Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

don bai taɓa zaton SALIMAH za ta iya dukansa ba duk da shi ne ya fara taɓa lafiyarta amma dai abin akwai mamaki.

"SALIMAH ni kika mara?"

"An mare ka who are you?" Ta ce cikin halin ko in kula.

"Kuma idan har ka haifu ɗan halal ba shege ba a cikin iyayanka to ka sawwake mini"


"Na sake ki saki ɗaya SALIMAH"

"Ayyiriri yiriiii" Karan guɗar da ta saki ne ya dawo da shi hayyacinsa tare da ankara da abin da ya yi. Sai dai kalmomin da ta yi amfani da su wajen karɓar sakin ne sun zafafa sun rura masa wuta a zuciya, sai dai ba zai ce bai shiga ruɗani da tashin hankali ba na kalmar sakin da ya furta mata wacce ta fito daga bakinsa tamkar an fisgo ta.


Yaraf ya zube a kan gwiwoyinsa don ya san SALIMAH ta suɓuce masa suɓucewa ta har abada kuwa, sai dai ya ɗauki na annabawa amma da wuya ta yarda ta dawo gare shi domin abin da take nema ne shekara da shekaru ya samu.

"Innalillahi wa inna alaihi raji'un" Ya faɗi hakan a fili sai dai kafin ya ankara har ta fita daga ɗakin ya san kuwa zancen gizo ba ya wuce na koki ma'ana zuwa za ta yi ta haɗa kayanta. Daɓas ya zauna ya haɗa kansa da gwiwa yana jin yadda gabansa yake bugawa gabaɗaya ya rasa ma wane tunani zai yi shi yunwar da yake ji ma bai san ta inda ta bi ba saboda wani ciwon ya danne wani zafin rabuwa da masoyi ya fi gaban wasa.

SALIMAH kuwa wani irin daɗi da farin ciki take ji, ji take tamkar ta zuba ruwa a kasa ta sha, har da wata rawa ta taka a ɗakin kayanta ta shiga haɗawa a wata babbar jaka sai da ta cika ta taf da sauran kayan amfanin da za ta bukata, kafin a zo kwasar kaya, rigar jikinta ta sauya ta yafo mayafi ta ɗakko jakar ta fito a kofar falon ta ajiye jakar ta shigo falon domin ɗaukan waya, jin shigowar ta ya tashi tamkar an tsikare shi yana jin da na sanin abin da ya yi. Cajar wayarta ta ɗauka da kuma wayarta kallo ɗaya ya mata ya gane tsantsar farin cikin da take ciki.

"ABBAS saduwar alkairi Allah haɗa kowa da rabonsa yau ka biya ni" Ba ta jira cewarsa ba ta bankaɗa labulen ta fita ta ɗauki jakar sai ga shi kamar an watso shi duk ya firgice sai ma ta so ta ji tausayinsa amma dai ganin bahaushe ya ce so, so ne amma son kai ya fi sai ta ji ta fi tausayawa kanta a kan shi.


"SALIMAH don girman Allah ki yi hakuri"

"Wa? Ai in ka ganni a lahira kai ni aka yi" Daga haka bata jira cewarsa na ta juya ta fice, zaunawa ya yi a kasa yana jin zuciyarsa tana suya tabbas in akwai abin da yake kaddararsa kuma jarabawarsa to bai wuce son SALIMAH ba, akwai lokacin da ta yi yaji ta ki dawowa ba tare da wani dalili ba dama mahaifiyarta ma ba kaunar auren take ba Babanta ne mai son auren kuma ya mutu. Tsawon sati biyu ta yi bata gidan amma sai da ya kwanta jinya hatta aikin kafinta ba ya fita, wata rana idan ya je gidansu SALIMAH aka ki kula shi kan maganar bikon sai ya zauna a kofar gidan ya wuni sallah ce kawai take tashin sa daga wurin idan ya yi ya dawo saboda kawai jurewa ya yi ta yi amma ya san ya azabtu da rashinta. Wasu hawaye ne masu zafi suke masa ambaliya a fuska tabbas ba kowa zai gane irin hali da raɗaɗin da yake ciki ba sai wanda yake cikin halin da yake ko wanda ya taɓa shiga irin halin.

'A kullum addu'a ta shi ne in rayu a duniya ɗaya da SALIMAH duk duniyar da babu SALIMAH sai in ji tamkar dai makabarta ce, amma yau kaddara ta gifta kaddara wacce take rubutacciya don in ba kaddara ba ba na jin akwai ranar da ni da bakina zan furta kalmar saki ga SALIMAH amma rubutacciyar kaddara wacce ba ta goguwa domin irin wannan kaddarar ita ce ake kira kaddara wacce ta riga fata, na san wasu za su ji haushina wani ya ji kamar ya hau ni da duka wani kuwa zai ga ai so ba hauka bane sai dai kash! Bai san irin ɗinbin so da kaunar SALIMAH da suke dankare a tawa zuciyar ba ni ban taɓa cin karo da irin son da nake yi wa SALIMAH ba, ko da kuwa a labari ne son da nake mata ya fita da ban ya fi karfin zuciyata, da ce SALIMAH za ta bukaci in ɗaye fatar jikina in bata babu wani dalili da zai sa in kasa ko da za a saka bakin bindiga a kaina a ce in sake ta ko a harbe ni, to tabbas ba zan furta mata kalmar saki ba amma yau tsautsayi wanda ba ya wuce ranar sa ya sa giyar fusata da gajen hakurin ɓacin rai da kasa jure kalamanta uwa uba shaiɗan mai amfani da dama idan mutum na cikin ɓacin rai ya ci galaba a kaina' Ya furta a zuciyarsa yana haɗa kai da gwiwa ji yake duniya ta masa kunci tabbas yana cikin matsatsi.

"Don Allah ki dawo gare ni SALIMAH" Ya furta a fili da karfi har jijiyar wuyansa tana bayyana raɗo-raɗo, yana mai fashewa da kukan tausayin kansa.


*SALIMAH*


Cikin wani farin ciki ta fito daga gidan kofar gidan ma a buɗe ta bar ta ko darajar rufewa bata samu ba, ji take tamkar ta taka rawa ji take rabon da ta ji ta cikin annashuwa tun ranar da aka ɗaura mata aure da ABBAS, tun daga wannan rana ta tsinci kanta cikin wani yanayi tun daga wannan rana wani abu ya tokare mata makoshi abin nan da ya tokare ta bata taɓa jin ya gushe daga wurin ba sai yau da ABBAS ya furta mata kalmar saki abin dai tana jin sa kamar almara sannan kuma sai take jin tamkar a mafarki.


Duk da soyayya suka yi da ABBAS ɗin sai dai ita ta kauna ce shi ne saboda kyau da yake da shi duk cikin maneman ta babu wanda yake da kyansa, kuma babu wanda ya haɗa duk abin da take bukata daga ɗa namiji kamar ABBAS su dai sauran kuɗi da manyan motoci da gidaje za su faɗa masa shi kuma Allah ya mallaka masa komai da mace za ta so ga ɗa namiji matsalarsa ɗaya cikas ɗinsa ɗaya mugun talaucin da ya kanannaɗe shi ya masa dabaibayi. Manyan alhazan da take kulawa masu hannu da shuni suna kashe mata kuɗaɗe jikinta suke so, don sun sha zuwa mata da kalmar ɓatanci amma ta ki bada haɗin kai, shi kuma ABBAS kaunarta yake da gaskiya wannan dalilin ganin yana jumuri da jure duk wani abu da za ta masa kuma nutsatstsan matashi mai girmama na gaba, uwa uba ibada da tarbiya hakan ya sa mahaifinta ya dakatar da kowa daga zuwa wurinta ya ce ABBAS zai aura mata. Ta yi kukan bakin ciki tun daga ranar ta ji ta tsani ABBAS kyansa da take gani ya koma mata muni domin ta fi kaunar kuɗi da morewar rayuwar duniya a kansa.

Kamar kumbo kamar katanta yadda abin nan yake a wajen SALIMAH haka yake a wajen mahaifiyarta, bakin su ɗaya ita ma duniyar ce a gabanta, don duk abin da mahaifin SALIMAH zai faɗa mata a kan rayuwar duniya da bin duniya a sannu da dai nasihu masu bin sassan jiki da shiga zuciya, yana tufka ne mahaifiyarta tana warwara abin da zai faɗa mata da ban wanda za ta faɗa mata da ban, idan ya biya mata karatun ta nutsu sai mahaifiyarta ta goge hardar. Har ya bar duniya bayan auren da watanni uku a sannan ne ruwa ya karewa ɗan kada domin kuwa sun bi duk hanyar da za su bi wulakanci kala-kala a kan ABBAS ya sake ta amma ya ki yau dai ga shi buri ya cika.


Tafiya ta fara yi tana rike niki-niki da jakar kayanta, sai murmushi take, sai sannan kiran kawarta EESHART ya faɗo mata da sauri ta kamo sunanta ta danna mata kira ringin ɗaya biyu wayar ta yi ta ɗauka.

"Hlo kawata...

"Albishirinki ce goro" Ta katse mata maganar tana dariya.

"Goro fari tassss" Ta ce cikin zakuwa da son sanin dalilin shigar kawar tata cikin wannan farin ciki, saboda bata yi wani tunanin komai ba.

"ABBAS ya rangaɗa mini saki EESHART yau ya warware wannan doguwar igiyar kaddarar da tsofaffin nan da shedu suka taru suka talaulaye ni da ita" Ta ce hakoranta talatin da biyu a waje.


Alhaji ALI da suka shawo kwanar layin yana waya, da ita ya fara tozali ganin dariyarta sai ya saka shi cikin wani yanayi har ya shagala da kallonta har suka zo saitin ta yana kare mata kallo tabbas ya shaidata ita ce dai ta safen nan da ya gani lokacin da suka fita.


"Eh, dariya, kyakkyawa" Ya ce a wayar saboda gabaɗaya ya ma sha'afa da abin da suke magana a kai. Daga ɗaya ɓangaren aka katse shi da mai yake nufi sai sannan ya dawo hayyacinsa don hatta direban sai da ya gane cewa Alhajin ya yi suɓutar baki, dariya ce ta so kwace masa amma gudun yi laifi sai ya danne, don ya lura da wacce yake kallo yana ganinsa ta madubi.

"Ke SALIMAH bana son wasa wallahi ai ko za ki yi wasa da komai ban da wasa da sakin ABBAS don na san wannan ɗan a nace ɗin ba zai sake ki ba"

"Wallahi kawata da gaske nake da bakinsa ya furta kin ganni har na haɗo kayana na baro masa agwajan gidansa, kin ga shi ma ya huta da da biyan kuɗin haya"

Wani ihu EESHART ta saka don ta rasa ma ina za ta ajiye wanna magana mai daɗi.

."Barka kawata na taya ki murna Allah mana tsari da auren masu dattin hula ƴaƴan malam shehu to ina dalilin auren talaka "

."Wallahi kuwa ai yanzu sai na zaɓa na darje"

"Hahaha wallahi kuwa kawata kina lokaci" Ta ce tare daɗa fashewa da dariya.


"Bari in na je gida ma yi waya so nake in je in yi wa Umma albishir ita ma ta ɗanɗani wannan farin ciki" Da to ta amsa mata tana mai kashe wayar sosai take ji da EESHART yadda take kaunarta tana bata shawarwarin yadda za ta kuɓuta daga auren ABBAS ta yi auren da za ta ji daɗi ta huta, sai dai bata san cewa ba turba mai kyau ba ce haka ba kuma hanya mai ɓullewa ba ce illa iyaka RUƁAƁƁIYAR IGIYA ce.


Alhaji ALI kashe wayar ma ya yi don ba ya so yake kwariɓi a waya, sai ya ga gwara ya bari idan ya zauna ya nutsu ya yi wayar. Raja'a ya yi da kallon SALIMAH da take waya har aka buɗe get ɗin bai sani ba sai da direban ya durfafi cikin gidan sannan ya dawo hayyacinsa. Ganinta yake tamkar ba bahaushiya ba sai ka ce wacce take ɗaya daga cikin ukun nan, larabawa turawa ko indiyawa saboda yanayin farin fatarta kamar ba na africa ba.


Napep ta hanga ta ɗaga masa hannu tahowa ya yi sai da ya zo saitin ta ya ja birki.

Jakar ta saka a cikin napep ɗin, tana shirin shiga kamar an ce ta ɗago kanta ai kuwa ta hango ABBAS ya fito daga gidan tamkar zararre kafarsa ko takalmi babu uwa uba fuskarsa da hawaye, da sauri ta yi saurin shigewa napep ɗin.


"Malam ja da sauri mu tafi kar wancan ya karaso na ga ya yi kama da mahaukaci kar ya warce ni ya mini duka" Ta ce tana hango yadda ABBAS ɗin ya rugo da gudu zai zo wajensu ganin da ya yi ta shige. So yake ya zo ya gwada sa'arsa ko za a dace duk da ya san da wuya wai gurguwa da auren nesa.

Mai napep kuwa kallon tsoro ya jefi ABBAS ɗin da shi duk da bai masa kama da mahaukaci ba ko ta yanayin shigarsa, sai dai dole ya bi umarninta tun da aikin kuɗi zai yi. A guje ya fisgi napep ɗin suka tafi. Cak! ABBAS ya tsaya bai san ma ya ɗaga hannaye biyu ya ɗora a kansa ba tamkar wanda aka yi wa mutuwa.


SALIMAH wata ajiyar zuciya ta sauke ganin bai cim musu ba domin ita a halin da ake ciki yanzu ko hanya ba ta son haɗawa da ABBAS ɗin don an yi mai gabaɗaya haihuwa har hanji.


A kofar gidansu aka ajiye ta, gidan kasa ne aka shafe shi da jar kasa, cewa ta yi ya jira ta ta ɗauki jakar ta shige cikin gida.

Umma da take zaune a kan kujera tana goga ɗanyar kuɓewa ganin shigowar SALIMAH da sallama tana rike da jaka riki-riki bata san lokacin da ta cillar da magogin kuɓewar ba, tare da kuɓewa guda ɗaya da take rike a hannunta tana gogawa tsaye ta mike tana kallon fuskar SALIMAH mai cike da alamar farin ciki hakan ne ma ya sa ko sallama ta kasa amsawa.

"Allah ubangiji ya sa ba ya ji bane" Ta faɗa tana kallonta don ta tsani yaji ma ta fi son ta ji kalmar saki duk da ta san mawuyaci ne a yi sakin amma dai ganin yanayin SALIMAH ya sa ta ji tana son jin karin bayani. Cilli SALIMAH ta yi da jakar hannunta, ta karasa da gudu ta kankame Umma cike da farin ciki.

."Umma ABBAS ya sake ni" Ta ce tana kara kankame mahaifiyar tata da karfi.

"Ke SALIMAH kin san dai bana wasa da ke" Ta ce lokacin da ta ciro SALIMAH daga jikinta tana kallonta ido cikin ido.


"Wallahi Umma ya sake ni saki ɗaya" Ta ce tana ta murna da nuna farin ciki..

"Ayyyyyiririr yiriiiiii" Umma ta rike hanci tare da kwarara guɗa.


"SALIMAH anya yana cikin hankalinsa kuwa ya sake ki, ko dai wani abu kika bashi ya sha ya bugu kika tambaye shi sakin?" Umma ta ce tana jinjina yadda aka yi hakan ya afku.

"Rass yake babu wani buguwa dawowarsa kenan ma daga...

."Assalamu alaikum" Wani yaro ya shigo da sallam. Amsa masa Umma ta yi tana masa kallon rashin sani.

"Wai in ji mai adaidaita sahu a bashi kuɗinsa" Ya ce yana ja ya tsaya.


"Lah ka ga na manta ma da shi, Umma kawo ɗari huɗu a bashi" Cewar SALIMAH.

"To zo ka karɓa" Ta ce tana mika masa ya karɓa ta fita.

"Oh wai kuɗin adaidaita ma sai kin zo gida baki da kuɗi, yau dai Allah ya yanke miki wannan wahala, mai za a yi da wahala na san yanzu manyan mutane masu faɗa a ji sai kin zaɓa kin darje" Umma ta ce tana dafa kafaɗar SALIMAH.

"Wallahi kuwa Umma na san layi za suke yi da motoci a kofar gidan nan kowa yana burin ya mallake ni" Ta ce tana rungume Umma tana jin wani daɗi domin ta rasa gurbin da za ta ajiye farin cikin da take ciki. Saboda har ta fara hango ta a kayataccen gida na alfarma tana cin duniyarta da tsinke.

"Ai babu wanda zai yi tozali da wannan kyakkyawar halittar taki, ya yarda ki suɓuce masa, shi ya sa nake jin takaici da mahaifinki ya aura miki fukara'u bayan na san na haifi babban jari farar mace alkyabbar mata" Umma ta ce, dariya suka saki a tare.



*ABBAS*


Tamkar mahaukaci sabon kamu haka ya juyo ya dawo gidan, yana shigowa ya ji wani kunci a ransa kamar zararre haka yake jin sa sai ya ji ba zai iya jure zama a cikin gidan ba, ganin SALIMAH bata nan kuma ya san cewa ba wai unguwa ta je ba gidansu ta tafi a matsayin ya sake ta. Bedroom ɗin ya shiga da niyyar ya sauya kayan jikinsa amma da ya shiga sai ma ya rasa mai zai yi a cikin ɗakin, fitowa ya yi ya shiga falon ya ɗakko mukulli ya kama hanyar waje sai a sannan ya tuna babu takalmi a kafarsa, dawowa ya yi ya saka takalman ya fita ya rufe gidan. Tafiya ya fara yi amma sai yake ji tamkar kafafunsa ba za su yi jumurin ɗaukan gangar jikinsa ba, saboda yadda kafafun nasa suka yi sanyi ba ma kafafun ba hatta jikin nasa ma sanyi karai ya yi kawai dai yana saka kafafun ne ba tare da sanin ina ma yake jefa su ba, ga wata juwa da take faman ɗaukansa. Machine ya tsayar ya faɗa masa inda zai kai shi a daidai kofar gidan da ya masa nuni ya ajiye shi ya bashi kuɗinsa.

Da sallama ya shiga gidan Mama da fitowarta kenan daga banɗaki tana rike da buta ta ga ABBAS ya shigo da sallama amsa masa ta cikin sanyin murya, ganinsa ba yadda yake, idanunsa jajur kai gabaɗaya a matsayinta na uwa mahaifiya a gare shi tana ganinsa ta san yana cikin matukar damuwa tana ganinsa ta san gabaɗaya ba ya cikin hayyacinsa. Butar hannunta ta ajiye tana nutar falo ya bi bayanta zaunawa ta yi a kujera yana shigowa ɗakin wani kukan ya taho masa irin kukan da mai yinsa yake yi idan ya ga mai rarrashin sa. Da sauri ya karasa gabanta ya durkusa gwiyoyinsa a kasa tare da kifa kansa a kan cinyarta ya fashe da kuka.


09013181851
[1/5, 8:57 PM] Sadiya Abdulrazak: *RUƁAƁƁIYAR IGIYA*



NA


MAMAN AFRAH


*GARGAGAƊI*

Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ko ta wace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowane kafar sadarwa ba sai da izinina a kiyaye⚠️

JAN HANKALI

Kirkirarran labari ne ban yi shi don wani ba, idan har ya yi daidai da labarin ki/ka to arashi ne.


SADAUKARWA

Kwacakwam labarin daga farkonsa har karshe sadaukarwa ne ga kawata HASSANA B.S Allah saka miki da alkairi ya raya zuri'a.



PAGE 4


*ABBAS*

Dakatawa Mama ta yi bata hana shi kukan ba, duk da sautin kukan nasa yana taɓa mata zuciya, ta san cewa ba karamin abu bane zai sa ABBAS ɗin kuka haka ba kamar wani mace, kasancewarsa mai hakuri da juriya haɗe da kawar da kai sai dai ta san kukan nasa ba ya rasa nasaba da SALIMAH domin ta san ita kaɗai ce matsalarsa, ita kaɗai ce damuwarsa, ya ɗauki son wacce ba ta son shi ya saka a ransa ko kaɗan SALIMAH ba ta tausayinsa bare ta ji tausayin halin da yake ciki na soyayyarta burinsa kullum ya faranta mata, amma bata gani ta raina duk kokarinsa a kanta shi kuma kullum faɗi tashin sa SALIMAH ce duk da Mama ta san yana matukar kokarin ganin ya kyautata wa Mamar matsayinta na mahaifiya a gare shi sai dai ganin irin jarabawar da ya haɗu da ita na matar da ya aura sai take yafe wasu abubuwan tun da bata rasa komai ba kanin mahaifin ABBAS ɗin bai rage ta da komai ba tun bayan mutuwar mahaifin ABBAS yake ɗawainiya da su har yau bai daina ba kuma bai gajiya ba.


Sai da ta ji kukan nashi ya tsagaita, ta tabbatar ko ma mene ne yanzu zuciyarsa ta yi sanyi, saboda duk idanun da suka zubar da hawaye to mai idanun yana samun salama a zuciyarsa. Jin yana ajiyar zuciyar sai ta saka hannunta wanda tun da ya kifa kansa a cinyarta ta ɗora hannun a bayansa, fara buga masa bayan ta shiga yi a hankali sai da ta tabbatar ya samu nutsuwa daga ɗimuwar da ta gan shi a ciki sannan ta saka hannun ta duka biyu ta ɗago shi. Sosai ta ji rauni a zuciyarta ganin yadda idanunsa suka yi wani irin ja hatta fuskarsa da saman hancinsa duk sun yi ja saboda kukan da ya yi, kasancewarsa mai farar fata. Ba ma wannan ne ya ɗaga mata hankali ba sai ganin ya yi wani irin zuru-zuru idanun duk sun faɗa, kuma ko jiya ya je gidan nata domin rana bata taɓa fitowa ta faɗa bai je ya ga Mama ba yana kaunar mahaifiyarsa ita ma tana kaunarsa kasancewar sa ɗa ɗaya tilo a wajenta.


"ABBAS mene ne?" Ta tambaye shi cikin sanyi da tausasa murya. Idanunsa ya runtse wasu hawayen suka zubo sosai ta ji hakan ya taɓa ta, ta rasa SALIMAH wace irin mace ce da bata tausayin mijinta kullum yana cikin damuwa sai dai ta ɗauki hakan a matsayin jarabawar da Allah ya jarabci ABBAS ɗin da ita tana masa fatan Allah ya bashi ikon cin jarabawar.

Idanunsa take kallo wanda ya rufe su hawayen suna surnanowa.


"Na sha faɗa maka kake rike sirrinka, su iyali da kake gani sirri ne, daɗi ko wuya ba a son a ke jin kansu sai in abin ne ya yi yawa sai a faɗa domin sulhu da kawo maslaha" Ta ce cikin murya mai kama tana masa nasiha, duk da ta san ABBAS yana da dauriya da zurfin ciki sai dai wani lokacin kasancewar ta na mahaifiya gare shi ba sai ya furta cewa yana cikin damuwa ba kallo ɗaya take masa ta fahimci halin da yake ciki, duk da cewar halin da gidan ABBAS ɗin yake ciki abu ne bayyananne wanda kowa ma ya sani sai dai wanda bai taɓa taka kafarsa a gidan ABBAS ɗin ba.

"Ka cigaba da hakuri wata rana sai labari, wata rana masu bada labarin ma babu kowa, shi zaman duniya ɗan hakuri ne duk abin da aka yi hakuri da shi zai wuce wata rana kamar ba a yi ba"

"Mama" Ya ce bakinsa yana rawa don har ya fara jin sanyi alamar zazzaɓi zai rufe shi, ga shi yana so ya faɗa mata cewa ya saki SALIMAH amma kuma bakin nasa ya masa nauyi.

"Na'am ABBAS"

"Na, na, na" Ya ce yana ta faman maimaitawa tamkar wani mai in'inna.


"Mai ka yi ABBAS? Ni mahaifiyarka ce da baka da kamata a faɗin duniya ina so ka sani da a ce SALIMAH ce take maka wannan kaunar da kake mata, ai dai ka san kana matukar kaunarta, kaunar da kai kan ka baka san iyakarta ba to da ita ce take maka kauna ko da ta fi wacce kake mata to ina so ka sani da bata kai ni kaunarka ba" Idanunsa da suke rufe ya buɗe har sai da gaban Mama ya faɗi ganin irin mugun jan da suka yi.

."Tabbas da bata kai ni kaunarka ba, ai a duniya babu wanda ya kai uwa kaunar ɗanta, na maka misali da kaunar da kake mata ne don ka gane, uwa-uwa ce kaunar uwa da ban take, shi ya sa ma aka ce a yi wa uwa biyayya sai da aka nanata sau uku sannan aka ce a bi uba amma sau ɗaya aka ambaci uba. Saboda kaunar uwa da ban take ɗanta tun yana cikinta bata gan shi ba take kaunarsa, jin sa take har cikin ranta, yadda take shan wahala rainon cikin da haihuwar da kuma shayarwa rainon yaro har ya girma shi ya sa ubangaji maɗaukakin sarki ya ambata a littafinsa mai tsarki, cewa wahala ce a kan wahala. Shi ya sa uwa kaunar ɗanta bata taɓa gushewa a

Please Login or Register in order to submit comment