Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Barauniya,Sannan yasake ce mata kazama kuma yau harda ballagaza Gabadaya sai taji Ruwan Hawaye sun cika idonta aranta Fadi take"Ni ba barauniya bace..kuma ni ba ballagaza bace..!
Ammh ta kasa Furta haka afili Tama kasa wani motsi.
Aliyu ne ya Dafasa yana Fadin"Cool down Shehi..Bana som Fushin nan naka mara kyau..!
Ya Nazeem ne ganin Amina taki tafiya yace"Au ke bazaki wuce bane..?
Ya uzairu yace"Duka fa take so ya Nazeem ba"a shiga Jikinta bane..!
Mamakin Tsayuwarta yake Cikin Daga Harshensa yace"Bazaki wuce ba..?
Yafada kuma yana Daidaita Fushinsa Da Sauri Aliyu yace"Amina wuce ki koma Cikin gida kin ji ko..?
Ya fadi sunanta kamar yadda yaji an Fada Bata Dago ba kamar wacce muryansa ta bata gwarin gwiwa maimakon ta Juya sai ta fara Tafiya kawai da Sauri ya Shamsu yace"Ke ina zaki..?
Daman wanda zata Huce akansa take nema wanda yayi mata yafi karfin ta Ja dashi yasa jin muryan Shamsu ta waigo cikin Fada tace"To gida zani..!
Tafada Lokaci Daya tana Sakarmai Idanuwanta tana kuma Murgudamai baki harda Harara sai kuma Hawaye dukkansu sun gani Shamsu ya Zaburo yana Fadin"Ke ni kike juyama baki..?zan karyaki in na rike ki..!
Amina ta Tsaya kyam tana Fadin"gani..Kada kabarni da rai ya shamsu don Allah..!
Tafada tana kallonsa da Jajayen Idanuwanta..
D'anmallam yakalleta ta fa Daina bashi mamaki Aliyu yace"Kai shamsu kyaleta..baka ga yanayinta ba inajin ba ita kadai bace..!
Ya Nazeem yayi Dariya bai ce komai ba acikin Salo Salon iskancin Amina wannene basu gani ba
Ya shamsu yace"Wlh lafiyarta Kalau..Duk Salon rashin kunyarta ne Daman bata tsoron kowa ta bari nazo ta gani..!
Ya fada zai nufeta yaji D'anmallam ya Dakamai Tsawa yana Fadin"Shamsu kyaleta...
Ke bar nan wurin..!
Ba musu ta juya bayan ta kara juyama Shamsu baki tana kunkuni ta wuce tana Sharan kwallah D'anmallam ya Saki Siririn Tsaki yana Fadin"Kazama kaawai..!
Ya Uzairu yace"Yaya da ka bari Shamsu yaci Ubanta..Ko"ina ta Addabi mutane chan ma bata bari Baba Sa"idu ya Huta koda yaushe Fitinarta..!
Hannu ya Dagamai yana Fadin"Nace ku bar mganar ko..?
Dole suka koma suka zazzauna shi kuma sai Sakin Huci yake Kafadarsa Aliyu ya Dafa yana Fadin"Allah huci Zuciyar Shehi..Ungo wayarka kila sai ta Hau kan Teburim mai gyara..!
Karba yayi Lokaci Daya yana ganin yadda Sreen din wayar ya tashi aiki.
Karamin Tsaki yaja kafin yace"Yarinyar nan bata jin mgana..kamar ballagaza bata da natsuwa ji asaran da ta jamim
Wayar nan fa sai dai na Sauyata ta gama aiki..!
Aliyu yace"Is ok..Kayi Hakuri muna da kudin Siyan wata kannen namu ne sai Hakuri..naji Uzairu na Fadin Baba Sa"idu Hala Diyarsa ce..?
D'anmaallam ya gyada kai bayason mgana ba Domin Kada mallam yayi Fada da Tuni yana gida ya kwanta ya Huta.
Aliyu yace"haba na kamar su da Yaya..Hala Diyarta ne..?
Nan ma kai ya gyadamai Aliyu ya Kalli Umar yana shafa gemunsa yace"Irin su ne Sweet Sisty Shehi..Anya bazan kama Daya Cikin kannen nan namu ba..?tunda kai ka yi auranka da balarabiya..!
Danmallam ya kallesa a adage kafin yace"Wadanan yaran zaka kwasa..?
Aliyu yace"ofcourse sun fi Dadin harka ne..!
Danmallan yayi Tsaki kafin yace"Wlh baka da Hankali..kai yanzu Gemi gemai dakai AA kace wadanan yaran kake so ka aura..?Ya"yan Cikinka..?
Aliyu yace"Bangane ya"yan Cikina ba..?nifa ba Tsoho bane mallam Shekara Talatin da taran ma ban cika ba..Sai watan jibi..!
Wani Tsakin ya kara ja kafin yace"Me yayi Saura a arba"in AA..?Wlh da auran Fari mukayi dukkanmu da muna da kamarsu ko basu kai su ba suna Tsaransu..!
Aiyu na Dariya yace"Kai nifa ba Tsoho bane..Ko yanzu naso zan auri yar 12 ma ballatana yaran nan sun Haura 15..!
Dan mallam ya Dafe kansa kafin yace"Plz ka kyaleni da wannan Shirmen naka am not in d Mood..!
Aliyu na Dariya yace"Kai Shehi..Kaifa nasan sai ka cike kofa Danmallan fa kake..!sunnar nan sai ka ciketa..Ina baka Shawara in zaka kara ka karo irin yan yaran nan sun fi Dadin Sha"ani nidai kar ka manta ina kamun Daya Daga Cikinsu duk wanda ka bani am Greetfull..!
Danmallam ya fara ma Aliyu kallon ya Tabu ganin haka yasa ya Buga Kafadarsa yana Fadin"Am Serouis fa Shehi..!
Danmallam ya Kauda Fuska yana Fadin"Plx ka cireni cikin Shirmen naka..Kuma wlh in kace zaka auri irin yaran nan sunanka Sorry ka kai Jidali Gidanka da kanka am Telling u..!
Aliyu yace"Eh bakomai..Tanque for ur Advice..!
Ko kara kallonsa bai yi ba shi kuma Aliyu na Dariya yace"Tunda ka gaji dani..Bari na kira Aliya nace ta fito ita da yaran mu kama Hanya..!
Kamar bai son mgana yace"Ka bari yaran chan su tafi mana..!
Aliyu yace"Wasu yaran..?
Yamutsa Fuska yayi kafin yace"Amaran mana..!
Aliyu yayi Dariya yana Fadin"Shehi Umar..Mijin Sakina ango Saratu..!
Hararansa yayi kafin yace"Sarood na ce maka..!
Aliyu yace"oh..Sarood kasan bakin ya saba da Hausa ba irin ku da bakin ya Juye da Laranci ba..Angon Balarabiya..!
Yake fada yana Dariya Danmallam Mirmishi kawai yayi kafin yace"kana da matsala AA..!

Sa da aka fara Haraman fita da Amare su Hanne suka Tabbatar da Amiba bata gidan sun Duba ko"ina basu ganta ba.
Zafira tace"To ina taje..?
Hamida tace"Gida ta koma fa..!
Zafira tace"Muje to..!
Hanne ta harareta kafin tace"Jeki a karya miki kafa..
Zafira ta kama bakinta kafin tace"Au na manta ne kai ban kara zuwa Bikin Gidan nan Wlh..mu achan gusai in ana Biki ba inda bama zuwa bamai Takura mana..!
Hamida da Hanne suka ce Hamm atare sun kasa mgana.
Suna gani aka fita da Amaran suna kuka ammh ba Halin su bi Tawagan masu Rakiya.
Falon Baba Maallam aka shiga Dasu Hajiya Babba,Sai Hajiya uwa sai Yaya kadai suka shiga dasu.
Baba Maallam da Aba sai su ya Danmaallam da Su ya jafar ya Nazeem ya Nasir ya Nazir dukkansu dai mazan suna ciki hatta su ya shamsu Sauran matan kuma suna Waje suna Jiransu Ciki harda Sakina da su Sarood da Aliya sakina taso ta bi Sadiya zuwa Dutse Umar ya hanata yace ta bari Daga baya.
Nasiha ne maallam yayi musu,Kadan Ba da yawa ba Domin yace duk abunda zai Fada musu an sanar dasu sai Aba shima yayi nashi sai Ya Danmaallam sannan ya Nazir sai su ya Jafar hatta su shamsu sun musu sallama.
Daganan Baba Mallam ya ba kowacce Qur"ani Izu Sittin da azkar da Casbaha yace in suka rike kyautarsa sun gama Lafiya..
Daganan ya mike suka fito shi da Aba da Hannayensu suka saka kowacce a Motar da za"a kaita gidan Mijinta suna kuka suna Daga ma iyayensu Hannu.
Su ya jaleela da su ya Nazifa da su ya Fatima duk suna Kofar gida bakin Motocin suna sallama dasu sauran matan suna daga cikin gida.
Daya Bayan Daya Motocin Amaran suka tashi sai fatan Allah yakai Lafiya sannan mata suka koma cikin gida.
Alokacin ne Danmallam suka shiga cikin gida shida Aliyu suka gaisa dasu Hajiya sannan yace Aliya ta fito su tafi sai da taje ta ma Hajiya sallama ta bata kayan Cincin na biki tana ta Godiya.
Kafin La"asar suka wuce Bayan sun Rabu kan suma suna nan zuwa.
Sallar la"asar kadai yayi a anguwan ya Shiga Mota ya koma gidansa ya kwanta Saboda Hayaniya.
Zuwa Dare gabadaya Amaren Dake nesa sun isa Mazajensu sun kira Baba Maallam suka shaidamai sai Hamdala gidan kuma sai aka Fara Hada hadan kayan Tafiya zuwa gobe hatta su Ya Jaleela ma Baba Mallan yace kada wacce ta kai mai jibi agida ya Jadwa ne kadai zai Dagama Kafa sai visan su ya fito.
Ya Akila da ya Fatima gobe zasu bi mazajensu su koma su jidda ne jibi zasu koma ammh gobe Dutse zata sauka bayan tagama ganin Dakin kanwarta ta wuce kano..!
Su hanne sai Dare suka ga Amina adakin Mamanmu taci kukanta ta Share hawayenta duk yadda suka so su Zolayata yau Amina bakinta ya Mutu kazil batace ba haka suka kwana gari na wayewa sun sani suka Fara shirin tafiya Hadda harta su ya Abida kuwa.
Kafin su tafi sukayi sallama da Zafira aranar zasu tafi Allah Sarki Sabo kamar kada su rabu,ko kafin su Dawo makaranta da yammah yan gusai sun koma,gida ba kowa sai goggo Husai da Ya Jadwa da Ya Jaleela da gobe jirgi zatabi zuwa Lagos ya Jawahir ta bi yan Gusai sun koma.
Ya Zahra ma jirgin yammah tabi ita da Mijinta Daman yazo Daurin auran sai ya Zulfa da gobe zasu koma ita dasu Ya Uzairu su ya Nazir da Matarsa tun safe suka hau jirgi suka koma Lagos.
Chan gidan Baba mallam ma kowace Danginta sun tafi yan maiduguri kadai suka Rage sai gobe zasu wuce Ya Jidda ta Sakina da Sarood sun tafi Dutse tun Safe,Danmallam yaso ya hanasu Tafiya Hajiya tace ya barsu su tafi sai gobe zasu dawo.
Ta bangaran kowacce Danginta sun Tafi Sai daidai su Baba Lami nata Faman gyaran gidan.
Koda sukaje Hadda Amina bata manta ba sai da Taja Mariya da fada aka Fitar dasu Waje Mariya ta rika yima Amina Allah ya isa.
Ta kalleta tana Dariya kafin tace"Allah ya isa taki ce awajen Amina kin ga kaina tafi Dubu..
Take fada tana ma Mariya gwalo sai Da aka tashi Hadda aka Sallamesu da aka shiga islamiya ba haka ta Dinga Tsungulinta sai da aka kara Kadata waje.









*Janafty*
[9/3, 2:30 PM] Aysha📚: *TA FITA ZAKKA..!*
_(Aminene)_
*BOOK 1*


*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty❤️*


*🅿️15*

*Jumma"a*
9:00am

Labulen Dakinmu Mamanmu ta daga tana kallon Amina Dake zaune Saman gadonta ta tasa kayan da mamanmu ta gama wanke mata jiya ko fara ninkesu batayi ba.
Hamida na Gefenta itama wajen Dirowarta tana shirya Littafanta Cikin Sabuwar Jakar makarantarta Mamanmu ta kalli Amina Data Zabga Tagumi kamar wacce akace mata nata ya rasu Cikin Lallami tace"Amina baki Fara Ninke kayan nan naki ba ko..?yi hakuri ki adanasu ina aiki ne da na Gyara miki..Kwashesu ki saka cikin Dirowarki in anjuma in nepa sun kawo Wuta Zan saka Hamida ta goge miki sai ki adana Kayanki..!
Hamida na jin haka ta Dago tana kallon Mamanmu kafin tace"Ni kuma Mamanmu..?
Tafada Tana Bata Fuska Mamanmu tace"Eh ke..Ko bazaki yi bane..?
Tunda ita haka Allah yayi ta bata da Zafin nama ku kuma yan"uwanta ne kun fita karsashi ba sai ku taimaka mata ba..?
Hamida bata iya mgana ba ta maida kanta Gefe Amina kuma sai Danne Dariyanta take yi kafin tace"Dama ta barshi mamanmu..!
Bata bi ta kansu ba ta saki Labulan ta koma tana Fita Amina ta Fara Dariya Har tana ma Hamida gwalo kallonta Tayi kafin ta girgiza kai tana Fadin"Kiyi Dariya son ranki..Lokacin ki ne ammh ki sani akwai watan watarana..Da babu mamanmu ba Hamida wlh sai kin raina kanki..!
Kamar ba mace ba komai sai dai ki zauna komai Mamanmu tayi miki ko kuma ta sa muyi miki..!
Tafada Cikin jin haushi Amina ta kara saka Dariya kafin tace"ko ba mamanmu ba gaki ba..?
Hamida ta Harareta kafin tace"Ni kuma sai bazan yi aure ba sai na koma kula Dake..?Sannu Amina yar gata..!
Amina tace"To miye..?Sai ki auri kanin Mijina..!
Karamin Tsaki Hamida taja Amina ta kara saka Dariya tana Fadin"Hamdiya..Hamdiya..Hamdiya..!
Take Fada cikin Sigar waka Da sai da Hamida tayi Dariya tana Fadin"Ke kika sani..Allah yasa ki shiga gidan mai mata Biyu kece na uku..Ya"ya kadai sun isheki Amina..!
Amina tace"jar uba..ya auran ma kansa dai..Mai mata Biyun daya kwashi Amina ai mai Budurwan Zuciya ne..Sai yayi Nadama Tijara ne da Jidali ne zai gani harda na Siyarwa..!
Take Fada tana Dariya Hamida na Tayata Daganan suka shiga Hirarsu Amina na tusa kaya cikin Dirowanta batare data Tsaya Ninkewa ba Hamida tace"Kai Amina mugunta ma harda karan kanki kike yi mawa..?
Amina ta tsaki kafin tace"Ki kyaleni Hamida ni nagaji..!
Hamida ta mike tana Fadin"Zaki ma mike ne yarinya yau ke kike da gyara mana Daki..!
Amina tace"Kan bala balagagge..Ranar fa ni na gyara..?
Hamida tace"Ai ba sau Daya ake gyaran Daki asati ba malama..!
Amina ta Tura baki kafin tace"To nidai na gaji bazam iya ba..!
Hamida ta bita da kallo batayi mgana ba Amina ta cigaba da Fadin"Mutum kamar jaki aiki aiki..Ni wlh nagaji..!
Hamida baki ta rike ta kasa mgana wai Amina na Mganar aiki me takeyi..?
Aiki sai ya zama Dole Amina ke yi in ba zama ba zamanta take Mamanmu na Daure mata wajen iskanci sanin da tayi bafa zata gyara Dakin ba yasa tamike ta fara gyarawa Amina na Mata Dariya sama sama tana jinta tayi mata banza kamar bata jita ba.
Har ta gama gyara Dakin bata gyara wajem kayan Amina ba ganin haka yasa tace"Hamida Kashi nayi miki akan gado da baki gyara barayina ba..?
Hamida tace"Bansani ba.!
Amina ta tabe baki kafin tace"Allah ya baki Hakuri Anty Hamidaaa..!
Ta karishe Fada tana mata gwalo karaf suka Hada ido Hamida tace"Don Allah nake yin komai ni..!
Amina tace"Allahu akbar..Allah ya Biya malama Hamdiya..!
Danne Dariyanta take yi kada Hamidan ta gani ta fasa gyara mata Sauran kayan ma Hamida ta gyara mata ta Ninke mata da kyau ta saka Cikin Wardrope din Amina ta kuma gyara mata gadon ita Amina Tuni ta shiga Tiolet din Dake Dakin zatayi wanka.
Koda ta fito har Hamida ta gama gyaran Dakin ta share ta goge ta saka Turaran Wuta Amina ta Hura hanci tana Fadin"Kai Allah yayi ma Hamida albarka..!
Komai yana son gyara ko"ina yayi kyau tas dashi,Zama tayi ta shafa mai ta saka wata Doguwar rigar Material tana cikin Daura bakin Dankwalin abaya ne Mamanmu ta kara Daga Labulan Dakin ta leko tana Fadin"Hamida zo don Allah..!
Gishiri ya yankemin ina girki..!
Amina ta Dago tana Fadin"Bata anan fa Mamanmu tana waje..!
Mamanmu tace"Ai ban ganta bane..?
Ta juya tana kiran"Hamida
Hamida...hamida..!
Yaya Dake Kofar Kitchen tana Taya Mamanmu gyaran wake tace"Hamida fa ta shiga makewayi..!
Mamanmu tace"Gishirin nan fa ya kare Yaya..Bansani ba ina Dago Buhu sai bakomai aciki..!
Yaya tace"Yafa Dade ya kusa shekara Tun Gishirin nan da Jafar ya hado cikin Wani siyayyan kayan abinci ne fa..!
Mamanmu tace"Gaskiya ya jima..Gashi Babansu ya fita ba kowa agidan..!
Yaya tace"Sai dai ki kirasa a waya,ki Fadamai ko kuma ki bada asiyo in ya Dawo sai ki samar dashi..in za"ayi Siyayyan kayan abincin wannan Watan kada a manta da gishirin..!
Mamanmu tace"Nayi tunanin haka bari Hamida ta fito ta leka shagon baya ta siyomin ta dawo da wuri kafin cikin yayinsu su ganta nasha Surutu..!
Yayaa tayi Dariya kafin tace"Aifa kinsan su masu yayyi ne..!
Mamanmu tace"Nasani ne Yaya..Yaran da ba"ason ko nan da chan sufita..!
Hamida wai ina ta shige ne..?
Yaya tace"Ki aika Amina mana..Tunda Hamidan bata fito ba..!
Mamanmu tace"Yauwa..Amina..Amina..!
Ta tafi tana kwala ma Amina Kira sai gashi sun hadu a bakin kofar Dakinsu Tana Fadin"Gani Mamanmu..!
Mamanmu ta kwanto kudi a Haban Zaninta ta mika ma Amina Dari Biyar Sabuwa tana Fadin"Maza sa Hijabin ki kije Shagon nan na baya ki amso min gishiri na Dora sanwa kuma na Duba ashe Gihirin ya kare yi maza Amina don Allah..!
Amina ta karbi kudin ta koma Daki ta Dauko Hijabin Hamida Data gani Saman gadonta ta fito flat din Takalminta ta saka baki tazo tana Fadin"Gishirin nawa Mamanmu..?
Tana gaban Famfo tace"Ki siyomin babban Jakan nan..Ki hadomin da Amo Amina wannan naga bazai kai an juma ba kuma shima shikenan jiya Zeenatu tace ta Dauko acikin Kwalin..!
Da Toh Amina ta amsa zata fice Yaya na Zaune kan kujeran yar Tsugunno ta Dago kanta tana Fadin"Saura kuma ki Dade..!
Juyowa tayi tana kallonta kafin tace"Ina zani to..!
Ta fada tana Tura baki Hararanta Yaya tayi kafin tace"Daman baki bace..Inda aka ijiyeki ba nan kike Tsayawa ba..!
Mamanmu tace"Amina kyale Yaya..Yi maza ki dwo yar albarka.
Da haka ta fice tana kunkuni afili tace"Yaya bata taba Fadin Alheri akaina..Yoni ina zani..!
Sai kuma Tayi Dariya sanin Halinta sai ta iya juya alaqanta zuwa gidansu Hanne ta ma manta da aiken Mamanmu karamin aikin Amina kenan.
Sakamakon Safe ne anguwan tayi shuru ba kowa maza sun tafi wajen aiki yara kuma duk suna makaramta Shagon yana ta bayansu kadam ne ba zuwa shago suke yi ba komai na Bukatar gida a kasuwa ake siyo shi,sai dai in wani abu ya yanke kamar irin rana mai kama ta yau
Bazata kirga Sau nawa tataba zuwa shagon ba kamar bai fi sau Biyu ba,Shagon babban Shago ne babu abunda baya saidawa mai shagon ba Dan garin bane bakano neyazo ya samu waje sai Allah ya saka ma kasuwancin nashi Albarka.
Samda ta shiga shagon akwai Layin mutum uku agabanta sai ta koma gefe sai da aka sallamesu sannan ta matsa kusa da katan Shagon ta mikamai kudin Hannunta Lokaci Daya tana Fadin"Bani gishiri babbar jaka da omo..!
Karban kudin yayi yana kallonta Ganin bai taba ganinta ba yasa yace"Wani irin Omo..?
Amina ta yamutsa fuska kafin tace"Kowani iri..!
Dauko mata yayi duka yana nemam ya Hadasu a leda Daya da Sauri tace"Tsaya tsaya..Mallama a ina kataba ganin an Hada gishiri da Omo waje Daya..?
Yana yar Dariya yace"Au na manta ne..Yi hakuri don Allah..!
Hararansa Amina tayi batayi mgana ba ya Raba kowannen Ledansa Dabam yana Fadin"Nace ba..A ina kike ne..?
Naga bantaba ganinki ba..!
Amina ta Tsaya tana kallonsa kafin ta saka Hannu ta warce ledan hannunsa tana Fadin"Ina ruwanka..?malam bani Chanjina na tafi..Tunda ba Sana"ar kake yi ba tambayan inda mutanen da suka zo siyayya shagonka suke kake yi..!
Tsiwanta ke bashi Dariya yanzu ma Dariya yayi kafin ya Hado mata Chanjinta ya bata Kamar zata Dakesa haka ta Fizge chanji kadan ya Rage ta Hada da hannunsa baki ya rike yana Fadin"Kai..Allah ya baki hakuri..!
Ko jinsa batayi ba tayi wucewarta Hankalinta na kan chanjin hannunta Tana Kirgawa shi kuma ya Sawo kansa Shagon Kansa na kasa yana Danna Wayarsa Daga bayansa kuma wani ne kebinsa yana Fadin"Oga da ka bari na amso maka..!

"Bazan iya da shiriritarka ba Nura..Na ri..!

Mganarsa ta makale ne sanda suka ci karoda juna kusan Tsawonsu Daya In maya fita da kadan ne yasa suka Daki Goshin juna Dayasa kudin hannunta da Ledan duka suka zube a kasa shidai Allah ya taimakesa wayarsa bata Fadi baya riketa Dakyau.
Amina ta saki karamin Tsaki ta Duka tana kwashe chanjinta da omon Daya Fado a leda Daga saman kanta taji anaa Fadin"Baiwar Allah ki rika Tafiya kina kallon gabanki ok..?
Sai da ta gama kwashe komai kana ta Dago suka Hada ido Hudu dashi Kallonta yake yi da Fararan Idanuwansa kamar yadda ta sakarmai nataa manyan Idanuwan Cikin kallon kama Raina ni tace"Dakata mallam..Ni dakai waye baya kallon gabansa..?
Ni fita zan yi kai kuma zaka shigo acikin ni dakai wazai kalli gabansa..?
Ta karishe Fada tana Hararansa Harda Murguda baki kafin ta Raba ta gefensa zata wuce.
Cikin Wata sanyayyar Murya mai Cike da yanga taji tace"Ya zaki tafi..?,Alhalin baki bani hakurin Laifin da kikamin ba..?
Juyowa Amina tayi tana kara kallonsa kafin ta Nuna kanta tana Fadin"Ni..?
Kai ya gyada mata cikin yanga Lokaci Daya yana Jaye Hulan kansa Facing cap Kyakyawan Farar Fuskarsa ta bayyana.
Amina tace"ai ban yi maka wani Laifi ba ballatana na baka Hakuri..Kumani Amina ban cika bada Hakuri a laifin da ban aikata ba wani Lokacin ma ko nice bani da gaskiya bana Laushi da wuri..!
Ta saman Lebenshi yace"AMINA...!
Nice name..!
Kin fada min sunanki batare da na sha Wahala ba..!
Amina ta Tsaya sake da baki tana kallonsa Wabda ke gefensa ne yace"Oga..!
Bai bari ya karisa ba ya Laluba aljihunsa ya Dauko Walet dinsa ya Mikamai yana Fadin"Kayi abunda ya kamata Nura...!
Karba yayi yana kallon Ogan nasa Daya Fara susucewa ganin wannan Kwailar yarinya to kwaila mana wannan ta wuce sha Biyar tsawon kafa ne kawai Kafada ya Daga kafin ya Nufi Cikin shagon Dutse zasu koma yanzu nan Kati ya yanke ma Ogansa acikin waya suka Tsaya su siya to lokacin ankirasa a waya ya Dauka sai Ya kasa jira ya fito da kansa zuwa Cikin Shagon..!
Amina bata kara mgana ba ta fara tafiya da Hamzari ya sha gabanta yana gyara zaman Jaket din Dake Jikinsa Cikin Mamaki da Budewar ido Amina tace"Malam lafiya?Mtsamin Daga Hanya tunda bata gidan ku bace..!
Mirmishi yayi har sai da Fararam Hakoransa suka bayyana Cikin Muryansa yace"Wani ya taba Fada miki kina Burgesa..?
Yafada yana kallonta Cikin wani Salo Sai kuma taji mganar ta shigeta Cikin Sausasauta Murya tace"Ni AMINA ba wanda ya taba cewa ina Burgesa..Ni ai bana Burgewa kowa.!
Wayarsa ya saka Cikim Aljihun Jaket dinsa Lokaci Daya yana Fadin"To yau Ni AMINU BUBA nace kina Burgeni...!
Ido Amina ta zaro tana kallonsa mganar ta shigeta kanta ta kara nunawa kafim tace"Da gaske ina Burgeka..?
Kai ya gyada mata Sai ta washe bakinta kafin tace"Nagode..yau na fara ganinka ammh naji Dadin Haduwa Dakai domin kai ne Mutum na Farko Daya fara cewa Amina Aminene na Burgesa bazan manta da wannan ba..Thank you..!
Tafada tana Juya idanuwanta cikin bayanna Farimcikinta Shagala da kallonta yayi baisan ya Furta"She is Beautifull...!
Bai an kara ba yaga tana Shirin Tafiya da Sauri yace"Ya zaki tafi kuma ki barni..?
Da mamaki Amina tace"Bangane ba..?
Mirmishi yayi kafin yace"Ke yar nan garin ce..?
Da kai ta amsa mai cikin mamakinta da kuma kara ganin yarintarta yace"Ammh baki sanni ba..?
Amina tajuya ido kafin tace"To a ina zan san ka bawan Allah..?
Da sauri yace"Sunana Aminu..Aminu Buba..!
Nayi matukar mamaki da baki sanni ba Shekararki nawa ne..?
Amina tace"Shekarata goma sha Biyar da Wata Goma saura wata biyu na cika Sha shidda..!
Tafada tana Kirgamau da hannu Dariya ta kamasa har sai da Wushiryansa ta bayyana.
Tsayawa tayi tana kallonsa yadda yake Dariya abun sha"awa.
Cikin Matse Dariyansa yace"Amina..Amina kina Burgeni..!
Zan so na rika ganinki koda yaushe ko domin ki rika sakani Nishadi Aji nawa kike a makaranta..?
Kunya Amina taji yasa ta sunkuyar Dakai kafin tace"SS1 sai monday ammh zamu fara zuwa..!
Yana mata Dariya yace"Kice Jjc ne...!
Amina yan matan SS1..!
YAadda yake Dariyan ne ya fara Kular da ita yasa ta Hade ranta Nura Daya Fito Daga shagon tun dazu ya gaji da ganin wannan Drmar yayi gyaran Murya yana Fadin"Oga lokaci fa na Tafiya....!
Hannu ya Dagamai kafin ya fiddo da wayarsa yana mikama Amina Lokaci Daya yace"Sakamin Lambarki..Amina ai daman Amina kawar Aminu ce ko..?
Yafada yana Dariya itama Dariyan Tayi Domin Farat Daya taji ya burgeta kamar yadda yace itama ta Burgesa.
Noke Hannu tayi kafin tace"Ni ai bani da waya..!
Ido ya zaro kafin yace"Duk girmanki Amina saura fa wata Biyu ki kai shekara goma sha Shidda!
Ya karishe Fada Cikin Zolaya Da sauri Ta kauda kai tana Mirmishi Kara Tura mata wayar yayi yana Fadin"Ko lambar Antynmu Babu Amina..?
Amina tace"Tab..Bafa mai waya agidanmu Daga yaya sai mamanmu to ta yaya ma Jawaad ya jefata ruwa
Ta mamanmu ce kadai ta rage sai kuma ta Aba..!
Da sauri yace"To sakamin ta mamanmu ko ta Aba din..!
Ido ta zaro kafin tace"Tabdijam..Rufamin asiri ba ruwana kaga mallam bansan ka ba sai anjuma..!
Kafin yayi mgana ta wuce da Sauri harda gudu Kiran sunanta yake yana Amina..Amina ita ko Waige batayi ba sai dai ta kule ya Daina ganinta sannan ya Dafe kansa.
Nura ya kariso yana Fadin"Oga Oscar na Kira na fa kuma nasan kai yake nema..Sannan ka koma mota kafin mutane su farga Dakai..!

Lokaci Daya yana mikamai katin Daya siyo Airtel na 1k Mtn ma haka bai tsayama karba ba ya wuce Ya bude gaban wata Farar Bugatti ya shiga yana Fadin"Nura bana son mita..Kyale Oscar tukani muje kawai..!
Kai ya girgiza yana mamakin Yar yarinya karama Oga ya zauna yana bata Lokaci a kanta kafin ya Zagaya ya shiga Mazaunin Direba ya Tada Motar sukar bar Layin da gudu kamar zasu tashi Sama.

Koda Amina ta koma gida sai da Mamanmu tace"Amina ina kika Tsaya..?
Amina tace"Mamanmu chanji ne Babu..!
Da wannan karyan ta Kashe mganar Duk Surutunta ta kasa bama ko Hamida Labarin Haduwarta da Aminu buba kamar yadda yace sunansa Ranar duk in ta Tuna sai tayi Mirmishi ita kadai a kallah yau ita Amina ta samu wanda yace komai nata na Burgesa ashe itama Macece kamar kowa wannan yabon ya xauna aranta da Har Abada bazai fita ba.
Ko washegari a hadda bata yarda ta Fadama ko Hanne da bata boye mata komai ta kasa bata Labarin Haduwarta da Farin mutanin da ya kasa barin Ranta Ko yaya ta Tuna dashi sai ta murmursa acikin Ranta.
Da suka tashi Sallah ne Amina ta kalli Hanne suna wajen alwala Tace"Hanne ashe nima ina Burge mutane..?
Hanne na kuskure baki sai da ta Furzan da ruwan bakinta kafin su hada ido da Hamida suka kwashe mata da Dariya Duka Amina ta Dirkama Hanne a baya tana Fadin"Bana son iskanci ban tambayi Hamida ba sanin Halinta yar bakin ciki ce.!
Hanne na Dafe inda ta Daketa tana Fadin"Muguwa..Uban wa zaki Burge..?
Hamida ta Karbe da cewa"Sai dai ki Gunduri mutane Jidalinki Amina wlh bamai iya Daukansa sai mu da muka Saba..!
Hanne tace"Wlh wani waje duka zataci in taje tayi..!
Dariya suke ta mata ita kuma bata su take ba Hankalinta ya tafi Tana Jin Muryan Aminu sanda yake Fadamata Tana Burgesa ita din abar Burgewa..!
Daga Ranar bata kara musu mganar ba sai dai yana Ranta Lokaci bayan Lokaci yana Fado mata acikin Ranta.
Har tazo Ranar Monday suka fara zuwa makaranta Sun samu Dalibai irin su da suka Cigaba da Unity sannan akwai Sabbin Dauka kamar yadda aka saba Amina

Please Login or Register in order to submit comment