Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ko
matakin da Haj Yay tace zata dauka a kaina ne?wata
zuciyar tace duk ba wannan bane tafy yayanku ce
wannan amsar da zuciya ta bani itace sanadiyar tashina
zaune saboda tashin hankali da naji ni a ciki na mike ina
safa da marwa nace a fili ban so akayi wannan rikicin ba
ba zanji dadi ba muddin yayanmu ya tafi kai zanje na
bashi hakuri in ya tafi na mutu,da sauri na dauki hijabina
na fita falo nan nayi turus ganin mama a falon tace ina
kuma zaki?karon farko da na soma yi mata karya nace
gidansu Amira tace me xakiyi?nace takalmina da gyalena
dauko tace ko bari zata aiko maki ko ki aika Jamila kar
ki fita ko ina ynxu zo nan kiji,na isa gunta na zauna tace
kin dai ga abinda ya faru ko?nace eh tace to ina son kiyi
taka tsan tsan da kowa a gidan nan banda yawan
shigewa duk wanda ya saki aiki to kiyi masa kamar
yadda kikaji Alhaji yace maki,nace to ta kuma duba na
tace yanaga kinyi wani sukuku dake?nace bani son
tashin hankali ne mama shiyasa tace kar ki damu aikin
shedan ne kuma ki cigaba da addua sannan daga ynxu
zan na tashin ki duk dare in tashi yin nafila sannan zaki
dinga yin azumin litinin da alhamis,sai mu dinga tare in
kuma an gama bikin nan zanje wurin kawunki na samo
mana addu'o'i na tsari mu dukufa,Allah ya ja mana
gaba,sauran maganganun da mama takeyi duk banji su
ba ina ta tunanin yanda zan ga yayanmu don nasan nice
na jawo wannan tashin hankalin gaisuwar da naji mama
ta na amsawa shine yasa na juyo Mami ce ta dubeni
tace ya dai?na mike muka shiga dakinmu kan gado muka
zube na dube ta nace ya dai tace ina gidan walima muna
shirya guri sai ga Sa'a wai ana fada da mamanku da su
Haj Laure har sunce sai sun zane ku?nayi tsaki nace kan
fa kaya ne kin gansu nan jikina yayanmu ya bani ashe
irin na Anty mimi ne shi kenan sai tashin hankali gashi
yanzu ma yace zai koma jibi,Mami tace ai dama bayan
biki da kwana biyu yace zai koma nace to ai gashi ba'a
gama bikin ba ni gani nake ma duk laifina ne hawaye
suka zubo mani akan kumatu Mami ta tsaya kallona baki
bude shi ne harda kuka?kuma ma ina wani laifinki anan?
nace nasa kayan tace to baya baki don kisa bane?shi
yayanmu in zai ma mutum kyauta ba ruwanshi da wani
nuna bambanci nace rakani na bashi hakuri,Mami tace
tab ai sai dai kije ke kadai yayanmu ba ya son ai ta
faman bashi hakuri musamman in yana cikin tashin
hankali gara makin zauna,ke menene naki na damuwa?
kina ganin zaki iya hana shi ya tafi ne?nace bani na ja
komai ba,tace sannunki da kai ta mike zo muje gidan
walima nace ni kaina ma ciwo yake bazan sami zuwa ba
ta tafi na koma na kwanta na cigaba da kuka rurus,saidai
za'a a tsira ni ko da bindigane ba zan ce ga abinda nake
ma kuka ba sai da nayi ya ishe ni sannan ciwon kai ya
yomin sallama kafin wayewar gari nayi rigif ko sallar
asuba kasa yi nayi sai wurin bakwai na safe yinin ranar
nan haka nayi shi, misalin karfe uku Alhj ya shirya da
Yaya Abdulrahim yace Habiba danku zai wuce fa,kan
Mama tayi magana shima Yayan namu ya shigo ban san
lokacin da na mike ba ya zauna a kan kujera yana gaida
mama bayan ta amsa sannan ta ce ikon Allah tafiyar ta
tashi ne Abdulrahim?na dauka gobe ne?yace eh gobe ne
zanje lagos ne na kwana shida na safe jirginmu zai tashi
yanzu ma jirgin karfe biyar zanbi zuwa lagos din yana
magana niko bakinshi nake kallo da sauraron muryarshi
mai dadi tamkar ba namiji ba ne yake magana ba Mama
da Alhj suka shiga dakinta ya bisu da kallo sannan ya
juyo ya dubeni na dukar da kai gabana sai faduwa yake
yi,ga mamakina naji yace Amina nayi sauri na dago kai
baki bude ina dubanahi shima ya kafa min idanu na
sunkuyar da kai don ba zan iya cigaba da kallon kwayar
idonshi ba sai ina ganin wani abu yana fitowa daga idon
shi,yana shigowa nawa,murya kasa kasa yace zan tafi
kiyi mani addua kaina a kasa nace adawo lfy Allah ya
bada sa'a,a lebanshi naga ya amsa,Alhj ne ya fara fitowa
yana cewa Abdul walarka nace Mam zata baka?yace no
Maman Sagir kar ki damu ba sai kin bani komai ba Mama
ta fito da dambun nama dayawa tace to ka tafi da
dambun naman nan Iman tayishi shekaran jiya ya dubeni
sannan yace to zan amshi wannan sai naji wani sanyi a
raina suka fita nima na daga labulen dakinmu ina kallo
ga yan biki nan sai a dawo lfy suke mashi harda su Haj
Yaya dasu mama aka fita harabar gidan wajen ajiye
motoci nima na fito ina daga can baya ina kallonsa har
aka shigar mashi da jakunkunan shi cikin boot din
motarshi yaya Kabir ne zai jashi,ga wasu abokanshi
suma zasu shiga wata motar ya fito daga dakinshi har
ya sauya kayansa da jc jajaye masu ratsin fari dogon
wando da riga mai dogon hannu sai takalmin kwallo Anty
Mimi ma ta fito sai kuka takeyi haushinta ya kamani a
ganina nice yafi dacewa inyi kuka ba ita ba ko mai yasa
oho zai shiga mota kenan ya hango ni sai naga ya tsaya
yana kallona har Anty Mimi ma ta juyo taga wa yake
kallo?sai taga ni yake kallo sai naga ta kawar da kai niko
sai na kwantar da kaina a jikin bango sannan na daga
mashi hannu alamr bye bye sai ya shige mota suka tafi
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Tun daga wannan rana ban kuma wani sukuni ko
walwala ba har mamakin kaina nakeyi kullum cikin
damuwa bana wani cin abincin kirki gashi kowa ya gane
halin da nake ciki a gida da makaranta sai dai kowa ya
tambayeni sai nace bani da lfy ne.Azumi da nafilflii
kullum cikinsu nake
,ranar da yayanmu yayi kwana biyar da tafy Mama taga
abin ya isheta bani magana sosai koda yaushe a kwance
ga jarabawa ta matso amma bana wani krt sati da lahdi
suka zo suka wuce amma banje islamiya ba wato
(sanawiyya),Ranar monday mama tace kar naje
makaranta na shirya muje Asibiti nace lfy ta kalau tace
na dai shirya muje kawai rimi clinic mukaje mama tayi
ma likita bayanin yanda nakeyi,likita ta barshi dani bayan
fitar mama sai likita ya dubeni yace sanar dani yadda
kikeji sai nace kasala nikeji sai kirjina da ke min nauyi
kuma bani son yawan surutu yadan gwaggwadani sannan
yace kina yawan tunani ko?nace eh yace to tunanin me
kikeyi?nace ba komai yace karya ne da na rasa ta cewa
sai na ce jarabawa ce nake tunani ba dan ya yarda ba
yace to shi kenan ki daina yawan tunani kisa Allah a
gaba ya rubuta mana magunguna muka tafi,haka nayi ta
shan magunguna amma tamkar ana zugani Mama ta
koma na gargajiya ni dai nawa shane a haka jarabawa ta
same ni mukayi ta nidai ban sa rai da zanci ba ranar da
muka gama ne a nata murna masu hoto nayi,niko sai
kallon mutane nake,Mami ta dafa ni tace ga wata yar
ajinku can tana nemanki nace ina take?ta nuna min ita
ashe Hauwa'u Aminu ce nan tamin korafin rashin sanin
gidanmu ita kuma ta bani no wayarta ni kuma nace mata
in na fara anfani da tawa sai taga tawa lambar,sai da
zamu bar harabar makarantar ne sannan naji duk kewar
makarantar ta ka mani.Abdulrahim zaune a kan kujera a
cikin falon Hotel din da yayi masauki, ko nace nan ne
dama club dinsu suka kama mashi tun farko,kanshi yana
jingine a bayan kujera, tebur ne dan karami cike da
kayan ciye ciye da shaye shaye amma sam ya kasa cin
komai tunanin yakeyi wayarshi tayi kara ya juyo ya dube
ta kamar kar ya dauka sai kuma ya dauka Mimi ce ta
kirashi bai san dalili ba sai yaji wani kunci a ranshi amma
sai ya daure ya dauka,tace yayanmu kana lfy?yace lfy
kalau,yake dinfa?tace ina nan lfy dama naga tunda ka
tafi baka kira ba ne,yau kwana shida kenan?yace ban
sami dama bane,tace to ina jiran kiranka,yace to kawai
ya kashe wayar juyawa yayi ya dubi abincinshi kusan
minti arbain kenan da kawo abincin amma ya kasa ci ya
kai hannu ya bude plate din abincin da yafi so yayi order
amma sam sai yaji kamshin abincin ma baya mishi dadi
kokadan a fili yayi magana yace yarinyar nan ta bata ni
da kalolin abincinta masu dadi,yayi shiru yana tunani tun
zuwan shi kasar nan bai wani ci abinci ba daga ruwan
lipton sai dambun naman nan,kwankwasa kofar akayi ya
bada izinin a shigo ne abokinshi ne shima dan kwallo ne
amma shi bature ne ya dubi Abdulrahim sannan yace
cikin turanci Maska naga baka shirya ba ne,wannan
karon baka so dawowa ba ne tunda ka dawo sam baka
da kuzari,me yasa?Abdulrahim ya mike yana fadin
tunanin gida nakeyi ya shige dakin barcinsa shima ya
shiryo cikin JC na training suka fita.A daran daya cika
kwana bakwai da zuwa yana zaune a harabar Hotel din
haske ne ya kewaye gurin kamar rana gabanshi
gwangwanin coke ne da dan karamin plate cike da
dambun nama sannan ya kai hannu ya dauki wayarshi ya
soma sana'ar wato danne danne wayarshi can yayi tsaki
ya kashe wayar ya mike,da ya kamata ya nufi gurin
abokanshi ne tunda ba dare ne yayi sosai ba kuma yasan
zasu sa ran zuwansa, amma sam sai yaji ba zai iya ba
saboda wani abu da ya taba zuciyasa sama ya nufa
dakinshi ya zauna a bakin gado sannan ya aje tarkaccen
hannunsa a kasa wayarshi ya rike sannan ya soma
sarrafata cikin kwarewa, Babanshi ya kira bayan ya
dauka sai yace Alhj ina yini?bayan sun gaisa sai yake
cema Alhj dama ya kira ne dan ya amshi lambar wayan
Maman sagir domin yana da lambar kowa a gidan itace
bai da ita,Alhj yace gata nan ma Habibar ku gaisa,bayan
sun gaisa ne sannan ya bukaci lambarta ba tare da wani
tunani ba ta bashi,ya jima yana tunanin dalilin karbar no
kafin daga karshe ya gane sai dai wani tunaninshi abin
zai zamar mashi abin kunya da nunawa cikin
abokai,muddin suka san halin da yake ciki,nan a dalilin
wata kankanuwar yarinya wacce da yayi auren wuri
tabbas zai haifi kamarta.Kwance yake akan gadonshi
amma sai sautin daddadar muryar yarinyar yake dawo
mashi ya tuno ranar da bashi da lfy duk gidan ba wanda
ya kula dashi tamkar ita muryarta ya tuna sannu
yayanmu za ai maka wani abu ne?ya sake tuno yanda ya
kara tsorata ta ranar da ta daukan mashi kujera tabbas
in tana cikin tsoro tana matukar burgeshi yayi magana a
fili inda yace nayi missing din ganin tsoranki.
(Lallai Iman kinga takanki, mudai daganan sai muce!
Allah yakyauta)
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Ya cigaba da juyi a kan gado ba komai ke dawainiya
dashi ba sai begen yarinyar da yake gani abin kunya ne
ace ya sota ya tuna da mimi yarinya mai kyau jinin
larabawa sai dai shi baya jinta a ranshi yanda yake jin
wannan yar mitsilar yarinyar zai auri Mimi ne kawai don
bin umarnin mahaifiyarshi kuma ya san duk inda suka
shiga ba zai ji kunyar nunata ba a matsayin matarshi
shekarunta ashirin da biyar shi kanshi shekara biyar ya
bata bugu da kari gashi ta soma zurfi a karatunta,amma
in yace wannan yarinyar zai aurà shima yasan rigima zai
jawo,yanda mahaifiyarshi ta tsane su wata zuciyar ta ce
mashi ga yaran nan da rashin kunya tana jin kace kana
sonta to raini ya shiga tsakaninku gara ma Mimi hadaku
akayi kuma kasan ta mutu kanka don haka baza ta maka
wani rawar kai ba,"A dawo lfy Allah ya bada sa'a" ya
kuma tuno muryata da yaji na karshe sannan lokacin da
ta rakube a jikin bango tana mashi bye bye ya dawo
mishi tausayinta yaji lokacin kuma jikinshi na bashi kamar
itama tana jin yanda yake ji a ranta,zaune ya mike yana
magana shi kadai tamkar wanda ya tabu yana fadin
Amina kiyi hakuri bani da shà'awar auran mata biyu ki
bari in runtsa ya kuma fadawa kan gado.Niko yanzu na
zama kurma bana magana sosai ban kuma cika son
magana ba sai dai maganar su Amira ce ke damuna da
suka ce wai ina ciki mayen soyayya na dai ki sanar dasu
wanda nake so,inko har zancensu gsky ne to na debo da
zafi don ko in har yanda zuciyata ke mani game da
yayanmu so ne to ko shakka babu gara na rufa ma kaina
asiri nayi shiru da bakina don nasan ko yaji ubana zaici
don nasan ni ba ajinshi bace,me kamar Anty Mimi?
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
kammala karatuna shi ya ba samari damar damuna
tamakar anbi su an gaya musu musamman ma yaya
Kabir shine yasani wannan ya sani wancan,su yaya ma
suna zuwa,ban manta wata rana yaya Kabir ya aiko Sagir
dinmu ya kirani na fito na sameshi a daki kan kujera na
zauna fuskata na kallon wani katon hoton yayanmu
sanye yake da JC kore da fari irin na yan wasan Nigeria
hannunshi a kan kirjinshi daga gani lokacin suna taken
Nigeria ne aka dauke shi,muka gaisa da yaya Kabir ya
soma yi min zancen soyayya niko hankalina ba ya tare
dashi, yayanmu kawai nake kallo da kyaun da Allah yayi
mashi ba abinda ya birgeni irin shedar sallah daya fito
mishi a saman goshinshi yayi baki tamkar ya diga ina
cikin wannan tunanin ne naji yaya Kabir na min magana
da karfi nayi ajiyar zuciya sannan na dube shi nace ka
gama?zan shiga gida yace na tambayeki baki bani amsa
ba nace ni ban wani jika ba na mike nayi waje yana
kirana na fito kirana naji anyi daga bakin gate ko ban
juya ba nasan yaya Abubakr ne dogon tsaki naja sannan
naje ina zuwa na hau shi da masifa shima kallona naga
ya tsaya yi,ina cewa nace ni ba aure zanyi ba amma kun
dameni don Allah ku rabu dani ko dole ne?na juyo abina
wani abin haushi ina shiga falonmu sai ga yaya Suleiman
zaune suna hira da Mama...(hhhhhhhhha.yarinya taki
tasameki.)
dakin kwananmu na wuce nayi kwanciyata naki fitowa
ban fi minti goma ba mama ta shigo ta dubeni tace
Sulaiman ya dade yana jiranki wai me kika tsaya yi wurin
Kabir din?nace ya aike nine bayan na dawo kuma sai na
gamu da da yaya Abubkr na cigaba da cewa gsky ni dai
mama ki samu su yaya Abubkr kiyi musu magana nifa ba
aure zanyi ba su rabu dani mana,mama tace aike ma yan
uwanki ne kuma nasan in ki sanar dasu zasu kyaleki
sannan suna ganin girmana sosai bazan iya tunkararsu
da wannan zancen ba, nace haka fa shekaran jiya yaya
Ibrahim yazo wai har yana takama zaije ya samu babana
kuma ko ina so ko bani so shi zai bashi ni mama tace to
bisimilla ai ga kinan taci gaba da cewa don haka ma ni
koda auren ne cikinsu gara Abubakr din nace ni dai
dukkansu har yaya Sulaiman din hakuri zaiyi dani dan
bana son auren zumuncin nan mama ta fita tana cewa
dai gashi can ku gaisa,na dauki hijabina na fito falo
fuskata a daure muka gaisa yace to Iman gani dai na
kuma dawowa duk da kin sanar dani krt zakiyi shine na
yanke shawara ki yarda a daura mana aure ni kuma zan
yarje maki kiyi krt har kiga karshen biro nace mu bar
zancen nan, ina Nana?yace Nana tana nan jiya aka sa
ranarta goron ne ma na kawo ma Mama nace lallai Nana
yanxu itama auren zatayi?yace shine mutuncin duk wata
'ya mace nace to Allah yasa alkhair ni zan shiga na
kwanta ka gaida min da su baba uwa kace da Nana inna
jiran zuwanta, yace amsata fa? ko zaki yi min waya don
Mama tace kin soma amfani da wayarki nace jiya na
soma sai dai ni bata dameni ba don haka ko lambar ban
rike ba in Nana tazo taje maka da lambar yace ai bazaki
min ko flashn bane tunda kinsan tawa nace to na maka
na shige daki ina jinshi yana fadin barakiya?
Sannu a hankali zuciya da gangar jiki suka tsananta da
so kauna da kuma begen wanda bazasu samu ba sannan
ni naki yarda da cewa sonshi nake ban yarda da nayi
nutso a kogin sayayya ba sai da na samu kaina da rashin
barci,sannan na kama karatun littatafai na
soyayya,kallace kallace da basu dameni ba yanzun nakan
zauna nayi duk saurayin da aka nuno sai naga bai kai
yayanmu komai ba ni fa gani nake ba wani namiji wanda
ya amsa sunan namiji in ba yayanmu ba,yauma kwance
nake akan gado yar karamar Rediyon da nike yin karatu
ce na manna a kunnena kaset na wakar fim din kugiya
na sa wakar na ratsani Idona a lumshe sai nakejin kamar
nice nakeyin wakar, duka naji an dada min da sauri na
tashi ganin Amira da Mami shine yasa nayi ajiyar zuciya
nace kin dau alhakina Amira ta cire wayar kunnena sai
ta dauke Radion ta sa a kunnenta dajin wakar sai naga
ta cire da sauri tace Mami ji wannan kaset din Mami ta
sa taji sai naga sun dubi juna sukayi dariya nace wai
menene?suka zauna suna cewa zancenmu gasky ne
nace kamar yaya zancenku gsky ne?Amira ta dauke
fuska tace Iman mun gamsu nace me na muku?Mami
tace akwai abinda yake damunki amma kin kasa sanar
damu,Amira ta amshe damu ne da munhau gaya maki
nayi shiru ina tunanin me zan ce masu can dai nace
Amira,Mami kunsan yayyena Abubkr,Ibrahim da
Sulaiman?suka ce sosai ma kuwa nace dukansu sunce
suna sona ni kuma bani son ko daya sannan yaya Kabir
shima yace wai sona yake na mike tsaye don girmama
maganar da zanyi na cigaba da cewa ni kuma zuciyata
da gangar jikina sun nutse a son wanda bai san inayi ba
kuma koda ya sani ba zai soni ba don yana da wacce ta
fini kyau da ilimi da kuma shekaru,hawaye suka soma
zubo min na juyo da sauri na rike kafadun Mami da
karfiina cewa ku bani shawara kawayena ku taimaka min
da maganin da zan daina sonshi don kukan ku da zaku
san ko wanene da kunce lallai zuciyata tayi wauta,suka
kamani suka zaunar dani tsakiyarsu suka yi shiru dakin
ya yi tsit daga ajiyar zuciata da nakeyi sai karan fanka
can Amira tace a ina yake?kuma yaya sunanshi?nace
kuyi hakuri wata rana zan gaya muku don ba anan yake
ba Mami tace dakin gaya mana ai da mun san yanda
zamu bullowa abin nace no ko zan mutu bazan taba
tunkarar wani da namiji da sunansa ba yanzu ku bani
shawara yaya zanyi na daina tunaninshi suka yi shiru
can Mami tace rokon Allah zakiyi muma zamu taya ki
nace sai dai mukara don kullum yi nake amma ba sauki
sai dai abinda ya karu nan dai suka lallashe ni gami da
bani shawarwari.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Haka naci gaba da rayuwa cikin kunci,wata safiya misalin
karfe takwas Mama tana dakin Alhaji ta kai masa abin
kari ni kuma ina ta faman gyaran dakinmu na gama na
koma dakin Mama ina cikin aiki naji wayar Mama tana
ringin na dauka sai ga lambobin rakwacam na dauka
nace Assalamu alaikum sai naji ance
Wa'alaikummussalam,jin muryar da ta amsa nan da nan
na gane yayanmu ne farin ciki da na ji baya misaltuwa
ina wannan tunanin ne naji yace Naman Sagir ina yini?
nace ba ita bace ni ce Mama tana dakin Alhaji yace ok!
nace ina kwana?yace lafiya amma mu nan rana ce kuna
lfy?nace lfy lau yace to kice da Maman Sagir ina gaishe
ta dama don mu gaisa ne na kira kafin nace to har ya
kashe ranar nayi walwala har yamma don jin muryar abin
sona.
Share




DOCUMENT CREATED BY
ZAHARADDEEN SHOMAR
WHATSAPP 08168575100








Tawa Tasameni1-04
Posted by ANaM Dorayi on 10:13 PM, 30-Dec-15
__________ NA HALIMA ABDULLAHI K/MASHI__
Lokacin da zai tfy nan ko ince da zaya koma ina cikin
wannan tunani sai naji yace kin gama?dama na gama sai
nace e yace to gashi na isa na dan rage tsawo yace
wannan ya turo mani akwati naki ne sannan daya kuma
zaki kaima Mimi nata nace to nagode Allah ya kara
daukaka duk da bai amsa ba nasan yaji dadin adduar,na
dau akwatin nayi cikin gida Allah yasa ba kowa a tsakar
gidan ni da mama muka bude muna ganin kaya nayi
mamakin kayan domin suna da yawa bayan haka kuma
zasuyi tsada english ne kala bakwai sai jakunkuna da
takalma sai rigunan barci masu kyau sai wani zobe cikin
akwatinsa mai kyallin gaske,na dauka ina dubawa zobe
ne na zinari mai nauyi akwai stone mai kalar ruwa gargar
tamkar kankara in ka kura ma stone din ido zaka ga an
rubuta A guda biyu daya kan daya nace la mama duba ki
gani harda farkon sunana tace kin gode sai dai fa in har
irin na 'yan uwanshi ne to ba zaki sa su ba na dan bata
rai sannan nace bama iri daya bane na tashi na soma
gwadawa duk wanda nasa sai su zauna min tamkar a
jikina aka kerasu,da yamma ina zaune a daki ni dai bani
son zuwa aiken yayanmu domin na tsani ganin Mimi
nasan ma wulankanci zasu min Sagir ne yace yayanmu
na kirana dama a shirye nake ina son inga ko ya manta
ne in share in ya tambayeni daga baya sai nace na
manta ne nima haka na tashi na tafi dakin mama na
sanar da ita tace sai na dawo,su hudu na samu na
gaishesu suka amsa dayan cikinsu yace Maska wannan
ma sister ka ce?yace ban sani ba ya wani daka min
tsawa yace shiga ciki ki dauko jaka adidas kizo ki wuce
kin wani tsaya kina kallon mutane na shige
dakinbarcinshi da sauri ya juya gun abokanshi yana ce
mishi dj bana son aboida kuke min baku san yaran nan
da raini ba sai taga kamar sa'aninta ne mu wani yace to
Nasir fa da zai auri Mami kanwarka?yayanmu yace ai
yaga zai iya ne sannan nace mishi kar ya yarda ya kawo
min karanta raina shi ga manyan babys a gari yazo zai
nace gun wadannan yaran,jikina yayi sanyi na sabi jaka
na fito ya dubeni yace kikai mata saura ki dade na fito
ba tare da ya bani kudin mashin ba, gidansu Amira na
shiga bayan mun gaisa da mamansu tace min tana cikin
dakinta na shiga tace daga ina haka?nace ina zani zaki
ce ta ce to sai ina?na zauna bakin gado na ajiye jakar a
kasa na dubeta na nace don Allah zaki raka ni?tace ina?
nace malali gidansu Anty Mimi tace to jeki ki gaya ma
mamanmu sai na shirya kafin ki dawo nace to amma fa
kece zaki biya mana kudin mashin tace wane irin ni zan
biya nace to bai bani kudin mashin ba gashi har yana
cewa inyi sauri ni kuma ban fito da ko sisi ba na fito gun
mamansu na sanar da ita tace sai mun dawo muka fito
muka hau mashin sai malali
Yanda na zata hakan ce ta faru domin da Mamnsu wato
Haj Laure ta ganmu haka ta hau zaginmu wai mu juya da
kayan ba'a so inshi ba zai kawo ba to ya bari,Anty Mimin
itace ta hana tace mu kawo Amira tace ki barshi mana
sai mu maida Anty Mimi tace ke bani son rashin kunya
Amira tace ba rashin kunya bane ance ne mu juya dashi
na dubi Amira nace don Allah ki rufa mani asiri Amira ta
jani zamu juya Anty mimi ta biyomu ta fisge jakar ta juya
ni dariya ma abin ya bani,muna jiran mai mashin wani
yazo da mota a gabanmu ya tsaya ya dube mu yace
kuzo muje yanmata ina za'a kaiku?kafin nayi magana
Amira tace unguwar rimi na dubi Amira nace kina hauka
ne?tace zauna nan in ba zaki ba sai dai kiyi ta zama
anan yace magana fa nakeyi nace ku shigo muje nima
can na nufa,nace nidai ba zan shiga wannan motar ba
Amira ta bude baya ta shige sannan tace ai kina da
kudin mashin ko?nan na tuna bani da ko sisi nayi
tsaki,saurayi mai mota yace yar kanwata shigo mana jan
ajinki ya burgeni kuma na yaba,na dubi Amira ta wani
kame tamkar motar kanin babanta nace bani naira dari
tace nace maki bani da kudi ko?in zaki shiga ki shigo
dole,dole na shiga motar nima bayan na shiga yace yi
hakuri kanwata dan dawo nan mana na koma don
surutun ya soma isata yaja muka tafi,sannu a hankali
yake jan motar sunana ya tambaya nace mashi Amira,
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Amira da take baya ashe taji tace yar iska sunanta Iman
yace yauwa mai sona fada min gsky Amira ta cigaba da
cewa xan kaika har gidansu yanda tace maka haka takeyi
ma samari tace sunanta Amira kuma ta yi masu
kwatancen gidanmu ina jinsu ban kuma magana ba sai
su keta faman labarinsu,muna zuwa kofar gidanmu ya
faka a daidai lokacin yayanmu yayo ma abokanshi rakiya
kallon motar ya tsaya yi da sauri na bude na fito daga
motar ido hudu mukayi da yayanmu nan da nan fuskarshi
ta sauya yayi murtuk tamkar bai taba dariya ba koda dai
dama ban taba ganin dariyar tashi ba,a hankali yake
tahowa har inda muke nayi zaton zai mare ni ne sai
naga ya wuce ya isa gun motar daidai kofar dreba ya
kwankasa gilashin motar,ina zaton Amira da bata fito ba
ita ce tace masa yayanmu ne sai naga ya fito daga cikin
motar da sauri sannan ya mikawa yayanmu hannu gami
da sallama,yayanmu nokewa yayi yaki bashi hannu sai
dai ya amsa sallamr a ciki ya dubeni yace menene
dalilinki na shiga motarshi?nayi shiru shi kuma saurayin
mai motar sai cewa yayi yallabai ai ina sonta ne kuma
banzo da wasa ba,sai ya kara daure fuska sannan yace
ita me tace maka?yace bamu yi magana ba
tukunna,yayanmu yayi mishi wani kallon wulaknci sannan
yace

Please Login or Register in order to submit comment