Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


Downloaded from GNOVELS.COM.NG




This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG
to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/gnovels

Twitter : https://twitter.com/gnovels

Telegram : https://t.me/gnovels

 writing by his eccellenciy novels group






****** DAN ALHAJI 1 ******
.
Iskace mai karfi hade da guguwa garin duk ya hargitse mutane sai neman wajen fakewa suke wasu kuma sun tsaya cak suna kalon ikon Allah rufaida ce a tsaye hankalinta a tashe ganin tasowar guguwa dake nufota tana dosowa ta dauke dan karamin hijab din dake jkinta ganin hkaa ta sake dinmucewa da sauri ta rungume jakarta ta makaranta ta rufe kirjinta.
.
duk wannan abin dake faruwa a kan idon safuwan tsye yake cikin motarsa ganin tasowar guguwar ne yasa ya faka motarsa.hijab din ko bai tsaya ko ina ba sai kan fuskarsa jin wani daddadan kamshi yaji a jikn hjab din sauri yayi ya cire shi ya bishi da kallo ga kuma kamshin jikin hijab din daya tafi da imaninsa.bude motarsa yayi ya fito ya doshi inda take da hijab din a hannunsa cikin takun kasaita nasu na ya yan masu ji da kan su kyakyawan saurayin ya karasa inda take tsaye tana ganin ya doso inda take ta sake rudewa ganin rashin hijab a jikinta tayi kamar ta taka da gudu ya karaso ya dan duka yace ga abinki da sauri ta karba ta saka cikin gaggawa suna hada ido yaji wani abu ya tsirga masa cikin jikinsa.
.
Take ya yardewa kansa ya sani matar da zai aura wacce ya dade yana mafarkin samu a zuciyarsa yace lalle kin amsa sunanki na mace ya nisa yace daga dukkan alamu daga makaranta kike ga kuma hadari na haduwa ga kuma ana wuyar mota ko zaki zo na rage miki hanya?ta girgiza kai cikin sauri ta fara tafiya cikin sarsarfa ta fara tafiya ya sake cewa da kin daure kin shigo na rage miki hanya kar ruwan nan ya sauko (hmm wai shin ana abun dole ne?) tayi har da ido tace a'a nace maka na gode Allah zai kawo min motar da zan shiga kafin ruwan ya sauko
bin ta yayi ya ringa mata magiya har ta fara jin haushin sa ta ci gaba da tarar motar ba ko wacce tazo a cike
shi kuma bai daina mata magiyar ta zo ya rage mata hanya ba dole hakan ta hakura ta shiga tsakiyar matar safuwan
cikin matar ba wanda yace da kowa uffan ya juyo yace yan makaranta wacce unguwar zan kaiki?
.
Tace waccan hanyar zaka bi yasa kan motar suka ci gaba da tafiya tace mun zo ya tsaya ta sauka tace masa na gode yace sai yaushe kenan kai!.ta tsallaka kwata ba tare da ta tanka masa ba ta shige gida.ya girgiza kai ya ja motarsa yayi gaba.tayi sallama ta shiga gida ta tarrar da umminta tsaye tana kalllon hanyar kofar gida ta amsa sallamarta tace yanzu nake zancen ki ganin hadarin nan ya taso tace wallahi yau wahalar mota ake ina tsaye a titi tasowar guguwar nan ban sami mota ba
yanzu wani bawan Allah ne ya dame nina zo ya rage min hanya kafin ruwan ya sauko da har naki ganin ban samu bana hakura na shiga ya rage min ( hmmm kaji yaran kirki ba kamar maryam ba uwar son dadi) habiba ta bude baki tace kin shiga mota wani ya rage miki hanya? duk nasihar da nake miki ta tashi a banza shine kika gaya min wani ya rage miki hanya to ba yau kika fara ba ta sassauta murya tace"wallahi ban taba shiga motar wani ba yauma ganin hadari ne in Allah ya yarda bazan sake ba dan Allah kiyi hakuri"
.
Tace mutunci ki nake taya ki karewa tace to ummi afwan tace a wuce a kiyaye gaba tashi kije kiyi abinda zakiyi wanka ta fada bangaren safuwan kuma ko yinin wannan ranar tunanin rufaida ne ya zamo masa abincinsa ya kasa sakat!! bacci ma kasawa yayi sai juye juye yake yi.daga ya rufe idonsa sai ya ganta lokacin da iska ta yaye mata hijab shi komai nata burgeshi yake a haka sulainman amininsa yazo ya same shi suka fita ya akayi yau ban ganka a majalisa ba? yace labari ne dani yace to bani na sha yace wallahi wata tsintuwa nayi akan hanya yace tame? yace wata zukekiyar yarinya nayi arba da ita yace wannan ba irin wadan can bace ina ganin ma auranta zanyi yaja da baya yace aure fa kace? yace kwarai kuwa.
.
yace amma wallahi ka bani mamaki mai ka tsinta a duniyar har zaka tunkaranwa kanka tsofa sai kace wani bagidaje ai mu yanxu muka fara cin duniyar mu da tsinke safuwan yace wai kai yaushe zaka san duniyar nan ba matabbata bace mu fa bana yau bane ya mike yace kaga tafiyata ya rike gefen rigarsa yace to zaka raka ni kona sami wani? yace Allah yakai mu daren yana fita safuwan ya zauna yana tunanin shi daga yau ma ya daina neman mata rufaida ta ishe shi auran ta zaiyi Allah yasa wani bai rigashi ba dan irin su rufaida wawuson su ake.
.
WANE NE MAHAIFIN RUFAIDA?
.
malam nasiru mahaifin rufaida ma'aikacin NEPA ne aiki ne ya kawo shi garin katsina.
haifaffan garin kano ne cikin karamar hukumar gaya cikin wata unguwar kofar gabas shida matarsa habiba.
.
WACE CE HABIBA? WATO MAHAIFIYAR HABIBA
.
ita kuma tana cikin unguwar alawa nan cikin karamar hukumar alawa dake ckin karamar gayan take bayan zaman su a garin gaya ne basu dade da aure ba aka mayar da shi aiki katsina suka koma can da zama .mallam nasiru mutum ne mai kishin matarsa habiba tana da hakuri sosai funanin gaye ne kyawawa ne sosai sun haifi yar su wato rufaida bayan shekaru goma sha takwas ta sake haihuwa ta haifo dan ta wato kamal. (hausan nawa sai a slow)
.

***** DAN ALHAJI 2 *****
.
kwata kwata yayan su biyu ne a duniya wannan shekarar ce rufaida take zana jarabawarta ta fita daga secondary.
motar safuwan taja ta tsaya a kofa gidan su rufaida sulainman ya yamutsa fuske yace ina gidan? safuwan yace gashi nan a fusace ya kalle shi yace wai kai wanni irin mutum ne ka duba matsayinka na DAN ALHAJI amma ka rasa wadda zaka ce kan sai yar talaka ai kwarya tabi kwarya in tabi akusa sai ta fashe" ransa a bace yace kai wai sulainman me yasa kake yawan shiga rayuwata?
.
ita na gani ina so kuma ba wanda zai hanani abunda nake so talaka da mai kudi duk Allah ne yayi su idan ka tashi naka auran ka auro yar karuna ba ruwana ya aika yaro gidan yace kace ana sallama da can ya tuna bai san sunanta ba ya tambayi yaron yarinyan gidan nan yace sunan ta rufaida nidai ita nasani sai kaninta kamal goyansa ake yana shan nono ya dafa kansa yace ka shiga kace ana sallama da ita yaron irin masu surutun nan ne yace inji wa zanceh?
.
suna tsaye jikin mota sai ga malam nasiru nan suka gaisa yace kune masu sallama da rufaida suka amsa da eh ya nuna musu waje suka zauna yace dasu "tasan da zuwanku? suka ce A'a,yace toh a gaskiya bana son ta fara zance yanzu saboda yana so tayi karatu mai zurfi kunga ba'a hada taura biyu a baki" safuwan ya marairaice yace dan Allah baba anyi mana afuwa mu ringa ganinta ko da sau daya ne a sati sulainman ko duk haushin safuwan ya kama shi ganin yadda yake ta zuba magiya.malam nasiru ya nisa yace ba wai na bazan baka auranta bane a'a zancen ne dai bana so yanxu ni din nan dakake gani ba yadda za'ayi nayi wa yata auran da bata so shi dai magiyar yake ta yawa malam nasiru sulainman kamar ya rufe shi da duka sukayi sallama akan nan da kwana biyu su dawo zai yi shawara ya gani haka suka tafi basu ganta ba zuciyar safuwan kamar zata buga shi ko sulainman kuka ne kawai yakeyi dan takaichi suna shiga mota ya hau masifa wallahi ka bani mamaki har ka tsaya wani talaka talak ya ringa wulakan taka.kana wani lallamin sa si kace yar gwal ce nasan ko yar shugaban kasa kake so za'a aura maka ba tare da wani dokoki ba amma ka tsaya wani banza yana hura hanci shi ga mai ya yace ai kasan an ce mai abu sarki shikenan sai kayi ta zuwa ana wulakan ta ka ni ai dan rakiya ne bangare malam nasir ko malam nasir yana shiga gida ya kira ta ya tambayeta tasan wanda yaxo gurinta?
.
da sauri tace bansan shi ba yace baki san shi ba yaxo gurin ki kasan magana tayi yace to koma mene ne ki natsu kisan abinda kike kar ina tufkar dama ta hagu na warwaeewa kinsan ra ayina ina san kici gaba da karatu kenake yiwa gata wataran zaki gani dan yanzu karatun mace yana da mahimmanci sosai ba sai ta dogara da mijina ba sabo da haka ki fitar da duk wani sauraron samari ki tsaya kiyi karatun ki.amma duk da haka tunda naga wannan yaron yanace kuma daga dukkan alamu mutumin kirkine ki sanar da umminki in kina son sa sai ya ringa zuwa dan kin isa zancen amma akula sosai tashi kije safuwan kuwa ya matsu kwana biyu tayi kamar ya jawo kwanakin gani yake sunyi masa nisa haka itama duk da taba soyyaya ba son sa yake mata ziyara lalle yayi sa'a ba irin tsiyar da kawayenta su halima abdullahi basa yi mata akan wulakanta samari da take yi dan kusan duk kwanan duniya indai zata fita sai samari sun biyota taki kula su wasu suyi ta yiwa kawayenta zarya akan suyi musu kanfen a wajenta sulainman abokin safuwan ne tun suna yaranta shima ubansa (kusane) mai kudi ne su a rayuwarsu ta duniya basu san babu ba kudi ne gasu nan kamar banza ba wanda a cikinsu bashi da kamfanin kansa,sama da hudu bnda iyayensu da suke kashe musu kudi kamr kasa tare suke sheke ayar su shi yasa suleman baya son sufuwan yayi aure saboda yasan dole abotar su zata yi nakasu group ne dasu bakwai dukkansu yayan masu kudine wannan yana wane wannan duk mutumin dake zaune a unguwar yasan da zancen su
.
WANENE MAHAIFIN SAFUWAN? alhaji mu'azzam sunan mahaifinsa yana da bala in kudi na gaske kusan in baizo na daya a masu kudi ba bazai wuce na biyu ba Allah ya jarrabe shida da son safuwan ko dashi kadaine yake dashi shiyasa oho! duk abinda yayi gani yake daidaine mutane suna yawan kawo masa tsegumin dan nasa amma sai ya hau fada yana mai cewa ansa wa yaro na ido taya ake so yayi masa so ake ya takura masa shi yasa yake tabargazar sa,
.
su uwa ba harara uba ba kwaba,da wuya mutum ya kalle shi sau daya bai sake ba yawancin abkansa suna ce masa yyai kama da wani mawaki MASARI
yaci gaba da cewa ba wnai abu bane yke tafe dani ba illa tsananin so da kauna da suka yi katutu a cikin birnin zuciyata suka hanani sakat tunda na dora idona a kanki ina fatan zan sami wani gurbi a zuciyarki ko yane kona sami nutsuwa ya kura mata ido tsawon mintuna biyu da wani mayataccen kallo da har sai da yasa taji kunya ta boye idonta cikin mayafi ya sake cewa baki ce komai ba tace to ni mai zance? yac e baki da abinda zaki ce? ta tsaya kiji indai kin yarda da soyyayat kuma kin yi amanana dani to kice I LOVE YOU safuwan (mtsww i love u din banza).




** DAN ALHAJI 3 ***
.
A cikin yan mata ya rinnga yaba wa da hankalin yaudarace kawai wannan yarinyar idonta a bude yake kana ganin kalaman ta kamar wata tsohuwar yar bariki yac e ba haka bne kawai mata masu tattausan lafazi soyya ce mai karfi take shiga tsakanin su a kullum sulainman na zuga shi mai zaiyi da yar talaka,dayaga abin bana wasa bane sai da yasan yadda yayi Alhaji muaz yasan zancen zai auri yar talaka sanin halin alhaji muaz na kin hurda da talakawa ko kadan baya son ya rabe shi ya dinga fada ya zubawa idonsa toka tun da yake bai taba yiwa safuwan fada ba sai karonnan ran safuwan ya baci yace shi ita yake so ya ko haukansa ta inda ya shiga batanan yake fita ba yace kaje ka dubo ko yar wa kake so ka aura zan aura ma,
.
safuwan yayi buris da maganar yaci gaba da zuwa gurin rufaida yasa a gaba yana ta wallafo masa illolin zama da talaka kuma ya dauki alkawarin in dai ya rabu da yarinyar nan zai kara masa wasu kanfanoni annan ne HAJIYA BILKI yar katsina wan asali kenan ga kunya ga kara haba yallabai kabar yaro ya auri wacce yake so talaka da mai kudi duk Allah ne ya haliccesu kuma ba wanda yasan wada yafi mu lokacin da mukayi aure kana dashine? da na sha yasar da kayan dakina ina mana abinci na kuma sha kwana da yini anan fa yace ina wuta ya sakata?
.
ya ringa fada wai tayi masa gori a gaban yaro itama ta daka ta tashi ba wanda ya saurara a ranar dai rai ya baci sosai dan sai da hajiya tayi masa fushi sosai wato yajin aiki ya rasa yadda zai sha kanta gashi baya son bacin ran ta kona miskala zarratin amma yana ganinin indai akan ya hakura safuwan ya auri yar talaka ne sai dai ko wacce wacce.haka sabani ya ringa shiga tsakanin su har sai da aminiyar ta hajiya jamila ta ringa tausar ta akan ta rabu dashi dan zamanine hajiya bilki tace baki san halin yallaban ba yana da bala'in taurin kai nima dakika ga muna zaune lafiya dan ni dince ta makaryaci kinsan dai komai yanzu ma wani lokacin birkicewa yake yi wai shi aure zai kara yana son karawa safuwan yar uwa tunda naki haifuwa kinji fa kamar ni nake bawa kaina ni yanzu na zubawa sarautar Allah ido kowa dai ya hau kujerar naki,a majalisa su sai zuga shi suke wai kar ya aure ta tunda abbansa baya so kawai yasan hanyar da zai yi ya yaudareta ya nuna musu sam shi auranta zaiyi nina daina hurda da ko wacce yarinya najashi cikin zolaya nace har tima yace koma wace ce suka hau dariya gaba dayansu yanzu kam kusan ace tunda ya hadu da rufaida ya daina kula ko wacce yarinya sai dai abin da ba'a rasawa dan abin ko rawa shima din ya yi bala'in ragewa yana kuma ganin da zarar ya aureta zai de na gaba daya su kuma sun kudirin niyar ko ta halin kaka bazai aure taba jarabawa ta fito gaba daya rufaida tayi passing malam nasiru yayi murna sosai ya ringa sa mata albarka habiba ko baki yaki rufuwa saboda murna bayan tayi wanka ta huta ta dauki waya ta sana da safuwan shima yayi farin cikin yace aina dauka baZa ki sanar dani ba ai labari ya iso min tun dazun a hanya naci karo da lubabatu suke bani labari
.
duk makarantar keda bahijja kun zarce kowa.ina mika sakon murna kafin nazo har gida sai dai ina ganin ya kamata mu shirya wani dan kwarya kwaryan party na taya ki murna tace a'a na gode abba bazai yadda ba su bahijja basun gaya maka munyi daxun a makaranta ba? ai ya isa wani haddan mota ya shiga ya wuce yayi mata siyyaya ya hada kaya kamar hauka dan sai daya cika motar da kaya atamfofi da dai sauran kaya basai na tsaya ina ir gosu ba da dai duk masu azabar tsada sai kuma bangaren takalma da gyalluluka da yan kunnaye fashion dasarkoki har dana gold yayi parking motar a kofar gidansu yara suka ringa shigar dasu daga habiba har rufaida ba wanda bai tsorata ba suka ce kai ku tsaya ba nan gidan aka ceku kawo ba wanan ai kayan masu kudine suka ce a'a nan aka ce mu kawo da yake sun san shi mutum ne mai kyauta kusan duk yaran layin suka ce safuwan ne fa yace mukawo umminta tace maza ku mayar ke kuma dauki gyalenki kije kice kin gode ya ajiye yi azama kafin abbanki ya dawo bake ba har ni sai ta shafa ganin yara yayi sunyi kaya niki niki suna dawowa dasu ya dubeta yace meye haka?
.
tace kabari ba yanzu ba yace wannan wacce irin magana ce? a fusace yake maganar duk abinda na baki sai kice kin gode kiki karba to wallahi ina tantama akan so da kika ce kina min itama ta fusata tace ai dama ba abinka nake so ba kai....bata karasa ba ya kwallawa yaran kira yace kowa ya dauki abinda yake so ya kai gida" suka tsaya tsororo suna mamaki.
.
yadaka musu ts
awa yace ba da kunake ba nan da nan suka sawa kayan warwaso kowa yayi gida da abinda ya samu yana murna yakai wa uwarsa ita ko kafin yaran su karasa ta shige gida ya shiga matarsa ya hada wata yar karamar guguwa yayi ficewarsa daga layin,tana shiga gida ta fada kan cinyan umminta tana kuka habiba tace lafiya ? tace yayi fushi ransa ya bace sosai tace gwara hakan dan wallahi abbanki yaga wannan kayan raina in ya kai dubu sai ya baci.
.
*** DAN ALHAJI 4 ***
.
Baci dama tunda ya fara ja miki kunne na gaya miki karki yarda kikar kwandalarsa kuma na gaya miki tuntuni kwana da kwanaki bashi ba dallilin sa sati wajen uku kenan amma fa duk da haka hankalinsa na kanta tsabar zuciyace irin tasa son ta da kaunarsa yana nann daram a ransa abin sai dai ya karu itama hankalinta na kanshi itama dai tata zuciyar na mata yadda taba shi hakuri asalima tana ganin ba abinda tayi masa dole ne tabi umurnin iyayenta dan bata da kamar su duk ta damu kanta abbanta ya tambayeta cewa bata jin dadine?
.
ita koh habiba tasan akan rashin zuwan safuwanne tayi banza da ita ko tambayarta mai ya dameta bata yiba kowa ya ganshi yasan ya rame kullum zuciyarsa kamar ta fashe da yaga abin na neman tarwatsa masa zuciya waya ya dauka ya kira ta cikin sanyi murya tace "HELLO"! yace ke baki san ki yiwa mutum laifi baki bashi hakuri sai kawai ki share ni tace kai baka gane ba bani da wani laifi bacin ran iyaye na nake gudu dan ban son bacin ransu kokadan.{hmmm matan kwarai kenan amma banda na zamani}
.
maganar ta doki zuciyarsa sosai yace shikenan sankin ganni gobe tace Allah ya kaimu bai masa ba ya kashe wayar hannun yasa ya dafa kumatunsa yana tunanin maganar data gaya masa jikinsa yayi sanyi yace laalle wanan yarinyar wato dole ta guji bacin ran ubanta amma ni akanta na sakawa nawa iyayen bacin ran a kanta na dauke kafana daga gidanmu sai alhaji ya tau tsawon kwana bakwai bai sani a idonsa ba idan abin ya dameshi sai dai ya kirawoni a waya shima dakyar nake amsa maganar sa duk saboda ita zuciyata ta ringa zuga shi kawai ya dauki shawarar abokanansa idan kuma ya tuna da son da yake mata sai yaga hakan bai dace ba gwara ya bari ta zama mallakin sa yayi niyar ya share ta kar ya kuma zuwa gurin ta hakan ta faskara,
.
daukar mota sa yayi ya ratsa ta majalisa anan ma sun yaudare shi ya ki,ya zare jikinsa yace to zan tafi wajen ginbiya yana bala'in basu mamaki da shagala irin ta DAN ALHAJI yanzu yarinya karama ta dauke masa hankalinsa yafi tsohon minti goma bai sami yaron da zai aikaba yana daga idonsa suka hada ido da ita ta fito daga kusa da gidansu da kamal a hanninta yana kuka kayanda tsa sunyi mata kyau shirt da riga nena material ta yafa dan kwali a kanta ganin safuwan taji gaba daya gabanta ya fadi ba karamin dadi tajiba bata bari yagane ba fuskarta ba yabo ba fallasa ya mika hannu ya karbi kamal ya sake barkewa da kuka yamika shi tasa hannu zata karbe shi dan kwalinta ya sullube sakar baki yayi yana kallon gashinta har baya bashi da maraba dana india gashi rigar tayi bala'in fito da suran jiikinta haba ganin hakan yasa shi ya direrece ta lura da hakan tayi sauri ta shige gida har ta dawo sam bai san tana tsaye ba ya shiga duniyar tunani.sai da ta dan daki murfin motar sannan yayi firgit tace tunananin mai kakeyi haka?
.
yayi murmushi yace tunanin naya wuce naki na ga kin zama mallakina tace kar ka sami damuwa insha Allahu kamar yaune haka sukayi ta hiransu cikin faranta zuciya a hanyarsa ta zuwa gida ba abinda yake illa tunanin surar da Allah ya bata a gaskiya gani yake idan ya sameta yafi kowa sa'a ya buge siteri yace ai ni indai na sami wanan yarinyar ba kuma wata yarinyar da zata bani sa'awa a rayuwata wani tunani ya fado masa sai daya ji bugun zuciya wani tsoro ya bayyana a fuskarsa tunawa yayi anya mallam nasiru zai bashi yarsa idan yayi bincike ya gano halinsa dana mahaifinsa na kin talakawa idan ko ta bincike ne a gaskiya bazan sameta ba a halin irin na mahaifinta mai ra'ayin rikau saboda duk wanda ya kwana ya tashi cikin unguwarsu ba wanda bai san tabargazar da sukayi da shi da abokinsa ga kuma halin da yake ciki shi da alhaji har yanzu yana kan bakarsa ta bai yarda ya aureta ba ko jiya sai daya dada jadda masa akn ya samo ko yar wacece indai ya amsa sunansa na mai kudi yanuna masa indai bai aureta ba zai iya shiga wani halin tatshin hankali yana gama wannan tunanin duk saiya ji ransa ya baci ji yake kamar zuciyarsa zata fashe ta warwatse gaba daya a daddafe ya ringa tukin har yazo gida d kyar yana shiga cikin gidansa firiji ya zarce ya bude ya dauko kwalban barasarsa bai tsaya tsiyayawa ba kwalbar ya daga ya tittila a cikinsa sai da ya tabbatar da ba komai a cikin kwalbar sanan ya jefar ya samu waje ya zauna idonsa ya kada yayi jajawur saboda tsabar bacin rai.
*** DAN ALHAJI 5 ***
.
ya saka wata kara yace DAN ALHAJI kace ka komo ruwa kenan? yace tsindim dan jiya zuwa yau tima ta shayar dani da. suka bushe da dariya" safuwan yace inna son ganinka akwai magana yace gani nan zuwa dama ina kan hanya zuwa gidan ke neni da mubashar suna gama wayar sulaiman ya daki kujera yace waya ce maka ana yiwa bariki fitar gaggawa mubashar yace DAN ALHAJI kenan, sulainman aa guje ya fada kan DAN ALHAJI yana cewa WELCOME TO BARIKI (Allah ya sawwaka dai) safuwan ya saki wata wawar dariya yace aini yanzu na zama bokan bariki yau wata goma dai na barta firij ya nufa ya balle kwalba ya tuntula safuwan yace ba'ayi bani ba mikomin haka dai suka ta yin kayan shirme shirme , mubarshi yace ya mutumiyar safuwan?
.
yace tananan da ai a kanta nake cewa zamuyi wata muhimmiyar magana ni fa ina ganin aurena da ita ba mai yuyuwa abne sulainman ya karkata hula ya ce kai kace kai da kan ka mutu ka raba kai da ita ku shawota can kai da ita kai da nasan iskancinka baka rabo da halin ka ka tsya muyi magana ya kakr gani yanzu za'ayi yace wannan maganar da muka gaya maka a majalisa itace abinyi ya nisa yace nifa yarinyar kwarjini takeyi min kasan duk tsawon lokacin da mukayi ban taba tabata ba ko da hannunta ba kuma kasan ban taba sati da yarinya ban san taba.a gaskiya ina son yarinyar dan haka bana son taba mata rayuwa tace to dan gidan rufaida ai ka zuba ido kanta kana kallonta kana hadiyar yau kana gani wani zai zo

Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2Chapter 3

Please Login or Register in order to submit comment