Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta cigaba da abunda ta saba sai ma abunda yayi gaba ta addabi Dalibai da malamai Sai kuma akayi Rashin Sa"a aka hadasu aji Daya da Sa"adatu Hanne da Hamida Ajinsu Daya.
Amina kamar ta mutu saboda Bakimciki tace ma Hanne"Naso aji Daya aka hadamu hanne..Sai dai ban da Sa"a anhadani da Shegiyar Sa"adatun nan..!
Hanne tace"Ina Ruwanki da ita..?
Amina tace"Ta shiga Harkata Dakuwa zatayi..!
Sa"adatun bata shiga Harkan Amina Saboda Anty Amarya taja kunnenta Sosai kan Amina shiyasa ko Aminar Zata takaleta bata bi ta kanta.
An hadasu Aji Daya da Zainab Isa Kawar Amina sai suka Kulle atare Sit dinsu Daya Dalili kuma tana Aro mata Littafan Hausa na kishiyar mamanta take Sato musu ta kawo makaranta su karanta ita Zainab Amina take kawo mawa,ita sai agida ta ke shigewa Dakinsu ta Boye ta karanta sannan bayan su Hanne Zainab isa ta jure Gwagwarmayan Amina da Jidalinta.
Kwanci tashi ba wuya a wajen Allah su Amina sun mika cikin Zangon karatunsu na Farko a SS1 dinsu cikin salama da kwamciyar Hankali kamar Amina tayi sanyi Saboda ta Rage Tonon Fada sai dai jidalinta da Masifarta sai abunda yayi gaba Dakyar Hajiya ta rokar musu Baba Mallam ya bari Idi Direba yakai su gidan ya Ikram Dukkansu har da su ya Abida su Amina an sha Murna har Fada sai da taja su hanne suka shiga da karambaninta.
Abida tace"Kai amina bala"i wlh watarana sai takai kanta inda zata mutu..!
Ya Ikram tace ko ita sai da mijinta take shiga Gidan Sarki batama san Hanya ba sai ga Amina tana kutsa kanta Kusfa kusfa,Chan suka mata wuni sai yammah suka dawo suna Santin Haduwar gidan kamar aturai Amina tace"gaskiya gida biyu suka tabamin kyau..Daga gidan ya Danmallam sai gidan ya ikram..!
Hamida tace"Gaskiya gidansa shima ya Hadu tsarin daidai kamar aturai..!
Haka dai sukayi ta santin gidan Har Mamanmu na saka baki tana basu Labarin Tsaruwan gidan Sadiya Dake Dutse Amina tabe baki tayi batayi mgana ba sai da Hamida tace"Kai zan so naje ngani mamanmu..!
Yaya na gefe tace"Naji kamar ance cikin watan man zata bi mijin chan kasar Dayake aiki..!
Mamanmu tace"Nima haka naji Haj.Nasara na tadin ita da Haj.Uwa..!
Amina tace"Ni kam ban sha"awar zuwa..Nasan bazai kai yadda nake Hasaahe tsaruwa ba..Shiyasa naga yau Sa"adatu nata wani yamutsa Fuska araina nace an ga inda aka fi su..!
Hamida tace"Kai Amina baki son zaman lafiya..?
Balla mata Harara tayi kafin tace"Eh din ke kuma an tabo masoyiyarki..!
Ganin zasu fara fadan nasu ne mamanmu ta Tsawarta Ya Zeenatu na Gefen Yaya tace"ZAman lafiya ko na Minti Daya ne Amina bata kaunarsa..!
Amina na jinta ta Daga kanta sama aranta tana Fadin"Eh din..!
Nan dai mganar tatashi ta koma Tsakanin su Mamammu da su Hamida Amina bata kara saka baki ba Kada tata ta karayin zafi.
Ana cikin haka acikin Satin Matar ya Jafar ta Haihu Anty Shamsiya.
Su Amina Sai ana gobe suna suka samu zuwa barka shima din su Yaya da su Hajiya sukabi da zasu barka mamanmu ita ke zuwa tana Ma jariri wanka wanda yaci sunan Baba Mallam
Suna zaune Jaririn na Hannun Hanne Amina ta karkato tana Fadin"Wlh bakinsa Sak na uwar ne..!
Hanne ta Zunkuleta tana Fadin"Ba Ruwana Amina..kada taji.!
Amina na Danne Dariyanta ta Dago tana Fadin"Mamanmu kalli jaririn nan yana karami bakinsa babba..!
Hamida da Hanne da suka san mganar suka yi tsumu tsumi.
Hajiya Uwa ce tace"Banda abunki Amina ai jariri ne yana girma zai Sauya..!
Mamanmu tace"Mai sunan mallam fa Shamsiya ce Sak..Kila sai nan gaba zamu ga Jafaru..!
Akayi Dariya Shamsiyan na gefe batace komai Amina nata Dariya sai da suka fito zasu tafi Hamida ta jawota Tana fadin"Amina wlh ki bari ba kyau kushe hallitar Allah..!
Hanne tace"Kuma bata san me zata haifa ba!
Amina ta toshe kunnenta tayi gaba Tana Fadin"Nagode da wa"azi Malama Hamida da malama Hanne..!
Kyaleta sukayi ganin bazataji ba Washegari sun so su koma Mamanmu tahanasu tunda ya Jafar din yace ba suna ba Taro an dai yanka Raguna Mallam yaje yayi barka da kansa.
Ranar kwatsam sun je makaranta sai ga Zainab tazo da karamar waya Tecno mai memory,Tsohuwar ta Anty ta ce aka bata akwai Memory aciki ita Amina waya ba Damunta tayi ba Shiyasa bata Damu ba
Acikin yan ajinsu akwai masu waya Ranar an tashi Break Taji Zainab na ma wata Saratun ajinsu mganar ta Turamata Sabbin Wakoki
Tana Daga sit dinsu tana karatun Wani Littafin da Zainab ta aro mata mai suna Yar Jagora.
Duk da kunnenta baya wajen taji Sunan Radau acikin kanta.
Saratu ta kalli Zainab tana Fadin"Ni ban da wasu wakoki Zainab..Sai dai ina da Sabbin wakokin AMINU buba Da yayi kwanan in kina so sai na Tura miki..!
Kamar a mafarki taji ankira sunan ta Taba jin sunan ta kuma Haddace sunan acikin kanta.
Da Zumudi a Murnan Zainab tace"Yauwa don Allah sakamin..Ina son wakokinsa..!
Daga sama kawai suka ga Amina Sanda ta Dafa Saratu tana Fadin"Wani Aminu Buban..?
Da mamaki suke Binta da kallo kafin Zainab tace"Mawaki ne mai Tashe Amina..!
Ido ta zaro kafin tace"Da gaake..?kina da Hotonsa..?
Zainab cikin mamaki tace"Hotonsa kuma..?a"a ni bani dashi wakokinsa kawai nakeji shima a wayar ya Kamal nasansu..!
Saratu ce tace"Yayata nadashi in kina son ganinsa ki bari gobe zan turo miki..!
Da sauri Amina tace"Yauwa don Allah ki turomin akwai wani dana sani ne in so nagani ko shi ne..!
Da mganarta suka yarda da ita Washegari kuwa suna zuwa makaranta Saratu tace ma Amina ta Turo Hoton a wayarta Vivo Lokacin da Amina ta ga Hoton sai da Gabanta ya Fadi.
Yana Sanye cikin Riga da wando Ja da Fari Wandon Ja ne Rigar ciki Fara sai Jaker dinsa ja Takalmin kafarsa Booth ne fari haka ma Facing cap din Kansa Ja ne mai Kalan Fari yayi Tsayuwar matasan wannan zamanin Fararan Hakoransa mai Wushirya duka suna waje a kasan Hoton an sanya A.A BUBA..!
Sai alokacin Amina ta tuna yana ta Nanata mata bata sanshi ba..?Ashe cele ne shi to ita ina zata sanshi..?
Ba waka suke ji ba ballatana kallo.
Saratu ta karbi Wayarta tana kallon Amina Zainab isa ce tace"Shine..?
Sai ta samu kanta da girgirza kanta Saratu tace"Kila suna ne yazo Daya..Shi wannan Aminu Aliyu Buba sunansa mawaki ne mai tashe yadda naji ana Fada bai Dade ba sunansa yayi Fice..!
Amina na jinsu batace komai ba Zainab ce ta karba tana ganin Hoton kafin tace"Kyakyawa dashi kamar Bafullatani..!
Saratu tace"Ance Bafulatanin Yola ne..Karatu ya kawosa kano..ya fada Harkan waka..!
Amina ita Daga Lokacin batama jinsu Tana chan Tana Mirmishi Lalle Amina mai Sa"a ce yau ga Wanda Duniya ta sani ya Taba cewa tana Burgesa anya in ta Fadama Mutane zasu yarda da ita..?
Taso gaban irin su Sa"adatu ne ta tabbata sai Haushi ya kashesu ita Kadai kawai in ta Tuna A.A Buba ranta sai yayi Fari kanta ya kara Girma Ho..Sai ita Amina Aminene Manya kasa..!





*Janafty*
[9/3, 2:30 PM] Aysha📚: *TA FITA ZAKKA..!*
_(Aminene)_
*BOOK 1*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty❤️*



*🅿️14*

Kimanin Sati Biyu kenan da Watsewar Bikin su ya Zulaihat baki na nesa da na kusa duk sun koma Gidajensu Goggo Husai ce mutanen Jordan da ya Jadwa basu Tafi da wuri ba saboda Mtsalan Visa sai cikin Satin nan suka samu tafiya.
Amaran suna gidajensu cikin Koshin Lafiya sai Fatan Allah ya Zaunar dasu Lafiya Bakin Madina ne kadai ya Rage basu koma ba suma suna ta Shirin Tafiya cikin karshen watan da muke ciki Zasu fara sabuwar shekarar Musulunci achan Madina din.

Yau ta kama Laraba ce Tun Safe Amina ke kwance kanta na ciwo Daga Dakinsu sai ta koma Dakin Mamanmu saboda Hamida ta isheta ta Mitar ta tashi ta gyara Kayanta data Zube kan gado wajen nemam Hula ta saka ma kanta ita kuma ta mata banza Tun bayan kallon Hamidan da tayi tana Fadin"Don Allah Hamida ki gyaramin kin ga fa ban da Lafiya..!
Hararanta Hamida tayi Kafin tace"Kin ma isa..?Wlh bazan gyara ba Daga neman Hula sai ki baro da Duka kayanki a kasa ai da gangan kikayi Tunda kinsan kina da mai gyara miki yau kam bazan yi ba ki tashi ki gyara da kanki ko kuma ki bar Kayan naki su Rube anan wajen..!
Amina kallon Hamida ta Rikayi acikin Ranta Tana Tunanin Hamidan ta Rage Mutumci yanzu ganin dagasken bazata gyara ba kuma tana ta Damunta yasa ta mike ta Bar mata Dakin Tana Fadin"Kici kanki ke Kadai..!
Allah yasa ya Zeenatu bata nan Tana makaranta Sai su agida tunda basu fara zuwa makaranta ba tukunnah.
Dakin Mamanmu ta shige ta Kwanta Chan saman gadonta Batama san tana ciki ba sai Daga baya ta shigo ta ganta Tashinta tayi tace ta tashi taci wani abu tasha Ko panadol sai da mamanmu tayi da gaske sannan Amina ta tashi tasha Tea ta Hada da Panadol ta koma ta kwanta Sai barci kuma barcin mai Nauyi ne ya Dauketa Ta Dadebatayi irinsa ba Tunda ba barcin Rana Amina keyi wani Lokaci ba.
Ba ita ta farka ba sai Wajen uku Saura na Rana taji kan nata ya Sauka sai kuma Kasala ya kamata ta kasa tashi ta koma ta kwanta Sama sama tana jin kamar tashin mganar mutane Daga Falon Mamanmu sai dai bazata iya tantance ko su waye ba Ita duk a zatonta su ya Zeenatu ne da Hamida yasa ta gyara Kwanciyarta sai Bayan La"asar taji mamanmu na Kiran sunanta Idanuwanta Cikin yanayin Barci da Nauyi ta Bude manyan Idanuwanta ta Sauke kan Mamanmu wacce ke Tsaye kanta tana Fadin"Amina ki tashi hakanan kiyi sallah kici abinci in kan bai Daina ba In Aba din ku ya shigo na Fadamai ko Asibiti sai akai ki..!
Amina na shirin komawa barcin Mamanmu tace"Tashi mana Amina...Kada ki koma barcin nan .!
Dole yasa ta mike tana Mika Lokaci Daya tana Fadin"Wash...!
Mamanmu na Shirin Fita Daga Dakin tace"Ki rika Salati mana Amina.!
Daga haka ta fice Daga Dakin Dakyar Amina ta zuro da Kafarta Ta Sauka Daga kan gadon tana gyara Zaman Doguwar rigar Dake jikinta na Wata jar Atamfa Sai ta Dauki Hulanta ta Rufe kanta sannan ta fito Daga Cikin Uwar Dakin kanta tsaye ta fito Falon Sai dai Fuskokin data gani ne yasa ta Dan Tsaya tana binsu da kallo kamar yadda suma suke kallonta.
SArood ne ta washe mata Fararan Hakoranta daya sa itama ta Sakar mata Dariya.
Sakina kuma Kanta na kasa tana Danna wayarta Sai da taji mamanmu na Fadin"Kin taso..?ki farayin Sallah sai kici abincin ina Fatan kan ya Sauka..?
Da kai ta mata mgama ganin yadda Sakina ta Dago tana mata kallon Sama da kasa,Mamanmu ta cigaba da Fadin"Matan D'ammallam ne suka zo mana Sallama jibi zasu koma tun Dazu suka zo Lokacin kina ciki kwance..!
Amina ko Tsayama bin mganar mamanmu batayi ba har takai Kofar Dakin Sanda Taji Sakina na Fadin"Yarinyar nan bata da kunya
Bata iya gaisuwa bane..?yar wajenki Hamida ta fita hankali da natsuwa..!
Sanda Amina takai Tsakar gidan Sai data juyo ta Harari Dakin na mamanmu kafin ta Murguda baki afili tace"Eh din baza"a gaishekin ba..Mutum sai gajarta kamar an kife kwarya..!
Tana jin Sanda mamanmu ke Dariya tana Fadin"Amina ta dai fi Hamida baki ne ita kuma Hamida ta fita Hakuri..!
Tabe baki Amina tayi kafin ta karisa Cikin Kitchen Babban Cooler da suke zuba abinci ta Bude Farar shinkafa Akayi miyar kifi bata wani Dameta ba,Kadan ta Diba ta saka Miyar nan Kitchen din ta zauna taci ta Bude babban Fridge din Dake Kitchen din ta Dauki Ruwa tasha Tana cikin shan ruwan sai ga yaya ta shigo Kitchen din,Kallonta tayi batayi mata mgana ba ta wuce tana Bude Dirowar saman Kitchen din Ko kallon inda Aminar take batayi ba sai da Aminar tace"Yaya duk yau ban ganki ba..!
Bata kalleta ba tace"ina zaki ganni tunda baki je inda nake ba..?
Meyasa baki je makaranta ba..?
Amina tace"Ban fa da Lafiya ne Tun Safe..!
Yaya ta Dauki kulin Ararrabinta Data ijiye ta fice Daga Kitchen din tana Fadin"Allah ya sauwake..Tunda kin ji Sauki ki kwashe kwanuka nan ki wanke yau hamida da Zeematu sukayi ta aiki acikin gidan nan..!
Baki Amina ta Tura afili ta Furta"Hamida bata da mutumci yanzu..Shine ko tamin ko..?
Kyafci tayi domin ta Tsani wanke wanke gwara tayi shara Daman Hamidan take tusama wanke wanken Sau tari ita kuma sai tayi shara to kwanakin nan taga Hamidan ta waye ne sai tace kowa yayi aikinsa.
Batasan komawa Dakin mamanmu Tanayin alwalanta ta shige Dakimsu kayanta kan gadonta Hamida ta Tula mata su baki ta karkace batayi mgana ba bayan ta idar da sallar kan gadon Hamida ta koma ta kwanta tana jin bayanta ya gaji Tunanin yadda zata fita tayi wanke wanken kadai take yi kara narkewa tayi In mamanmu tazo sai tace ciwon kam ya Dawo Dole Dai yaya ta kyaleta Domin mamanmu bazata barta ta fito bata da Lafiya tayi wani aiki ba.
Sai dai addu"arta bata ci ba Domin tana jin an Daga Labulen Dakin ta kara Lafewa har tana wani Nishi Sama Sama Yaya ta kalleta kamar tayi Dariya ammh sai ta kanne Cikin Kaushinta tace"Zaki taso zuwa aikin ki ko kuwa sai na shigo na iskoki kan gadon nan..?
Amina ta tura baki jin Muryan Yaya Kafim ta Mike Zaune tana Fadin"Kai Yaya ciwon kan fa bai daina ba..!
Labulem ta saki Tana Fadin"Ki gama aikin ki in bai Daina ba In Jafaru ya shigo sai ya kaiki Chemist ayi miki Allura..!
Ido Amina ta zaro Kafin ta Diro Daga kan gado afili ta Furta"Na yarda yaya bata Kaunata..!
Yadda ta Tsani Allura kuma sannan ma a rasa wanda zai kaita sai ya Jafar ai data Kade har gayenta an samu mugayen duk sum koma inda suka fito ya shamsu ne sai a islamiya suke Haduwa su ya Jafar kuma sai dai taji muryansu in sum shigo gaida su yaya bataama yarda su hadu tun bayan Watsewar sha"anin suna gida Tunda ba makaranta suke zuwa ba ko Hanne ta rage shiga wajenta itama Ganin haka yasa sai ta kwana Biyu bata shigo ba sai dai su hadu a islamiya da yammah.
Hakanan tana Tura baki tana kunkuni ta fito da kwamukan wanke wanke zuwa Bakin Famfo Dakin mamanmu ta leke bakowa ita ta shiga wanka su Sakina kuma suna Dakin Yaya Daga Tsakar gidan ma tana jiyo Tashin Hirar Sakina da yaya Sarai Sarai ta kwashi kwanukan da suka bata nan Falon mamanmu tana kunkuni ita Kadai.
"Sun wani zo sun bata mana kwanukan sun karamim aiki..Mtsewww..!

Nuku nuku ta dinga yi Saboda Mamanmu ta fito ta hanata sai dai Addu"arta bata amsu ba Mamanmu bata Leko ba sai ma yaya ce ta Leko raka su Sakina suka leka Dakin mamanmu suka mata sallama sai gasu sun fito Tare tana gyara Daurin Dankwalinta Lokaci Daya tana Fadin"Ke Sakina yar"uwar taki bata jin Hausar tamu sai labarcimu kuma bamu kware ba..!
Tafada tana Dariya Sakina ke Fadin"Mamanmu wanda aka Haifa achan yayi Rayuwarsa achan ina zai ji Hausa..?Sai dai hankali zata iya Tunda yanzu ta shigo Cikin mu..!
Yaya tace"Kwarai tunda ta auri Bahauahe ba..koda yake shima ai Danmallam din Harshensa ya Karye kamar Balaraban chan..!
Mamanmu tace"Ai ya Dade fa achan yaya..Ina jin yafi shekara goma ko..?
Sakina tace"Yana cikin shekarata ta ashirin ne fa naji yana Fadi..!
Mamanmu tace"Koda naji..!
Yaya tace"Zai yi fa Tun su Zahra na kanana fa alokacin..!
Ita dai Sarood sai dai tayi ta washe baki in ta tambayi Sakina me akace ne sai Sakina ta gayamata da Larabci Duk da itama ba wani kwarewa tayi ba Harda iyayi ita Adole tana jin Labarcin.
Amina na Tsugunne tana wanke wanke ta tabe baki aranta tace"Allah yasa ma tasanme take fadi..!
Mamanmu ce ta ganta cikin jin Dadi tace"A"ah jiki yayi kyau Amina..!
Dole ta Dago tana yake tace"Eh Mamanmu kam ya daina ciwo..!
Da sauri tace"Masha Allah..To kiyi Sauri ki gama kada mangariba ta Sauko baki gama ba!
Da toh ta amsa batare data kara mgana ba,har suka wuce har korido suka Raka su Sakina suna kara musu sallama da alkawarin agoben kafin su tafi zasu shigo gidan su kara yin sallama.
Tana jin har sanda su mamanmu suka Dawo tana mata Fadan tayi ta gama Ko mgana ma batayi ba da kai ta kara amsaa mata,nuku nuku ta Dinga yi sai tafi minti Biyar bata wanke Kwano Daya,Har Su hamida suka shigo sun Dawo Daga islamiya Ya Zeenatu ne ta kalleta tana Fadin"Har duhu ya shiga Amina kina zaune bakin Famfo alhalin kinsam har Aba yayi Fadan hakan.!?
Amina taso ta dago tace"Ina Ruwanki ne..?
Sai kuma ta fasa ta Tura baki ta Kauda kanta Ya Zeenatu ta wuce tana Fadim"Ke kika sani..!
Hamida ne ma tace"Kin warke kenan..!
Daman jiranta take sai ta mike ta Rike kugu tana Fadin"Ina Ruwanki..Im ma na warke in ma ban warke ba..Duk ba Damuwarki bane..Kada kuma ki Dameni Mutum ba Taimakaa maka zai yi ba sai ya isheka da mita akyaleni ko sai gobe ne in gama ina Ruwan wani..!
Hamida bata tanka ta ta wuce Daki abunta ta ijiye jakarta,Duk tana wajen suka fito sukayi alwala ba wanda ya tankata ta juye Jidalinta akansa itama sai Harare harare take yi karshenta dai kan Jawad ta Sauke Haushinta wai ya Watsaa mata Ruwa haka ta mike ta Rikeshi ta Falfalmai mari har sai da yayi kuka da kuka ya fita masallaci Lokacin Yaya tana Sallah Hamida ce awajen kuma batace komai Domin tasam ba karamin aikin Amina bane ta Dawo da duka jidalin kanta Shiyasa bakinta kanin kafarta ta koma Daki.
Amina har aka Idar da salla tana bakin Famfo bata gama wanke wankenta ba,Yau din ma Ya Danmalam ya bada Sallah Ita Rabonta da gansa tun Ranar Daurin aure da yayi mata wannan Tijaran ta gujema haduwa dashi Shine mutuum na Farko Daya taba Cin Zarafimta bata samu ko Baki ta Turamai ba yana da ta wata baiwar da komai Rashin kunyarka sai kaji Shakkarsa.
Afili ta Furta"a Muryansa kamar mai kirki nan kuwa cikinsa fal Tozarta Mutane..!
Bazata ce taji Sallamamsa ba Daga sama kamar acikin kanta taji Sansanyayyar Muryansa cikin Zatinsa yana Fadin"Waye anan..?
Ya ke fada domin Lokaci akwai Duhu kuma ba"a riga a kunna injin ba.
Kyam Amina ta kame Daga inda take Sai kuma jikinta ya fara rawa da taji Muryansa batasan Dalili ba Bata son Haduwa dashi bata son jin muryansa Domin Fadar mata da gaba Muryansa yake yi sannan Uwa uba ganinsa ba Alheri bane sai ya Tozartata.
Kokarin Fito da wayarsa yake ya Haskata sai Haske ya gauraye Tsakar gidam,Nepa sun kawo Wuta Daidai Lokacin da Idanuwan Amina suka shiga Cikin na Umar Dake Tsaye Gabda da ita yana kallonta kamar yadda itama take kallonsa.
Sanye yake da Jallabiya mai Ruwan kasa da Hula a saman kansa sai Bakin Wandon Dake jikinsa Tunda Jallabiyar bata kaai mai Kasa ba.
Fuskarsa ta kara kyau ya Kara Haske har wani Kiba taga ya karaa mata.
Cikin mamakin ganinta acikin wannan yanayin yake Fadin"Ke me kike yi anan da Mangriban nan..?
Yake Fada yana kara Nazarinta da Sauri ta Sadda kanta kasa ta kasa mgana,Jikinta ba inda baya rawa,Lebenta Kamar ya Nane haka taji ta Kasa mgana shi kuma Ransa ya fara baci yarinyar nan bata da kunya Rainin Da take yi ma su Jafar shi take so tayi mai yasa ya Dakaa mata Tsawa Cikin Bacin Rai yace"Bada ke nake mgana ba..?Kika bari na nazo wajen nan sai na Lahira yafi ki jin Dadi..!
Ki bari na taso ki gani..!
Tsawamsa shi ya fito da su Hamida Harda Mamanmu da Yaya sai suka ga Danmallamm
Mamanmu ce ta washe baki tana Fadin",A"a Umaru barka da zuwa!
Kallonta yayi kafin yace"Mamanmu me yarinyar nan take yi anan wajen nan har yanzu..?
Mamanmu tace"Amina ce wanke wanke take.!
Katseta yayi da fadin"Haba Mamanmu tana mace?
Da mangariban nan ita Kadai acikin Duhu bata tsoron lafiyarta.?
Mamanmu ta kalli Amina da Kanta ke Kasa tana ta fiki fiki da ido tace"Wlh Danmallam sai da nayi mta magana Tayi ta gama Kafin Dare yayi..Dayake ba Lafiya ne da ita ba..!
Amina taso daga wajen nan Hamida da Zeenatu ku taaimaka ku karisa don Allah ina ga Kan ne ya Dawo mata!
Zeenatu tace"Mamanmu Wlh lafiyarta kalau Aminar ce baki sani ba!
Hararanta tayi Kafim tace"Bazaki yi ba kenan?
Dole tayi shuru bata kara mgana ba Amina kuma kamar mumafuka kanta na Kasa ta taso tsomai Tsomai kamar Wata kazar da aka Cirota Daga Ruwan Zafi Danmallam ya bita da kallo Cikin kyama aransa yana Tunanin yarinyar nan ta wuce Tunaninsa
Yaya ce ta faraa mai maraba tana Fadin"Maraba da zuwan Dan mallam
Ga bakin Larabawa..Lale..!
Jin Muryan yaya yasa ya kariso Cikin Fara"a nan Tsakar gidan ta Shimfida mai Darduma ya zauma suka Fara gaisawa Zeematu da Hamida suka gaisheshi ya amsa kafin mamanmu tazo ta zauna su gaisa Daganan ta koma Daki ta bar su shi da Yaya suna ta Fira
Amina dai tunda ta samu ta shigo Daki bata kara fitowa ba Hamida da Zeenatu suka karisa aikin suka maida komai Kitchen suka share wajem abayin Dakin tayi alwala tayi sallah Ta Haye kan gadonta bata Damu da Kwashe kayanta akansu ta kwanta bata Damu ba

Ya zeenatu ne ta shigo tana ta Fada Fadi take"Wlh Amina ki rika Karisa aikinki..Domin nan gidam ba bawanki..Ni ba Hamida bace Darajan Mamanmu kikaci Wlh..!
Amina na jinta tana Danne Dariyanta Daga kwamcen Tana kallonta kai ta kada kafin tace"Ba Laifinki bane..Mamanmu ce take Daure miki gindin Iskanci Watarana ai ba Maman ko..?
Naga uban da zai zauna kina wannan iskancin bai ci ubanki ba..!
Ita dai bata tanka ba har ta gajii da Mitan ta fice bayan Fitar Danmallam Daman Sallama yazo yi ma su Yaya Gobe Jirginsu na dare me zai tashi zuwa Jidda a Filin Sauka da Hawa na Aminu kano.

Sai da ta ficen ne Amina ta fito da Dariyanta tana Fadin"Allah Sarki..Ya Zenatu kawar ya Abida...!
Hamida ta kalleta kafin tace"Ke kam ki tashi ki gyara kayanki Amina Harda fa Sabbi ciki..!
Amina ta kyabe baki kafin tace"In kin Damu ki gyaramin Hamida!
Hamida tace"Na rantse kuma bazan yi Kaffara ba..!
Tsaki Amina taja Kafin tace"To sai ki kyaleni malama!
Hamida tace"Yau anyi Fada da Mariya da Sa"adatu..Har da Dambe sai da mallam Auwal ya Zanesu..!
Da Sauri Amina ta Mike tana Fadim"Don Girman Allah..?
Hamida tace"Wlh suna Zage Zage..Kinsan Hanne da tsoro sai kuka take yi..!
Amina ta Daka Tsalle har da shewa kafin tace"Ahyayyeee...Yau naji Dadi karshen alewa kasa.
daman ai xaman munafunci baya karko..Tacizi yatsa Kafin ta cigaba da Fadin"Naso yau naje..Da sai na kara Yamutsa wajen munafukai..!
Hamida tace"Gwara dai da baki je ba..!
Amina ta balla mata kafin tace"Ga Shedan ko..?
Hamida kina shigarmin hanci fa ki kyaleni.!.
Hamida tace "Daga Fadin gaskiya..?ai ba karya nayi ba Da kina nan wajen Allah kadai yasan iya inda abun zai kai..!
Amina ta karkace baki kafin tace"Hanne wai me aka mata take kuka..?
Hamida tace"Me kuwa..?tsoro gareta Taga suna Ta kwasan Dambe..!
Amina tace"Aikin banza Hanne banza ce..Meye abun kuka..?
Allah ya Tsareni..!
Hamida dai bata kara mgana ba Domin Har ga Allah taji Dadin da Amina bata zo ba Domin Allah kadai yasan Iya inda Fadan nan xai kai Amina sai ta hau Fadan ta siyeshi ta kara Maggi da gishiri.
Waashegari Da Safe ta shiga wajen Hanne ta iske Su Sakina suna gidan suna ta shirin Tafiya Ya Jafar zai kai su kano Ya Nasir yana da aiki a asibiti.
Amina ta kalli Hanne tana Fadin"Wai ganin ana Fada da Sa"adatun ne kike kuka..?
Hanne tace"Ni bana son ganin ana Dambe ne..Ko ke kike Fada ai ina kuka..!
Amina tace"Wlh karya kike yi..Natan Dai kike kuka ke mai yar"uwa Ki kama Kanki Hanne Domin in kece Dariyama zata yi kina abu kamar wata sakarya..!
Hanne tace"Bakomai naji..!
Kinsan yau su ya Danmallam zasu koma..?
Amina ta tabe baki kafin tace"Jiya sun zo gidanmu naji Mamanmu na Fadin yau zasu koma
Dukkansu zasu koma..?
Hanne tace"eh mana..!
Amina tace"To in suka tafi sai yaushe..?
Hanne tace"Yace ma Hajiya sai wani abu ya taso..Im bai taso ba sai nan da wata Shidda zai zo..!
Amina tace"Allah ya tsare..!
Aranta kuma Fadi take"Allah ya raka taki gona..!
Lallabawa tayi ta gudu gida abunta batama san Tafiyarsu ba su yaya dai da mamanmu sun je sun karayin musu sallama sai yamma suka Dawo suna Fadin wai har ya Jafar ya Kira suna kano basu dai tashi ba sai Dare.
Sai washegari wajen chan Rana taji ana Fadin sun sauka a jidda Daganan zasu hau Mota zuwa Madina ko ajikinta Sai taji kamar wani Nauyi ya tafi Bata ko kaunar ganinsa ma ballatana jin muryansa.

*******

Bayan wata Daya..!

Amina na kwance da Safe tana barci Taji ihun Hamida asaman kanta tana Dukanta Lokaci Daya tana Fadin"Amina tashi..Tashi.!
Next week zamu fara zuwa makaranta an gama mana komai..!
Amina da sauri ta Bude idanuwanta cike da barci tace"ke a ina kika ji..?
Hamida tace"Yanzu naji Ya Jafar yana Fadama Mamanmu..!
Amina tace"Ina zamu koma..?
Hamida tace"Ina kuwa..?Unity...?
karamin tsaki taja kafin ta gyara kwanciyarta

Please Login or Register in order to submit comment