Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

zuciyarta na wani Lokaci cikin Sanyin Jiki ya Dago yana kallonta kafin ya Juya yana kallon Aba da kaifaffun idamuwansa da na ya jafar suke kallonsa da su Hamida Mamanmu kuma Sai kuka take rusawa..!
Aba ya kalli Baba Mallam yana Fadin"Ta rasu ko..?Don Allah in ta rasu ka fadamin..Na yarda da Allah ke kashewa kuma shi ke rayawa..!
Baba mallam yayi mamakin Kalaman Aba aransa yaji salama Cikin Dattakomsa yace"Kayi hakuri Sa"idu..Allah yayi ma Hadiza RASUWA..!
yafada Lokaci Daya yana Dafa kafadarsa alamun Lallashi abun mamaki bai ce komai ba illah matsawa da yayi ya shafe idonta sannan ya Dagata ya cire mata Hijabin jikinta ya Lullube kanta dashi Lokaci Daya yana Fadin"Allah ya jikan ki Hadiza..Allah ya kyautata zuwanki...Allah ya Sadaki da Mala"ikun Rahma hakika ke yar aljannah ce Laifin da kika aikatamin da ganga da wanda kika sani da wanda baki sani na yafe miki Duniya da Lahira Allah ya yafe miki kema yasa ki kwanta Cikin kabarinki Cikin Salama ke da kika tafi baki Gaggawa ba..Muma da muke duniyan Jiranta muke Allah yayi miki Rahama Hadiza..!

Sai alokacin Muryansa ta fara rawa yasa ya Dakata Baba Mallam da ya Jafar dake kuka Suka amsa da Ameen Mamanmu ce ta fasa wani ihu ta Fadi kasa sumammiya shi ya shigo da ya Zeenatu Dake kuka itama ganin Yaya Lullube yasa itama ta fasa kuka tabi ayarin su Hamida Dake durkushe gaban Mamanmu suna kuka ya jafar ne yayi jarumtar fita ya Debo ruwa suka shafa mata sai gata ta farfado tana kuka tana mganganun Rudewa da yadda Mutuwar ta Daketa matuka..!
Baba Mallam ne yace"Balaraba ba kuka Hadiza ke bukata ba sai addu"a ayi hakuri..kinji ko Allah ya jikanta..!
Mamanmu fadi take"Yaya ta rasu..?Innalillahi..Wayyo Allah na..!
Haka take fada tana kuka jikin ya Zeenatu dake ta kuka itama su sun samu Damar kuka ita Amina ta nan Tsaye kukan ma yaki zuwa mata maimaitawa kawai take yi wai yaya ta rasu..?ina wannan ai ba gaskiya ne yayan da jiyanan lafiyanta kalau..!
Baba Mallan ne ya Dago Aba Dake duke gaban Yaya yana kokarin Daidaita Numfashinsa cikin lallashi yace"Sa"idu tashi.kayi hakuri ka nuna Jarumta..In ka rushe suma iyalanka zasu rushe..!
Ba Musu ya Mike yana Rike Jawaad da Zuwa Lokacin ya Fahimci abunda ya Faru shekarunsa goma sha Daya yasan Mutuwa rumgumesa yayi yana kallon Baba Mallam Lokaci daya yace"Asanar ma da Mutane Baba..Jafaru kuma sai yazo da mai awon Likkafani domin ashiryata mu sallaceta zuwa gidanta na gaskiya..!
Baba Mallam ya jinjina kai kafin yace"Shine abunda zamu mata mu nuna mata soyayyarmu.muje waje..Bazaku iya zama da gawa,kuna wannan koken koken ba..Bari naje na Turo Hajiya..!
Ya jafar gaban yaya ya karasa ya Bude Fuskarta kafin yace"Allah yayi miki Rahma yaya..
Kuka ke neman kwacemai yasa ya fice da Sauri Su ya zeebatu suka kama Mamanmu dake kuka Sai alokacin Baba Mallam ya Lura da Amina cikin wani yanayi yace"Mamana sai hakuri kin ji..?Hadiza addu"an ku take Bukata kawai..!
Abun mamaki kallonsa tayi da idanuwanta cikin wani yanayi tace"DA gaske yaya ta rasu..!
Kai ya gyada mata kafin ya samu Zarafin mgana tace"Ba sai ka kira Hajiya ba..Ni zam zauma da ita har ku dawo..!
Gabadayansu suka kalleta Har Aba da su Mamanmu Cikin Sautin Amon muryan data Sadaukar dakomai tace"Eh zan zauna da ita..Don Allah kada ku hanani..Ku barni na zauna da ita na wani Lokaci na karshe a Rayuwata..!
Sai kuma taji kamar Rauni zai bayyanan mata sai ta Dake domin ji tayi kamar zuciyarta ta kara Bushewa ba wanda bai ji Tsausayinta ba Baba Mallan ya dafa kanta yana Fadin"Shikenan Mamana ki zauna da ita banda kuka kiyi ta mata addu"a..!
Da kai ta amsa mai kafin ta Nufi gaban Yaya ta tsaya sai kuma ta Sulale ta Zauna da katon Hijabinta Cikin wani irin Sauti tace"Nan zan zauna..har Ku dawo baba Mallam..Ko bata ji Dumina ba..Zan tuna watarana na zauna da ita alokacin da Numfashinta ya bar jikinta..!

Ba wanda ya tankata har suka fice Baba Mallam da Aba suka fita daga gidan su Zeenatu kuma tsakar gida suka koma suna ta kuka kafin kace me Mutuwar yaya ta Zaga ko"ina duk wanda ya kamata yaji wannan Mutuwar data girgiza mutane da Dama kowa akace yaya ta rasu sai yace Daman tayi ciwo ne..?Mutuwa ko babu ciwo ana tafiya..!
Hajiya babba Mutuwar Yaya ta Daketa Matuka duka matan Baba Mallam suna gidan Baba sa"idu tare da Mamanmu da Yaran,Amina taki Fitowa Daga Dakin yaya tana zaune gaban gawan ba kuka take ba sai dai da ka ganta bata cikin natsuwarta Fata take taga komai ya koma ba yadda take gani ba Hajiya tayi tayi Amina tatashi ta koma Falo in da su Mamanmu ke zaune dasu Anty Amarya su hanne suna Dakin mamanmu sanye da Hijabai su da matan su ya jafar sun saka hijabai suna ta karatun Qur"ani suna Hawaye tunda Hajiya ta hana su kuka..!
Ammh Amina taki tashi fadi take"Hajiya ki kyaleni..Wlh Lokacin Yaya na Raye ban taba zama da ita ko na minti biyar ba..?Bazaki barni na zauna da gawanta ba ko naji Dadi..!
Daganan Hajiya tasan Amina ba kalau take ba,Sai ta kyaleta sai itane tazo suka zauna anan tare tana mamakin ko Kwallah Daya Amina batayi ba..!
Tana fatan kada abunda suka faru da su saka zuciyarta ta Harbu da wani matsala..
Alokacin bataasan me Amina ke Tunani ba..Mganar Aminu ta Tuna da taba cemai ta fison Mamanmu akan yaya alokacin Dariya yayi yana mata kallon yarinta kafin yace"Meenata ke yarinya ce har yanzu shiyasa baki san girman uwa ba..Ammh Har Abada Uwa uwace bamai kwace wannan Matsayin Allah ne ya basu..Bazaki Fahimce matsayin Uwa ba sai Ranar da kika rasata ina mai Tabbatar miki ko muna tare ko bana Tare sai kin fi kowa kukan rasa yaya..Ga Mamanmu din da kike fada ammh Bazata iya kare miki wannan Jinin ba Amina..Bazata iya shafe miki makwafin UWA BA har Abada..!

Sai ayanzu mganarsa take Dawo mata Domin abaya in ya fada bata Damuwa da mganarsa ashe ashe ranar ma tanan nan kusa abu Daya ke damunta Yaya ta bar duniya tana Fushi da ita da ZArginta sannan Tunda ta haifeta bata taba Hutawa da Jidalinta ba Abun yana Sakata jin kamar ta Mutu in ta Tuna bata taba zaman minti Biyar da yaya ba da sunan Hira ba..Anya bata zama asararriya ba kuwa..?Kaiconta ita Amina in akwai wacce Mutuwar Yaya zata kasassara to itace domin su ya Jafar har ta bar Duniya bata taba Daga baki akansu ba sai ita kadai da ta fita Zakka cikin ya"yanta..!
Karfe Daya na rana aka saka za"ayi Jana"izarta zuwa Lokacin harta kannen iyayenta da suka rage na nan Gumel din sun zo sai wata goggonta goggo Jumai Sun zo suna gidan Sai su ya Zulaihat da suna Jigawa Labarin Rasuwar ya isketa sai ya Ikram da ke kusa duk suna nan gidan suna ta kuka Goggo Husai Mallam da kansa ya Kirata ya Fadamata,Ita ta shaidama Jadwa wanda akace sai da ta suma Mijinta na chan na nema musu Visar tahowa sai Mutanen gusai da Aba ya Kirasu ya shaida musu..!
Jaleela kuma ya kira mijinta ya Fadamai shi ya Fadamata sai kuka Domin mutuwar farar Daya tafi shiga Jiki sosai ance sun samu Jirgi sun taho Ita da megidanta da ya"yanta da Ya Nazir da matarsa tafiyar su daya..!
Sai ya Jamila Dake gombe ita din ma Mijinta aka kira aka Fadawa yace suna Tafe suma,Jawahir kuma da yan Gusai zata taho Allahu akbar rai bakon Duniya..!
Zulfa ma an gayamata tana Hanyan Tahowa ita da Nazeem Uzairu na Exam,sai Zahra Dake parthercourt Itama Tafiyar Jirgi tace zatayi sauran Iyalan Baba Mallam na kusa duk sun ce suna Hanyar Tahowa..tunda Rasuwar ta Safe ce..!
Dan mallam Dake chan Madina abakin Ya Nasir yaji Rasuwar Yaya Mutuwar data sanyayamai jiki matuka yana cikin makaranta sanda yaji Rasuwar ko kafin ya koma gida Sakina taji Labari itama cikin Tashin hankali ya fita nema musu Visar tafiya shi da Sakina Sarood nan zai barta Saboda kada Zirga zirgan tayi yawa..!
Ko kafin karfe Dayan an gama Hada yaya,Hajiya Babba da Wata Tsohuwa daga Gusai da suka iso suka hadu suka mata wanka suka shirya har alokacin Amina bata bar dakin ba kuma ko Hawaye Daya batayi ba..!
Kofar gida kuma ya cika Damkam da Jama"a tunda har agidan Radio an Sanar da Rasuwar zuwa Lokacin yan gusai sun iso sannan Ya Fati dake Dutse ta iso ita da Ya akila da Jidda ko"ina ya cika ba matsaka tsinke domin Yaya ta jama"a ce uwa uba kuma Aba dasu ya Jafar da abokan aikinsu sun cika wajen Allah sarki Aliyu abokin Danmallan yazo Jana"iza Tunda Umar ya fadamai yace sai yazo ya samu Janaza..!
Gida bai kara Daukan Kuka ba sai da aka zo fita da gawa bayan an kira duka Ya"yan Aba domin su mata addu"a wadanda suka iso kenan Ya Jawahir da ya Jafar sune manya sai su Amina da su hamida addu"a suka mata da Fatan dacewa Har Hamida da Hanne sun duka gaban gawanta sun mata addu"a Amina kuma sai da Hajiya ta Dukar da ita gaban gawan tana Fadin"Mamah yi ma mahaifiyarki addu"a..!
Sai ta zama out of Control yan"uwanta nata basu damu da Rashin kukanta ba susan bata Damu da yayan ba sai dai abunda basu sani ba awannan gabar Amina ta fisu bukatar uwa a raye domin ita ke cikin Tsaka mai wuyar da Uwace kadai zata Tsaya akanta da addu"a ammh kuma addu"a uwa ga ya"yanta har gaban Abada bata yankewa..!
Tana gaban gawan Kanta sara mata yake yi gabadaya yan Dakin sun koma masu fararan kaya haka take ganinsu kuka take so tayi ammh ta kasa kawai sai ta Sulale ta Rumgume gawan Yaya tana Fadin"Ki yafemin Ki yafemin..MAMA..!

Haka take ta fada cikin ihu Saboda tana so tayi kuka ta kasa sai Tsausayinta ya kamasu Da jawaad suke Tsausayamawa ammh Halin da suka ga Amina sai Rauni ya Tarun musu mamanmu na wajen tana ta kuka Hajiya Babba ke fadan ba kyau wannan kukan da suke mata..!
Ya Jafar ne ya jawo Amina Jikinsa ya Rumgume su ya Nasir suka kama gawa zasu fice tana ganin haka ta fara Fizge fizge tana Fadin"Ku bar min gawanta..Don Allah ku bar min ita..!
MAAMA...!

MAAAAMMAA..!!!!

Hake take fada cikin karyen Sautin da duka kowa yasan ba Sautin Amina bane Ana fita da gawan ta fara Bige Bigen da sai da tafi karfin Jafar su Hajiya suka taso suka sakamata karfi. Da Karfi take fadin"Ku dawomin da ita..Mamatace..!
Haj Nasara na sharan Hawaye tace"Allah sarki..akace Uwa uwace Ko da akan Bola take kwana..!ba wanda yayi Tunanin Amina zata damu don Yaya ta bar gidan Duniya..!
Ana gama Fita da gawan sai ta Daina ihu da Fizga ta koma kuma ta Sume musu kamar yadda aka kwashi mamanmu da ya Jawahir suma sun Zube kai anga Tashin hankali gida ya Rude da koke ba wanda akayi mamakinsa sai Aba ya nuna Jarumta ko Daya ba wanda yaga kukansa Dashi aka sallaci gawan Yaya aka kuma kaita makabarta yana rike da Hannun Jawaad da yaci kuka ya koshi..Aba bai yi kuka ba sai da Mallam yace ya matso shi da Ya Jafar da Ya Nasir da yan"uwanta suka sakata Cikin Kabarinta su ka kuma Debo kasa suka Rufe dashi sai alokacin yaji kuka ya taho masa Baba Mallam na bashi baki kan kabarinta ya Duka har su ya jafar suka gama mata addu"a bai tashi ba Fadi kaawai yake,"Tun zamana da ita bata taba Sabanin da gangan ba..Allah ya jikanki Hadiza har abada bazan samu makwafinki ba..!
Dakyar Baba Mallam ya rikosa suka bar makabarta suka Dawo nan Haraban gidan Mallam aka Saka Dardumai da Tabarmu ana karban gaisuwan maza, mata kuma suna cikin gidan Aba ko"ina Kaje sai yabon yaya ake yi ba wamda zai Bude baki bai Fadi Alherinta ba an samu su Amina sun Farfado sai dai ita Tunda ta Farfado bata kara mgana ba kuma bata kuka tana kusa da Hajiya kogaisuwa akazo sai dai tabi mutane da kallo..!
Sai Dare gidan ya kara Rudewa isowar sauran baki su ya Zahra da ya Zulfa da su ya Jaleela da yaya Jameela sai ya Nazir da Matarsa su ya Aisha duk sunzo karon farko zuwansu gida ba cikin Dadin rai ba,ya Sadiya ce bata zo ba suna Ameriaca inda Mijinta ke aiki tadai kira tayi gaisuwa..!
Ita Mutuwa daman ai bata da Sabo..ko abinci ba wanda ya Nema duk da ana ta kawowa Sadaqa,haka wadanda Mutuwar ta shafa sukayi kwanan zaune suna kuka da addu"an Allah ya jikan Yaya su ya jafar kuma suna waje suna karban gaisuwa sai dai in Mazan sun nemi shigowa sai suyi musu Jagora..!
Ko su saka su shamsu su shiga dasu hatta yan makarantar Islamiyansu da Hadda sun zo gaisuwa su da Malamanau da Dalibansu Sai alokacin akaji Amina tayi mgana data amsa gaisuwan mariya yar ajinsu Sa"adatu duk suna nan gidan suna tare dasu Hanne duk wani mai imani in yaga Amina sai ya tsausaya mata ta Fyade ta rame bata ci bata sha sai an matsa mata..!
Ranar da akayi sadakar uku Goggo Husai ta iso da ita da Jadwa sai mutuwar ta Dawo sabo aka fara koke koken Zuwa yammah sai ga Yaya Danmallam da Sakina sun iso suma..!



*AKWAI SOFTY COPY DA HARDCOPY NA LITTAFIN GIDANMU MAI BUKATA SAI YAMIN MGANA SANNAN LITTAFIN ZAMAN GIDANMU MAI CIKE DA KUNCI SHIMA ZA"A SAMESA A SOFTY COPY DA HARDCOPY KAN FARASHI MAI SAUKI A TUNTUBE NI TA WANNAN LAMBAR DOMIN KARIN BAYANI 09069067488*






*Janafty*



Downloaded from GNOVELS.COM.NG




This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG
to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/gnovels

Twitter : https://twitter.com/gnovels

Telegram : https://t.me/gnovels


Please Login or Register in order to submit comment