Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ya ce don har lokacin a buge yake, a kufule Hajiya ta karasa ya wanka masa mari wanda ya sa sai da ya tuntura daga zaunen da yake.


"Kara masa shege tsinanne...


"A'uzubillahi haba Alhaji Bukhari ya haka, da bakin ka kake tsinewa ɗanka? Shin baka san baki shi yake kara kangarar da yaro ba? Akwai lokutan karɓar addu'a idan mutum ya yi tana karɓuwa ko lokacin da mala'iku za su ce amin. Shi ya sa ake son iyaye su rika saka linzami a harshensu suke yin furucin mai daɗi ga yaransu ko da kuwa yaran sun ɓata musu rai su yi kokarin danne zuciyarsu su faɗi kalma mai daɗi, ko da karamin yaro ne idan ya yi laifi kar ka ce masa shege ɗan iska, ko munafuki da sauransu, ka yi kokarin cewa Allah maka albarka Allah sa wannan abin da kake yarinta ce, amma furuci mai muni shi yake kara kangarar da yaro maimakon al'amura suke baya sai suke yin gaba bayan kuma duk halin da suka shiga mu ne dai a ciki" Alhaji Khamis ya katsewa Alhaji Bukhari maganar.



Dantse bakinsa ya yi yana jin yadda zuciyarsa take zafi so yake ya furzar da maganar ko ya ji sassauci amma kuma an taka masa birki da mummunan furuci.



Wani ashar Hajiya ta yi wa Umar mai maiko...



"Hajiya Rayyanatu ana ga yaki kina ga kura, ana hana wani maganar ke kina yi"

"Wallahi Alhaji Khamis yaron ne sai da haka kullum daga an hana shi sata sai ya koma sane"


"Kin ji fa, wai a nan fa kina nufin daga kin hana shi wannam sai ya koma wancan amma maimakon ki faɗi hakan sai kika ce daga an hana shi sata sai ya koma sane, shin sata abu ne mai kyau? Ko sane yana da kyau? Amma kina danganta ɗanki da shi ko zagi da iyaye suke yi wa yaransu tun suna kanana ba tarbiya ba ce saboda yara suna harda a kwakwalwarsu, sai kun ki yaro ya yi zagi sai ku kama shi ku duka kuna ikirarin ba kun hana shi yin zagi ba bayan kuma ku kuna yi kenan idan ba abu bane mai kyau mai ya sa kuke yi? In dai ana bada tarbiya sai an kiyaye da wasu abubuwan sosai saboda yara sun fi ɗaukan abin da ake yi a aikace fiye da wanda ake koya musu" Ya ce yana kallonta daga ita har Alhaji sai suka yi ɗif domin su basu san duk wannan abubuwam da yake faɗa ba saboda su dama ba wani damuwa suka yi da tarbiyar ba.


"Ai komai ya zo karshe a gobe zan ɗaura maka aure domin ka sani ma, babu fashi ko ka san annabi ya faku ba, idan ka ga kana da iyali ka hankalta" Baba ya ce yana nuna shi da yatsa.



"Kuma wannan shawara ce mai kyau aure yana sa nutsuwa da hankalta musamman in aka yi dace da yarinyar kwarai, sai dai ba a nan gizo yake sakar ba, shin a ina za ka samu matar? Ka san dai abokin kura guza kuma na san kalar zaren kalar yadin, ma'ana ba za a samu wata mace budurwarsa mai nagarta ba don babu nutsatstsiyar da za ta kula shi, kuma in ba ta kirki ba ce maimakon ya shiryu sai dani ya kara shiga dawa wato lamura su kara taɓarɓarewa" Cewar Alhaji Khamis.


"Akwai matar da yake so kuma nutsatstsiya ce" Alhaji Bukhari ya faɗa.


"Ikon Allah!" Ya ce da mamaki don ya san dai wace ce za ta yarfa da haka, kafin ya dawo daga duniyar tunanin da ya lula na kankanin lokaci sai ji ya yi Alhaji ya ɗaga waya yana ta kiran mutane yana cewa akwai ɗaurin auren ɗansa da za a yi gobe karfe goma sha ɗaya na safe, haka ya ringa kiran jama'a yana gamawa ya shiga kwalawa Hawwa kira.

"Hauwa'u! Hauwa'u!! Hauwa'u!!!" HAWWA da take ɗakin tana ɗinke wa SABEER rigar islamiyarsa da ta yage da zare da allura ta daɗe tana ta yi kasancewar bata iya ba, ita hatta keken ɗinki ma bata taɓa ganin yadda ake ɗinki da shi ba sai dai in an ɗinko musu kaya ta saka kawai wata rana ma in ɗinkin bai yi mata ba ta ce Ummie ta bayar da kayan saboda gata da suke da shi amma sai ga shi yanzu rayuwa ta juya musu maraici ya sa har tana iya ɗinki da allura da zare, ga kayan duk sun tsufa sun koɗe ko ɗan aikin gidansu ba zai saka kayan da suka yi mugun tsufa haka ba, amma sai ga shi abin da suka fi karfinsa ya fi karfinsu dama yawanci gata na iyaye ne daga ranar da ka rasa su a duniya daga lokacin za ka fahimci girma da darajarsu babu wanda zai gane hakan sai maraya wanda ya rasa uwa ko uba ko ma ya rasa su gabaɗaya. Ko da za ka samu dukkanin gata a bayan ransu to ganinsu kaɗai ma rahma ne, daga lokacin da mutuwa ta yi yankan kauna a tsakaninku za ka gane girma da ɗacin maraici!.


Yar aikin da ta shigo ɗakin da sauri take faɗa mata ta jiyo Baba yana kwala mata kira, da sauri ta yi jifa da riga da zare da allurar hannunta, don ta san yanzu za a ce ta yi laifi a hukunta ta ita kuma bata ji ba saboda hankalinta yana a kan SABEER suna hira suna ta kyalkyalar dariya saboda su biyu ne farin cikin junansu.



Fitowa ta yi da sauri ta nufi sashen Baban ta shiga da sallama, tana shiga ta samu gefe a kasan tiles ta durkusa gwiyoyinta a kasa cikin ladabi ta ce.


"Ga ni Baba"

"Gobr da karfe sha ɗaya za a ɗaura auranku da Umar.... Idanu ta ɗago tana kallonsa gabanta yana bugawa da karfi, hatta jin ta sai da ya ɗauke na wasu sakkani don kunnen nan nata dummm ya yi.

"Alhaji ƴar aiki za ka aurawa Umar?" Alhaji Khamis ya tambaya yana kallon HAWWA wacce kayan jikinta suka tsufa hatta hijabin jikinta wuyan ya yi yawa ga shi daga gefe da yaga yadda daga gani dutsin guga ne ya kona. HAWWA jin an ce mata ƴar aiki sai da idanunta suka kawo ruwa duk da bata da bambanci da ƴan aikin, hatta kayan jikinta har gwara na wasu ƴan aikin, ita mutumin ma kallon sani take yi wa fuskarsa.



"Ƴar gidan Yaya ce marigayi"


"Wai HAWWA ce wannan?" Ya tambaya da mamaki.

"Ita ce" Hajiya ta ce, shi kuwa Umar lokacin ma bacci ya ɗauke shi yana yashe a tsakiyar falon don tun mangyarin da Hajiya ta masa sai ya kwanta duk kafafunsa a cikin aman da ya yi.

"Amma Alhaji Bukhari baka kyauta ba, yanzu ƴar zumun naka ce ka bari haka a wulakance? Yanzu da shi ne zai bar tsatsonka su wulakanta idan baka raye?" Ya tambaya cike da mamaki

"Dakata! Alhaji Khamis kar ka ɗora mini jakar tsaba kaji su bini, kar ku ka sa duniya ta zage ni ya zan ɗakko yaran su biyu in rike su cin su shan su sutura da karatunsu duk in ɗauki nauyi amma kake mini wata magana a karshe don in kara dankon zumunci ma ɗauki ɗana sukutum zan aura mata"

Murmushin takaici ya yi mai ciwo kafin ya ce

"A ina rufin asirin yake? Wannan ne gata, kalli suturar da take jikin yarinyar nan kamar wata almajira yanayin jikinta da na nutsuwarta bai yi kama da na wanda yake cikin farin ciki ba sannan maganar aura mata Umar kuma ai ita za a zalunta tun da duk wanda yake da dogon tunani ba zai ɗauki ƴa mai kamala da hankali kamar HAWWA ya aurawa mashayin giya ba d...

"Ya isa haka Alhaji Khamis! Wasa ya yi wasa ban da tsinkarin uwar miji, idan magana za ka faɗawa mutane da tada tarzoma haɗe da tada zaune tsaye to mun gode ka je umma ta gaishe da aisha" Hajiya Rayyanatu ta ce rai a matukar ɓace.

"Na ji kuma zan fita muku a gida amma ina so ku sani zalunci ba abu ne mai kyau ba, kuma cin dukiyar maraya haramun ne domin Allah maɗaukaki ya faɗa a littafinsa mai tsarki cewa, kada ku ci dukiyar maraya da zalunci, a wani wajen kuma ya ce hakika masu cin dukiyar maraya da zalunci ba komai suke ci ba a cikin su, illa wuta, kuma za su shiga cikin wutar sa'ira. Domin na sam tabbas kun hau dukiyar marayu kun yi kaka gida, saboda dukiyar da mahaifansu suka bari basu ba hatta ƴaƴa da jikokinsu sai sun mora, amma tun ba a je ko ina ba tun ana shekara biyu da mutuwarsu ga shi nan suturar kirki ta gagari ƴaƴansu suna rayuwa kaskantacciya, yanzu da iyayansu za su dawo duniya mai za ku ce musu? Tabbas duniya ta zo karshe zumunci ya ki daɗi amana ta yi karanci amma a juriya zuwa tafi wata rana tulu zai fashe! Na bar ku lafiya" Ya ce yana juyawa ya fice.


Daga Baban har Hajiyar ransu ne ya yi matukar ɓaci don kalamnsa basu shige su ba illa haushin sa da takaici. Haushi ne ya sa Hajiya Rayyanatu ɗaga kafa ta hamɓare Umar da ya yi shame-shame don asara yana sakin munshari. Jin an masa kafa ya tashi zaune a kiɗime yana rarraba idanu kamar shege a rabon gado.
[1/5, 8:58 PM] Sadiya Abdulrazak: *RUƁAƁƁIYAR IGIYA*



NA


MAMAN AFRAH


*GARGAGAƊI*

Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ko ta wace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowane kafar sadarwa ba sai da izinina a kiyaye⚠️

JAN HANKALI

Kirkirarran labari ne ban yi shi don wani ba, idan har ya yi daidai da labarin ki/ka to arashi ne.


SADAUKARWA

Kwacakwam labarin daga farkonsa har karshe sadaukarwa ne ga kawata HASSANA B.S Allah saka miki da alkairi ya raya zuri'a.



PAGE 9


"Sai ka tashi malalacin banza gobe ɗaurin aurenka amma maganar auren kana yashe kamar kayan wanki" Ta ce tana harararsa ganin ya saki wata uwar hamma.

"To a kai ni ɗakin amaryar tawa mana" Ya ce yana kallonta da lunsassun bugaggun idanunsa.

"Hajiya ki kyale wannan ba a hayyacinsa yake ba, da yana cikin hankalinsa da yanzu yana cikin farin cikin murnar auren nan"

"To Alhaji"

"Yanzu dai ita wannan ki binciko mata kaya a cikin kayan Lawisa wanda za ta saka goben'

"Wallahi ba za a ɗauko a kayanta ba wannan yarinyar da ta tsani a taɓa mata komai nata, kana gani yanzu kamar ita ce uwata ko raga mini bata yi ina faɗa tana faɗa"

"To ki ɗakko mata marar ɗinkawa a kayanki sai a bada ɗinki"

"Nawa ai sun fi karfin ajinta amma zan san yadda za a yi"

"Don Allah Baba ka taimaka mini ni bana son a mini aure karatu nake so na yi" HAWWA ta ce tana hawaye.

"Matsayinki na mai rangwamen gata wato marainiya, har kina da zaɓin kan ki? To ai karatun secondry ma sa kika yi ya ishe ki son ko yo zurfi a karatu shi mijinki da bai san ko bihim ba ki zo kina goranta masa to ba za ta saɓu ba bindiga a ruwa" Cewar Baba.


Sai da suka gama faɗar abin da za su faɗa suka ce ta tafi, dama ba shawarar ta ake nema ba umarni ne, haka ta tashi ta fito ta nufi ɗakin Baba Sadiya tana zuwa Baba da take linke kaya ta je ta faɗa jikinta tare da fashewa da kuka sosai Baba ta ji abin ya taɓa ta lallashinta ta shiga yi har sai da kukan ya tsagaita, sannan Babar ta shiga tambayarta dalilin kukan nata, nan ta shiga labarta mata abin da ya faru, sosai ta tausaya mata kuma take jinjina rashin imani da tausayi na mutanen gidan uwa uba rashin amana.


"Baba ki bani wannan zoben da na baki ajiya"

"Hauwa'u shi kaɗai fa ya rage miki mai ya za ki karɓa suna ganinsa a hannunki za su kwace"

"Guduwa zan yi Baba, barin gidan nan zan yi ba zan zauna a rusa mini burina na karatun likita ba, burina na taimakawa al'umma mararsa lafiya, burin da tun ban san inda yake mini ciwo ba yake damfare a zuciyata"

"Haba Hauwa'u ina za ki dosa a halin yanzu?"

"Kaduna zan je Baba wurin yayan Ummiena da aka hana ya tafi da ni, kuma da kunnena na taɓa jin Hajiya tana waya tana cewa wurin malamai ta je aka masa mantau, wai ba zai kara tunowa da mu ba bare har ya zo neman mu, sai dai makarin abun shi ne idan ya yi ido huɗu da mu tun da ta san mu ba za su bari mu je gare shi ba" Ta ce cikin sanyin murya sosai Baba ta jimanta maganar tana kallon HAWWA sannan tana jinjina rashin imani na su Hajiya Rayyanatu.

"Kar ki damu zan baki ko ni ba zan so ki auri wannan yaron ba da shi kansa bai san kansa ba, amma wani hanzari ba gudu ba ta yaya za ku bar gidan nan bayan gobe ne ɗaurin auren kar ki tafi da igiya a kan ki'

"A daren yau za mu gudu Baba, ba zan bari igiyar aurensa ta ratayu a wuyana ba, ni dai ki taimaka mini Baba ki je kasuwa ki sayar mini da zoben ki bani kuɗin mu samu kuɗin mota " Shiri Baba Sadiya ta yi tana nazarin maganar tana son gano matsalar da za a iya samu idan aka aikata hakan ko aka san da saka hannunta a guduwar yaran sai dai irin halaccin da mahaifiyarsu ta mata da kirkin ta gare ta ba za ta bar ƴaƴanta su tozarta ba daidai gwargwado za ta yi iya yinta kuma ta shirya tunkarar kowane ƙalubale a kan hakan.

"Don Allah Baba" Muryar HAWWA ta katse mata tunanin.

"Hauwa'u dama zan je kasuwa siyayya da Hajiya ta aike ni sai na tafi da zoben na sayar miki na kawo miki kuɗin" Sosai HAWWA ta shiga mata godiya domin har ta hango sun bar gidan ta tsallake auren mashayi. Ɗakin nasu ta koma ta samu SABEER zaune ya jingina da bango yana gyangyaɗi a zaune ga rigar da take ɗinke ɓasa nan lokacin da aka kira ta a kan cinyarsa. Kai ta jijjiga cike da tausayin kansu da tausayin kaninta kasancewarsa karami wanda maraici ya masa dirar mikiya tabbas mutuwa tana da yankan kauna in ba haka ba mai zai raba uwa da ɗa ko kuma mai zai raba iyaye da ƴaƴa sai mutuwa, domin mutuwa ba ta duban girma ko kankantar wanda za ta raba da iyayan. A hankali ta samu wuri ta zauna a kusa da shi, tare da janyo shi ta ɗora shi a kan cinyarta, tana karewa fuskarsa kallo tana tuno yadda mahaifansu suke kaunarsu tare da lulawa duniyar tunanin ranar da ba za ta taɓa mantawa a rayuwarta ba, ranar da ya kasance rubutu a kan dutse wanda ba zai taɓa goguwa ba, ba rubutu a kan ruwa ba wanda zai gogu.

A ranar wata juma'a da yamma, HAWWA ta ce tana son zuwa gidan kawarta ziyarar juma'a ai kuwa SABEER ya ce sai ya bi ta, sai da Ummie ta saka baki sannan ta yarda za su tafi tare, lokacin da za su fita Ummie tana cikin kicin tana girki, a hanyar fita suka haɗu da Abbie zai shigo gidan.


"Sai ina kuma ƴaƴan Ummie?" Ya tambaye su yana murmushi mai nuna so da kaunar ƴaƴan nasa.

"Abbie Aunty HAWWA ce za ta je gidan kawarta ziyara shi ne zan raka ta" SABEER ya ce yana rungume Abbie.

"To kai da ba kawarka ba ya za a yi ka je?" Ya ce yana dariya saboda ya san yanzu HAWWA za ta ce wani abu.

"Sai da na ce fa ba zai bini ba amma Ummie ta ce sai ya bini" Ta ce tana kumbura baki.

"To ke da ɗan uwanki ai sai ku je dama ai na ga tare kuke uzurinku ko my HAWWA" Ya ce yana kama hannunta.

"Ai ni ma yawo nake son zuwa tun da yau babu islamiya ga shi na saka babbar riga da hula" Ya ce yana yi wa HAWWA gwalo. Sai da ya lallaɓata sannan ya kama hannunsu ɗaya a hannunsa na dama ɗaya a hagu shi yana tsakiya, ya raka su har wurin mota suka zaɓi wacce za su fita suka shiga direba ya ja suna ɗagawa Abbie hannu yana ɗaga musu har aka fita da su daga get ɗin sannan ya juya ya nufi cikin gidan.


Basu san mai ya faru ba sai dab da magriba direba ya zo a kiɗime ya ce su zo su tafi gida in ji Ummie sosai HAWWA ta yi mamaki don ta ce za ta kira shi a waya in sun gama amma kuma ga shi bata kira shi ba ya zo kuma ga shi duk ta gan shi a rikice, ko da ta tambaye shi dalilin rashin nutsuwarsa sai ya ce mata waya aka masa daga garinsu mahaifiyarsa ba lafiya. Ko da ya ɗakko su maimakon ya nufi gidansu sai ta ga ya nufi gidan kanin mahaifinta, da ta tambaye shi sai ya ce wai Ammie ce ta ce ya karɓo mata sako.


Tun kan su karaso gidan ta hangi yadda jama'a suka yi dandazo a kofar gidan, sosai ta ji faɗuwar gaba ganin mutanen babu alama ta abin farin ciki ko abu mai daɗi ne ya tara su, sannan ta san dai da ɗaurin aure ne ko makamancinsa da za ta sani saboda shakuwar Abbie da ta kaninsa Baba ta wuce a ce an yi wani taro ko da kuwa na wani ne da ban ba tare da Abbie ya sani ba. Ta shiga tashin hankali da ta gane mutuwa aka yi tun da lokacin Baba da Hajiya Rayyanatu so da kauna marar algus suke nuna musu kamar su haɗiye su. Don bata taɓa kawowa cewa mahaifanta bane. Tashin hankalin da ta tarar na gawar mahaifan nasu ya haifar mata da suman da sai da ta kwanta asibiti, ganin su kwance babu kyan gani yadda tukunyar gas ta yi bindiga suka kone har da wasu daga cikin ma'aikatan gidan.


Hannu ta saka ta sharenhawayen da suka gangaro mata tana jin tamkar yau abin ya faru. A ɓoye Baba ta kawo mata kuɗin zobe kulle.a bakar leda dubu ɗari biyu da hamsin da yake zoben da girmansa. Dubu ɗari ta ba Baba wanda dakyar ta karɓa shi ma saboda HAWWA ta nuna mata kuɗin ya musi yawa. Da za su kwanta Baba ta musu sallama saboda gudun kar ta fiya zama tare da su zargi zai shiga idan aka neme su aka rasa. Tana jin babu daɗi rabuwar da za su yi.


Tsakiyar dare wajen karfe biyu HAWWA ta tashi ta ɗauki ruwan da ta ajiye a kofi ta zuba a hannunta ta shafawa SABEER a fuska yana warewa ta shiga raɗa masa cewa za su tafi saboda dama ta faɗa masa cewa za su gudu Kaduna gidan Baffa Nasiru. Yanzu murna yake don haka kuɗin ta saka a wata karamar jaka marar nauyi da Baba Sadiya ta bata ta ce ta saka, sai da ta goye shi a bayanta ta rataya jakar a wuyanta ta tsaya ta yi ta addu'a a kan Allah sa su fita ba tare da wani ya gan su ba. Dama tuni ta zari mukullin kofar da za ta sada ta da get ɗin gidan haka ta fito cikin sanɗa ta fara lallaɓawa har suka zo kofar gabanta yana ta faɗuwa ta saka mukullin ta buɗe a hankali ta fita ta ja kofar wurin mai gadi ta nufa da yake sharara bacci da munshari tana zuwa ta shiga dube-dube cikin ikon Allah sai ta ga mukullin a cikin hularsa ta ga mukullin ta lallaɓa ta ɗauka ta buɗe get ɗin suka fita cikin sanɗa ta ja musu get ɗin. Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke ganin sun kuɓuto daga gidan, sai dai inda gizo yake sakar tana fatan su samu mafaka kafin da asuba su nufi tashar motar.


A wani kango suka samu mafaka inda suka yi addu'a suka shiga saboda gujewa abu mai cutarwa. A nan suka karasa kwanan da asubar tun gari bai yi haske ba suka fito wannan karon hannun SABEER ta kama suka kama hanyar tashar. Sai da suka kusa sannan suka samu napep kai su suka yi sallah ganin mota za ta tashi suka shiga motar ta tashi duka lokacin shida da rabi, sai da ta ga sun ɗaili hanya sannan ta sauke ajiyar zuciya tana rungume da SABEER wanda bacci ya yi awon gaba da shi kasancewar jiya basu samu wani bacci ba.



*SALIMAH*


Da tsananin murna da farin ciki wanda bashi da kwatankwaci ko misaltuwa da lokacin fa kwanakin iddarta suka cika, domin a wannan lokacin ne take ji ba ya ita domin ta samu cikakken ƴanci, ƴanci wanda take jin tamkar na wanda yake gidan yari ya samu fitowa daga ciki. A ganinta a yanzu ne take ganin tama da damar da za ta dama wacce ta daɗe tana jiran zuwanta a inda za ta ci karenta babu babbaka. Don tun da ya sayi kaya ta yi ɗinkuna na kece raini ɗinkuna na fita taro take jin kanta yana hayaki take jin kanta daidai da kowace shegiya da take jin ta samu dama. Kayan da suka janyo mata farin jini haɗe da kwarjini, kayayyakin da take shiga ta kece raini wacce ta kara fitowa da aji da mugun kyan da take da shi wanda a da take ganin talauci ya yi wa mutane shamaki da ganin kyan nawa kasancewar tana gidan ABBAS babu kayan da za ta yi tinkaho matsayinta na babbar yarinya amma yanzu tana ganin buri da mafarkin ta zai cika na zama matar manya.



Tun da ta yi idda ta fara ba mazan da suka yi mata caaa suna son samun dama a wajenta kasancewar bata yi idda ba sai ta ɗan dakatar da su amma tana kammalawa sai ta shiga rangaɗa musu kira ta wayar salula da yake tana karɓar lambobinsu. Hakan ya sa lokaci kankani ta sha kwana kamar yadda ta yi tsammani. Manyan mutane ne masu hannu da shuni suka fara rububin aurenta wannan ne ya sa ta karyata maganar BASEERA, da kuma RUKY don yanzu dai ga maza nan kowa yana so ta bashi dama ya dama, kowa yana bayyana mata irin tsantsar son da yake mata tare da koɗa irin baiwar kyawun da Allah ya mata. Wannan ya sa kanta ya fashe take ta jin takaici da ta kare a gidan talauci bayan ga rayuwar da ta dace da ita duk da tana ganin lokaci bai kure mata ba.



"RUKY kin ga abin da nake faɗa miki ko, zawarci ya danganta da irin kyau da aji da kuma iya kamun ludayin bazawarar yanzu dai idanunki sun gane miki dama bahaushe ya ce gani ya kori ji, kina gani har gajiya nake da amsa kiran maza a wayata kuma kaf cikinsu babu na jefarwa kowanne yana takama da dukiya yana kuma ji da kansa, kowanne yana nuna mini so da kauna da kulawa ga su wayayyun maza ba kamar wancan fakirin da na baro gidansa ba ga bakin talauci ga kansa kife a cikin kwarya ba ma tukunya ba"

"SALIMAH ba za ki gane bane, ai fa haka suke fitowa a farkon zawarci ai kamar budurwa ce da za ki ga farkon fara budurcinta za ki ga maza gasu nan manema kamar me amma da kaɗan-kaɗan za su watse sai wanda yake da gaske da aure yake sonta shi ne zai tsaya. To zawarci ma

Please Login or Register in order to submit comment