Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

abinda zasuci ne babanta ya rasu sai mamanta suka kulla soyayya mai tsanani bayan auransu da sati uku mahaifiyar Sa'a ta rasu ta shiga tashin hankali Agaishina ita take kwantar mata da hankali ta kuma riƙeta kamar ƴarta, karima an sami abin habaici da gori amma Agaishina ko kallo bata isheta ba sabgar gabanta take. Bayan shekara ɗaya da auran su Sa'a ta sami ciki murna wajan Sa'ad ba a magana da Agaishina da Sahabi.
Akwana a tashi Allah ya sauketa lafiya ta sami ɗiyarta zankaɗeɗiya kyakywa baƙa mai farin jini abin ba cewa kome Ranar suna taci sunan *Ma'azzara* Ma'azzara ta taso cikin gata da kulawa Sa'ad na ƙoƙarin bata tarbiya sosai, saboda tin daga kanta Sa'a bata kuma haihuwa ba da ta sami ciki sai ya zube. Ma'azzara kyakywace ajin karshe mai diri da surah, ta taso da sangarta akwaita tsokana da faɗa kusan kullum sai an kai iyayanta gidan megari ƙara, karima tayi ta masu gori Sa'a tayi ta mata nasiya tana gaya mata lillar abinda take idan suka mutu wuya zata sha ta bari, da irin wannan nasihar ta mahaifiyarta yasa ta rage rashin ji ta maida hankalinta da karatun islamiyya da boko...

Kwatsam ana cikin haka Sahabi ya kwanta dama, Sa'ad ya shiga tashin hankali shi da Agaishana dan abun kansu zai ƙare.
abinda ya idar da hargitsa gidan baki ɗaya dan bayan Arba'in suka ce ayi rabon gado ɗaki ɗaya suka basu Sa'ad ya ce Agaishana ta zauna shi zai nemi haya da matarsa da ƴarsa, Agaishina taki taje ta siyar da raƙuminta ɗaya da ya rage ta sami dan filinta tasa aka gina mata ɗaki ɗaya da soron kofa guda tace abata Ma'azzara aka bata suke zaune abinsu, idan ba school ko islamiyya tare suke zuwa tallar maganin zafi kuma suna samun kudi sosai suna rufawa kansu a siri har ma dasu Sa'a...

Kwatsam watarana aka aiko surikin Fauziyya ya rasu Sa'ad da karima da Sa'a sune suka tafi Tahoua gun gaisuwa salamatu tace bazata ba kuɗin mota tsada ita matar malam ce ta kira a waya tayi gaisuwa. Haliru kuwa cewa yayi baya da kudi.
Kwanan su uku suka juyo zasu dawo wanda aka cika su da abin arziki anan ne mai afkuwa ta afku Bus ɗin da suka shigo tayi hatsari kusan mutum goma suka rasu ciki harda Sa'a da Sa'ad da Karima dan ko shurawa basu yiba.
Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un!!
Wannan mutuwar ta girgiza jama'a Ma'azzara kusan haukacewa tayi Agaishana kuwa ba a cewa kome sai godiyar Allah, salamatu tayi sanyi ta rinƙa saka Ma'azzara ajiki wai tausayinta take yanzu amma kafin ake arbain har ta manta har an koma ƴar gidan jiya, sai kyama da tsamgwama daket Agaishina ta daure akayi arbain suka ɗauki duk wani abu mai ɗan kyau zasu bar gidan su koma can gidan ta, Salamatu da Haliru suka hana suka ce kayan ɗan uwansu ne gaisha tace iya ko da ta haifesa fa nan Ma'azzara tace a barsu da Allah su tafi haka ko suka bar gidan suka koma can gidansu na da...

Ma'azzara yanzu tayi sanyi bata hayaniya sai afkin kuka tana faɗin bata da gata Agaishana tace tana da gata itace gatanta da kuma Allah.
Cikin wannan yanayin ne Adamcy ya rinƙa zauwa mafarkinta ko da yaushe ta kwanta shine take gani suna wani irin gurin shaƙatawa, yana yawan rungumeta da shan bakinta da faɗa mata kalaman soyayya masu taushi kullum burinta Allah ya gwada mata uncle ɗinta namfarki ya sha bakinta taji dadi.
Ana cikin hakane ciwo ya kwantar da Agaishina zama daket tashi daket Ma'azzara itace ke komai na gida ta dafa maganin zafi taje ta sedo da kudin take masu abunci suci har maganin ya kare nan ta shiga tashin hankali ta rinƙa zuwa gidansu lailah kawarta tana amso abunci yau da gobe sai Allah, iyayen lailah suka ce ta rabu da ita ba kunya ubanta yace da Ma'azzara ta rabu da lailah dole ta fasa zuwa ta shiga neman aiktau, tana wanke-wanke ana bata abunci da ɗan kudi tana sayama Agaishina magani, a gidansu ɗan malle tunda ya ganta ya haɗa mta miyau yasha ɗana mata tarko Allah ya kubutar da ita sai ranar ne da ciwon Agaishana yay tsanani, Ma'azzara ta fito neman wanda zai temaka masu kar Agaishana ta mutu, shine fa da ya ganta ya bita har ya samu nasarar kamata sai de kafin ya kai ga cinma burinsa Allah ya temake ta baɗa masa ƙasa idanu ta gudu daidai lokacin Allah ya kawo mata gatanta wato Adamcy da Hussiana wanda suka canza rayuwarta daga rashin gata zuwa gata sai, de bamu san meye zai sake saka Ma'azzara wani rashin gatan ba ko akasin hakan, hummm kude ku biyo ni tare da alkalamin Ladingo yanzu labari zai fara na *bani da gata*

Wannan ne cikaken tarihin su

*Na kudi Ne kan farashi Nera 200 kacal +22792589446/ +22796515805*


*💃🏻Daga Alƙalamin Real ladingo Sweet baby* uwa ga Fareesatu😘

*💖BANI DA GATA💖*




*MALLAKIN*
👇🏻
*Real ladingo Sweet Baby*💋
Yar mutan Niger🤙🏻



*Bismillahir Rahamanir Rahim*



*Chapter 12*


...Yanzu kam cikin Hussaina ya girma sosai haihuwa ko yau ko gobe, duk wani abu da ake buƙata na haihuwa Adamcy ya tanada domin fariya ce kawai bayayi wajan siyan kayan beby, ita kanta Hussaina har ƙorafi take yayi yawa amman baya jinta ko kaɗan dan shi zai iya kashe ko nawane akan Hussaina da babynta.


zaune suke a porlour da yake weekend ne Adamcy na kallon labaran yamma a tashar *CNN* Hussaina ce ta dafa Adamcy ta miƙe, shima miƙewa yayi ya bita yasan bata da lafiya duk kwana kinan yana lura da ita bata da lafiya, amman kara da kawaici na Hussaina bazata faɗa ba sai dai shi ya fahimta hakan yana bashi mamaki, har upstair's ya bita yayin da ita kuma taje ta haye bed ɗin tana maida numfashin wahala, domin nakuda takeyi ranga2 saukar tautausan hannunshi taji a tsakiyar gadon bayanta yayin da kamshin turaransa mai sanya zuciya nutsuwa ya daki hancinta, ƙara tamke idanunta tayi tana jin wani sassauci, sannu a hankali ta buɗe magic oil eyes ɗinta ta zuba masa cikin yanayin wahaltuwa, tace"Mn trèsor" ta faɗi tana ciza baki ta damƙe hannunsa sosai.
Adamcy ya zuba mata lumsassun eyes ɗinsa daya zama identity ɗinsa na sanyi da kuma nutsuwa, yasa yace "bebeta sorry little one ne ko?".
ita dai ji takeyi cikin yana murɗamata, sakinta yay wordrobe ɗinta ya nufa wa'ash abaya mai ƙaramin mayafi ya ɗakko mata janyo silifas ɗin ƙofar bethroom ɗin yayi da sauri har yana ɗan tuntuɓe tsugunnawa yayi ya sanya mata sannan ya sanya hannuwansa da iya ƙarfinsa ya sungumeta, sai bakin parking lot Ma'azzara tana ganin haka itama ta miƙe ta bisu a guje tana kiran "Uncle Aunty Hussy haihuwa zatayi ko"? Adamcy ba sautareta ba. Hankalinsa a tashe, bayan wata mota mai kyau ya buɗe ya kwantar da set ɗin duka yayi ya kuma kunna Air Condition ɗin daidai yadda bazai cutar da itaba ko bebyn duk cikin sauri yake gudanar da komi, haka ya koma yana ƙoƙarin zama Ma'azzara ta iso da sauri ganin bazai tsaya sauraranta ba yasa ta sanya wani kuka mai matuƙar firgita mai saurara, da sauri ya dakata yace "Shiru Oyo shigo muje" bata wani yi wata wata ba tabuɗe bayan inda Aunty Hussyn take tashige kan Aunty Hussyn ta dauka ta ɗora a kanta tana shafa fuskarta, Adamcy a guje yabar gidan masu aiki na masu Addu'ar sauka.lafiya. Ma'azzara ko motsi kadan ta kara fuskarta jikin Hussy, ta hau mata magana tana cewa "Sannu Aunty insha Allah zaki haihu lafiya sannu Aunty da sauri Adamcy ya bugi sitiyarin motar yace"shatop kin cikawa mutane kunne da surutu." Ita kam Hussaina zuwa yanzu bata fahimtar komi.

Haka Adamcy yake driving ,cikin tashin hankali har suka isa Hospital, Suna zuwa aka amsheta cikkn gaggawa aka nufi rroom labour da iya, freind ɗin Adamcy ne Faruq ya iso da sauri yasa a ka amshi Hussaina da gaggawa.
Hankalin Adamcy duk ya tashi se goge zufa yafi a kirga amman daya goge sai ta ƙara tsatsafowa tamkar shike naku dar, Ma'azzara tana liƙe dashi tana shara kwalla, Adamcy ya kama hannunta suka zauna ai kuwa ta ɓarke masa da kuka ta faɗa jikinsa ta cusa kanta kirjinsa tana shasheƙar kuka.
Adamcy bai mata magana ba sai hannunsa da ya zagaye bayanta yana buga bayanta cikin sigar lallashi, jin bazata kyaleba yace"Ke bana son damamuwa Addu'a zamu mata Oya yi shiru maza haɗiye kukan ki." Shiru Ma'azzara tayi tana sauke ajiyar zuciya, ta ɗago tana goge hawayen fuskarta, ta janye jikinta daga na Adamcy saboda wani irin yanayi da takeji, ga wani fitinanan kamshinsa.
Ta sanyan tattausan hannunta saman fuskarshi tana goge masa zufa tana hura masa isakar bakinta, tace"Uncle kayi hakuri zata sauka lfy , uncle ina toilet na ɗauro alwalla nayi nafila na roki Allah ya sauke min Hussy na lfy?" ta faɗa ta kura masa idanunta masu matuƙar haske, hawaye na kwaranya a kan fuskarta.
Adamcy ma ita yake kallo ya miƙe ya kama hannunta ya nufi toilet da ita, suna zuwa ya buɗe ya sakata ya tsaya a kofar ya mata nunu da idanu, da sauri ta shige ta rufo kofar, shiko ya tsaya nesa da ita ya fara kai komo, phone ɗinsa ya zaro ya kira number Baffa kakansu, bugo biyu ya ɗaga yake sheda masa suzo hospital shida lallah Hussy na kan guiwa.
Bai jira me zaice ba ya kashe ya kira Rukaiyya mamar Hussaina ya faɗa mata itama nan a rikice ta shirya ko alhaji bata faɗama ba ta kamo hanya.
Ma'azzara na fitowa Adamcy ya kama hannunta ya kaita Office ɗin Farouq nan ta fara sallah.

*BAYAN AWA UKU*

Su mamah da inna lallah duk suna hospital ɗin sunyi cirko-cirko, sai Addu'a suke.
Tunda Hussy ta fara nakudar bata wani lafa ba nakuda take kamar an jona drip, sosai ta galaɓaita dan nurse ɗin dake kanta harta fara tunanin ko bazata iya haihuwar bane? cikin haka taji Hussainar ta saki wani salati da wani irin nishi inda da sauri ta dawo daga tunanin datake ta daina ɗan mamatsa mata cikin daidai nan kuma kukan bebyn ya kartaɗe room ɗin inda ta ida zaroshi aka fita da uwa ciki ɗan lokaci aka gyara mejego da beby masha Allah nurse ɗin ta faɗa dan ganin kyaun beby har tafi iyayanta kyau kamar baturiya.
Tsaf aka naɗota a towel aka fito da ita nurse ɗin da doctor Farouq suka jera inda Adamcy na ganinsu ya taso da sauri,! suma murmushi ne bisa fuskarsu suka miƙa mashi bebyn tana tsokanar shi, ya amsa cikin farin ciki abu ga sarkin kyauta wani haɗaɗɗan ring ne a hannunsa mai matuƙar kyau da tsada dan wani yawan shaƙatawar da sukaje Egipt ya siyeshi ko a lokacin Hussy ce ta yaba dashi shiyasa ya saya, sai walkiya yake yi domin zallar gold ne zareshi yayi yadda yake jin farin ciki bazai iya barin nurse ɗin haka ba dan haka ya miƙa mata yace"Ga tukuice amman bayawa ki jira babban." ya faɗa yana beƙa mata.
Zaro ido nurse Huzaiyya tayi dan tasan zubon nada tsada tace"Ni!"kai ya ɗaga mata dan ya matsu yaje yaga Hussyn amsa tayi hannunta na rawa cike da zumuɗi tana mashi godiya. Adamcy nan ya ma baby Addu'a haɗe da kiran sallah a kunnenta.
Baffa suka iso tare da mamah da lallah suna murna Baffa norènzo ya dirkama Adamcy duka a baya yace" mara kunyar banza bani ɗiyata to na gani."0 Adamcy ya bushe da dariya ya bashi ɗiyar nan suka fara mata Addu'a da mamkin zallar kamarta da Baffan ita sak baturiya ta fito. Ma'azzara cikin murna ta mashe ɗiyar ta matsa gefe tana sunsuna wa ta hana kowa.
Adamci yace da nurse ta kaishi gun matarsa kafin wannan dattijawan su cika ɗakin, gaba ta shiga ya bita a baya har suka isa, inda Ma'azzara ta dinga binsu cikin sauri tana rungume da babyn se murmushi take saki Lallah ce ta mashe babyn, dole Ma'azara ta shiga hannunta goma tana zaro idanu.

Adamcy na shiga ya rungume Hussy yana manna mata kiss ta ko ina yana sunsunata yana zuba mata godiya babu iyaka, Hussaina kuwa kumya ta cikata.
Ma'azzara ce shigo amman bata so tayi magana ya mata tsawa zuwa yanzu tsoron sa takeyi,dan baya mata sauƙi ga barazanar maidata gurin su Salamatu da yake yi in tayi mashi lefi, ita kuma batasan maganar komawar.
Doctor Farouq ya shiho yama Hussyn barka inda ita kuma Ma'azzara ta isa da sauri ta rungume Aunty Hussyn tana mata sannu ciki shagwaɓa, jikinta ne yabata ana kallanta ɗago kan da zatayi suka haɗa ido da doctor Farouq wanda tunda ya ganta a Office ɗinsa yake binta da mayen kallo sai a lokacin ma ta lura da jikinta sanye take da riga da siket ɗinkin sitaila kanta yasha ƙananan kitso shaɗe sai takalmi filet a ƙafarta bayan haka bakomi ajikinta domin tana ganin Adamcy ya sungumo Hussy batayi wata wata ba ta biyosu kuma dama shigar dake jikinta kennan sai kallabin data cillar kamar itace keyin nakudar sanda taga fitowarsu, dan sallah da tayi ma Adamcy ne ya amso mata hijab gurin nurse aro tana idarwa ya maida mata, da ƴar kunya ta ƙara shigewa jikin Hussy, Adamcy ya watsa mata mugun kallo, dan sai yanzu ya lura da yanda tazo hospital ɗin, mayafin Hussy gudan ya bata wanda Hadiza me aiki ta kawo, cikin rawar jiki ta masa ta yafa. bayan an kawo ma Hussy hadaddan tea tasha taci farfesun hanta Adamcy bai damu da mamah da kakanni su ba shida kansa ya temaka ma Hussy taba baby nono yana lallashinta, dole mamah ta fita tana murmushi, Ma'azzara kuwa wani irin abu takeji ga zufa na karyo mata duk da tna farin ciki amma wannan abinda Adamcy yake ma Aunty Hussy ya tsaye mata a rai, dole tabar kallonsu.

Sai dare aka sallame su bayan an duba beby da maman beby babu wata damuwa inda nan take aka basu sallama.

Bayan sun koma gida kuma granny lallah ce ta dawo nan gidan dan kula da ita.
masha Allah maijego da baby suna matuƙar samun kulawa daga ɓangarorin duka Adamcy ingari ya waye zaizo ya dau baby ya mata addu'a sannan ya koma kan maman baby ya tsotsi nan ya shafi nan ita kanta Hussyn tana jin daɗin kulawar dayake basu kwarai, tayi ta zuba masa sangarta idan ta kama taotsar bakinsa kuwa sai yaji yana son shiga wani hali yake tsayar da wasan, ganin haka granny lallah ta hanashi shigowa dan ta kamasu suna tsotse-tsotsen, haka kullum gidan cike da mutane yan barka ummee ma tazo.

Ranar suna anyi bajinta iya bajinta dan babu ce kawai ba a rababa agurin kuma kuɗine kawai ba a liƙawa ba pic ɗin beby aka raba amman robobi jakunkuna takalma manshafawa sa ili turare faka dosbin aasu ma ba Adamcyn bane yayi su saidai yagani abokansa sun mashi kara kwarai bama kamar Farouq daya ke jifan tsuntsu biyu da dutse ɗaya saboda tunda yaga Ma'azzara yaji shikam duniyar ga yayi matar aure.

beby tace sunan Ummu Saudat yarinya kyakyawa kamar ƴar larabawa danko su larabawan ba abinda zasu gwadawa bebyn, se Jiddah tayi sati kafin take juyawa Agadez Yaronta mai wayo sun shaƙu da Ma'azzara haka Adamcy duk inda zai shiga yana tare da Na'eem, Ummee tana nan ita ke kula da Hussy sai ta zubda ruwa.
A haka baby da momynta sukaci gaba da wanka Ma'azzara na kula dasu duk da kwana biyu nan mafarkin Adamcy ya adabeta se dai in bata kwanta ba gashi da zaran ta gansu da anty Hussy zataji kunci, abinda ya isheta take tambayar kawarta Nazifatu a school ta zaiyana mata kome akan abinda takeji game da uncle ɗinta, Nazifatu kuwa kasancewar ta girmi Ma'azzara gashi tasan kome akan soyayya sbd karatun novels ɗin hausa da take, nan take ta faɗama Ma'azzara cewar son uncle take ba so kaɗan ba... Ai kuwa ranar sai ɗa aka rabasu harda dambe tace me zatayi da mutumin da yake zaman uba gareta.... kuka ta rinƙa yi harda majina ai kuwa cikin sa'a Adamcy yazo ɗaukarta tana shiga mota ta kece masa da kuka ta rungumeshi ta faɗa masa abinda Nazifatu ta faɗa mata, wai yakai ƙaran Nazifar ta mata sharri kuma suna zuwa gida zata faɗama Aunty Hussy... nan Adamcy ya shiga mugun tashin hankali dan tabbas indai abinda ta faɗa gaskiya ne yo Amana sonsa take ba tare da ta sani ba, amma sai ya dake ya nuna mata karya Nazifa take kuma karta faɗawa antynta kuma karta kuskura ta sake faɗama kowa, da haka ya mata wayo ya lallasheta ya goge mata hawayen fuskarta ya biya ya sai mata ice cream, yana mai mugun jin tausayinta dan yasan abune ba mai yuwa ba...

Yau kam baƙo sukayi a gidan Farouq ne da kansa yazo dan gaskiya ya kasa daurewa tunda ya ɗora idanuwansa akan Ma'azzara shi kam ya kasa sukuni, hakan tasa yagayawa Adamcy be ɓoye mashi komi ba a ɓangaran Adamcyn yayi murna sosai dan tinda ya gano mahaukacin son da take masa, mutiƙar bai ɗauki mataki ba akwai matsala, shiyasa yayi gagawar aminta da Farouq dan yasan Farouq zai riƙeta amana kuma yana da komi na rayuwa wanda mace zataji daɗi agurinsa, hakan ma yasa Farouq ɗin tuntiɓar Adamcyn kan cewar yanaso yazo ya fara shigar da kansa inda Afamcy ya tabbatar mashi da cewar yaje dan shi ko baby Ummu zai iya bashi saboda ya yarda da nagartarsa.

To shi nefa yazo taɗin. Zaune take a porlour ta baje uwayan takardu sai home work takeyi bayanta goye da Ummu Saudat wadda masha Allah har sun kusa gama wanka kuma tayi girma fiye da tunanin mai karatu, Ma'azzara kanta tayi wani irin girma ta kara buɗewa tayi wani irin kyau na ban mamaki baƙinta ya washe ta ɗanyi haske.
Ummee ce ta safko take yiwa Ma'azzara magana ta daina goyo tana buduruwa zai cutar da ita ta sauke ta ta dinga saɓata kokuma rungumeta, iyaye mukula mudaina barin yaranmu nayawan yin goyo ya zubda nono kuma hakan na kawowa yaranmu naƙasa agurin maza in sunyi aure.
daidai nan Farouq ya fito daga cikin motarsa camrry 8+1 mai masifar kyau wata shadda ce a jikinshi ruwan zaiba sai walkiya take ɗinkin muhmmad Abacha yayinda yasanya hula itama dai ruwan zaibar zannah Bukar ta auna mashi tayi kyau, kamshin turaransa bag one sai tashi yake yana yawo a duniyar farfajiyar gidan siririn gilas ne a fuskarsa da ka ganshi kasan ya saba sawa, kuma ya dace dashi tafiya yake cikin kuzari da ka ganshi kinsan namijine mai lafiya da kuzari.

Yana isa ya kira Adamcy yace" to yayanmu na iso fa" Adamcy yace"freind gidan baƙonka ne to ?"ido ya lumshe ya ƙara buɗewa yace no. Friend but kasan wannan zuwan ya banbanta da irin wanda nakeyi a can baya yace" kashiga to nayi Hussy bayani." yanaɓfaɗin haka ya tsinke kiran yana lumshe manyan idanunsa masu ruwan zaiba yana tsotsar lips ɗinsa. Cikin farin ciki Farouq ya nufi cikin gidan.
Tunda Aunty Hussyn takira ta ciki dibara tace mata" Ma'azzara kingane doctor Faruq wanda aka kaini Hospital ɗinsa na haihu?" shuru tayi alamar tunani can kuma ta kalli Aunty Hussyn tace"eh Aunty nagane shi" Hussy tace" Ok to yanzu yana nan zuwa kuma gurinki zaizo inya tafi zan maki bayani amman idan yazo ki bashi kulawa kinji kuma banda shirme yanzu kije ki kai kujeru biyu Lambu sannan ki shiga kitchen ki duba abin taɓawa kikai masa ke kuma ki shirya sosai kiyi kwalliya shuru" Ma'azzara tayi inta fahimci Auntyn dai santa yake taɓ ita kam bata sansa. Ganin tayi shuru yasa Auntyn ta sake yi mata magana, da sauri ta tashi ta fita kitchen ta nufa kamar yadda Auntyn tabata umarni komi takai amman batayi kwalliya ba nan ma Aunty Hussyn ta biyo ta ta dinga lallaɓata inda ta zage ta caɓa mata kwalliya sosai cikin duguwar rigar shadda fich tasha blue ɗin aiki mai tsari turaruka ta fesa mata masu dai kamshi, haka Ummee ta mata maganganu da dibara irin wanda uwa keyi ƴarta dan in ganta lamurranta taɗan saki ranta amman dole wai saida Ummu zata gun zancan Ummee take faɗama Hussyn ce tace Ta barta suje tare ai gaskiya yarinyar naji da Ummu batasan rabuwa da ita kokaɗan...

itama bebyn anyi mata wanka da kwalliya cikin wasu lafiyayyun kaya tayi kyau ba ƙarya ga kamshi mai daɗi tana fitarwa .

Da sallama ta isa gurin Farouq ɗin inda tunda daga nesa yake addu'ar Allah sa da rabonsa domin komi da yakeso agurin mace yana hangoshi ga Ma'azzara itama tun daga nesa ta hango shi yayi matuƙar yin kyau a kan kujerar dake ajiye ƙarƙashin flawer's ɗin koba komi ya haɗu sai dai kash ita bataji komi ba game dashi, haka ta ƙarasa da sauri ya tashi ya amshi beby Ummu yana cewa"Sannu da isowa sarauniyar ruhin Umar Faoruq." itama ɗan murmushi ta mashi tana amsawa balefi taɗan yi wayau sunyi hira kamar masoya haka kuma yaya ba da girman Ummu shikam yana matuƙar kaunar Ma'azzara fatan da yake shine Allah mallaka mashi ita a matsayin matarsa ta sunnah, duk yaga akwai sauran yarinta a tare da ita amman zai koya mata sonshi nan kusa, tunta ya samu ɗaurin gindin Adamcy...

Adamcy ne ya dukufa aiki yake yi sosai amman wayarsa ta dameshi da ruri wannan tasa ya ɗaga badan yaso ba dan ya share amman ba adaina kira ba, kuma bakuwar number ce, Picking ɗin call ɗin yayi amman sai yaji muryar Halliru ya mas aslm, Adamcy ya amsa ba wai dan ya gane shi bane, nna Halliru ya masa bayanin babban Ma'azzaea ne, inda yake shaida mashi yana so a basu Ma'azzara aure zasu mata.
Adamcy bai ce kome ba ya tsinke kiran ya kifa kansa smaan katon table ɗin ya lumshe idanunsa, dan yaji daɗin neman da suka mata,
shi kam ya godewa Allah da Farouq yace yana san auranta gara a mata auran itama ta kafa iyalinta tasami ƴancinta dan haka ya ɗaho da sauri! Ya danna number Hallirun, bugo ɗaya ya ɗaga, nan ya cewa Hallurun ya bari zasuyi magana yayi hakanne kawai dan bashi da lokacin sa bayaso yana ɓata lokacin sa a irin abubuwa marsa amfani...

Yau kam da wani irin mahaukacin ciwon mara da baya tatashi jitake kamar zata bakunci lahira da sauri Hussy dake jiyo kukanta ta nufi room ɗin Mu azzara, yadda taga bayanta da kugunta ariƙe da hannuwanta ga kuka tanayi jikinta ya jiƙe sharkaf da gumi itama sai ta ruɗe da sauri ta ɗaga wayar hannunta takira Adamcy inda yace" tasanar da get man yasa driver ya fito da mota sutafi Hosptal shima gashi nan zuwa su haɗu acan"


Hussainar kanta duk ta ruɗe haka suka kaita Hospital ɗin da Aunty Hussy ta haihu wato Hospital ɗin Faruq, daidai lokacin ya fito daga parmacy yana ƙoƙarin shiga teater room kawai ya hango car ɗin gidan Adamcy dan ya tabbatar ko suɗinne sai ya ƙara nufarsu yana zuwa kuwa yaga sune da sauri ya isa ganin Ma'azzara na murkususu yasa aka kawo mashi ɗan keken da ake ɗora marasa lafiya... Daidai lokacin Adamcy ya iso ɓai ɓari aka dorata akeken ba ya cicciɓeta ya rungumeta sukayi ciki da ita, inda Farouq yake nuna masa inda zasu shiga, emargency room nan Adamcy ya shiga da ita har gadon da Farouq ya nuna masa, ya kwantar da ita ta ko riƙeshi gam tana kiran "Uncle nah" Adamcy ya damƙe hannunta yana sauke ajiyar zuciya ya kura mata idanu.
Hussy ta rungume Adamcy tana hawaye, Ma'azzara tace"uncle nah kace Aunty tayi shiru uncle Farouq zai kula dani." Hannunsa ya janye cikin na Ma'azzara ya kama Hussy suka fita ya mashi ummu yana jijigawa, yanaɓriƙe da hannun Hussy ɗin.
Nan fa Farouq ya fara binci kar lafiyarta ranar tiyata ɗin da bai shiga ba kennan sai wani ya chanje shi.

Farouq ya jima yana ba Ma'azzara temakon gaggawa ya gano matsalarta inda yake

Please Login or Register in order to submit comment