Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

aka dauki tafi director ta rasa inda zata sa kanta dan farin ciki byn waje ya nutsu aka raba gifts ga overall da wacce tafi kowa respect, sanan aka kira head girl me barin gado wato ya sally ta taso tana wani iyayi ta fara jawabin godiya cikin harshen turanci sai wani make murya take duk don ta burge Prince shikuwa bema San tanayi ba, byn ta gama prince ya mike yayi sallama ya tafi, aka rakashi har bakin mota sanan suka dawo akaci gaba da events anci ansha, akayi drama da wake wake kowa yayi hotuna da yan uwansa da iyaye sanan taro ya watse.
[6/10, 11:01 PM] amina yakubu: 💙💛💚PRINCE AFFAN💜💖❤
4⃣5⃣to5⃣0⃣

Ni kuwa tunda su samiha sukai min waya na kaishe wayata nayi kukana na koshi ciwon kan danake ya karu bansan lkcn da wahalalle bacci ya dauke ni ba, sai can wajen azahar na farka naji hayaniyar su Sumy suna waya da Yaya Faruk yana fada musu jibi zai dawo na sakko nayi musu sannu da dawowa mum tace ya jikin nace da sauki sbd yanzu ta rage tsanata sbd ina kyautata mata sosai, ya Faruk yace a bani mugaisa na karba mun dan Dade muna hira dake jininmu ya hadu sosai dashi sanan ya kashe wayar dama da wayar ya Sumy aka kirashi ina bata wayar naga ta fisga ta tafi saina tuno da taron da akayi a sch yau to ko prince yaje ne ? Dan iam very sure da bejeba dana shiga uku a wajen ya Sumy da suna shigowa gidan dani zata fara da gudu na koma daki na dauki wayata na kunna na fara kiran sameeha tana dauka tace banza matsoraciya shine kika kashe waya to Prince yazo kuma har ya bawa director kyautar five millions wani wawan ihu na saki nace alhmdl Allah nagd maka, Allah ya fitar dani kunya sameeha shiyasa naga Yaya Sumy tana harara ta ashe eh mana ai danma bakya wajen da kinyi kallo uhm Allah ya rufa asiri tace amin sai mun hadu OK bye
[6/11, 8:50 AM] amina yakubu: ❤💛💙PRINCE AFFAN💜💖❤
5⃣0⃣to5⃣5⃣

Yau Yaya Faruk zai dawo kowa na gidan da wuri ya tashi muka hau gyare2 ni naje na gyara masa dakinshi na wanke toilet nasa turaren wuta sanan muka shiga ktchn nida mum mukayi fried rice, pounded yam with egusi soup, dambun shinkafa Wanda yaji kayan hadi, farfesun naman kaji dana ostel lemon kankana da madara, mango juice etc. Bayan munjera komai a dinning kowa yaje yai wanka muka shirya sai air port muna can jirginsu ya sauka dake tun wajen 12am suka taso ba a jima ba sai gashi sun fara saukowa ya Faruk yana tahowa bilal ya tafi da gudu ya rungumeshi suka krs tare ya Dan risina ya gaida mom ya Sumy tace tayi Hoggin dinshi sanan ya karaso inda nake tsaye ya danyi hogging dina my sis ya kk nace lpy kalau wato kin zama yan mata ko? Shi yasa kika wani basar mukasa dariya gabadaya nida shi, daga nan muka wuce gida muna zuwa ya wuce part dinshi yayi wanka yayi sallah sanan ya fito yaci abinci aka bude sabuwar hira, dan aranar har kusan 11pm muka kai muna hira sanan mum tace kowa yaje ya kwana

Maman Aysha
[6/11, 9:37 AM] amina yakubu: 💚💖💙PRINCE AFFAN💜💛💖
5⃣5⃣to6⃣0⃣

Yau asabar hutun makrntr islamiyarmu ya kare da wuri na tashi na hada lafiyayen break fast sbd yay Faruk ina gamawa naci nayi wanka nasa kaya na dauko katon hijabi na blue har kasa nasa shine uniform din martr, sanan na dauki books dina na tafi dama 9 to 12 ne da aka tashi muka taho nida wata kawta mardiya itama a unguwar take muna zuwa wani Dan junction kowa yayi hanyar gidan su ina daf da karasawa gida sainaji an kwala min kira balarabiya ina juyowa gbn ya fadi ya salm dama haka yake dakyau? ranan ganin tsoro nayi masa kenan? kodan lkcn duhu ya fara ne? Kunsan waye? Me machine din da daukoni ne last zuwana gdn Prince na dade ina ganin maza masu kyau amma ban taba ganin me kyan wanan bawan Allah ba saidai abin tausayin shine kana ganin kayan jiknsa kasan me karamin karfi ne. Ya karaso yace balarabiya ya kike nayi murmushi nace lpy kalau yace run ranar dana dauko ki kullm sainazo kofar gdnku amma saina kasa aikawa a kiraki sbd idan kin fito bansan me zance miki ba, inaso na zama abokinki sbd naga you're very simple saidai ban Sani ba ko zaki Iya abota da talaka. Nayi murmushin da har saida kuma tuna ya lotsa nace da me kudi da talaka duk Allah ne ya hallicemu kuma nima ai bamai kudi bace, karka damu daga yau ka zama friend dina. Dariya yayi har fararen hakoransa suka bayyana yace nagd sosai, amma ya kamata kisan koni waye nace gaskiya ne. Ni sunana Umar sunan kyauyenmu ajawa kuma iyayena talakawa ne amma duk da haka sun tsayamin nayi krtn boko dana addini domin kuwa har masterszariyaarchitecture na krnt a ABU zariya, shekarata daya da yin service amma har yanzu ban sami aiki ba sai dan buge2 kawai nake gashi iyayena suna tsananin bukatar temakona wanan shine dalilin da yasa na sayi machine na fara Sana'a okada yayi wani lallausan murmushi wanan shine lbrna balrby nayi ajiyar zuciya nace ba komai friend karka damu kowa da yanda Allah ya tsara masa Rayuwa, kuma ka gode Allah kayi karanci course me tsada insha Allah nayi maka alkawari idan daddy na ya dawo zan temaka maka, yace to nagode nace zan wuce gida saida safe yace Allah ya kaimu

Maman Aysha
[6/11, 10:10 AM] amina yakubu: ❤💚💙PRINCE AFFAN💜💛❤
6⃣0⃣to6⃣5⃣

Tun daga wanan ranar shakuwa me tsanani ta shiga tsakanina da umar sbd shu mutun ne me barkwanci sanan baya shiga sabgar da bata shafe shi ba kuma bashi da son zuciya sbda ko kudi na bashi da kyar yake karba duk da yana bktrs, kusan kullum sai yazo munsha hira duk ranar da bamu hadu dashi ba kuwa bana Iya baccin kirki tun ina ganin abin kmr shakuwa ne yanzu na gane sonshi nake, INA tsananin sonshi son da nima bansan lkcn da ya shiga zuciyata ba. Amma shi Umar bema San inayi ba domin kuwa ko kadan banga alamar sona a kwayar idonsa ba kullm treating dina yake a matsayin kanwarshi.
Yauma kamr kullm Umar ya kirani a awaya dake nasai mishi waya me tsada, a gefen gidan su mardiya muke hdw sbd banaso yar renin hnkln nan ya Sumy ta ganshi da hanzari naje muka fara hira sai yace na bashi aron wayata yana cikin duba inbox sai yaga rply din da prince yayi min lkcn da nayi masa tuni, sai ya dawo out box sai yaga text din da na tura masa.

Maman Aysha
[6/11, 10:46 AM] amina yakubu: 💜💚💖PRINCE AFFAN💛💙❤
6⃣5⃣to7⃣0⃣

Kawai sainaji yace meye hadinki da prince balrby nace meka gani? Naga kinada contact dashi directorn sch dinmu CE ta taba aikena wajen sa nakai mishi IV, kuma yaje wajen events din? Eh to meyasa director sai ke ta aika na kwashe lbrn abinda ya faru gaba daya na fada masa, sainaji yace alhmdl suhailat lkc yayi da zaki temakamin basai dad dinki ya dawo ba, (daya fadi sunana saida tsikar jikina ta tashi sbd be taba fadar sunana ba sai yau) wane irn temako kenan? Inaso ki koma wajen prince for the 2nd time ki nemo min aiki sbd last WK sunyi announcing zasu debi maaikata a companynsu kuma har architect ake nema sbd banida Wanda zai tsayamin shiyasa banje ba don Allah suhaila ki temaka min. Nace friend don Allah kayi hakuri wallahi banason abinda zai mayar dani wajen prince wallahi, yace ba zaki temaka min ba kenan? Shi kenan nagode ya tashi yayi tafiyrsa ya barni a wajen na Dade a tsaye INA tunani wanan wane irin balai ne? Me yasa Umar zai min haka? Kodan besan irin wulakanci da prince yayi min ba kfn ya amsa gayyatr.
[6/11, 11:14 AM] amina yakubu: 💙💛❤PRINCE AFFAN💜💚❤
7⃣0⃣to7⃣5⃣

Yau kwana uku kenan ba Umar ba lbrns idan na kira wayar shi switch off wajen karfe 8:30pm INA kwance a daki sainaji kira INA dubawa naga friend da sauri na dauka hlo haba friend ina ta krnk waya akashe meya faru yace caji ne babu yanzuma batur na ara sabd inaso na kira nayi miki sallama gobe insha Allah zan tafi Lagos neman kudi nagode da temakon da kikai min Allah ya biyaki da gdn aljanna dammm naji gabana ya badi don Alla friend karkayi min haka indai sbd zuwa wajen Prince ne na amince zanje nayi mishi mgn gobe I.s.a, amma don Allah karka tafi duk yanda mukayi dashi I will call you. Yace to shiknan sainaji ki.
Washe gari tunda safe gabana yake faduwa sbd zuwa gdn Prince amma haka na daure dole naje sbd masifar son Umar danake. Ba wata kwaliyya nayi ba super nasa me adon blue da fari na yafa blue gyale nasa takalmi flat shim blue yar pos kadai na dauka na tafi amma fa duk da haka nayi kyau.

Maman Aysha
[6/22, 10:17 PM] amina yakubu: 💚💜❤PRINCE AFFAN💙💛💖
7⃣5⃣to8⃣0⃣

Ina zuwa srkin gd yayi min iso ba wani bata lkc yace na shiga, yauma kmr kullum a kishingide na sameshi nayi sallama ya amsa, na gaisheshi sanan nayi shiru sai yace inajinki me ya faru kuma? Na nisa nace na dawo neman taimako ne for the 2nd time OK ina jinki, na sami lbrn sanarwa da kukayi akan diban ma'aikata nakeso dan Allah ka taimaka ka dauki broda na dago kai yayi ya kalleni sanan yace alright meya krnta nace architect yace that's good amma bakiyi kama da masu karya ba sbd hk ki fadamin gaskiyar abinda yake tsakaninku inba hk ba ko na daukeshi aiki ranar dana gane gasky to zan koreshi na dago muka hada ido kawai sainace masa mutumin da zan aura ne I.s.a, murmushi yayi sanan yace kinzo Neman alfarma da farko nayi miki amma ko kimin godiya kuma gashi kin dawo neman wata, waima na tambayeki aganinki me yasa na amshi buktrki ta farko nace sbd na hadaka da Allah da annabi yace tabbas hakane amma akwai dalili na biyu da kema baki sanshi ba, shine sbd INA sonki, INA tsananin sonki suhailat tun ranar da kika zo nan na kamu da sonki, kuma kullum dashi nake kwana nake tashi naso naje sch dinku a kiramin ke nayi miki bayani sai tafiya ta kamani zuwa USA sai last WK na dawo, ina shirin zuwa kuma sai gaki sbd hk nafi dacewa dake akan kowa ni yakamata ki aura bashi ba, kuma magnr offer gobe ma ki fada masa yazo karba amma da sharadin zaki amince da mgnr aurena. Kuka me karfi ne ya kwace min nace don Allah prince kayi hakuri wallahi shi nakeso inayi mishi sonda bantaba yiwa wani mutun irinsa aduniya ba don Alla ka taimaka min, yace kinga daina kuka kije kuyi shawara bani no ki zan kira gb insha Allah, nayi masa sallama na taho jiki ba kwari

Maman Aysha🌲🌲
[6/22, 11:43 PM] amina yakubu: 💜💖💚PRINCE AFFAN❤💙💛
8⃣0⃣to8⃣5⃣

Ina idar da sallar magrib na kira Umar a waya nace yazo inason ganinsa ba a jima ba kuwa ya kirani yace na fito yazoi, naje inda muka saba haduwa bayan mun gaisa yace ya kukayi da prince nace ba hope me yasa kikace haka? Yace gb ma zai Iya baka offer, amma saina amince da bukatarsa, meye bukatar tashi? Wai yana sona zai aure ni Kawai sainaji yace alhmdll Allah na gode maka suhailat yau Allah ya amsa addua ta, na dade INA rokon Allah ya baki miji na gari inda zaki huta prince shine irin mijin daya dace dake suhailat, sai kawai nabishi da kallon mamaki ya matso kusa dani yace ya kikayi shiru sainaji hawaye sun fara zuba a idona nace haba friend yanzu kana nufi kace baka taba sanin INA sonka ba? Inaso yau kasani kai kadai nakeso na aura, kuma idan ban aureka ba komai zai Iya faruwa dani. Yace ki daina fadin haka ni ba saan auranki bane, prince shi yafi dacewa dake inaso kiyi Rayuwa me inganci bata talauci irin tawaba na katse shi kana nufin kace baka sona yace ba mutumin da bazaiso ya mallakeki a matsayin mata ba suhailat amma matsalar shine ni talaka ne, gaskiya bazan aureki ba kiyi hkr ki amshi bukatar Prince ki karbomin offer kawai ya tafi ya barni awajen cikin takaici. Haka na koma gida inata tunanin mafita, daga karshe na yanke shawarar na rabu dasu gabadaya kawai, da haka bacci marar dadi ya dauke ni da kyar

Maman Aysha💞💞
[6/23, 8:22 AM] amina yakubu: 💙❤💚PRINCE AFFAN💜💛❤
8⃣5⃣to9⃣0⃣

Da safe a gajiye na tashi dake nayi sallar asuba wanka kawai nayi na saka uniform nasha corn flakes na dauki jakata na tafi sch, dake yanzu mune a ss3, bayan anyi break muka kebe dasu nabeeha na basu lbrn abinda ya faru from AtoZ suma dai shawara suka ban akan na auri Prince a zuciyata nace dan basu San yanda nake son friend bane. Bayan mun tashi daga sch tare da sameehat muka taho gdnm sbd akwai sakon da zata karba, muna shiga mu kaci karo da Yaya Faruk sameeha ta dan risina ta gaisheshi sainaga ya bita da wani irin kallo muna hada ido dashi yayi murmushi yace ya akayi ne sis nayi dariya nace ba komai Yaya muka krsa ciki ba yanda banyi da ita ba ta tsaya muci abinci amma taki da muka fito still Yaya na waje ya tmby wane unguwa zata tace fatara qtrs sai kawai naji yace bari nayi dropping dinki mukayi sallama suka tafi
Har dare INA zuba ido naga kiran friend amma shiru, nima kuma nace bazan kirashi ba, can wajen 9pm sainaji wayta tana ringing INA dubawa naga Prince take naji gbn ya fadi amma hk na daure na dauka nayi sallama ya amsa sanan yace tun safe nake jira naga kinzo karbar offer amma sainaji shiru wanan shine ya tabbatar min da cewa kina nan akan bakanki, inaso ki Sani inayi miki son ban taba yiwa wata mace irinshi ba amma tunda kin zabi choice dinki shukenan nima inason farin cikinki sbd hk na janye mgnr aure a tsakaninmu, kuma gobe kizo around 10am ki karbi offer wani irin farin ciki ne ya lullube ni na rasa inda zansa kaina da dadi na fara jero gdy yace ba komai yiwa kaine, yana kashe waya na kira friend nayi mishi albishir

Maman Aysha💖💞
[6/23, 6:40 PM] amina yakubu: ❤💛💙PRINCE AFFAN❤💚💜
9⃣0⃣to9⃣5⃣

Cikin tsananin farin ciki yace dagaske ko mafarki nake nace wanke idonka reality ne yace alhamdl iam so greatful wallahi nagd suhailat hk mukaci gb da hira cikin dishadi da annushuwa daga karshe mukayi sallama akan idan na karbo zaizo.
Bacci me dadin gaske nayi dan ko juyi banyi ba har asuba INA tashi nayi wanka nayi salla, na fara kartn alkur'ani har gari ya karasa wayewa na sauka kasa muka fara hada break fast nida baba ramatu saiga Yaya Faruk y shigo kitchen din nace gud mornin Broz yace mornin sis me ake dafa mana nace duk abinda kk so shi zaayi yace to danwake nake so nace ba prob zanyi maka, yace yauwa my sis, au na manta ban fada miki ba iam in Luv wit your friend sameeha wani ihun dadi nayi nace kai amma naji dadi wallahi Allah ya tabbatar da alkairi yace amin a zuciyata nace shikenan munyiwa yan clicks din ya Sumy zarra, sbd ya ruky ce take mugun sonshi. Bayan nayiw Yaya danwakensa nayi toasting din bread, nayi shawarma na dafa ruwan zafi na zuba a flask sanan nayi pepper chicken nakai dining sbd zumudi kasa cin komai nayi, fito na koma na dauko wata gown dina ja 20k mamana ta sayomin a Dubai nayi rolling da mayafin rigar dake yana da dan girma kadan nayi wankan turare, na shafa powder da wet lips nasa flat shoe ja n dauki purse dina na fito
[6/23, 10:59 PM] amina yakubu: ❤💜💚PRINCE AFFAN💙💛❤
9⃣5⃣to1⃣0⃣0⃣

Mummy da Yaya Faruk nagani suna cin abinci na durkusa na gaida mum tace ina zaki da sassafe hk nace kai 9:30am fa yanzu garin ne da hadari shiyasa kike ganin haka wata yar lajinmu ce a islamiya bata da lpy shine zamu hadu da yan ajin mu dubota a asibiti sukace Allah ya sauwake sai kundawo. Ina fita na sami machine har kofar gidan wata gaisuwa ta musamman naga fadawan gidan sunayi min mu karasa ciki da sarkin gida har reception sanan ya nuna min kofar guarding yace nan zaku shiga ranki ya Dade nace to muna shiga na daburce Ashe da ba kallo nayi ba haduwa tana nan wato wasu Haddadun flowers ne a zagaye acikinsu kuma wasu lafiyyayun kujeru ne irin na turawa, ga wata katuwar darduma an shinfida ga wani Haddadan decoration na torrow pillows da akayi, me kart kowa yayi imaging da kansa sbd kyau da tsaruwar wajen bazai fadi anan ba.
Cikin runfar na shiga na zauna kafin ya fito INA dubawa naga wani kato aquarium da kifaye aciki sai wasa suke dake transparent ne sai kawai naji sun bani shaawa na mike na karasa bakin wajen inata kallonsu inajin dadi kmr daga sama sainaji ance ko kina sone akai miki gdnku a hargitse na juyo, (me kart ba wai maganar da akayi bace ta figitani aa muryarsa CE) wata shegiyar gezna ya saka maroon color yar wajen 50k da wata shegiyar hula kunsan waye kuwa? Friend ne yanamin wani shu'umin murmusma muryata tana rawa nace me ya kawo ka nan friend? Yace cool down suhailat don Allah ki nutsu kinji ya matso kusa dani ya rike hanuna yace mutumin da kike gani a matsayin Prince Affan bashi bane suhailat nine AFFAN din gaskiya amma muje mu zauna zanyi miki bayanin komai.
Masu krt Ku biyoni

Maman Aysha
[7/9, 12:59 PM] amina yakubu: [6/25, 11:49 PM] amina yakubu: ❤💛💜PRINCE AFFAN❤💚💙
1⃣0⃣5⃣to1⃣1⃣

Kamar yadda na fada miki sunana AFFAN Umar Faruk, kuma maifina shine me martaba sarkin wanan garin wato HRH Alhaji Umar Faruk, kuma ya gaji sauratar ne daga wajen mahaifinsa. Kafin ya zama sarki ambassador ne shi a kasar Holland kuma tun banfi 3yrs ba aka bashi, mu uku suka Haifa nine na farko bayan anhaifeni da shekara 12yrs sanan aka Haifamin kanne twins wato hanif da Hanifa, sunan mahaifiyata Haj BINTA makinta shuwa Arab kuma yar asalin yobe state ce a England suka hadu da babana lkcn sunje yawon shakatawa da babanta dake babanta business man ne. Shi haneef yana wata mkrnt a Istanbul yana krnta civil Engineering, Hanifa kuma tana ABU zaria tana krntar Law kuma Dan sarkin zazzau take aure da danta guda daya. Ni kuma kmr yadda na fada miki da farko architect ne ni kuma nine managing director na kamfanunuwan mahaifina domin kuwa sunkai guda goma. Kasancewa ta da na farko da suka fara zamu sun sai suka dauki son duniya suka doramin misali mai martaba bayaso yaga bacin raina ko kadan, iyayena sun Dade suna so suga nayi sure domin kuwa sunsha turani wajen yayyan sarkuna da yayyan abokansu amma banga wacce tayimin ba tun suna damuwa har sun hakura sun zubamin ido sbd wallahi suhailat inada high test.
[6/26, 8:52 AM] amina yakubu: ❤💛💜PRINCE AFFAN❤💚💙
1⃣1⃣0⃣to1⃣1⃣5⃣

Kallona yayi yai wani lallausan murmushi sanan yace na amsa tambyrki ta farko, sabd mahaifina sarki ne shi yasa na zama prince. Yanzu sai 2nd and last questions zan amsa ko? Na gyana mishi Kai kawai ba tare da nayi magana ba sai yaci gaba
Wato abinda ya faru shine acikin friends din sisterki da kika bawa lbrna akwai cousin din wani friend dina Ahamad, kina fara basu lbrn ta dauki waya dai dai inda kika fara fadamusu yanda akai muka hadu, daga nan ta fara recording ba tare da kin gane ba. So bayan ta koma gida saita kira Ahmad take tambayarshi da gaske ne Prince yana son wata yarinya kuma tana wahalar dashi? Sai yace kai bansan wanan lbrn ba ke waye ya fada miki? Kawai saita kunna mishi ya farajin magnrki very cleared abin ya bashi mamaki sosai sai yace ta tura masa wayarshi zaiyi bincike akai. Lkcn daya bani labri raina bakaramin baci yayi ba nace wacce yarinyar ce take son batamin suna, aikuwa sainyi mata rashin mutunci, saina yi mata wulakancin da bazata karayiwa wani sharri ba sai Ahamad yace bari na kunna maka recoding din ko zaka gane voice dinta yana kunnawa sai naji muryarki ta daki kunnena kawai sainaji inason voice din, sai nace nima ya turomin kuma ya deleting din na wayar sister shima kuma ya goge nashi
[6/26, 11:27 AM] amina yakubu: ❤💚💙PRINCE AFFAN❤💛💜
1⃣1⃣5⃣to1⃣2⃣0⃣

Anyi haka da kwana biyu na tafi Paris zanyi order kayan da zamusa a company nmu na takalma da zamu bude, saida nayi 2mnth sanan na dawo a satin da nadawo ne Ahamad yake bani lbrn sister shi ta fada masa sbd karyar da kikayi musu sunsa director SCH dinsu ta baki IV card ki kawomin ranar Saturday kuwa sai gashi kinzo. Lkcn da sarkin gida ya sanarmin da zuwanki tasowa nayi sbd nafiso nayi miki rashin mutunci a inda kike a tsaye batare da kin shigo Palo ba, kinsan me ya faru suhailat? Nace aa kinsan nida nake aciki ina kallon ki amma ta waje madobi ni sai dai kiga pic dinki ko nace eh, to abinda ya faru shine INA ganoki sainaji on the spot na kamu da sonki sbd kice irin type din matar da nake nema, sai wata zuciyar tace min ta hali fa kasan yaya halinta yake? Sai kawai dabara tazomin nace sarkin gida yafada miki ki dawo gobe bazan sami damaar ganin ki yau ba. Kina tafiya nakira aminina Mahmud nayi mishi bayanin komai kuma muka hada plan akan idan kin dawo gb ya saurare ki a matsayin prince kuma na tsara mishi yanda zaiyi treating dinki.

Maman Aysha💛
[6/26, 12:06 PM] amina yakubu: ❤💛💜PRINCE AFFAN❤💚💙
1⃣2⃣0⃣to1⃣2⃣5⃣

Phone no daya baki sabon layi ne kuma wayar a hanuna take lkcn da kika yi min text ana gb zaayi program din ni nayi reply, kuma ni naje sch dinku wani abu da yasa ni farin ciki kuma shine na tamby ina kike akace bakizo ba baki da lpy kinga baki ganni ba kenan zaki ci gaba da ganin mahamud a matsayin Prince, wanan shine ya bani damar zuwa wajenki a matsayin Umar kuma shiyasa naki yadda mu hadu da kawayenki sai mardiya sabd ita kadai ce bata Sani ba.
Suhailat ba karamin farin ciki nayi ba dana gane cewa muna raayi daya dake na tausayi da kuma son talaka, kin gade mahaifina sarki ne ko amma wallahi idan kika ga yadda nake wasa da dariya da bayin gdnmu zakiyi mamaki sbd duk wani Dan Adam da kika sani a duniya yanda irin tashi baiwar da Allah yayi mishi, shiyasa baa so a rena mutun. Wanan dalilin ne ya hana nayi aure tun tuni sabda karna auro matar da zata ringa wulakanta Mutane, kuma wanan shine dalilin da yasa nazo miki a matsayin talaka sabd naganecewa AFFAN kike so ba prince ba INA fata zakiyimin kyakyawar fahinta suhailat? A sanyaye nace masa eh sanan na mike nace ni zantafi yace OK muje nayi dropping dinki naso nayi gardama amma daya tsare gida irin na jinin sarauta kawai saina bishi inda ya packer motar muka tafi.

Maman Aysha❤
[7/2, 10:16 AM] amina yakubu: ❤💛💜PRINCE AFFAN❤💚💙
1⃣2⃣5⃣to1⃣3⃣0⃣

Muna fara tafy saina tuna ban dakko yar purse dina ba nace mishi nayi mantuwa sai yace ok , ya juya kan motar sbd dama bamu fita daga surrounding din gidan ba daidai inda ya tsaya da farko ya

Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3Chapter 4

Please Login or Register in order to submit comment