Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

card ta wannan Numbobi 08081202932*




Da ido Hajiya Turai ta raka shi , yayin da a zuciyar ta take faɗin " Wannan wacce irin musiba ce ,wannan baƙin Zuciya haka? Tun da nake a tarihin Rayuwa ban taɓa ganin fitinanne mai shegen zuciya irin Umair ba, tun yana yaro idan yaso Abu to a bashi kawai ,idan kuma ba'a bashi ba shi zai san duk yanda zaiyi ya samu . Ɗan tsuwa ta ja a hankali ,kana a sarari ta furta " Umaima zata lalata mun komai na shiri na , banda iskanci ga yanda muka yi dake , sai Kice kina da wanda kike So.! Hauka tayi ne???. Jin Muryar Ammie na rarrashin Umaiman daga ciki yasa Hajiya Turai kutsa kai tana shigewa daga ciki ita ma. Ammie kam sai rarrashin Umaima take , don Umaima ta gama tsorata da lamarin Umair , wato shi ba zai taɓa sauyawa ba? Bai san yaya ake rarrashi da ban haƙuri ba ,koda kuwa shi ne da laifi akan komai . Surayya ne ta buɗe baki tana cewa " Umaima kiyi haƙuri , Don ALLAH ki zauna da Yah Umair , Kin san a yanzu kece koman sa kaman yanda yace ,kece zaki controling nasa , kin san gargagarar halin da ya shiga sanadiyar rashin ki a tare dashi . Pls Umaima kiyi Haƙuri ki zauna tare da Yah Umair ... To ya na iya?? Hakan nan zan zauna dashi tun da ya riga ya zama miji na..! Ƙare maganan tayi tana sakin marayar kuka mai ban tausayi , a hankali take tunanin a zuciyar ta , don da fari cewa take Umair ya koma tamkar sauran maza babu wannan maganan a gadaran ce . Ashe ina har yanzu ba sauyawa yayi ba . Haka ake So? Tambayar da take mawa kan ta kenan ,kana tace " Wannan bashi ne So ba , sai da Haukan So . Dafata Da Ammie tayi ne yasata firgigi tana dawowa hayyacin ta ,Muryar Ammie ne taji tana ce mata" Umaima kiyi haƙuri Kinji , kin san halin Umair ba bu mai lanƙwasa sa shi.... Maslaha ɗaya Ammie gare ta shine ta daina Kula kowani namiji , ai Ya Umair shine mijin ta bai dace tana kula wasu ba ,don nasan duk wanda zaki kula basu kai ƙyau da nagartar Yah Umair ba. Hamdala ya kamata kiyi ki gode mawa ALLAH da har namiji Ajin farko kaman yaya Umair ya ce yana Son ki. Fareesat ce mai wannan maganan a gadarance. Sunkuyar da Kai Umaima tayi don dama tuni ta fahimta wacece Fareesa ,Sam bata da kirki , ita a Son Ranta ma Umair ba zai zauna da Umaima ba . A cewan ta yayi baya ,kaman shi ya rasa wanda zai aura sai dangin ƙasƙantattu talakawa... Wani irin Kallo Ammie ta watsa mawa Fareesat wanda yasa ta tasha jinin jikin ta . Juyawa tayi tana sa ƙafa tare da ficewa daga Bedroom ɗin . A hankali Surayya ta sauka tana bin bayan ta ...


****




Ɓangaren Umair kuwa yana fita a falo ya tadda Daddy Kaman yanda ya barshi . Zubewa yayi gwiwowin sa ƙasa gaban Daddy Hankalin da tashe yake roƙon sa akan cewar kar a raba shi da matar shi ...Amma Daddy sai yayi ruwa yayi tsaki wurin cewa " Abun da Umaima take so ,shi zaiyi mata ,itama tamkar ƴace a gareshi ba zai mata dole akan Abun da bata So ba . Yana gama faɗa masa haka ya tashi yana kakkaɓe babbar rigar sa ya bar Umair anan . Dafe kan sa yayi da yake sara masa . Kusan mintuna biyar yana a haka ,kana ya miƙe cikin ganin jiri yana barin falon tare da nufar farfajiyar gidan moton sa ya shiga yana mata key tare da ɗaukar hanya yana barin gidan .




***




Surayya ne ta biyo bayan Fareesat , a falo suka tsaya Surayya tana bin Fareesat da wani irin kallo na ba ta ji daɗin Abun da tayi ba. Ke Fareesat wannan meye kika yi kenan? Ya wa'annan kalamin zai dingi fitowa daga bakin ki? Ke ma fa macace?? Kuma sanin kan ki ne Abun da Ya Umair yayi bai kyauta ba. Ya cutar da Rayuwar ....Don ALLAH ya isa.! Cewan Fareesa tana ƙwatse Surayya cikin sauri. Dama ke ai na daɗe da fahimtar baki da kishin naki. Kina gani ba fa ,a gaban idon kowa ta nuna tana da wanda take So ba Ya Umair ba , Wato shi zuciyar shi tayi bindiga ta fashe kenan ?. To wallahi ta ALLAH ba nata ba . Zata ga Ya Umair ya rayu ,kuma Inshaallh sai ya cireta ya goge ta a tarihin Rayuwar sa ,sai ta Auri wanda take so. Ina banda So makaho ne ,har ita ajin Auren Ya Umair ne ,ai ya fita tamkar sama da ƙasa don ko a ƴar Aikin gidan sa ba zai ɗauke ta ba . To kuma dai a hakan ya ganta ya kuma ji yana Son ta sai akayi yaya??? Ban sani ba. Fareesa tace ga Surayya cike da tsiwa. Surayya ne ta kalleta tana cewa " Kin san dai Hali na , wlllh yanzu kika mun na daka ki ,na dake banza . Dariya Fareesat tayi kana tace To bismillah , wai duk akan waccen Banzan ne kike shirin duka na? To ai gani . Girgiza kai Surayya tayi tana juyawa tare da barin Fareesa tsaye tana cigaba da rashin kunyar ta .


***




Kusan Mintuna talatin Ammie ta ɗauka tana rarrashin Umaima kana daga bisani tayi masu sallama tana fitowa tare da zummar Tafiya . Hajiya Turai ne tayi masu rakiya har zuwa farfajiyar gida ,don a wannan karon har da Fareesat aka shirya Za'a tafi , a cewan ta zata je ta rarrashi Yayan nata ya cire soyayyar Umaima a zuciyar shi. Ya nemi dai dai shi ba ita dangin talakawa ba .! Tun da Ammie ta fita Umaima ke zaune tana tunanin kalaman Ammie n , A hankali a zuciyar ta ta furta" Ina ma Umair ya biyo halin Ammie? Amma shi komai a gadara da miskilanci yake yin shi . Ɗan tsaki ta ja tana faɗin mugu kawai. Wallahi ba zan zauna da kai ba , a wancen j
Karon kwana biyu ne ana uku nayi da kai ,Kabi ka gama wargaza mun Rayuwa , kullum baka da aiki sai na saduwa , kayi mun Rauni ba kaɗan in just 3 days , Ina ga kuma yanzu ace maka Ni na zama taka har abada .? Gaskiya bazan iya ba ,Ni tsoro ma nakeji , sunan kayi na dama ne ,amma Ni ban haƙura akan Abun da kamun ba.! Murɗo Handle door ɗin Hajiya Turai tayi tare da takowa tana isowa zuwa inda Umaima take zaune . Umaima wannan wani irin shashanci ne??? Ya zaki ce kina da Wanda kike so? Ahir kar na ƙara ji ,kisa A ran ki Umair ne mijin ki bayan shi babu wani ,wannan ai sakarci ne ma. Kina sane da abun da zamu yi. Dole kece wacce zaki cika mun burina a kan Umair , tun da tun tasowar shi bai ɗauke Ni a uwa ba,sai Dai Hajiya Maryam . Don haka kisani Ko da Daddy ya tambaye ki , Kice kin yafe masa zaki zauna dashi a matsayin miji . Komai nasa sai naga bayan sa sannan idan na rabuwar Auren ne kuyi.




Kallon ta Umaima tayi tana mmkin meye Umair yayi mata hakan? Sai kuma ta yi shiru tana nazarin wannan wani irin hali ne Hajiya Turai ke dashi ?. Muryar Hajiya Turai taji tana cewa " Idan kuma ba zaki iya ba , zan nemo wanda zasu yi mun aikin na biya su . A'a Momy zan yi , Ni mene damuwa na a ciki ,kawai dai na tsane sa . Murmushin jin daɗi Hajiya Turai tayi kana tace " Haka nake son ji. Kema sai ki ɗau fansar abun da yayi maki. A satin Nan zan shirya komai na tarewan ki a gidan Umair . Shiru Umaima tayi kamun daga bisani tace to .


***




Da misalin ƙarfe 7:00am ne , Umaima dake ƙwance a gadon ta ,tun da ta tashi da Asalatu ta gama sallolin ta ta kasa rintsawa ,maganganun Hajiya Turai suke mata yawo a ƙwaƙwalwa . Ji tayi ana buga mata ƙofa ,sai kuma Muryar Hajiya Turai da taji tana magana ƙasa ƙasa amma bata san da waye take yi ba...A hankali ta sauko da ƙafafuwan ta ƙasa tana nufar ƙofar tare da zare key ɗin tana buɗe wa ... Saurin baya tayi ganin Umair tsaye wanda bata yi tsammanin ganin sa da wannan safiyar ba....Ya Umair me kuma ka zo yi?? Ba bata amsa ba sai kutso kan sa da yayi cikin Bedroom . Tsayawa tayi tana kallon Hajiya Turai da itama ita take kallo ,kana tayi saurin bin bayan sa tare da maimaita tambayar ta , Yah Umair me ya kawo ka da wannan sanyin Safiyar? Laifi ne don miji ya zo ya duba matar sa..?










*MMN TEDDY*
*Littafin the sexxy boss na kuɗi ,duk wanda ya karanta bai biyani ba ALLAH ya isa.! Regular group₦300... VIP group₦500...SPC ₦1000 via 6037312299 Mohammed Aisha keystone bank ko ki turo da MTN card ta wannan Numbobi 08081202932*






Tsayawa Umaima tayi sororo tana kallon ikon ALLAH , to wannan me ma zata kira abun da yake mata rainin hankali ko mulkin mallaka?. Shiru tayi ba tare da ta tanka shi ba , Muryar sa ne ya kuma katse ta tana kallon Hajiya Turai itama da ta tsaya tana kallon Yanda Umair ke masu mulkin mallaka ,tun da take dashi bai tabo wuto ko ina na falon ta ya shigo har ƙurya haka ba. Maganan tasa ce ta kuma katse su yana cewa " Momy wai Haka kika ba ƴar taki Tarbiyya? Yayi maganan yana kallon Hajiya Turai da ta rasa bakin magana ,duk iya karya lafazi nata ,yau dai ta kasa ko tanƙwara kalma ɗaya ,don tayi amfani dashi wurin masa magana gaba ɗaya ya cika mata ido ƙwarjini yake mata tun ba yau ba . Taho ki gaishe da mijin ki .! Yayi maganan yana yafito Umaima da hannun sa. ganin ta tsaya bata motsa ba sai raba ido take ta kalle shi ta kalli Hajiya Turai ne ya saki murmushi mai ɗan sauti kana yace " Ni mijin ki ai na yi maki Tarbiyya... Kallon sa Umaima tayi tana cuno bakin ta tare da cewa " A'a nifa ba kai ka bani tarbiyya ba , ka ganni da haƙora na talatin kace kai ka bani tarbiyya ?. Iyaye na suka suka yi mun komai a rayuwa , su suka bani tarbiyya tare da nuna mun abubuwa da yawa wanda yin su da aikata su yake babban zunubi , tun a duniya mai aika ta su ,yake ganin Sakamako . Na ɗaya shine Zina, na biyu shan giya da duk wani Abu da zai gusar mawa bawa daga tunanin sa . Ni iyaye na sun....Keeee da wa kike wannan maganan?. Yayi maganan cikin daka mata tsawa ,wanda sai da Hajiya Turai tayi saurin kama hannun Umaima . Idon ta ta zuba akan nasa , duk da taji tsoron sa ,amma sai ta dake tana kallon sa tare da cigaba da cewa " Ai kai ka bukaci nayi wannan maganan ,kuma naga duka tunatarwa ne , bance da kai nake yi ba. Umaima ..! Ya kira sunan ta irin na mamaki , da kuma yaushe har ta iya yayi magana ta basa amsa kan ta tsaye babu tsoro haka . Tun da yake a rayuwar sa bai taɓa haɗuwa da wata mace ta fuskance shi ido cikin ido tana watsa masa maganganu irin haka ba .




Ni kike faɗa mawa Wannan maganganun? Kallon sa tayi kana tace " To Sir Umair yi hakuri naga wannan ai duk tunatarwa ne?. Sir Umair??. Ni kike kira da wannan sunan? Meye matsayin ki a wuri na? Ni mijin ki ne ,ki Kirani da sunan da zai sa inji daɗi a zuciya ta .




Wani irin kallo ta watsa mashi ,idon ta na ciko da ƙwallah , sai hawaye sharrrrrr³ , ganin yanda Take xubda hawayen taana sauke ajiyar zuciya , wannan ya nunar she shi ,ko a juya tayi kuka har ta gode Allah. Ya Umair Me yasa ba zaka sauya ba? Abun da take faɗi kenan a zuciyar ta a sarari kuma jifan shi take da kallon dake nuna tsantsan tsana da ƙiyayyya . Ina Son ki ,kuma kema dole ki Soni.! Yayi maganan yana takowa zuwa inda take . Wannan shine maganan da kayi mun tun da fari . Amma kuma kai yaci ace ka ƙaryata kan ka ,tun da ba na Son Ka har yanzu . Kallon ta yayi yana sa hannayen sa biyu tare da tallabo kuncin ta ,idon ta ya ƙura ma ido yana kallon ta .kamin yace " Ƙarya kike ga So na nan ina gani a idon ki .! Umaima kina Sona, Bama So kaɗai ba...Fuzgar kan ta tayi daga garesa tana cewa " A haka zan So ka? Ka kasance mazinaci, Mashayi , wanda har duniya an yi maka shaidar Shaye² .na haɗa zuri'a da kai me ƴaƴan da zamu haifa idan suka tashi zamu ce masu ?. Nan da nan fa.....maganan nata ne ya sarƙe tana sakin kuka tare da sa taffan ta tana rufe bakin ta . Sorry Yah Umair , baxan Zauna da kai ba . Ban san mene zan faɗawa yara na ,baxaka sauya ba . Ba zaka daina abubuwan da kake yi ba . Nan a gidan muna zaune da Momy muke gani a news ake watsa labaran ka , na tayatar da ka amsa a ƙwalɓe , da kuma lalata sunan Ƴan uwan ka likitoci ... Ni dai a'a ya Umair ka sauya tukuna .




Jah baya yayi yana kallon yanda take xubda hawaye , a hankali yake motsa hannun sa , Jikin sa gaba ɗaya yayi sanyi , a Rayuwar sa abu ɗaya ya tsana shine ya bude ido yaga Umaima a cikin wannan hali ... Umaima wannan wani irin magana kike ? Hajiya Turai tayi maganan cike da rashin jin dadin maganganun ta , a ganin ta kar Umair ya fusata abubuwa su dagule .




Kamin Umaima tayi magana ne , ta ji Muryar Umair yana cewa " Momy zanyi magana da matata. Saurin ware idanun ta Umaima tayi ,Kana tace " Me kake nufi to??. Kamin yyi magana ne Hajiya Turai tayi saurin cewa ' A'a bari na baku wuri . Momy babu inda zaki je , Kasan wacece wannan kuwa?. Na sani , yayi maganan yana kallon idanun ta . Haɗa ido sukayi nan ya daga mata gira yana cewa " Yass nasani Yayar Umman ki ce ,wacce take uwa gare ki. To ka sani kake wannan maganganun ? To babu inda zata je . A'a bari dai na fita. Cikin Muryar Kuka Umaima ne ta kuma kwatse shi da cewa " A'a Momy babu inda zaki . Kamin ta rufe baki ita dai taji ya rungume ta ne yana haɗe bakin sa da nata , wani irin hot kissing yakeyi mata , wanda jikin Umaima ne ya hau rawa so take ta ƙwace kan ta daga gare shi ,amma ya rungume ta ƙammm a tare da shi . Juyawa Hajiya Turai tayi da sauri tana fichewa daga ɗakin. Tafe take tana sambatun da bata sani ba tana cewa ' Oh Ni Turai Ni naga Zamani?? Shi yasa yace na basu wuri , wannan tacewa da mai yayi kama???. Naam Hajiya magana kike yi?? Muryar ƴar Aikin ta taji ,wannan yasata farga ashe a sarari take maganan . A'a zubaida ba dake nake ba. Wuce yar aikin tayi cikin sauri tana nufa falon ta. Itako Zubaida da ido ta rakata a zuciyar ta tana cewa " Yau Hajiya Lafiya kuwa ?.






Kusan mintuna biyu da sakanni suka ɗebe yana tsotsan bakin ta ,kana ya shagala ƙwarai ya saki jikin sa a natse yana Kissing ɗin labɓan ta tayi saurin janye kan ta tana yin baya , tare da cewa " A'a Umair... Shiiiii yayi saurin sa yatsar sa a laɓban ta ,hannun sa ɗaya ya riƙo nata , bin sa da kallo take tare da cigaba da xubda hawaye . A hankali taga ya sa gwiwowin sa a ƙasa yana kallon ta cikin Muryar karaya da ladabtawa tamkar yana gaban na gaba dashi .Umaima faɗa mun abubuwan da kike so na daina daga yau nayi miki alƙawarin dai nasu. Na bar shan barasa ,na bar shan sigari ,haka na daina Sex da kowacce mace sai ke kadai mata na... faɗa mun abubuwan da kike kuma son na daina yin su zan daina badon komai ba saboda ke...!




Aƙwai supliment masu ƙyau da inganci babu illa ,muna sayar da na breast da kuma na hip up. Aƙwai na ƙiba , da kuma na hasken fata mai ƙyau ba na bliching ba. Ga masu buƙatar ƙarin bayani You can chart me up .


*MMN TEDDY*
*08081202932*
*Littafin the sexxy boss na kuɗi ,duk wanda ya karanta bai biyani ba ALLAH ya isa.! Regular group₦300... VIP group₦500...SPC ₦1000 via 6037312299 Mohammed Aisha keystone bank ko ki turo da MTN card ta wannan Numbobi 08081202932*








***






_Kuyi manage da posting yau , wallahi mun koma school ,next week kuma zamu yi resuming work, kunga yanzu sai kuna haƙuri da posting babu yawa,Amma a hakan zan rinƙa ƙoƙarin yi mana sau biyu , ko zuwa can dare zana rinƙa maku night update in Sha ALLAH.!_




"Kallon sa Umaima ta tsaya yi kaman maitantaman wani abu na daban kamin cikin sanyin murya tace " Ni ai ba tawa rayuwar ka gyara ba naka ne?. Idan ka daina duk abubuwan da ka faɗi zaka daina alhmdllh shine Abun da zana ce. A matsayin ki nawa kenan a guri na? Yayi maganan yana zuba mata lulun idanun sa . Shiru tayi tana murza ƴan yatsun ta kana daga bisani tace" Ai ni kasan daiii...Pls Umaima ki yafe mun , wallahi tun bayan rabuwa na dake na daina mu'amala da kowacce ƴa mace. Kawai dai abun da nasan ina cigaba da aika tawa shine shan barasa na . Kuma daga yau na daina . Bana komai yanzu ki sa na bar wannan duk abun da kika san ina yi. Pls Umaima ki zauna dani Muyi rayuwa mu haife yaran mu masu kama dake. Kunya ne ya kamata saurin ƙasa tayi da idanun ta da kallon sa tana murmushi , hannun ta ya kama yana miƙewa daga tgurfanan da yayi gaban ta . Murmushi shima yake wanda rabon da yayi irin wannan sanyayyar murmushi ya manta . Kallon sa tayi cikin sauri tana zame hannun ta , tare da cewa " Kar Momy ta shigo ta gan mu ...Aaa ke ba mata na bace ba? Ai wuri ta bamu. Saurin fiddo da idanun ta tayi waje na mmkin tare da jin nauyin furucin nasa ,kana ta juya da sauri tana ficewa daga Bedroom din . Murmushi Umair yayi yana sa hannayen sa sama tare da godiya ga ALLAH da ya nuna masa mafarkin sa a zahiri , hamdala yayi yana biyo bayan ta . A dirning Area ya tadda Hajiya Turai da Umaima da ta amshe ta aikin tana taya ta hidimar haɗin karin kumallo .




A'a Umair Har ka fito?. Hajiya Turai tayi maganan cike da fara'a . Saurin kallon Ta Umaima tayi kana ta juya suna haɗa ido da Umair . Ɗaga mata gira yayi yana murmushi ,bai damu da Hajiya Turai dake gaban sa ba. Saurin kauda kan ta Umaima tayi tana cigaba da gyara zaman wani babban bowl dake akan Dirning table ɗin . Hajiya Turai ne ta cigaba da cewa " Ai baka tafi ba , don yanzu nake haɗa maka break nasan bakayi ba a gida ka fito . Murmushi yayi yana cewa ' Momy sauri nake yi yanzu haka zan wuce Lagos ne wani aikin ujula ya kamani ,shi yasa nazo nayi sallama da Matana . Eyyaaa kuma bata faɗa mun wai tafiya zaka yi ba. Cewan Hajiya Turai tana juyawa tare da kallon Umaima da itama batasan wai tafiya zaiyi zuwa wani wurin ba .




Murmushi yayi har hushiryar sa na bayyana kana yace "itama ai taki tsayawa ta saurari abun da ya kawo Ni ,guduwa ma tayi ta bar Ni kaɗai . Murmushin yaƙe Hajiya Turai tayi kana tace " To ai shikenan Allah ya kaiku lafiya . Ammm Momy don ALLAH kimun wani ƙoƙari mana kamin dawo. Kallon Sa Hjy Turai tayi cike da mmkin yanda ya tausasa lafazin sa kana tace " Ƙoƙarin mene ne Umair??.




Don ALLAH Momy kisan yanda za'a yi kamin na dawo a maida Umaima gida na , Ni nayi magana da Ammie ko a gida na nan Abuja zan zauna na hakura da zaman Lagos ɗin . Ki shawo kan Daddy ya amince . Murmushi Hajiya Turai tayi tana ƙara faɗaɗa Fara'a kana tace " In Sha Allah Umair zaka dawo ,ko Umaima bata tare ba ,tana gab. Thknyou . Yayi maganan tare da Kallon gyefen da Umaima take ita dai tayi shiru tana faɗawa tunanin rayuwar su idan ya kasance daga ita sai Umair ɗin ..wani irin gwagwatuwa zatayi a hannun sa .




Zo ki mun rakiya.! Taji Muryar sa ya katse ta , amm...Tsayawa tayi tana kame kame don tana tsoron bin sa , bata san me kuma zai mata a farfajiyar gidan ba a gaban ma'aikata , don bai ji kunyar Hajiya Turai ba , inaga kuma sauran ma'aikata da baya ganin su a bakin bakin komai . Hajiya Turai ne ta katse su da cewa " Aaaa Umaima raka sa mana ? Mijin ki kuma zai wuce kin kasa masa Rakiya . Ɗago da idanun ta tayi kawai sai ƙwallah ya ciko idanun ta suna dab da zubowa . Saurin cewa Umair yayi " A'a mom ta bar shi kawai sai na dawo.! Yana maganan ya fice daga falon . Bin ta da Kallo Hajiya Turai tayi ,kamin tace " Meke damunki ne Umaima??. Shiru Umaima tayi tana sada kan ta ƙasa ,tare da cewa " Ba komai . Ohk kina ji ,nasan ba Son Umair kike ba , ki sa a Ranki zaman da zaki yi dashi na ɗan lokaci ne ba mai ɗorewa ba Kinji Baby na.! Murmushi Umaima tayi tana jan kujera tare da cewa " Mom Bara na fara breakfast . Alright . Abun da Hajiya Turai tace kenan tana juyawa tare da nufar Kitchen. cookies Ta fara kaiwa bakin ta , amma sam bata jin daɗin abincin nata ,wannan yasa Umaima turewa gyefe tana ɗaukar tea cup tare da sa spoon tana juyawa , shiru tayi tana tunanin abubuwa da yawa dangane da Hajiya Turai akan Umair . Me yasa Momy bata Son Ya Umair da alheri? Me yayi mata ne?? Dole ina Son sani. Sauke ajiyar zuciya tayi tare da kai cup din bakin ta tana shan tea ɗin kaɗan tare da saukewa . Tun da na sauya Ya Umair itama in Sha ALLAH zan sauya Momy ta koma tamkar sauran iyaye mata masu fatan alheri da kowa , bazan iya cutar da Umair ba , Saboda Ni kaina nasan ina Son sa a zuciya ta ,tun ban san So ba nake Son ya Umair , har daga ƙarshe na yarda da cewa Zuciyata ta kamu da Son Umair . ALHMDLLH da sauyin da Allah yayi mun ina sake godiya. Wayar ta ce tayi ƙara dubawa tayi kirar Fa'iza ne kusan sau goma sha Ciki har dana Fahad.




Mikewa Tayi daga dirning Area tana nufar Bedroom din ta . A hankali ta fara shafa wayar nata tare da fara kirar Numbern Fa'iza . ringing ɗaya biyu ta ɗauka . Umaima kina ina ne??? Me ya faru?? Umaima ta katse ta da wannan tambayar . Tun jiya Fahad yake neman ki da mutanen sa har gidan mu sun zo . Yanzu dai haka in taƙaice maki Yana hanyar zuwa Abuja ,wai zai kira ki idan ya iso.! Ƙirjin Umaima ne ya buga

Please Login or Register in order to submit comment