Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

By

CHUCHUJAY✍🏽

Episode 2⃣7⃣➡2⃣8⃣

*'

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

    ACCRA GHANA.

    Kallo ɗaya zakayiwa dattijuwar matar dake zaune kan katafariyar couch ɗin dake cikin katafaren mansion zaka gane inyamura ce saboda irin yanayi na hasken fatarta wanda yawancin inyamurai suka da akwai ,yar gayu ce wadda a kallonta ma ba sai wani Ya faɗa maka hakan ba,MRS Ella Hans kenan mahaifiya gurin Evans,

Cikin wani irin yanayi take kallansa yayin da shi koma yake durƙushe kan gwiwowinsa a gabanta kansa a ƙasa,da harshenta na igbo tayi masa yare a yayin da take cewa"Evan ka fara magana,ban fahimci maganar kana san converting ba for what?

Saboda yarinya ?kana san yarinyar musulmai shine zaka yi converting ,you are a born christian and kasani barinka addinin mu is An abomination,ka cire yarinyar nan a ranka zaifi maka sauki,muna da kyawawan yaran igbo kamar sune sukayi Kansu ,you choose one,ga Amarachi cousin dinka ,yarinyar nan ba karamin sanka take ba amma kana nuna wa kamar baka san tanayi ba,just dare me i wont tolerate this. "

    Zama yayi Ya kamo hannunta yace "Mommy please ba ina san converting bane saboda Nadiya ,i Had to go through My bible again over and over again,jesus said i am a man(john 8:40)

And mommy a musulunci ma shi mutum ne,

And mom yace "i am a son of man(mathew,11:19)"

And God is not a man Mom,haka a musulunci shi ɗan mutum ne bana Allah ba ,

Yace "God sent me only To the lost sheep of israel (mathew15:24,mathew 10:5-6)"

Yace Allah yafisa girma a (john14:28).

Ya aikosane dan yayi ba a matsayin Allah ,bai aikosa dan a bauta masa ba amma dan ayi masa bauta shi kaɗai(matthew 20:28).

"He said i never claim tO be God because i have God To whom i cried and prayed to (matthew 27:46 and Matthew 26:39).

"He said i cant do anything on My Own i Do only what God commands me to Do(john 5:19,30).

Sake riƙe hannunta yayi gam gam yace "Mommy mun sani but we still Call him Son of God"

Ƙwace hannunta tayi tace "bansan mene yake san juya maka tunanin ba,im sure muslim girl d'in Chan ce,and komene zakace a cikin bible da ka karanta yesu ɗan Allah ne haka muka yarda dashi dukkan Kaka da kakani,so kar ka nemi ka chanza "

    Marairaice fuska yayi yace"Mommy abunda na lissafa miki wanda bible Ya faɗa is islam,saboda cikin ɗan abunda na sani a musulunci duk ya kunsa,and Trust me mommy Nadiya na ɗaya daga cikin hujja ta na ƙarban musulunci amma badan soyayyarta kawai ba saidan gamsuwa da naji hankalina da zuciyata yayi da islam,i sense peace there."

Da wani irin kallo da uwa takewa ɗanta idan Ya faɗa wata harka da ta yarda da zuciyarta da hankalinta akancewa ba dai dai bace tace "Oge ,islam addini ne na yan ta'adda they are all terrorist ,bana san ka ƙare a hell fire,kullum idan kaji an'a kashe kashe sune,duk wani kungiya na kashe mutane sune ,"

    Licking lips ɗinsa yayi 'dan yasan yana da l'ong way kafun Ya shawo kan ta Mommynsa duk da kuwa ita macene Mai saukin kai,

"Mommy dan wasu na ta'addancin da sunan musulmaine ba shine yake nuna duk wani musulmi terrorist ne ba,wasu sunayi ne dan bata addinin da kuma bacewa da sukayi ko kuma wata akida da manyansu suka saka masu a zuciya ,yana nufin kenan christians dake kashe kashe suma kowa Ya zama ɗan ta'adda kenan muddin yana cikin addinin? "

Akwai Good muslims out there da idan kikace su kashe maki goat ma bazasu iya ba ballantana ɗan adam,bai kamata muna yiwa juna kallo mara amfani ba bayan munsan akwai innocent one's out there,and masu kashekashen Chan suna kiran Kansu musulmaine amma basu san menene ma musuluncin ba,

Kamar yarda na faɗa maki it means peace and a ciki nake hango peace ɗina da naki dana Dad dana sister na mercy ,

Saurin ɗaga masa hannu tayi tace babu peace ɗinmu a ciki ,kai dai da kagano naka kaje kayi tayi.

Tasowa yayi Ya zauna a kusa da ita yana Mai sake  kama hannunta yace "Mom wallahi idan Ban Auri Nadiya ba Zan mutu ,idan kuma ban mutu ba zan haukace ,idan ban haukace ba kuma bazan kuma moruwa ba,sannan musuluncina Shine babban abunda zai sa na samu Nadiya da Peace."

    Da sauri tasa hannu ta toshe bakinsa tana Mai kaɗa masa kai tace "God forbid ,babu wanda zai faru da yarona ,indai kuma Nadiya ne na shirya zuwa Nigeria magana da mutanenta,and na yarda bazan maka dole Akan ka zauna kan addinin mu ba,idan ka Aureta im sure a hankali zaka gane gaskiya har Ita ka dawo da ita hanyar dai dai,amma for now kayi abinda kake so Evans Mommy na tare da kai and zan baka dukkanin goyan baya ."

Rungumeta yayi ƙam ƙam yana Mai jin wani irin dadi yana ratsa dukkan wani jikinsa,yadarta yake nema amma Ya riga yayi converting sannan ko bata yarda ba bazai hakura ba a hankali zaina cusa mata ra'ayinsa,

Raba jikin sa yayi da nata yana Mai gano yar karamar kwallar dake gefe idanunta ,hannunsa ya saka daidai inda ƙwallar take Ya goge yace "Mommy wata rana da zatazo ki yarda dani kice gwanda danayi converting cos im sure ranar zaizo."

   " Wanene yayi converting ,hope ba gizo kunnena kamun ba?

Mahaifin Evans, MR craig Hans Ya faɗa a yayin da Ya tsinci maganarsa ta karshe da Ya shigo gidan,

Saurin goge hawaye mahaifiyar Evans tayi tace "don't start it craig,Evans yayi converting and bana tunanin Laifi ne cos kaima daga wani addinin ka biyuni nan kar ka manta you were a jew and My love turned you a Christian "

    Zama yayi yana Mai shafa gemunsa yace "bazan damu ba sai naji idan Naji ba Islam Ya koma ba."

Cikin haɗe rai tace "kafaɗa dai dai,He's a muslim now ,"

Yana ƙokarin fara kunfar baki Ta dakatar dashi saboda ita ɗin a tsaye take ta fannin magana dan 'in ta faɗi ɗaya baya ƙaucewa .

    Tashi yayi ransa a mutuƙar bace yace"kar ki manta Ella muslims suka kashe kakana and muslims sune manyan maƙiyan Family ɗinmu dan haka kafin yaranki yaje yayi abunda zai dame shi Ya dame mu kisan ta inda zaki gyara cos curse ɗin da kakata ta aje ma duk wani danginmu da Ya koma musulmi zai kamasa sai dai idan har Kina so yaranki Ya talauce yakuma rayu babu jininsa ko ɗaya."

Yana gama maganarsa Ya bar Falon.

    Dukan kirjinta tayi a hankali tana Mai jin wani abu yana Mai tsaya mata a kirjinta tace "God ,God have mercy on me"

Kama hannunta Evans ya kuma yi yace "mommy kinsan ban tab'a yarda da superstitions ba and bazan fara yarda dasu yanzu ba,babu abunda zai faru dani,Na yarda da Addinin dana ƙarb'a zai kareni daga dukkan wani curse da yake akwai ,Ballata na ma ban yarda da wani curse ba,

Duba agogonsa yayi yace mommy lokacin sallah yayi let me Go and pray zamuyi magana more idan na dawo ,

Har yakai baki kofa tace"Evans you're walking on the wrong path My child."

    Murmushi kawai yayi mata baice komai ba Ya bar ɗakin yana Mai jin kamar an sauke masa wani irin nauyi a ƙirjinsa ,

Bayan yaje yayi sallan Azahar a masallacin da Ya karbi shahada Ya biya gurin wani abokinsa GodFavourite wanda shine Ya fara saka masa interest nayin Tattoo a gefen cikinsa da bayansa wanda da fari yayi ta cewa ayi masa Permanent amma Ya kafe Akan A'a saboda any time zai iya gogewa saboda dama bawai dan yana masifar so bane yayi,sannan gashi a ranar daya karbi musulunci Imam ɗin sai da yayi masa maganar Tattoo Ya faɗa masa da wuta za'a Goge masa Ranar gobe ƙiyaman,dama ba Mai zama har abada yayi ba ,menene yayi zafi,ba ƙaramin tsoro wutar da ake ta faɗa masa take basa ba,dan haka Dole yayi ƙokari wajen ganin ko yayane Ya kauce mata.

    A bar ɗin da suka saba haɗuwa Ya tarar dashi ,Cup ɗin Whiskey ɗin da yake sha Ya basa yana faɗin "Man where have you been"

Kallan wine d'in Evans yayi kana yasa hannu guda Ya tura masa yace "i don't do alcohol  anymore And nazo gurin ka ne kazo ka raka ni".

Yar dariya favour yayi yace"Man don't tell me that What i heard was true"

Kaɗa kai Evans yayi yace"its beyond tunda gani gabanka ina san ka tashi yanzu muje gurin tekashi Ya goge mun wannan Tattoo ɗin na jikina My religion is against it."

    Kaɗa kofin giyar Favour yayi ƙanƙarar ciki na motsi yace "that's sad man,tho i wont Judge you ,but Bro you gonna deprive yourself duk wani enjoyment na rayuwa cos muslims na living boring life ne,no Alcohol,no clubs ,no Amazing sex Before marriage ,Zero 1 night stands Bro ko masturbation ɗinan fa i heard that islamically is haram,you and your body again ,You wont even have the space to steam out your seed your self,juyowa yayi yana Mai kallan Evans da kyau yace "ina ƙokarin suggesting maka Dick pierce da nayi ,omo Bro i had sex With juju this morning and it was hell because she oath not to leave me saboda yarda ring ɗin ke kara mata pleasure,its so sad that you're still a virgin and more ka shiga addinin takura.

"Murmushi Evans yayi yace "ban san inda Bible yace maka duk abun nan da ka lissafa a musulunci Ya hallarta a Christianity,a good Christian yana avoiding duk wani abu da ka lissafa a yanzu , "

    Shiru favour yayi kana yace "zaka iya  zama a addininka sai ka kare duk abun da na lissafa why do you convert."

Dafasa Evans yayi yace "babu abunda zan faɗa maka ka fahimta dan haka kawai ka tashi muje ka Kaini inda za'a cire mun abunnan Ya dameni already."

    Dariya favour yasa yana Mai ƙarasa shanye wine ɗinsa Kana yace"lets go man you're My gee for life ,be an idol worshiper and imma love you equally ."

    Yana tunani kiran Nadiya amma ya hana kansa cos yana san yaje mata ne a mutum as pure as honey ,

Dan suna ma ita yake so ta bashi.


A/N:

A page ɗinan wanda yaji kamar cin fuska Ya yafe mun sannan Note im not trying to say this religion is better than this,akwai christians readers hello im not saying ku juya cos addininku ba dai dai bane i have no place, i just state' the fact .

Allah yasan dai dai ,sannan ya yafe mana baki ɗaya.


Chuchujay✍🏽
[3/6, 5:16 PM] Chuchujay✍️: AHALINA

(Siblings of different father's)

Book 2 'in AURE UKU series

           By

CHUCHUJAY ✍🏽

Episode 2⃣9⃣➡3⃣0⃣

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ

    Cikin Yauƙi Jamaimah ke takawa dan zuwa motar da Nameer Ya shiga ,ganin Ya wa motar key tasan tabbas idan bata hanzarta ba zai tafi yabarta Ya saka ta ja akwatinta gudu gudu sauri sauri ta nufi motan tana Mai faɗin "Baby mana wai menene hakan?"

Buɗe bayan motar tayi ta saka akwatinta dan kit din kana ta koma passenger seat ta zauna,

Tun kan ta rufe ƙofar da kyau Ya fafareta dan har sai da ta saka ƙara saboda yarda ta tsorata,

Tunda suka fara tafiyar har suka isa gidan bai ce mata komai ba hakazalika itama dan ganin yarda Ya haɗe rai kamar an aiko masa da saƙon mutuwa,

Bakin katafaren gidansa dake cikin GRA ya tsaya yana Mai yin horn,sau ɗaya yayi Mai gadin gidan yazo da gudunsa Ya buɗe masa dan yasan motar Nameer sarai,

Bai tsaya kula gate man ɗin ba Ya nufi ma'adanar aje mota Ya aje,

Shi Ya fara fita Kana ita ,

Get man d'in da Ya tako garesu ta kalla da wani yauƙin wulaƙanci tace "kai zo ɗauki min akwatina ka shiga dashi ciki sannan kabi mun shi a hankali dan yayi costing salary dinka sau goma."

    Da mamaki Nameer Ya juyo yana kallanta dan a haife Mai gadin Ya haifeta,

Hannayensa Ya saka a kugu yayin da Mai gadin Ya nufi akwatin dan dauka amma Ya tsaya a lokacin da Nameer yace "Baba sulaiman bari mata akwainta ka koma kan aikinka dan aikinka yafi ɗaukan akwatin nan."

Babu musu Baba sulaiman Ya juya yana Mai faɗin Angama ranka shi daɗe.

    Buɗe baki tayi tawani shagwab'e fuska tace "yanzu dan Allah Baby mene hakan,Mai zaisa kayi humbling ɗina gaban Mai gadi kaskantacce,wannan ai salan kaja mun raini ne ina matar gida.

Karamin murmushi yayi Ya Kalleta a kyau yace "Jamaimah kenan,kina bani mamaki,ke gani kikeyi kamar ke kinfi kowa a duniya saboda kawai an haife ki gidan sarauta ko?

Ku gani kukeyi kowa ma banza ne saboda kuna da mulki ko?

Bari kiji da kyau ki kuma saurareni,abunda kikayiwa iyayena Yau yana daya daga cikin abunda zaisa bazan tab'a sakinki ba sannan bazaki tab'a samuna miji ba muddin ke wulakanci shine jigon rayuwarki,sannan zan nuna maki ke ba kowa bace face mutum wadda idan kika mutu kasar da za'a saka kaskantacen almajiri kema nan za'a sakaki ,kilanma nashi kabarin yafi naki idan yafiki aiki mai kyau domin abinda baki sani bs shine wulaƙanta dan adam kawai zai halaƙar dakai,.

Abu Mai muhimmanci kuma da nake san ki sani shine  a kasarki ne kike gimbiya amma a ƙasata a gida na a matsayin Matata ke bakowa bace sai wadda zata zauna tayi mun biyyaya tayi ibadar Aure,idan kina so fa kenan,amma duk ta inda kika bullo nima na iya bullawa ta gurin ni dake kuma shege Ya fasa,kina wannan wulƙancin kuma wallahi zanyi Aure har mata uku musha soyayya ke kuma ki sha wulaƙancinki ke kaɗai tunda shi kika zab'a 

    Yana kai ƙarshen zancen sa Ya juya dan shiga cikin gidan,binsa tayi da ido tana Mai jin zuciyarta na mata wani irin zafi musamman da Ya kawo mata maganar Aure,Cije leb'enta na ƙasa tayi tace "ina sanka Nameer sannan kai nawane ni kaɗai ,bakuma zaka chanza ni daga yarda nake ba ,haka nan zaka karb'eni domin wannan sarautar a jinina take babu wanda ya isa Ya cire mun wannan izzar ."

Da haka tabi bayansa da kayanta,

A falon dake ihun Naira ta tarar dashi tsaye hannunsa cikin aljihu ya juya mata baya wanda ya tabbatar mata da jiranta yake,

Aje akwatin tayi ta taka garesa ,cikin wani irin salo ta saka hannunta ta ƙugunsa ta rungumesa ta baya wanda sai da Ya saka shi ajiyar zuciya,idanunsa Ya rufe gam yana Mai jin jikinta kwance a nasa kamar dan shi akayi,

Lafar da kanta tayi a bayansa cikin wata irin shagwab'abbiyar murya tace"Baby ban iya faɗin im sorry ba da na fada maka koda zuciyarka zatayi sanyi,a jininmu yake faɗar Kalmar haƙuri tana bamu wahala,amma komene nayi maka bazaka iya barinsa Ya wuce ba idan ka tuna saboda kai na baro  komai nawa nazo gareka ,i love you very much Nameer sannan ni banyi tunanin zuwana gidanku zai jawo abunda Ya jawo ba da zan nemeka ne ko ta yayane na sanar da kai tunda address ɗinka  ma a company dinka na samu,kar ka saka na shiga wani Hali ,ka kalleni mana da kyau,nasan kaima kana jin abunda nake ji akanka gareni,cos ni macene da babu Mai ganina da tayin soyayya ya dauke ido,please Baby."

    Ƙaramun murmushi yayi Mai sauti da tagama maganarta ,tabbas yana san Jamaimah amma soyayya bata rufe masa ido ba Ya zauna yana kallan wanann rashin tarbiyar tata dan hatta a kalami bata da tarbiyya wanda dole Ya gyara mata zama tasan cewa mulki ba hauka bane,sannan sai Ya gasa masa aya cikin ruwan sanyin da bazata taba sanin lokacin da zata faɗa masa sorry ba mara iyaka,

Duk da yana jin kamar yayi ripping duk wani kaya da ke jikinta saboda irin rungumar da tayi masa amma ya danne lust dinsa Ya kama Hannayenta Ya b'anbare su daga jikinta Ya juyo yana kallanta yace "Gimbiya Jamaimah Rais,tashen ki yana burgeni,wato baki iya faɗar sorry ba sannan kike ikirarin Kina sona ,okay barka da zuwa rayuwar Nameer Babu gayyata , "

Ɗaki ɗaya Ya nuna mata cikin ɗakuna biyar d'in dake jere da juna yace "ga ɗaki Chan ki kai kayanki sannan kiyi amfani dashi,"

Cike da mamaki ta juyo ta kallesa tace"ni bazan zauna ni kaɗai ba a ɗaki idan Babu kai sannan naga gidan dagani sai kai ,ina yan aiki dan ni wallahi bazan iya aiki ba",

    Baice mata komai ba Ya juya dan shiga ɗakin dake nasa yace "idan bazaki iya aiki ba gimbiya JAMAIMA zaki iya komawa gidan ku ,amma ki sani da Aurena zakiyi ta yawo dan wanann karen nima yin kaina bazan sakeki ba.

Yana kai karshen maganarsa Ya shige ɗaki na huɗu dake daga Chan ƙarshen corridor Ya barta tsaye.

    Tab'e bakinta tayi taja kayanta tana mai faɗin"zaka biyu ne indai muna gida ɗaya".

    Bayan shigar Nameer shahararren ɗakinsa kan gadonsa Ya faɗa yana Mai duba lokaci ƙarfe Ɗaya da rabi na rana,wayarsa Ya ɗauko yayo ordering pizza dan bashi da komai na abinci gidan sannan pizza ɗin yake sha'awa amma yana fita zai siyo mata kayan abinci duk da kuwa yasan ba iya girkin tayi ba amma a hakan sai Ya gyara mata zama tasa ita ba kowa bace.

Wayarsace ta fara ruri,Nadiya ke kiransa, kira ɗaya Ya ɗaga,conference ne su uku,daga ɗayan bangaren Nadiya tace "Hamma are you okay?"

Ajiyar zuciya yayi yace "im Okay Nadiya and nasan yarda zanyi da Jamaimah Yes i was planning to talk about her da su mami idan komai Ya lafa cos ina santa ,we made mistake amma Aurenmu a ko ina Aure ne wanda ya ɗauro,amma yarda tazo wa su mami dole ne nayi da gaske wajen ganin na gyara mata zama."

Daga ɗayan bangaren Abdallah yace "Hamma ka dai kula kar ka shiga hakkin ta cos tun ranar da aka ɗaura maku Aure hakkinta ya hau kanka.

    Rufe idanunsa Yayi kamar yana gabansu yace"Insha Allahu bazan cutar da ita ba ,Ni dai alfarma ɗaya zakuyi mun wanda shine ku tayani wa mami magana da Papa dan Allah."

Assuring ɗinsa sukayi inda Abdallah Ya fara fita a wayan Akan zaije wani taro da aka gayyace,

Yar hira Kaɗan suka taba da Nadiya wadda duka akan lallashin junane kafun sukayi hanging Call ɗin .

    Pizza ɗinsa ce tazo ya fita ya shigo da ita,

A ƙaton dining table Ya zauna bayan Ya ɗauko holandia da cup,

Ya buɗe zai faraci ta fito a dakin nata cikin buguwar riga mara Nauyi baƙa wadda ta ɗauki farar fatarta sosai,

Saurin ɗauke idanunsa yayi akanta yana Mai gutsurar pizzan da Ya ɗauko,

Cikin wani irin Yanayin ta tako garesa tana Mai yarfe hannu tace"Baby pizza God abunda nake craving kenan."

Zama tayi tana Mai ɗauko cup d'in da Ya zuba hollandia ɗin tayi sipping,bai hana taba sanann shima bai hanata sha ba ,a haka suka fara cin abincin suna shan hollandia ɗin a cup ɗaya yana Kara masu,

Bayan sun gama Ya kalleta yace "anjima zan kawo Food stuffs zanki fara girki".

    Wata irin dariya ta saka har tana ƙwarewa tace"amma wasa kake ba?"

I mean hatta ruwan wankan kaimun ake a gidan mu ,ni ko ruwan zafi bansan Ya zan ɗaura ba.

Tashi yayi bayan ya goge bakinsa yace "Ai kin iya kunna data dan haka kiyi browsing,"

Wayarta dake gefenta Ya ɗauka yasa numbernsa yayi dialing tana shiga Ya kashe yana Mai aje mata yace "Ni zan fita ki kula mun da gida sannan bathroom ɗina yayi datti kije ki wanke mun,bana san na dawo nagansa haka nan."

    Kafun tace wani abu Ya fita a gidan,

Murmushi tayi bayan fitar sa tace "abu na technology ,kafun ka dawo na samo yar aikin da zata wanke maka bayin amma ni kam sai dai a soni a lallab'a ni. "


    CHUCHUJAY ✍🏽

*
[3/6, 5:17 PM] Chuchujay✍️: AHALINA
(Siblings of different fathers )
Book two 'in Aure uku series
       By chuchujay
Episode 3⃣1⃣➡3⃣2⃣.
   NASREE VENUE.
Cike Nasree Venue yake ,katafaren guri da aka ƙirkiresa saboda taro irin na manyan malamai da walima,
Taro ne ake a gurin na manyan malamai waɗanda kana kallansu kasan malamai ne na gaske da gaske ,
Duk cikin su malami ɗayane yaro wanda bazai wuce shekaru Talatin da tara ba da haihuwa,
Wani dattijan malami ne Ya tashi yana Mai gabatar wa ta buɗe seminar ɗin da suka taro domin ita,
Kiran babban baƙo aka fara wanda shine Abdallah amma bai ƙaraso ba.
    Tunda ya iso harabar gurin yake jinsa gashi nan dai amma hankalin sa ba kwance ba baki ɗaya,
Daliban da suka taru dan bawa ilimi a gefe Ya kalla bayan Shigarsa gurin bayan sa da masu basa tsaro,
Yana shiga Ya samu gurin da aka tanada dominsa ya zauna ,
Bayan wasu mintuna aka gayyacesa domin zuwa kan stage yayi jawabi,
Tafi guri Ya ɗauka inda shikuma ya taka yana Mai faɗaɗa fara'arsa ,
Bayan yayi sallama yafara jawabinsa cikin iyawa da sani,
Bayan wasu lokuta ya bada filin tambaya inda yake amsawa duk wani Mai tambaya cikin hikima da ilimi,
Daga chan baya guy d'in dake baya ne fuskarsa ɗauke da face mask Ya ɗaga hannu alamun zaiyyi tambaya inda aka basa dama yayi,
Daga zaune mic na hannunsa yace "akaramakallahu munajin labarai akanka wanda muke da yakinin gaskiya ne amma muna so ka sake sanar mana da gaskiyar akan maganar tunda mu nan kowa yanaso ne a ɗora ka a kujerar shugaban matasan malamai,"
Tambaya ta anan kuma itace"shin menene gaskiyar zama mahaifinka ɗan shan jini wanda Ya tara dukiya da kuɗin jinin mutanen da basuji ba basu gani ba,sannan mun tsinci labarin cewa ka gaji wani abu daga cikin dukiyarsa ta haram ,Shin menene gaskiyar Al'amarin?"
Shin ka zama babban malamine a yarda kake yanzu dan kawai ka boye tabon mahaifinka da baka san mutane su faɗa?
    Daga kusa dashi ɗayan yace "Haka maganar take dan Babu wanda bai sani ba dan hatta mahaifiyarsa ance kafun ta Auri mijinta na uku abu yayi ta yaɗuwa Akan suna zaman daduro ne ."
Daga nan sauran abokan da suka zo tare suka fara fadin "a faɗa mana gaskiyar Al'amari,"
Take jikin Abdallah Ya fara karkarwa dan a rayuwarsa ta duniya babu abunda bayaso kamar ace yau ana masa magana kan mahaifinsa ko Akan clip ɗin mahaifiyar sa da yayi yawo a baya wanda yake ƙanzan kurege ,
Haka nan yaji jikinsa Ya fara kyarma musamman da yaga kowa kallan sa yake yana jiran yaji ta bakinsa sannan ga yan jarida kowa na faman haska masa camera suna san ɗaukar zazzafan shayi ,wani irin jiri yake ɗibansa,cikin nutsuwa ba tare da yace komai ba Ya fita daga kan mambarin yana mai jin kamar zai faɗi,
Ɗaya daga cikin waɗanda suke basa tsaro ne yayi saurin zuwa Ya kamosa inda suka taimaka masa suka fitar dashi a gurin yayin da kowa ke ihu da ikirarin Ya dawo Ya fadi gaskiyar abinda ake faɗa ɗin yayin da shikuma yake jin muryoyi da yawa suna masa tsiwa a kunne ,
Yana zuwa bakin motarsa hannu Ya ɗagawa wanda Ya  kawosa inda Ya fahimta yaja baya,
Ya jima a motar shi kaɗai yana san kansa Ya dai daita kafun yaja motar yabar harabar gurin,
Shikadai yake bulayi a titi dan baya san zuwa gida a haka,so yake yayi kuka sannan yana so wani Ya ara masa kafaɗarsa yayi  ,bashi da kowa a wannan lokacin da Ya wuce yan uwansa biyu,Nameer da Nadiya waɗanda bazaiso takura masu da damuwarsa ba Ya ƙara masu ciwo Akan wanda yake damunsu,hakazalika iyayensu sunfi kowa shiga damuwa dan me zai ƙara masu da nashi,
    Duk cikin yan uwansa shine wanda Ya samu uba mafi muni wanda Ya barmasa tabo mafi muni,duk yarda yaso Ya nuna He's okay amma abun yaci tura He's not and yau Ya kara tabbatar da He's not,
Duk ƙokarin da yake wajen zama mutum nagari amma sai da aka samu waɗanda suka binciko bakin mumunan bayansa suka yab'a masa a wajen taro mafi muhimmanci gurinsa,a gurin taro da matasan dalibai ke dubansa a matsayin abun koyinsu manyan malamai suke ganinsa da daraja amma a yau magana ɗaya wadda take dole tana jikinsa ta zubar masa da dukkan wannan kimar ,
Yana wannan tunani tunannin ya juya kan sitiyarin motarsa ya nufi gidan Auntynsa shatuh wadda sau da dama takan basa shawara ga damuwarsa sannan yaji hankalinsa Ya kwanta da shawarar saboda iirin shakuwa da yayi da ita tun yarinta,sau tari idan komai yayi masa zafi gidanta yakanje yayi Clearing kansa na kwana biyu.
    Yana

Please Login or Register in order to submit comment