d'an sakin murmushi kad'an.

Gyaran muryar da Doctor Fahat yayi ce yasa gaba d'ayansu suka mai da hankalinsu gare shi.

"Kamar yadda kuka sani a safiyar yau ne muka ji labarin wata Annoba ta kunno kai a K'asar Goa, wacce ta hallaka mutanan k'asar da yawansu, dan hakane manyan k'asar Goa d'in suke neman taimakon manyan Doctors wa'inda suka san aikinsu had'e da taimakon Hukumar Soja, ga duk K'asar dake son taimaka masu k'ofa a bud'e take. Mun samu umarnin cewa shugaban k'asamu Nigeria ya bada Umarnin tura Sojojinmu had'e da Doctors a kowanne asibiti dake fad'in k'asar nan zasu iya bada kamar mutum uku, abunda yasa mukayi gaggawar taraku a nan kenan, mun rigada mun gama zab'ar wa'inda za'ayi tafiyar dasu, ga duk wadda muka je muka dawo lafiya dashi, shugaban k'asa ya ce zai bada gagarumar kyauta wacce zata girgiza mutum, dan haka mun zab'i Doctor Anam had'e da Doctor Halisa sai kuma Doctor Asiya sai kuma ni da za'ayi tafiyar".

Shuru wajan ya d'auka kamin kuma a fara y'an k'ananun maganganu, wasu sunji haushin cewa bada su aje ba, domin jin cewa ai shugaban k'asa yayi albishir d'in zai bada gagarumar kyauta, kyautar ce kawai da suka ji za'a bada ta rud'e su, sai cece kuce suke akan wa'inda aka yanke dasu za'aje, wasu ma kai tsaye suke maganar son kai aka nuna a cikin wa'inda aka zab'a za'ayi tafiyar dasu.

Sai da Doctor Fahat ya d'an buga table d'in dake gabansa, sana suka yi shuru.

"Idan akwai wadda yake da magana k'ofa a bud'e take, ga duk wadda aka zab'a idan baida ra'ayin zuwa zai iya fad'a a canza wani a madadinsa".

Kowa shuru yayi domin wa'inda aka zab'a kowa dama so yake aje dashi.
Doctor Sa'adha ce ta tab'e baki ita ce farkon tashi ta fice daga d'akin taron tana jin zafin ba'a sa da ita ba a tafiyar.

Doctor Asiya ce ta take mata baya, domin suna d'asawa da ita.

"Haba k'awata ya da haka Kuma?, ba'a gama taro ba kin tashi".

Tsayawa Sa'adha tayi tana kallon Asiya kamin ta ce.

"Dole zaki ce haka man, tunda kin san an zab'e ki a tafiyar".

"Noo wallahi na so asa dake a ciki, amma dan Allah kiyi hakuri, ni kwata-kwata ma jikina ne yayi sanyi, kamar na ce ma fasa zuwa ma, kinga fa inda zamu kamar lahirarmu ce muka kai kanmu, kinji bayanin da Doctor Fahat yayi ai?, wa'inda suka kamu da Cutar fa cin naman mutum suke da ransa fa, abun ya d'an so ya bani tsoro, ba dan naji za'a bada number yabo ga duk wa'inda akai tafiyar dasu aka dawo lafiya su za'a basu kyauta had'e da number yabo, wallahi da ba abunda zaisa na amince ayi tafiyar dani".

Wani tsaki Doctor Sa'adha ta saki tana bankama Doctor Asiya harara, tayi gaba tabar Asiya da sakin baki.

Au yanzu haushinta take ji duk bayanin data tsaya tayi mata?, gani take kamar bak'in ciki Sa'adhar ke mata dan kawai an zab'e ta, ita kuma ba'a ce da ita ba.

Tab'e baki Asiya tayi tana d'aga k'afad'arta, alamar Doctor Sa'adhar taji dashi dai.

______________________
*Umaru Musa Yar'Adua Airport Katsina State Nigeria*

Gaba d'aya Hukumar Sojojin Nigeria ne had'e da Kwararrun Likitoci wa'inda aka tantance zasu tafi zuwa K'asar Goa, wadda K'asar Goa d'in ta riga da tasan da zuwansu a yau d'in, sosai kuma suka jinjinama Nigeria d'in a bisa taimako na farko da aka fara kowa masu, Nigeria ce ta farko wacce ta fara amsa zata turo mutananta domin taimakon k'asar.

An riga da an shirya tarbarsu a can, da duk kayan aikin

Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6

Please Login or Register in order to submit comment