Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

🤡
🤡 🤡
🤡🤡🤡🤡🤡🤡🤡
MURMUSHIN AJALI
🤡🤡🤡🤡🤡
🤡🤡🤡🤡🤡
🤡🤡🤡🤡🤡🤡🤡
Written by Aysha wakili
*Mrs ahmed*

*ma'abota karanta littafina inamai baku hkr na tsaiko da ake samu 'tunfarko nariga nashaida maku halin danake ciki 'inafata kuna fahimtata ngd 'kuci gaba da kasancewa da ni*

*dedicated to friend bee kalbi Miemie*

Page3⃣0⃣

A tsorace tsoho ya kwanta cos baki dai jikinsa 6ari yakeyi ganin yadda baabaa laure ta firgice lokaci d'aya ya tabbatar cewa ba k'aramin abune duna va 'tunda gashi har tana ambaton Allah ya had'ashi da duna'''' duk su biyun sun kasa bacci inda baabaa laure takasa rufe ido shikuma tsoho ya tsorace'''''


*washe gari* da asubah kamin akira sallar farko misalin karfe hudu mahaifin muntari yaxo kor gidan tsoho yana bugun kofar kamar zai 6alla ' tsoho daya samu bacci yasace shi a firgice yatashi sbd jin yanayin bugun kofar 'ga dukkan alamu bana lfy bane ''toh kodai yan'fashi ne? Tambayar dayake yiwa kan'sa kenan'' baabaa laure itama a firgice tamik'e tana cewa tsoho bugun kofa nakeji'' cikin sanyin murya tsoho yace jeki bud'e kiga kowaye'' ahaukace ta dubeshi tace lallai ma wlh ba enda zani '''

Sunan nan zaune sukaji bugun k'ofar yakara tsananta ba shiri tsoho yamike yabude kofarshi yafito
Yana xuwa bakin kofar yafara tambayar waye''' sama sama yakejin ana cewa baba nine kabude muntari ba lfy gashi can kwance rai hanun Allah ''' da sauri tsoho yabude k'ofar yana tambayar meya sami muntari?
Cikin sauri Baban muntari yace wlh tun karfe biyun dare bamuyi bacci va """sai ihu yakeyi yana bada hkr wai wani yayi hkr ya yafe masa yanayi yana kuka '
Tsoho yace wanene wannan toh? Girgiza kai baban muntari yayi yace nima bansani va wlh'' dasauri suka fita tare da tsoho ,
Tsoho yace kirawo mahmuda yaxo ynxu '''
Nan baban muntari yafiddo wayarsa yashiga kiran mahmud '' ringing biyu yad'aga yana tambayar lfy nan baban muntari yamikawa tsoho wayar'
Tsoho yacewa mahmud yayi sauri yaxo gd ba lfy 'munari jiki yatashi''


Koda suka shiga gdn a tsakar gd suka iske muntari ya durkusa yana cewa kayi hkr wlh baran sakeva 'kuma nibansan alak'arku va daban,,,,,,,,,,,,,,,,,,,kamin yak'arasa bakinsa yajuye yakoma gefe hannunsa yashiga murmudewa '' yanason yin magana amma yakasa'''

Faduwa yay awurin yana juyi ' Kan kace me nunfashin sa yafara tsayawa dakyar yake jan numfashin''' dagudu tsoho da babansa suka rufu akansa suna kiran sunan shi 'yayinda mahaifiyarshi da sauran kannensa suka fito suma suka shiga kiran sunan sa' suna jijjiga shi amma ina numfashin nasa yariga yafara nisa , dasauri mahaifinsa ya sunkuce shi xuwa waje daidai lokacin mahmud na xuwa aiko da sauri suka sakashi a mota sukayi asibiti'''


suna isa aaibitin sun bude motar zasu d'aukosa kenan sukaji hannunsa da jikinsa ya sake ' take mahaifin'sa yadubi mahmud yace basai munfito dashi va mukoma gd kawai''
Cikin rashin fahimta mahmud yace bangane mukoma gd va 'bayan munriga mun iso asibitin'',
Shiru baban muntari yayi kamin yadubi mahmud yace :babu muntari ,rai yayi halinsa '
Innalillahi wainna ilaihiraji'un shine kalmar da mahmud yake nanatawa ,,da sauri yashiga jijjiga muntari amma ko motsi ba yayi''

Kifa kansa yayi asaman murfin motar yana ta'ajjabin wannan al'amari ''' jiki a sanyaye suka shigo motar suka juyo xuwa gd 'suna karasowa ana shiga masallaci 'danhaka suka bar gawar acikin motar sukai alwala suka shige masallaci '''

Bayan an idar da sallan ne 'tsoho yadubesu fuskarsa da alamar tambaya ,mahmud ya girgiza masa kai' amma shi bai fahimci abinda mahmud d'in yake nufiva'' danhaka yamike yafita mahmud yamara masa baya""'

Awaje tsoho yafara tambayar ko ambasu gado ne? Mahmud yace a'ah baba saidai muntari rai yayi halinsa 'muna karasawa yana cikawa'' ynxu haka gawar tana cikin mota""

Salati tsoho yashiga yi '' da sauri ya isa inda motar take domin gasgata maganar mahmud 'nan yakama k'ofar yan kokarin budewa amma dayake arufe take bai iya budewa va' saida mahmud yaxo yasa key yabude '' saidai abin mamaki babu gawar muntari acikin motar'' mahmud bailura da babu gawar va '' saida tsoho yace kai mahmud dama wasa kakemin koh'''

Da sauri mahmud yace a'ah baba wlh ba wasa bane bakaga gawar bane kodai yana motsi ne 'yana maganar yana latsa wayarsa ''' tsoho yace toh aini banga kome cikin motar va mahmuda'''

Daidai lokacin baban muntari na k'arasowa '' afirgice suka shiga duba gawar muntari amma basu gani va' cikin tsananin tashin hankali dawani irin firgici " mahmud yace toh ina gawar tashiga ? Baban muntari shima yace aimun barta amota yaza'ai ace kuma ynxu babu ita'? Sannan ba'a bude mukabar motar va'' saida muka rufe koena',sannan babu alamar anfasa motar ne aka fito'''

Innalillahi wainna ilaihiraji'un tsoho ke maimaita fada 'sbd abun yafara fin karfin tunaninsa 'to ena gawar tashiga ne ? Wayazo yadauki gawar? Kodai muntari ba mutuwa yayi va?
Toh taena yafita acikin motar?




*Muje xuwa readers ynxu aka fara shiga cikin labarin kuci gaba da sambada min addu'ar samun lfy nikuma naita sambado maku typing ""sannan comment naku zai kara karfafamin guiwa*




*Ana tare*👌
[19/10 2:49 pm] Me Kosai✍: 🤡 🤡
🤡 🤡
🤡🤡🤡🤡🤡🤡🤡
MURMUSHIN AJALI
🤡🤡🤡🤡🤡
🤡🤡🤡🤡🤡
🤡🤡🤡🤡🤡🤡🤡
Written by Aysha wakili
*Mrs ahmed*

*aunty maijidda musa ngd da k'aunarki ga wannan nvl en Allah yasaka'''nima ina k'aunarki irin sosai d'in nan*❤


*dedicated to friend bee kalbi Miemie*

Page3⃣1⃣

Nan suka shiga neman gawar muntari amma sama ko kasa sun rasa'' hankali atashe mahmud yashiga kiran sauran yan'uwansu awaya yana shaida masu halin da ake ciki''''' mutanin unguwa ma ba'a barsu abaya ba wurin nemo gawar muntari ' duk edan sunxo wucewa sukaga su mahmud sai sun yambayesu abinda ke faruwa' aiko kan wani lokaci har unguwa tafara cika da yan'neman gawa'''
Can cikin gd labari yakai masu 'nan suka shiga matsanan cin tashin hankali ' '

Har kusan karfe bakwai da rabi ana neman gawar muntari amma ba'a ganiva ' hankalin kowa yagama tashi ' dawowa akai kor gdn tsoho aka shimfida tabarma aka zazzauna ana jimamin wannan abu daya faru'''



*EGYPT* karfe goma da rabi na safe 'sultan tafe shida ameer sunfito daga hostel zasu shiga skull'' suna cikin tafiya suna fira , ta baya sukaji anyi masu sallama danhaka suka juyo domin ganin wanda ke sallamar''

Mamaki ne karara ya bayyana afuskar sultan cikin murmushi yace muntari ? Shima muntarin murmushi yayi yace na'am sultan kana mamakin ganina koh? Gyada mashi kai sultan yayi yace sosaima 'mekazoyi a egypt? Cikin dariya muntari yace nida ogana ne mukazo narako shi zai gudanar dawani aiki awani company ,shine natuna ai kaima nan kake karatu 'shine nace bara naxo mugaisa'naga dan'uwa na ,,,murmushi sultan yayi yace aiko naji dad'i wlh ' amma gashi kuma zamu shiga skull muje nakaika d'akinmu kazauna kamin mudawo kaji''

Girgiza kai muntari yayi yace a'ah karka damu nima ba dadewa nazoyi va 'nadai zo ganinka ne 'kutafi babu damuwa zandawo wani lokacin''
Murmushi sultan yayi yace pls ka gaidamin da kowa da kowa 'da my lil miemie nd pls karka rika dukanta kaji? Dariya yayi yace naji bansake dukanta ma gaba daya''' nan sukai sallama suka tafi''


*NIGERIA*Shabiyu na rana tayi anraba yan'sanda takoena ana neman gawar muntari amma ba'a samuva' yan'uwa da abokan arziki anshiga tashin hankali sosai ' inda mahaifiyar muntari ke kuka tana cewa ataimaka akawo mata gawar d'anta tagani da kanta 'taimasa addu'ah ,amma shiru kakeji babu gawar muntari babu alamun sa 'dan kaf cikin unguwar nan saida yan sanda suka bincika amma basu ganiva''


Har la'asar ana abu daya' danhaka tsoho yatara dukka family d'insa a farfajiyar gdn sa''' nan akaita jajantawa yan'uwa abinda yafaru 'daga bisani tsoho yace , shifah wannan al'amarin yana d'aure masa kai da tunani' yaza'ai ace gawa ta 6ata ba'a ganta va' ga dukkan alamu akwai wani abu dake 6oye wanda mu bamu saniva ' saidai ina umartar kowanne daga cikinku daku tsananta bincike akan wannan al'amarin ,domin agano bakin zaren'Sannan ina ganin wannan zaman makokin da akeyi bashida amfani tunda bamu da tabbacin mutuwar tasa 'musamman idan mukayi la'akari da 6atan gawarsa" da haka aka watse kowa da abinda yake sak'awa acikin ransa''


Miemie da salma zaune cikin daki 'kowacce tayi tagum tagum'' salma tadubi miemie tace ynxu ina gawar muntari zata shiga ?,wayaxo yadauke shi? Kodai ma ba mutuwa yayi va?
Miemie tace oho ni inazan sani 'ke bakima ji dadi ba koba kome aizaki huta da tijarar dayake maki'' girgiza kai salma tayi tace ko kad'an bana murna sbd kome muntari zaimin dan'uwana ne baranyi fatar wani mugun abu yasame shi va''''

Shiru miemie tayi tace hakane amma tabbas abaki kike fadan wannan maganar amma a zuciyarki bahaka bane'' kuma idan kin musa zan iya fada maki abinda zuciyarki ke ayyanawa '' ido waje salma ke kallon miemie domin tabbas abinda miemie tafada gsky ne saidai ya akai tasan abinda ke xuciyarta?

Lallai gara tayi shiru kar miemie ta tona asirin zuciyarta''''''' bata sake magana va ''miemie tace salma ynxu saiki saki jikinki domin babu muntari balle yatakira maki' yanacan lantsandan 'kema inkina bukata kina iya binshi'''😂


*washe gari* da safe haka kowa yatashi da tsammanin ganin gawar muntari amma shiru kakaji kamar an aiki bawa garinsu'''' inda hankalin mahaifiyarsa yakai matuka wajen tashi 'gaba dai tafita hayyacinta ' sai rok'o takeyi akawo mata gawar d'anta tagani''

Mahmud kam yakasa koda bud'e motarsa domin koda daddare dazasu wuce gida cewa hafsa yayi taxo su shiga adaidaita danshi bare iya shiga motarsa va'' sbd gani yake kamar muntarin na ciki ko kuma gawar zata dawo'haka suka koma gd amma basuyi bacci va ,mahmud yakasa bacci wanda dalilin hakan yasa hafsa itama bata iya barcin va''


Sultan kwance a dakinsa yana hutawa shida ameer 'kamar antsikare shi yamike yadau wayarshi yashiga kiran numbern mommansu 'saidai har wayar takare ruri ba'a d'auka va'' nan yasake kira still ba'a dauka va' abun yabashi mamaki saiya sake kiran na abbansu 'shima harya kare ruri ba'a dauka va'''duban ameer yayi yace ameer ji wani abun mamaki tundazu sai trying numbern mommah da abba nakeyi amma basu d'auka va komeyasa ? Ameer yace toh kabari xuwa anjima saika sake kira mana mayb dey re busy ne''''

Kan dole sultan ya hkr 'suka cigaba da fira' ji sukai ana buga masu k'ofa nan ameer yatashi yaje yabud'e ''wanda yai sallamar yabashi hannu suka gaisa 'suka shigo d'akin tare ''
Ganin wanda suka shigo tare yasa sultan saurin mik'ewa fuskarsa da murmushi yace a'ah dama baku tafi va? Shima murmushi yayi yace eh wlh oga yace saigobe zamu tafi shiyasa nace bara naxo mui fira da d'an uwana kamin natafj'' nan sultan yacika da murna ' duk suka zauna suna fira cikin annashuwa""

Sultan yadubi muntari yace yauwa zanbaka sak'o ka kaiwa my lil miemie kace mata inasonta sosai nd ina missing nata tunda ita bata sona''' nan yamik'e da nufin d'auko sak'on sai muntari yarik'e masa hannu yace dakata kaji'' aiba gd zamuyi va daga nan misra zamu tafi kuma ina ganin zamu d'auki lokaci me tsawo kamin mukomo nigeria 'mezaihana ka aje sak'on agunka dan gudun karnaje na salwantar dashi'?
Jinjina kai sultan yayi yace hakane kuma '' barshima zanbawa abokin abbanmu inzai tafi saiya kai mata'''


Muntari bai bar hostel d'insu sultan ba 'sai bayan magrib ''wanda ameer dake sauraren firarsu duk yak'osa muntari yatafi sbd Shi amatse yake yafad'awa sultan abinda yabashi tsoro'''

Sultan na dawowa daga rakiyar muntari ameer yatareshi 'yana cewa sultan anyako wannan muntarin mutm ne?
Cikeda mamaki sultan yace meyafaru ?ko meka gani?
Ameer yace gani nayi gashi nan zaune kan kujera amma kuma bana ganinshi ajikin madubin dake fuskantar kujerar saidai nahango kujerar amma ba mutm akai''

Cikeda zaro ido sultan yace me 😳😳
Wani irin magana kakeyi ne ameer? Ameer yace wlh gsky nake fada maka kaima dan dai baka lura bane''





*Ana tare*👌
[30/10 4:41 pm] Me Kosai✍: 🤡 🤡
🤡 🤡
🤡🤡🤡🤡🤡🤡🤡
MURMUSHIN AJALI
🤡🤡🤡🤡🤡
🤡🤡🤡🤡🤡
🤡🤡🤡🤡🤡🤡🤡
Written by Aysha wakili
*Mrs ahmed*

*dedicated to friend bee kalbi Miemie*

Page3⃣2⃣

Da sauri sultan yaja hannun ameer yana cewa zomuje tunkan yayi nisa mugansa''' dagudu suka fice a d'akin sukabi hanyar da sultan yaimasa rakiya ' sunyi tafiya sosai amma ko kurwansa basu gani va inda ameer harya gaji da gudu''' wuri suka samu suka zauna suna maida numfashi sultan yadubi ameer yace amma fah baici ace muntari yayi nisan wannan tafiyar damukayi va ' sbd awnawa da irin gudun damaukayi''
Ameer yace aikam 'mu hkr kawai mukoma dan nikam nagaji'
Haka suka juyo zuwa xuwa hostel kowannensu na haki"


*Nigeria* da safe bayan tagama aikinta tashirya itada yaranta suna jiran mahmud yafito domin xuwa family house ' hannu tasa tadau wayarta tana dubawa ganin misscall dayawa yasata mamakin yaushe ma aka kira 'tana dubawa taga sultan ne nd tunjiya yakira'' batare da 6ata lokaci ba tashiga kiransa'''

Ringing biyu yad'auka cikeda farin ciki yace mommah na ina kuka shiga keda abba tunjiya inata kiranku ba wanda yad'auka ' ajiyar zuciya tayi tace sultan bamu cikin hayyacinmu shiyasa bamu d'auka ba nd wayarma bata tare damu''
Cikin damu sultan yace meyafaru mommah meya fiddaku cikin hayyacinku?😳.

Cikin damuwa hafsa tace wani babban al'amari ne yafaru jiya wanda yatada hankulan dukkan ahalin tsoho''' cikin k'aguwa sultan yace mommah menene wannan abun pls fad'amin'
Nan hafsa tabashi labarin kome tundaga farko har xuwa mutuwar muntari da 6atar gawarsa'''''dayake tunda suka fara wayar a handsfree yake ameer najin duk abinda ake fad'e ''''aiko yanajin mutuwar muntari da 6atar gawarsa dagudu yamik'e zaibar d'akin sultan yajanyo shi yadawo da baya ' yace wlh saikaji k'arshen labarin ' cikin rau rau da ido sultan yace pls kabarni nafita karnai mafarki ''
Ko kallonshi sultan baiyi va yaci gaba da tambayar mommansu ko'anga gawan ynxu '' tace ai hrynxu ba'a gansa va ynxu hakama gdn tsoho zamu tafi muji a ena aka tsaya''''
Nan sultan yace ok tafadawa abbansu zaikira shi anjima yad'au wayarshi'' nan ta amsa da toh sukai sallama''

Sultan na aje wayar suka k'urawa juna ido shida ameer 'kana ganin yadda ameer yayi xurum da ido kasan a tsorace yake' sultan yace kai farar kura ,munhadu da fatalwar muntari ne fah ''inko ba fatalwa bane to aljani ne''
Da sauri ameer yace kaii sultan yi shiru dan annabi nifah ynxu hatta d'akin nan tsoro yake bani ''''

Haka suka zauna jungum jungum ameer duk yabiyatakure 'sultan yadubeshi yace kaifa kafaya tsoro saikace wanda yahad'u da mugun abu' ameer yace tomenene inba mugun abu ba 'wlh dama ni tunda naga muntarin nan jikina yakasa aminta dashi ashe ko ba karamin abune atare dashi va''



Bayan fitowar mahmud hafsa tadube shi tafada masa sultan yakira nd yace zaikirasa anjima 'nan yace ok barima inda suka karasa gdn tsoho zaikira sultan d'in ''

Bayan isarsu gdn akai yan'gaishe gaishe dayiwa juna jaje ''nan mahmud yafita xuwa waje inda sauran yan'uwansa suke xaune'''. Bayan yazauna ya fiddo wayarsa yashiga kiran layin sultan ringing biyu sultan yad'aga'
Bayan sungaisa ne sultan yace abba idan kana kusa da mutani ne kad'an matsa kad'an sbd zamui wata magana dakai'

Nan mahmud yamike yakoma jikin motarshi yatsaya 'sannan yacewa sultan yana jinshi'''
Sultan yace abba mommah ke fad'amin wani lbr mekama da tatsuniya wai muntari yamutu kuma ba'aga gawarsa va?
Mahmud yace eh ba tatsuniya bace gskyr abinda yafaru kenan''' sultan yace amma abba kasan wani abu kuwa?
Mahmud yace a'ah saika fada '''sultan yace wlh tlh abba muna tare da muntari jiya yaxo wurina har bayan magriba muna tare'' cikin rashin fahimta mahmud yace wani mutarin kake magana akai waima?

Sultan yace muntarin mu wanda kukace yamutu 'cikin mamaki mahmud yace yaishe yaxo?sultan yace tunsafe yaxo guna lokacin zamu tafi lecture harmukayi sallama dashi akan zaitafi saidai kuma bayan dawowar mu daga skull saigashi yasake dawowa har bayan magrib muna tare dashi muna hira''''

Da sauri mahmud ya isa gun yan'uwanshi yasaka wayar a hands free '''sultan yacigaba da cewa ''harnace zanbashi sak'o yakawo wa miemie saiyace min wai ba gd zasu dawo ba daga nan wani kasar zasu sake nufa shida oganshi'''

Bauan naraka shi nadawo sai ameer yake cemin shifah baiyarda da wannan muntarin ba sbd tun sanda yashigo yazauna a dakin 'tagaban madubi ba'a ganinsa ''' nace da ameer banyarda va nan ameer yace muje munemo shi agani in karya yakeyi ' amma koda muka fita dagudu munyi nemansa bamu gansa va '''''''
Nayita kiran lambarku baku d'auka va'' saidaga baya mommah tad'auka shine take fad'amin batun rasuwar sa da 6atan gawar ' saidai banfad'a mata abinda ake ciki ba nace zankiraka'''

Ba mahmud da wayar ke hannunsa ba hatta da yan'uwanshi dake sauraren batun sultan saida cikin kowa yaduri ruwa bama kamar tsoho da kakeji sautin kukan da cikinsa yakeyi'''🤣

Cikin wata wahalalliyar murya mahmud yacewa sultan bari zankiraka '''nan yakashe wayar yana duban fuskar yan'uwansa '''cikin damuwa yace kunji wata sabuwa''

Tsoho yace wannan tafi gaban sabuwa saidai gagaruma '' shiru duk sukayi kamin babban yayansu baki dai' yace wannan al'amarin akwai sarkakiya acikinta ' inaga abinda zaifi dacewa sultan yaje yanemo inda yake da zama sannan musan abinyi''
Mahmud yace taena zainemo shi bayan ba fada masa inda ya sauka yayi va'

Tofah wannan wani irin cakwakiya ce haka ''





*Ana tare*👌
[01/11 6:49 pm] Me Kosai✍: 🤡 🤡
🤡 🤡
🤡🤡🤡🤡🤡🤡🤡
MURMUSHIN AJALI
🤡🤡🤡🤡🤡
🤡🤡🤡🤡🤡
🤡🤡🤡🤡🤡🤡🤡
Written by Aysha wakili
*Mrs ahmed*

*dedicated to friend bee kalbi Miemie*

Page3⃣3⃣

Haka sukaita tunane tunane daga karshe suka yanke shawarar barasu fad'awa kowa wannan al'amarin va harsai Allah yasa angano inda muntari yake''
Da wannan batu suka bar gdn tsoho saidai kowanne zuciyarsa da al'ajabi da tsoro bama kamar tsoho dako motsi yaji sai cikinsa ya murda azatonsa muntari ne ''

Acikin gd kuwa baabaa asabe ba abinda takeyi banda kuka tana cewa shikenan tarasa jikanta muntari inda baabaa laure keta faman rarrashinta da sauran mutani''



Tundaga ranar da sultan sukai waya da mahmud yaketa binciken inda zaigano muntari saidai hakan baisamu ba 'sbd duk inda yake tunanin ganinshi baisamu ba'' haka sukaita yawo shida ameer amma babu ko burbushin muntari'

Haka suka gaji suka hkr ''a nigeria kuwa kullum mahmud jiran kira na musamman yakeyi daga sultan ko Allah yasa andace sunganshi amma shiru kakeji''

Bayan sati hudu 'family na tsoho sunriga sun fidda rai da ganin muntari kuma sunriga sun tabbatar yamutu ' bakin cikinsu shine rashin ganin gawar tasa''
Kowa yaci gaba da harkokin gabansa kamar yadda aka saba'''





*bayan shekara biyu* abubuwa dayawa sun faru kadan daga ciki sune 'anyi auren salma itada kamal jikan baabaa asabe '''saikuma soyayya data 6ullo kai tsakanin mahmud mahaifin miemie dawata bazawara makwabciyarsu mesuna baraka inda mahmud baki dai yamaida hankalinsa ga soyayyarta yadena kula da iyalansa kamar yadda yasaba adah can '' hafsa tashiga damuwa sosai inda duk tabi tarame domin mahmud yajuya mata baya itada ya'yanta''
Shi kawai burinsa yaga ya auri baraka yakawota gdn shi'''

A 6angaren baraka kuwa dama ba karamar shedaniya bace domin babu bokan dazai fito dabatasan shi va 'a kalla aurenta zaikai biyar dazarar tagama talauta mijin zata nemi yasaketa,inko yaki to karshenta saidai awayi gari aga gawarsa''
Wannan labarin da hafsa tasamu yasa tashiga matsanancin damuwa domin ta tabbatar mijinta yana cikin halin ha'ula'e ''

Ana cikin haka mahmud yaxo mata da labarin aurensa nan da sati biyu masu xuwa''hafsa ta girgiza matuka 'amma haka tadake tace Allah yanuna mana'' 6angaren inna amarya koda mahmud yaje mata da batun karin auren nasa batayi naam da zancen ba' amam dankar tashiga hakkinsa yasa taimasa addu'ah akan Allah yasa ayi a sa'a'''nan mahmud yashiga shiry shirye baji bagani' inda hafsa tadukufa da addu'ah ga ubangijinta tana neman agajinsa''


Miemie zaune itada baabaa laure suna fira gwanin birgewa kamin baabaa laure tadubeta tace oh ni miemie ashe zakiyi hankali ,da can fah yadda kikasan mahaukaciya haka kike amma gashi ynxu kindawo daidai koda yake shekaru bai bar komeva''' tsaki tayi tace nikuma cah nake zaki dena magana tunda kina gab da mutuwa amma harynxu kin kasa denawa wlh ki kiyayi ranar da walakiri zaimaki xuwan bazata''' tafi baabaa laure tazubawa miemie abaya tana cewa yar'banza saikisa yaxo d'in shegiya mai mugun alkba'e"" miemie koh ganin yadda baabaa laure ta birkice yasata kwashewa da dariya tana cewa su baabaa laure ba'ason maganar mutuwa''

Suna nan zauneTasi'u yashigo yanemi wuri yazauna yana duban miemie yace sister meya had'aki ne da k'awar taki 'dariya miemie tayi tace ai wannan matar batason zancen mutuwa shiyasa kaga muna fad'a
Yace to tunda bataso aisaiki rabu da ita' miemie tace wlh bare yuwuva dole ai zancen mutuwa ita datake gab da rami harma zatana wani Cewa batason zancen mutuwa, wlh sai anyi saidai tamutun''' naushi baabaa laure takai mata tana cewa saikizo ki kasheni shegiya me mugun abu kawai' keni wlh kizo ki koma gdn ubanki ni nagaji da zama dake wlh shegiya mekama da k'wak'wa '''

Dariya miemie tayi tace ai wlh ba inda zani zama daram dakam babu tafiya koena '''tasi'u yamike yana kallon miemie yace sister xomuje kirakani wani wuri ''batare data kalleshi va tace kaii yah tasi nifah banason yawan fita wlh'''caraf baabaa laure tace aiko shiyasa harynxu kika rasa meshin shina ki 'gaki dai kyakkyawa takarshe amma ba meso''kinyi kwantai'' tsaki miemie tayi tadau mayafi tana cewa kanki akeji 'yah tasi mutafi kaji''

Baabaa laure tace oho dai sai afkin iyayi amma ba masoyi 'nan da wasu watanni dazarar kingama jarabawa zamui sadaka dake kowa yahuta'''
Dariya miemie tayi tace haba saikace zamanin aurenki da tsoho da aka lankaya mashi ke '''
Mikewa baabaa laure tayi tabi bayan miemie dagudu tana cewa ubanki aka lankayawa shegiya kawai'''' tasi'u dai dariya yayi domin ganin dramar dramar tasu bame karewa bane'''






*Ana tare*👌👌
[03/11 8:29 pm] Me Kosai✍: 🤡 🤡
🤡 🤡
🤡🤡🤡🤡🤡🤡🤡
MURMUSHIN AJALI
🤡🤡🤡🤡🤡
🤡🤡🤡🤡🤡
🤡🤡🤡🤡🤡🤡🤡
Written by Aysha wakili
*Mrs ahmed*

*dedicated to friend bee kalbi Miemie*

Page3⃣4⃣

Bayan fitar tasi'u da miemie tsoho yashigo cikin gd'yasamu baabaa laure zaune kan tabarmar da miemie ta tashi 'shima zama yayi kusada ita 'yace laure ina mairo take? Bata nan taraka tasi'u cewar baabaa laure 'gyada kai tsoho yayi yace toh Allah yasa adace baabaa laure tace dame?
Tsoho ya gyara zama yace dama tasi'u ne yazomin dawani batu kan cewa shiyana son mairo a had'asu aure kamar yadda aka had'a kamal da salma''
Afirgice baabaa laure tadubi tsoho sannan tace tab saikace a film d'in hausa wai a had'a miemie da tasi'u kaima kasan bame yuwuwa bane sbd asabe ba yarda zatayi va' tsoho yace dake asaben itace megidan ko kuma itace yaran dabarata yarda ba '
Barikiji kije kisameta kifada mata domin ni nayanke shawarar had'asu daga sun amince da junansu toni Nawa fatan alkhairi ne danhaka kema kifad'i alkhairi ko kiy shiru'''
Nan yamike yafice yabarta zaune tana kwallawa baabaa asabe kira''koda fitowar baabaa asabe ta shaida mata abinda tsoho yace tsaki baabaa laure tayi tana cewa toh ayi mana can su suka sani tunda dai tasi'un ne yace yaji yagani ai shikenan 'sannan inbanda sakarci irin na tasi'u ina shi ina miemie yarinyar dabata da maraba da k'wara 'ni dan annabi kubarni naji da matsalata ,,nan takoma d'aki ,,



Miemie da tasi'u kan hanyarsu 'tajuyo tadube shi tace wai ya tasi ina zamuje ne naga sai lula tafiya mukeyi kamar zamu bar garin' murmushi yayi sannan yace aimun iso inda zamuje ma 'nan suka nemi gun wani

Please Login or Register in order to submit comment