Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


Downloaded from GNOVELS.COM.NG




This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG
to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/gnovels

Twitter : https://twitter.com/gnovels

Telegram : https://t.me/gnovels

Compiled by Princess Aysha Muhammad (Humaira)


BABANA DA MIJINA

©Fertymerh Xarah

1

Agogon alarm dake manne a bangon falon ya buga qarfe ďaya dai dai na dare,

Ta ďauke kanta daga kallon agogon ta maida jikin TV tana kallon aljaxeera....

Xaune take akan sofa tana sanye cikin rigar barci mai tsantsi fara sol,

Ba wata muguwar kyakkyawa bace can, tana da kyau dai dai nata sai dai kuma mace ce Mai aji na qarshe,

Akan tsinin hancinta tawwadar Allah ce da aka haifeta da Ita tayi mata kyau kasancewarta farar mace

daga nan xaune taji tsayuwar motar mahaifinta, idan da sabo ta saba da wannan hali na mahaifinta da mijinta na fitar dare ko dawowar dare, gwanda mahaifinta ďan siyasa ne shine mataimakin gwamnan birnin kebbi, sukanyi meeting ďin dare akai akai wataran ma a gidan sukan taru suyi tana jiyo hayaniyar su daga nata gidan,

Bai jima da tsayuwa ba taji ya shige sashensa, tayi hamma haďe da yin miqa cikin wani irin yanayi na barci dai dai lokacin daya shigo falon da qatuwar kwallo a hannunsa,

Ko kaďan bai raxana da ganin matar tasa a Wannan lokacin tana xaman jiransa ba Co's ta saba,

ta xuba masa idanuwa tana kallonsa cikin wani irin yanayi fuskarta ba walwala, ya cillar da Kwallon dake hannunsa haďe da xare socks ďin qafarsa duk Idanunsa akan ta

har ya gama cirewa yayi sassanyar ajiyar xuciya, duk hankalinsa da attention ďin sa yana kanta, ya sami kansa da ruďewa, akwai wani sassanyan kallo cikin kwayar idonta Wanda ba duk mata Allah ya mallakawa ba, ya nufeta cikin wata irin tafiya ta izza cike da taqama ya xauna a kusa da ita haďe da ďora hannunsa akan nata hannu,

Kiyi haquri Iman kamar yanda kike a kullum wasan kwallo wani abu ne d.... yayi shiru sakamakon wani kallo da tayi masa,

A iya sanina wasan kwallo anayinsa ne da rana ko da safe amma ku bansan wane irin Wasa ne naku da sai dare kukeyinsa ba,

Ya tsura mata ido,
Iman baki yarda dani bane, ko kina xargina?

Ba xargi a nan illah gsky nake son ka gayamin, bayan albashinka na banki kana nufin duk wannan dukiyar daka tara duk akan kwallo ne ? Ya gyada kansa

Kwarai Kuwa, kije ki tambaya kiji duk ďan kwallo na asali Mai fita waje yana ball ba qaramin kuďi suke samu ba, ki yarda dani Mai sunan mamana bani da wani mugun hali Wanda xai cutar dake, tayi shiru kawai idanunta sun kawo kwalla ta kasa yarda da mijinta da mahaifinta, tsakanin *babana da mijina* baxan ce ga Wanda yafi wani so na da kula dani ba, ga kuďi har batason ganin su kasancewar tana xargin masu su, ta goge hawayen fuskarta, yana kallonta cike da so da tausayinta yana jinta har cikin ransa shi kansa baisan wane irin so yake wa Fatima ba, ya riqo tafin fuskarta haďe da sanya yatsansa yana share hawayen fuskarta,

Babban tashin hankalina shine naganki cikin damuwa, har sai yaushe xaki yarda dani Iman, idan baki yarda dani ba Waye xai yarda dani, wallahi ni ďan kwallo ne kidaina xargina,

taja numfashi haďe da Sakin malalacin murmushi tana kallonsa

na yarda da kai mijina, amma Ina so ka kiyaye kayi a hankali da duniya ka Kuma ji tsoron Allah, jikinsa yayi sanyi

Yace Insha Allah Iman, ya riqa hannunta suka tashi da kansa yaje ya kashe tv da komai, tana tsaye sarqe da hannayenta a qirjinta tana kallonsa cikin so da qauna, ya juyo yana kallonta
'let's go... ta juya yabi bayanta, har suka hau step ba mai mgn a cikinsu kowa da saqe saqen xuciyarsa,

ďakin qanwarta Fauxiya ta nufa ta buďe dakin a hankali ta shiga, ta same ta tayi barci sosai ďakin ya ďauki sanyin a.c ta qudundune guri ďaya da alama tana jin sanyi sosai,ta juya tana kallon sa,

'you see Fauxiya bata jin magana duk ynda nayi da ita akan shan sanyinnan bataji,

Ahmed yaje ya kashe a.c ďin kana ya ďauki blanket ya lulluba mata bayan ya gyara mata kwanciya, ta matsa ta gefenta ta xauna, addua tayi mata kafin su bar ďakin,

Kai tsaye toilet ya nufa yayi wanka, yana shirin barci ta shigo da coffee a hannunta, ya karba yana kallonta da murmushi,
'thank you wify ,tayi murmushi ta xauna bakin gado tana kallonsa,

Yana gama shan coffee ďin ya juyo ya sumbaceta a goshi yana fadin gudnyt, kafin tayi mgn har ya faďa Kan gado ya kwanta, ta bisa da ido cikin tausayin kanta hawaye suka xubo mata,

Wannan wace irin rayuwace, wane irin aure ne wannan, am a doctor, mijina yana aikin banki, idan ya fita tun da safe baxan qara sa shi a ido ba sai 6pm da yayi wanka yaci abinci ya fice sai 1 ko 2am wataran ma sai da safe take ganinsa ya dawo wai yaje training ďin kwallo,

Yau satinta biyu rabonta dashi tana buqatar mijinta tana da haqqi akansa bai damu ba saboda ita tana da buqata sosai ba Kamar shi ba ko xasuyi wata a hakan baxai damu ba,

A matsayina na matarshi abokiyar rayuwar sa bashi da lokacin da xai xauna dani and sai dai kullum idan nayi masa Mgnr fitar dare yace bana yi masa uxuri da yawan ayyukan dake gabansa a banki, da dare Kuwa xaije training na kwallo,

Ban rasa ci ba ban rasa sha da sutura ba amma na rasa kulawa da soyayyar mijina abin tambaya anan shi wannan shine ginshiqin auren, am not satisfied with my husband, bama Wannan ba rashin xamansa gida...

Babana ďan siyasa ne shi ba mai xama bane idan baya gari yau gobe yana wata qasa, idan yana gari shima baxaka ganshi ba sai cikin dare yake dawowa, idan taje mashi da complain na fitar mijinta sai dai yace
'haquri xakiyi tunda koni mahaifinki kina ganin ba maxauna bane, muna meeting sosai Mai muhimmancin acikin dare, tunda ya gayamiki wasan kwallo suke xuwa kiyi haquri ki barshi komai lokacine, ta share hawayen ta cike da mamakin kalaman mahaifinta,

shekara biyu da rasuwar mamana, banda kowa a duniyar nan bayan *babana da mijina* sai qanwata fauxiya, bansan wa xan kaiwa kukana ba ya share min shiyasa ko aiki naje banda tunani sai na *babana da mijina* babu wanda baya fuskantar challenge(qalubale) a rayuwa, and is up to us to accept such challenges mu bita da duk fuskar da rayuwa ta xo mana....

Jin shiru bata kwanta ba ya juyo yana kallonta,

'lafiya Iman, me kike tunani, ta tashi da sauri tana fadin ba komai ta nufi toilet, ta saki ruwa tana kuka sosai yanda baxai jiyo ta ba......

*Dedicated dis buk to*
*Rabi'atu Sk Mhs*
*Sadiya Lawal bala*
*Aysher Gambo*

BABANA DA MIJINA

©Fertymerh Xarah

2

Asalin labarin......

Ahmed mutumin jihar Birnin kebbi,

Daga kallo na farko mawuyacin haline ka gane qabilar da ya fito Hausa ko Fulani, wani mutum ma'abocin cikar zati da kamala da duk wani nau'in daidaito na rayuwa,

Mahaifinsa malam Abubakar buba malamin islamiya ne mutum ne mai ilimin addini, haka mutanen unguwa suna tsananin girmamashi,

Sai mahaifiyar Inna, shika dai ne ďa a gunsu, bayan rasuwar mahaifinsa suka shiga wani hali na rashin babu, gashi qarami a lokacin primary 6,

Ba Mai taimaka masu wani sa'in ma Inna ke xuwa wankau ta sami kudin da xata ciyar dashi, shi Kuma Ahmed a rayuwarsa yana son karatu shiyasa yake dagewa akan karatun, he is gifted tun yana qaraminsa malamai sun San dashi,

Ahmed yayi karatunsa da taimakon mahaifiyarsa dake siyarda qarfinta dan ganin farin cikinsa, lokacin da ya shiga babbar makaranta I mean higher institution duk qaddararta sai da ta saida ganin ta cika masa burinsa,

Alhamdulillah ya kammala degree ďin sa lfy duk aikin dayaje nema na gwamnati bai samu ba, duk inda yaje nema baxai samu ba, abokan karatunsa Waďanda iyayensu suke da kuďi sun fara aikin banki saboda suna da ďaurin gindi a gwamnati wasu ma sun fita waje neman wani ilimin, shikam degree ne iya qarfinsa yana so ya sami aiki dashi ko yayane dan ya tallafi mahaifiyarsa....

Kwanci tashi asarar mai rai yau gashi an kwantar da Inna asibiti babu kudin magani Babu babban tashin hankalinsa kamar ciwonta ulcer da kuma hypertension, duk inda ya buga bai sami kudin ba, abokansa dake bashi aro sun daina saboda baya biya,

Ya qara komawa asibiti kai tsaye ya nufi inda likitan ya roqesa ya taimaka ya duba mahaifiyarsa fisabilillah saboda bashi da kuďi, fafur likitan yaqi har kuka yayi wani mutumi dake xaune office ďin shima yaxo likita ya dubashi ya dubi likitan,

Nawa ne kudin maganin,
Dubu biyar ne fa bawani yawa, kamarsa baxai iya biyawa mahaifiyarsa kudin magani ba, baxaije ya nemi aiki ba, muma karatu mukayi muka sami aikin,

Ahmed ya dubesa, ko xaka daukeni aiki ne, ko wane irine inaso indai xaka biyani na kula da mahaifiyata

Likitan yace bama daukar mutum aiki sai mai ilimi kai kuma baka dashi,

Ahmed yace inadashi nayi karatuna na kammala na nemi aiki ban samu ba yaciro takardunsa ya nuna masa, likitan ya duba sosai Ahmed ya cancanci a daukesa aiki saboda matakin karatunsa Kuma result ďin sa mai kyau ne...

Xan iya samama aiki da wannan result amma sai idan xaka iya biyan dubu hamsin, kasan aikin gwamnati ynda yake Kuma a banxa baxaka sami aiki ba sai ka kashe kuďi....

Ruwan cikinsa na soma qugi Wanda bai sami dubu biyar na magani ba Ina xai sami dubu hamsin a ynxu, ya karbi takardunsa ya juya ya fice yana hawaye,

dakin da aka kwantar da mahaifiyarsa ya nufa har lokacin bata farfado ba barci takeyi, qarqashin pillow ďinta ya cusa takardun xaije ya nemo kuďi da qarfin jikinsa ya juya ya fice....

Ya fito harabar asibitin ya haďu da wannan mutumin na ďaxu ya kirasa yaje,

Sannu saurayi,
Ahmed ya qara gaida mutumin,
Na ganka kana da hankali sosai Kuma da ganinka xakayi jarumta xan baka kuďi ka taimaki mahaifiyar ka kakuma sami na aiki indai xaka iya min aiki,

Wane aiki ne xan iya....ya faďa muryarsa na rawa

Mutumin yace ka taba riqa bindiga? Ahmed ya girgixa kansa yana kallonsa cike da mamaki,

Xaka sami kuďi sosai indai xaka iya shiga cikinmu, ni babban ďan ta'adda ne nayi irin Wannan rayuwar taka ta talauci da haka hr na rasa iyayena, saboda rashin kuďi gurin haihuwa matata ta rasa ranta, bansan wace irin rayuwa muke ciki a ynxu ba da masu kuďi basa taimako dan Allah, Mai kuďi daga shi sai xuri'arsa, ďan siyasa ma haka, neman aiki ynxu baxaka samu ba sai dai su bawa yan uwansu, shugabannin mu na Yanxu basa aiki kamar na da, shin miye laifin talaka? da haka na nemawa kaina aiki nakewa masu kuďi fashi, inada yara biyar duk aka sami kuďi kowa Ina bashi kason sa da haka nake gayyatar ka kashigo cikin xaka sami kuďi Kuma xakaji daďi....

da'ace mutumin ya lura da yaga xufar dake ambaliya a fuska da jikin Ahmed, yayin da gudun jini ya Katse a jikinsa, hanjin cikinsa ya dunqule guri ďaya

ďan fashi kenan xai xama, barawo Mai daukar haqqin mutane haqqin da ba nasa ba, duk wahalar nan da yayi wajen neman ilimi da kwalinsa sai ya qare a sata.... tor miye amfanin karatun da yayi? Wata xuciyar tace rayuwar mahaifiyar ka fa, kana nufin karatun yafi tane?

BABANA DA MIJINA

©Fertymerh Xarah

3

Shiru yayi yana kallon mutumin sosai xuciyar sa sai bugawa take yayinda take ingixa sa akan ya amincewa mutumin ya sami kudin da xai Kula da Inna, tunda yan uwansu ma sun gujesu basa taimaka masu da komai tunda ba su da,

Baya manta sanda mahaifinsa na da rai yan uwansa kamar xasu haďiye su saboda kulawa Kuma saboda mahaifinsa mutum ne dayasan haqqin ďan uwa yake biya masu buqatocinsu, yau gashi babu ran mahaifinsa sun gujesu saboda basu da komai, mahaifiyarsa na kwance ba kuďi Kuma ba Wanda xai iya xuwa ya xauna da Ita asibitin sai shi.....

Wannan dalilin ne ya Sanya Ahmed amincewa ya karbi tayin oga nas Wanda yayi matuqar jin daďi da ya amince kai tsaye ya bashi dubu goma da address ďin inda xai same sa....

Bayan ya karbi kudin jikinsa na rawa yaje pharmacy dake nan asibitin ya siyo magani ya nufi inda mahaifiyarsa take,

Yanda ya sameta hankalinsa yayi matuqar tashi ya juya xaije ya Kira likita ta riqo rigarsa, da kyar take iya mgn

Baxan tashi ba Ahmed, buri na bai cika ba inganka yau ka xama wani mutum da duniya xata so kuma tayi alfahari dashi, kayi haquri da duk yanda rayuwa ta xoma, ka nemi halal, ka Kula da kyau kada kabari ruďin duniya da abinda ke cikinta ya ci galabarka,

Hawaye yake sosai, jikinsa na rawa hankalinsa yayi matuqar tashi da maganganun mahaifiyarsa,

Baxaki mutu ynxu ba Inna sai nayi maki gata, ya banbare hannunta da kyar ya fita da gudu neman likita,

Ko kafin su xo rai yayi halinsa, Allah ya gafartawa Inna......
*

Alhaji Abdallah mutumin xuru ne qaramar hukumar Birnin kebbi,

Babban mutum ne mai ji da kansa Wanda duniya ke damawa dashi a siyasa, shine mataimakin gwamna a Yanxu kafin ya sami matsayin da yake a yanxu sai da yayi fafatukar duniya da shige shige Wanda Dama a Yanxu idan mutum na neman cimma wani buri nasa yakan manta Allah ya kauce hanya, a taqaice sai da ya bada jinin ďaya daga cikin yaransa kafin ya sami kujerar da yake Kai a yanxu,

Ya'yan shi biyar mata biyu maxa uku sai matarsa Mami, mace mai kirki da mutunta ďan Adam..

Naxir shine babban yaron sa, sai fatyma(iman), Musa, Ismail da qaramar su Fauxiya,

Acikin yaran kaf ya fison Fatima da Fauxiya ko kaďan baya son Abinda xai tabasu, soyayyar da yake nuna masu daban ce da ta sauran yaransa.......

Kuďin sa Kuwa baa magana, yana da dimbin tarin dukiyar da yabayarda ya'yan sa uku duka maxa,

Mutuwar su tana xowa Mami a baxata, babu ciwo babu komai xaka ga kumfa na fita bakin su daga nan Kuma rai yayi halinsa, da haka ta fara rasa yaron ta Naxir...

Naxir ba qaramin mutum bane, a shekaru yabawa 26 har an nema masa mata, fatyma Kuwa a lokacin ba Mgnr aure a gabanta she is 24 karatunta ta sanyawa gaba, she want to achieve the goal, bata da buri a duniya kamar ta wayi gari yau ta ganta cikakkiyar likitar mata tana jin haushin yanda mata ke Kai matsalolinsu da sirrin jikinsu ga likita namiji,

Sanda babansu ya fara siyasa a lokacin komai ya soma sauyawa daga rayuwar gidan na rasa babban ďan gidan, sosai Mami ta shiga damuwa shi kansa Baban ya nuna damuwarsa duk da shine sila akan komai,

Sai wani lokaci da matsafin nasu ya nemi ya bada ďaya daga cikin ya'yan sa mata, sosai hankalinsa ya tashi domin a duniya ba abinda yake so kamar Fatima da Fauxiya komai xai iya akansu,

Ya qara russunawa haďe da gyara hannu jar rigar dake jikinsa ta tsafi,

Kiyi haquri shugabata xan bada yarana biyu maxa a maimakon matan Ina matuqar sonsu musamman ma Fatima Iman.......

Ta kece da wata dariya mai raxanarwa sai da gurin ya ďauka kafin tace

Sima ta amince yau da dare nake buqatar jinin Ya'ya ka,

An gama ya shugabata ya faďa yana russunawa,

Ta qara wata dariyar kafin ta juya Kan amininsa Wanda shine sanadin kawo sa gurin,

Me xaka bawa Sima gobe tayi Kari dashi labaran? Ya sunkuyar da kai cikin girmamawa...

Babu ya shugabata sai abinda kika yanke min, banda kowa ynxu a duniya duk na bayar matatace kawai ta rage...

Bana son matar ka, bana son jininta tuntuni na gayama dan haka ka nemomin jinin wani mutum ko wane irine ka kawo min a gobe,

Shikenan ya shugabata.... ta qara yin wata dariyar bayan ta nuna na kusa dashi,

Kai kuma munada labarin anyi haihuwa a gidanka jinjirin mukeso kafin ayi suna......

Da haka kowa Sima ta gaya mashi Abinda xai kawo ta Kuma cikasu da kuďi iya adadin da suke so....

Dama hakane idan har xaka shiga wannan har ka xaka wayi gari baka da kowa a duniya duk ka bayar saboda neman haram da son abin duniya ka sami kuďi, mecece ribar wannan sana'a?

Da dare duka yaran na tare da Mami, sai Kai da komawa yake naganin yanda xai ďauki rayuwar yaran biyu.....

BABANA DA MIJINA

©Fertymerh Xarah

4

Already Fauxiya tayi barci, Fatima Kuwa tana study room ta matsawa kwakwalwarta da karatu,

Musa ne da Ismail ke tare da Mami, sun jima sosai tare da Ita kafin suyi mata Sallama suka fice...

Yana xaune a falo suka fito, fridge suka buďa kowane ya ďauki yoghurt Wanda dama al'adar su ce basa kwanciya sai sun sha,

Baba Xamuje barci kayi mana addua, ya ďago yana kallon yaran bawai bayason yaransa bane son xuciya da neman duniya suka rufe masa ido, yayi matuqar tausayawa yaran,

Shikenan musa ka Kula da qaninka, Allah ya tashe ku lfy ya raba ku da sharrin mutum....

Suka ce Amin,

Ismail yace baba ni gobe baxan tsaya lesson ba ka gayawa driver yaje ya ďauke ni da sauri,

Meyasa Ismail...
Mami tace xataje dani da Fauxiya unguwa banda musa,

Yace tor shikenan xanyi masa magana, musa yace
Baba baka cika min alqawari na ba, kace xakaje dani waje nayi karatu irin anty Iman

Fatyma ai tagama karatun kaima xakaje ni xan kaika da kaina,

Yaron yayi tsalle ya rungumeshi, thank you father Ina sonka..... Jikin Baban yayi sanyi sosai da kyar ya iya rungume yaron a jikinsa kafin ya rakasu har dakinsu da kanshi, yana labe yana kallon sanda suke game suna shan yoghurt Wanda a ciki yayi siddabarun sa, basu jima ba Kuwa suka xube gurin suna kakaki kumfa na soma Fita bakinsu, yaje da sauri ya ďauke yoghurt ďin ya musanya shi da Wanda baida komai ya fice, idan xakayi masa kallon natsuwa a Wannan lokacin xaka fahimci baya cikin hayyacinsa ko kaďan....

Mami ta fito daga ďakinta Kai tsaye study room ta nufa ta sami fatyma da tulin takardu a gabanta, gefenta kofin coffee ne da take korawa akai akai...

Iman ya kamata ki riqa bawa kanki hutu ki samawa xuciyarki sauqi, wannan karatun yayi yawa haka ke kullum akan takarda....

ta ďago idanunta da kyar tana kallon mahaifiyarta idanunta sunyi jawur sosai sun nuna kalar barci,

Mami you won't understand,karatun likita is quite different da sauran karatun, kibari nan da shekara ďaya na kammala karatuna na xama cikakkiyar likita xn fara maki surgery..

Surgery? ta tambaya da mamaki tana kallonta, surgery akan me?

Tayi far da ido tana kallon ta cikin shigar wasa irin ta ya'da uwa,
Tace Mami har ma sai na gaya miki kibari lokacin yaxo xaki sani...

Mami tayi dariya tana tattara littafan dake gabanta,
Ko Alhuda huda yana samawa xuciyarsa sauqi Iman, ki tashi kije ki kwanta,

Ta tashi tana miqa, a tare suka fito suna tafe suna hira, baba na ďakinsa yana jinsu hr lokacin da yaji Faty na fadin,

Mami Ina ya'yanki ko sunyi barci bnji hayaniyar game ba,

Me yiwuwa haka ne, amma bara na dubasu, ta nufi ďakin Faty na bayanta, yana daga window yana kallonsu har suka shiga, basu jima ba ya jiyo qarar fatyma tana kiran baba... ya koma yayi kwanciyarsa kamar mai barcin gaske,

Iya ruďewa sun ruďe bama kamar Mami da ta xama mutum mutum, batasan meke faruwa akan ya'yan taba, suna haka baba ya shigo cikin yanayin barci sosai ya nuna damuwarsa hrda kuka yayi.....

Tun daga lokacin abubuwa sun soma faruwa, walwala da jin daďi sun rageshi a gidan, ga kuďi kamar me, basu taba xargin sa akan Kuďin da yanda yake kashe dukiya ba saboda sun San dan siyasa ne,

Iman da Fauxiya ne kaďai suka rage masu a ynxu duniya, yana son su fiye da xaton mai karatu haka yake ji komai xai iya dan ganin farin cikinsu....

2 years later

Siyasa ta tashi sai faman xabe ake ana campaign, baba yaje wa Sima da buqatar Wannan Karon yana son matsayinsa na mataimakin gwamna kowane mutum ne yaci gwamna a birnin kebbi yana so yaxama mataimakinsa, wani xabe mai xuwa yana so ya fito takarar shugaban qasa....

Sosai sima tayi dariya wadda tayi matuqar raxana su,

Buqatar ka xata biya Abdallah, xakaci siyasa idan har xaka bada jinin matar ka......

Sosai ya raxana da jin kalamanta, bai taba xaton akwai abinda xai rabashi da Mami a ynxu ba saboda ta xamo ginshiqin rayuwarsa,

Auren soyayya sukayi, tun saurayi da budurwa, yana sonta tana sonsa.....

har ya dawo gida bashida sukuni tunaninsa yanda xai bada jinin Mami, ya kasa barci sai faman juye juye yake akan gado, duk abinnan da yake akan idonta tana kwance tana kallonsa,

Ta matso a hankali xuwa garesa,
Meke damun ka alhaji, yayi firgigit yana kallonta da mamaki,

Kada dai hr ynxu kana tunanin su musa ne? Ya girgixa kansa hawaye suka xubo masa, hankalinta yayi matuqar tashi,

Meke faruwa meke damunka? Ya janyota sosai jikinsa ya rungumeta...
Ki yafe min, ki yafe min Amina,

Jikinta ya ďauki rawa,
Ba abinda kayimin a xamana dakai, inma kayi na yafe ma nima ka yafemin,

Ya sauke ajiyar xuciya yana qanqame da ita yana jin sonta har cikin ransa Kuma har lokacin bai daina hawaye ba,

Ta maida kanta qirjinsa hankalinta ya kasa kwanciya da yanayin mijinta tabbas akwai abinda ke damunsa yake boye mata, Gobe da safe xata tuntubesa ya gaya mata damuwarsa....

Suna haka hr barci ya ďauke ta, ya sumbaceta sosai kafin ya janyo wani Jan kyalle qarqashin pillow ďinsa....

BABANA DA MIJINA

©Fertymerh Xarah 💞

5

Rumtse idanuwansa yayi kafin ya ďora mata kyallen a jikinta,

A hankali ta buďe idanuwanta tana kallon sa sakamakon wani raďaďi da taji a xuciyarta,

A hankali bakinta Na soma motsi kafin idanun su rufe dai dai lokacin numfashinta na ďauke,

Cikin wani irin yanayi ya rungumota jikinsa haďe da fashewa da wani irin kuka mai tsuma xuciya,

Mutuwar Mami sosai ta girgixa mutane, yan uwa da abokan arxiki bama kamar fatyma da fauxiya,

Shi kansa baba idan ya shiga gidan ya sami Fauxiya jikin fatyma sai hankalinsa ya tashi saboda tsananin tausayinsu da tausayin kansa, a lokacin Fauxiya is 6yrs, sun xama marayu.....

Ma'aikatan gidan ya qara saboda kula dasu, basu da wani aiki a gidan daga ci sai kallo sai barci, Fatin ce batada hutu saboda karatu...

Bayan wani lokaci akayi xaben siyasa Kuma yaci, sai ya Gina masu wani qaton gida mai hawan bene guda biyu kowane da gate ďinsa sai aka xagaye gidajen aka maida shi gate ďaya as 2 in 1,

Cikin ďaya suka tare sai ďayan ya ajiye idan fatyma xatayi aure su tare a gidan saboda bayaso tayi nesa dashi ko kaďan,

Sosai taji daďin haka ynda takeji a xuciyarta baxata iya barin qanwarta da mahaifinta ba, she is happy with the house, sai ta rungume mahaifinta cikin farinciki shima sai ya tsinci kansa cikin nishaďi ganin fatyma taji daďi...

*

Ahmad Deedah bayan rasuwar mahaifiyarsa, ya karbi tayin oga nas suna xuwa wurare da dama sata, ya kware ya iya bama kamar harbin bindiga, baya kissa kamar sauran abokansa sai dai ya tsoratar da bindiga, haka Kuma idan police sun masu taurin kai wajen bibiyarsu yakan harbi mutum a hannu ko qafa,

Cikin lokaci qanqani yayi fice ya xama gwarxo aciki Wanda oga nas ke alfahari dashi, duk suka fita operation sai sunci nasara wannan shine dalilin dayasa oga nas yabawa Deedah matsayi babba a cikinsu Kuma yakeji dashi and again yana

Please Login or Register in order to submit comment