Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ubansu ne in tana jin masifar
tata ta yi da wanda ya ajiye ta bada yara ba,wannan
rigima har gun baba jin bata sami gsky ba shi ne tayi yaji
sai da tayi wata sannan ta dawo,dawowarta shine ya
zama sanadin juya mana baya duk yanda baba yayi sam
baya sauraron mama da farko ban gane ba saida
sunanmu ya fito munci makarantar mu salmat da mama
ta sanar da baba sai yace kar mu dameshi ya gaji da
biyan kudin makaranta,ni ba wani kokari ba shi maimuna
gwarzo zai maida ni na ringa kuka ina rokonshi sai ce
min yayi inyi hakuri shi ya gaji,haka na cigaba da zuwa
islamiya da hadda boko kam ina ganin saudat tuni har ta
shiga SS1 niko ina gida ,anty yagana tace da mama ta
biya mani da ita tana da kudi tace ai ta mashi magana
yace bai yarda ba,wata rana na dawo daga hadda da
rana jugum na samu mama tayi a dole na zauna kusa da
ita na dafa ta nace wai mama baki da lafy ne?tace kaina
ke min ciwo iman,na tashi na nufi gun da muke aje
magunguna na dakko mata panadol na dibo ruwa a kofi
na kawo mata ta amsa tasha sannan tace kije dakin
yayan ki duk wanda kika gani cikinsu kice yazo zan
aikeshi wajen kawunku malam nace nima zanje mama
tace to amma sai kinci abinci ko?nace e nayi sashen su
yaya da gudu,a kofar dakinsu na tsaya nayi sallama yaya
Abubakar shine ya amsa nace in shigo?yace in dai
tsohuwa ce kar na ganta anan(haka su kan tsokane ni
wai tsohuwa)na shiga nace kaine dai tsoho bani ba yace
me yasa zaki sa mana tsufa daki don Allah kije waje
nace naki din aje wajen baka girmeni ba ma zaka ce min
tsohuwa,ya kwashe da dariya yace waneni da girmanki
kece fa kika haifi su kawu da mama da baba anan gidan
haushi ya kamani na hau tsaki irin na shagwaba ina son
inyi kuka nace sai na gaya ma mama na juya zan fita ya
jawo ni zo mana yar kanwata tawan zo mana kiji mama
ta aiko ki guna ne?nace eh tace kazo zata aikemu gidan
kawu malam ya mike ya dungureni shine baki fadi mani
tun dazu ba?ya rike min hannu muka tafi dakin mama
ban san me tace mashi ba na dai ga ta bashi kudi sanna
tace in tafi falo inci abinci kafin ta gama bashi sakon,na
kunna tv na kamo cartoon ntwk ina kallo ina cin abinci
sai naga anty Faty ta fito ni ban ma ganta ba sai gani
nayi an kashe tv din na dube ta nace aunty ina kallon
tom and jerry ne,tace na kashe ko zaki kunna ne?niko
ban san gatse ba sai nace eh cikin masifa tace to zo ki
kunna har ga Allah ni ban san gatse tai min ba sai kawai
na tashi na kunna tv din remote din na hannunta kafin na
juyo sai saukar mari naji dau na yanke da ihu sai ga
mama da gudu ita da yaya Abubakar dama shi akwai shi
da zuciya yace faty me tayi maki,anty faty tace in dole
sai kasan abin da tayi min to ka nemi sani daga gareta
dube ka dan kauye don kazo ka waye shine zaka kawo
mana raini ko?yace naji ni dan kauye ne ke baa ma san
asalin naku kauyan ba,don ba muga yanuwanki ba waya
sani ma ko daga sama kika fado banza yar iska haka
zaki kare a neman asiri,sai tayi kanshi da zagi harda
duka nan da nan ya sharara mata mari gami da ture ta
mama da tuntuni take tsaye tace kai Abubakar wuce
kasai kabar aiken sai anjima,ta nuna ni ke kyma yi daki
na mike sannan na jiyo mama tana cewa kin gani ko faty
wannan shine abinda na jima ina sanar dake ki daina
shige ma yarannan kinki ji to kinga irin.......kan mama ta
karasa sai ta katse mata hanzari da masifa ke munafuka
bake kika sasu ba?to albishirinki yau dinnan zaki san
matsayi na bakinsa Abubakar ya mareni ba?zaku gane
baku da wayo yau,nayi shiru a daki ina kuka mama tace
to ina jiranki da alkhairi anty Faty tace ni kuma da sharri
nake jiranki yau da nai nasarar rava alkhairi da tunanin
wata ya mace haka zan rabaku da gidan nan mama ta
ce to ai Allah ya fiki kuma ba ya barci kuma yana tare
da masu hakuri ta cigaba da cewa ke ko nasan baki san
haka ba tunda kin yi nisa ba zaki taba jin kira ba to sai
muce Allah ya shiga tsakaninmu da ke in kuma mai
shiryuwa ce Allah ya shiryaki,Ku ziyarci blog dinmu
domin karanta Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
ta shigo ta sameni inata faman kuka ta zauna kusa dani
ta jawo ni jikinta tace iman wace adduar kike min,nace
ina rokon Allah yasa ki daina samun matsala da
baba,mama tace ki hada da babanki shima ki dinga yi
mishi ki roki Allah ya kareshi sannan ya raba shi da
dukkan sharri da ake mashi,nace mama wanene yake ma
baba sharri?tace aa mugun abu ai ba sai kasan me maka
zaka roki Allah ba,nace to insha Allahu zan dinga yi
mishi,da dare sai ga dan aiken baba,yaya Ibrahim ne
baba ya aiko wai muzo ni da mama babban falo babu
neman ba'asi ya dauki hannu a gaban mutane ya mari
mama ga yan aiki ga yayyena ga ni ga anty faty bayan
marin ya cigaba da fada wai kar ya kuma jin an taba
mishi mata inko ta kuma marinta ta mari aurenta mama
tana rike da kumatu sai nan tace cewa tayi maka na
mareta?yace to yau kuke me yasa tun da kuke tare bata
ce kin mare ta ba sai yau kuma tace tana son in rama
mata shi yasa mama tace shi kenan ni Allah ya rama
mani ta shige daki,duk da karancin shekaru na sai da
nayi mamakin baba wai ya rama wa anty mari?na juya
na dubi anty sai naga tana wani ciccika tana batsewa
wai an rama mata, na bi mama daki na iske tana kuka na
dafa ta nima na soma kuka ina cewa mama kiyi hakuri
Allah ya saka maki. Anyi haka da kwana biyu na dawo
daga kitso in da yaya Abubakar ya kaini tudun wada na
mari yaya Abubakr din da wasa don ya dameni da
tsokana tun a mota wai tsohuwa mai dan koko Allah
kashe ki musha gumba,nayi banza dashi sai da ya tsaida
mota sannan na dan kai mashi marin wasa kadan na
bude motar nayi cikin gida da gudu,yace ni kika mara?sai
na rama shima ya fito yana dariya ya biyoni yana kirana
nayi falo da gudu ina cewa so kake in tsaya ka rama ban
kula ba na bude labulen falon na fada sai kawai naji na
bige mutum lokaci guda kuma naji anyi jifa dani ashe
nayi karo da anty faty ne shine ta jefar dani kuma ta
biyoni da duka takeyi yaya da har ya juya da yaga na
shige falo sai kuma yaji kukana nan da nan ya dawo ya
iske anty nata faman dukana cikin zafin rai yake ma anty
magana yace don Allah me yarinyar nan ta yi maki kike
dukanta haka?yanzun nan fa muka shigo?ta juyo kanshi
da zagi da gori,jin hayaniga shi yasa mama ta fito ta
dubeni ta dubi yaya sannan tace Abubakr ba zaku daina
daukar min magana ba ko?yaya yace wllh mama bamuyi
mata komi ba niko sai faman kuka nake ita ko anty faty
sai zage zagenta takeyi jin mama bata kula ta ba sai
kawai ta shaki kwalar rigar mama tana cewa yau din nan
na tsara zaki bar gidan nan duk na cinki miji ya
wulakanta ki amma don bakin naci kin dage kin ki tafiya
ko,ta cigaba da cewa to yau din nan za'a kama kai a
koma wurin mai dattin hula,yaya ya fincike hannunta a
wuyan mama sannan ya daura mata mari yace marar
mutunci yar dangin jaraba rigima dai ta ki karewa har
yamma sai da tayi ma babana aike har kasuwa wai yazo
nan da nan sai gashi lokacin ma kowa ya kama gabanshi
yaya Abubkr bai ma nan ni kuma ina daki mama tana
koya mani karatu sai ganin baba mukayi ya shigo ko
sallama babu ya jawo ni a gaban mama ya hau duka da
wayar wuta ina ta ihu gami da neman taimaki amma ina
mama ko kallo ban isheta ba sai da ya gaji sannan ya
barni don kanshi,sannan ya dubi mam yace ke kuma in
tambayrki?mama ta dubeshi ba tare da tayi magana ba
yace dake muka hada muka sayi gidan nan?mama tayi
shiru yace ba dake nake magana ba mama tace ai ina
jinka yace to ina son daga yau na sakeki saki daya
sannan na barki minti goma ki barmin gidana.....Ku
ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Duk da nike karama ina jin ya ambaci saki sai na kara
yanka ihu itako mama duk da dauriya da tayi don kar tayi
kuka ace gabana sai da kuka na ya sata hawaye koda
mama ta gama kimtsa kayan ta ta fito falo zata tafi na
biyo ta da gudu ina kuka babana yana zaune yana cin
abinci da bai tanka ba sai da anty tayi mashi wata
magana sai yace da mama ki tafi da yarki in kinji
shawarata don ni ynxu nafi son yaya maza daga tsatson
faty ga mamakina sai naji mama tace to Allah ya baku
sannan na gode da shawara amma ko mun tafi da iman
ai kanan nan a matsayin ubanta ko?maimakon yayi
magana sai kawai ya kalli anty faty komi tace mashi oho
sai ya juyo ya kalli mama yace kuje dai sai yanda hali
yayi idan nine ubanta to na aiko maki amma fa gunki
zata ci gaba da zama ba ba tare da mam tayi magana ba
ta jani ko takalmi babu mukayi waje,wannan fita da
mukayi itace fita ta karshe daga gidan babana mahaifi
kuma har yau ban kuma zuwa ba ban kuma ganin
babana ba ko anty fati ba. Muka koma gidan kawuna
marikin mamana daki guda kato bayan sati biyu babana
ya aiko ma mama da dukkan kayanta haka mama ta
cigaba da zaman iddarta har ta gama, itace tayi mani
komi na shiga SS1 a makarantarmu wato salma,ina jin
dadin zama da baba uwa wato matar kawuna suna da
yay biyar yaya suleiman shine babba sai yaya nura,anty
rukayya ke binshi sannan sai nana itace sa'ata sai
karamin su mai sunan kakanmu liman ake kiranshi don
sunan liman din yaci wato isuhu,nana maimuna gwarO
take itama js1,yaya suleiman tela ne kuma yana zuwa
poly ko da yake san da muke a maigidansu saura yan
kwanaki ya gama shi ko yaya ustaz ne don yanzu haka
ya na koyarwa a wata islamiya nan kusa da
gidansu,sannan shima zuwa tashi wato sanawiyya a
unguwar ma'azu,anty rukayya kuma tana aure ne a
badarawa yaya suleiman yana debe mani kewar su yaya
Abubakar don shima yana tsokanata kasancewar mu
abokan wasa ne ya kance mani matar ni kuma ince
mashi ya mani tsufa bana sonshi yaya nura baida faraa
shiya sa nima ban cika kulashi ba,Ku ziyarci blog dinmu
domin karanta Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
wata rana ina zaune daki sai mama ta shigo lokacin
kuma gab da babbar sallah ne mama tace iman shirya
muje kasuwa nace to dama na riga nayi wanka sai kawai
na dauki hijabina mai less a kasanshi nasa takalmina
nace mama na shirya muka nufi kasuwa,bayan mama ta
gama mana yan saye sayenmu nida nana sai tace muje
wajen yan zinari zata sai wani nace to muka je shagon
shi makare da gwala gwalai kala kala da fara'arshi ya
tari mama,naji yana cewa haj Habiba sai yau kikazo
kasuwa?mama tace wllh ko Alh mukhtar maska inafa son
nazo amma ban samu lokaci bane sai yau ya turo mana
kujera yace mu zauna ya nunani yace wannan yarki ce
ko?mama tace aa yace ke yarta ce ko yan mata?nayi
murmushi yace ga murmushin nan irin naki ke ya
sunanki?nace sunana iman yace suna mai dadi,sannan
ya juya gun mama yace kin sami sakona a gun yagana?
don tazo shekaranjiya ta kawo wasu karyayyun yan
kunne,mama tace bamu hadu ba gsky mun dai rabu akan
zata zo nan din yace sakona bai isa ba kenan?mama
tace eh sai ya dubeta ya ce zaki samu ganina zuwa
yaushe?sai nazo gidan naku,mama tace lafy dai ko?yace
sai alheri mama tace to ko yaushe kaxo zaka sameni sai
dai da safe ina zuwa islamiya yace ba matsala zan shigo
tudun wadan yanzu me kike so?mama tace ina son in
saima Iman dubai ne kasan da na daukar mata a cikin
kayan da ka kawo mana wancan sati ukkun da suka
wuce to sai na ga kuma sun mata girma sai naba yagana
tace kace mata sai bayan sallah shine nace bari nazo
gunka ko zan samu wani,yace ba zaa rasa ba in kuma
kinga ba wanda yayi miki to ki sai mata saudiyya mama
ta zabar kirar dubai na wajen dubu tamanin har da abin
hannu guda biyu yace gasky kina ji da wannan yar taki
mama tace kai maska don na sai mata yan kunne?yana
dariya yace sai nazo zan amshi kudin mam tace a'ah ga
dubu hamsin nan bansan zan sami masu tsada haka ba
mukayi sallama ya bani dubu daya yan hamsin hamsin a
cikin kudin nayi godiya muka tafi,bani manta ana jajibir
sallah Alh mukhtar maska yazo gun mama ni dai na
dawo daga kitson sallah nida Nana na iske bako a dakin
yaya suleiman da zai tafi mama ta shigo tace naje na
gaida shi don yana ta faman magana in na shigo nazo
mu gaisa,na zauna a kasa dashi na gaishe ahi yace kin
dawo muga kitson na nuna mishi yace iyye yayi kyau
sosai yasa hannu a cikin aljihun shi ya dauko kudi
sababbi yan naira ashirin bandir daya yace ga goron
sallah don kilan ba zaki ganni ba naki karba nace ka
barshi muna musu mama ta shigo jin musun da mu ke
ne tace sunyi yawa ne alhaji ka rage yaki dole na amsa
nayi godiya.Amira wacce tayi shiru tun da na soma
magana kamar ruwa ya cita sai da nayi shiru sannan
tace gsky iman ke yar gata ce to amma sai nan gaba
zaki sani in Allah ya kawo karshen muguwar matar
babanki,nace Allah yasa,Amira ta gyara zama sannan
tace anty faty matar babanki ta haihu?nace kai har
yanzu Allah bai basu ba tace to ina yayyenki Abubakar
da Ibrahim kuma?yanzu basa zuwa nan?nayi murmushi
nace kin cika tambaya Amira zaki yi kyau da yar aikin da
nake ra'ayi wato yar jarida Amira ta basar da abunda
nace tace baki amsa mani ba nace basu san nan gidan
ba don kwanaki baba uwa tace masu mama tayi aure,sai
kuma ta kuma cewa to ina yayansu mami abdul wa ma
kika ce mani?nace abdulrahim sunanshi mami tace yana
england shi dan wasan kwallo ne nima ban sanshi ba
amma ya sha masu aike nima na gani,shi kuma kabir
aikinsa shi dai amira tace haba nasan shi mana ba shi
ne yake karatu a kano ba,tace ai shi naga ba ruwanshi
don naga yana maki wasa nace gsky shi kam ba ruwan
shi ko zai zo hutune ya kanzo da yar tsaraba su sweet
biskit da yan kayan lashe lashe ya ba kannenshi tonima
yanda ya basu haka yake bani don haka nima nake
sonshi a raina ganin shi nake kamar yaya abubakar duk
da bai tsokanata irin na yaya abubakar din amma kinga
yayan nasu da ke waje ina tsoron ranar da zai dawo,ta
dube ni don mi kika ce haka?nace don ina jin yanda suke
lbr shi wai ya cika masifa ga duka sannan nasha jin
yanda suke bada lbr irin son da yake ma hajiya
yaya,sunce yana son mamarsa kamar ransa don bai hada
ta da kowa ba yanda mami take bada lbr sai kinyi
mamaki sosai abin kamar ba gaske ba to kuwa ai kinsan
dole ne ya kuma ki duk abunda taki gami da tsanar shi
tunda sunce komi tace mashi yayi,don haka ina jin ance
yau zai dawo zan hada ya nawa yanawa na kama gabana
na koma can gidan kawu na malam,Amira ta dinga man
dariya wai na cika shegen tsoro nace ai ke dariya ma
nabaki?lallai Amira, tana dariya tace dole ne nai maki
dariya ma naga dai komai son uwar shi sai kin mata abu
sannan zata sanar dashi sannan in baki sani ba su maza
ba yawancinsu basu da daukar zance na tsegumi haka
wannan sai mata sai ko sakaran namiji ina jin wannan ba
zai maki haka ba don shi dan boko ne nayi shiru ina
nazarin maganarta can nace wannan gasky ne to Allah
yasa dai kar ya kulani,Amira tace amin,mun kaure
munata zuba lbr sai kawai ganin yaya Ahmed mukayi
nace a'a yayanmu ustazi ba sallama ne?yace ku dai
bakujin sallamar to mama tace a tashi ayi sallah dama
masallaci zani,yasa kai ya yi waje na mike nace bari na
wuce gida kawai,Amira tace ai baki isa ba sai kinyi
sallah kinci abinci sannan zaki bar gidan nan,na kwace
daga riko da tai min nayi waje ina dariya nace yaushe
rabon da ki shigo gidanmu,ta biyo tana kira na gudu
gashi nayi sa'a mamansu tana daki tana sallah a
gidanmu ma mamanmu sallah na sameta tanayinima sai
na shige dakinmu naga jamila tana barci na tashe ta
muka yi alwala muna idar da sallah nima na kishingide.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347








DOCUMENT CREATED BY
ZAHARADDEEN SHOMAR
WHATSAPP ,08168575100












Tawa Tasameni1-02
Posted by ANaM Dorayi on 01:20 AM, 20-Dec-15
Under: TAWA TASAMENI
TAWA TA SAMENI
NA
HALIMA ABDULLAHI K/MASHI
Ranar lahdi da daddare sai gasu yaya abubakr sunzo
nan muka sha fira, ynxu anty faty ta gama mallake
babana sai abinda tace gashi har ynxu Allah bai basu
haifuwa ba sai karyar bari,na tausaya ma mahaifina
kuma na yi alkawarin sa shi a addua insha Allahu zan
kuma roki mama ta barni inje na gaida kakata in munyi
hutu mun jima dasu sannan sukayi sallama damu suka
tafii,muna shirye shiryen soma jarabawa zango na ukku
don shiga SS2 aka yaye mu a islamiya inda mukayi
walima a gidansu Amira duk gidanmu ni kadai nayi
sauka mami kuma sai shekara mai zuwa don tayi wasa
da karatun mama da maman su Amira harda Anty
yagana duk sun mana bige bigen abubuwa irin su
kalanda da robobi,hankici da sauransu,da zamuyi rabon
katin walimar har su yaya Abubkr sai dana bawa Amira
nayi mata kwatancen taje takai masu kuma sunxo mani
da kyautututukan su inda suka bani waya a kwalinta
wai inji babana na amsa cikin fargaba na kai dakin
kwananmu na boye shima yaya Sulaiman yazo kuma
shine ya dinko mana kayan da muka sa ranar walima
nashi gudummuwar kenan wata shadda ce galila mai
kyau da hijabai. Sai da komai ya natsa sannan na
dauko wayar dasu yaya suka bani na kai ma mama na
mika mata leda ta amsa ta gami da tambayar menene
a ciki?nace su yaya Abubkr ne suka kawo wai inji
babana na fada mata cikin tsoro,ta saki ledar daga
tsaye tace ke kuma ki ka amsa to ko menene ma a ciki
zan maida musu ni,haka kuwa akayi ta kira yaya
Abubkr a waya ta bashi gami da yi mishi gargadin karta
kuma ganin wani sako daga babana da sunan wai nawa
ne tun daga nan suma su yaya Abubkr din ta daina
sakar masu fuska.mun shiga SS2 cikin sa'a da nasara
ranar wata jumaa mun tashi daga makaranata na tsaya
ina amsar sakon wani littafi da zan amsar ma Amira
gun wata yar ajinmu Hauwa aminu don yanxu in tana
karantawa nakan zauna ta bani lbr ko ta karanta mani
na amsa na isa gurin da Musa yake tsayawa wato
direbanmu ban sameshi ba na tsaya nayi sororo can na
hango wata yar ajinsu mami don yanxu ba aji daya
muke dasu ba ni ina A su suna C na isa gunta sai na
tambayeta ko taga su Sa'a?don mami bata zo ba tace
mani sun tafi abinsu nayi shiru na kuma ce mata motar
tazo?tace ba bus din gidanku ba?na daga kai tace to
sun dade da tfy,sai da nayi nisa a tfy kasa sannan wani
tunani yaxo mani na tsaida mashin na hau sai da muka
zo har kofar gate din mu sannan nace bari na shiga na
amso maka kudinka ina shiga harabar gidanmu naga
matasan layinmu sun cika a kofar dakin yaya Kabir har
da wadanda ban taba ganinsu a layinmu ba,nace a
raina ko yaya Kabir ya dawo ne?don ynxu yana bautar
kasa ce a Bayelsa na shiga gida na sanar da mama
abinda ya faru tace to a nawa ya kawoki?nace 40,ta
bani 50na kai mashi a hanyar dawowa cikin gida ne
nayi karo da Anty Hadiza dasu Anty Mariya suna dauke
da manyan tururuka da kuloli a kai,Bilkisu kuma tana
dauke da dauke da plates da cokula ga wani kwando
mai dauke da kayan shaye shaye na dube au na kauce
a hanya,amma duk da haka sai da anty Mariya ta daka
min tsawa ke akuya ban hanya,na matsa musu suka
wuce,na shiga ina mamakin wane bako ne yaxo ake
mashi hidima haka?bayan naci abinci nayi wanka nayi
sallah na shirya cikin riga da siket yan kanti ina zaune
a tsakar daki ina yin note sai ga mami da gudu ta shigo
tana kwala min kira iman! iman!!na tashi da sauri ina
fadin gani nan nace menene?don duk na tsorata sai
tace min ki tayamu murna yayanmu ne ya dawo ya
bamu waya nayi ajiyar zucya na dungure mata kai nace
har kinsa duk na tsorata na amshi wayar kirar nokia yar
karama mai murfi gsky ta burgeni sosai nayi mata
murna tace su dasu Sa'a iri daya ya sai masu don
dama ya sai ma su anty Mariya tun tuni,nace kunji
dadin wllh tace muje ku gaisa mana ko zai baki kema
na dube ta cikin sauri nace ki rufa mani asiri ai ni ynxu
ba zan taba yarda ya ganni ba bare da hankalin kaina
naje inda yake ta soma dariya gami da fadin kin fiye
tsoro me zaiyi maki?daga ganinki sai ya hau dukanki
sai kace mahaukaci?tacigaba da dariya na ture littafin
gabana na dube ta nace don Allah ki sanar dani wani
abu game da yayanmu mana, Tace Abdulrahim
sunanshi na gasky wato Abdulrahim mukhtar maska a
yanda naji ana cewa tun yana dan karamin shi sam
baida yawan fara'a ga miskilanci don zai iya kwana bai
damu da yayi ma wani magana ba in ana son aga
fara'arshi to a bashi kwallo sannan kwallonshi ta samo
asali ne tun yana makarantar primary inda yayi ta cin
gasar da aka sha hada su da wasu makarantun,haka
yacigaba har secondary,bayan kammala yaso a barshi
yaci gaba da kwallonshi amma sai babanmu ya kiya
sam dole yaje ABU zaria inda ya karanci politics har ya
samu degree bayan ya gama sai ya shawo kan
babanmu da kyar yayi wasanni da dama a nan gida
nigeria kafin ya fita england inda wani coach yayi mishi
hanya,
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Na dakatar da ita nace ke ni ban tambayeki lbr kwallo
ba,kunce yana dukanku ko?mami tace Allah yana duka
sosai ma,amma sai ka mashi ba daidaiba,na dubeta
nace kamar yaya ba daidaiba?tace baya son ya saka
abu kaki ko kai shirme,bai son kazanta kuma in ka
ganshi yana son ka gaisheshi amma baison yawan
gaisuwa ,kana ce mashi ina kwana is ok,yana da cin
abinci kinsan yan kwallo gashi da tsafta yana son
kamshi ke gadai abubuwa nan,in har kin kiyaye komai
babu abinda zai faru tsakaninku ko ynxu ki tashi muje
ki gaishe shi mana,nace a'a mami gaisa wata rana
nace to ynxu ya dawo kenan?tace aah bai dawo ba
kenan,zai koma wannan zuwan ma in gaya maki haj
yaya ce ta matsa yazo don su gana da yar gidan haj
laure,anty mimi nace ita zai aura kenan?mami tace
kuma abinda baki sani ba yana matukar bin maganar
iyayenshi don ko wuta suka ce ya shiga zai iya shiga
musamman haj yaya bai hada ta da kowa ba yana
matukar jin maganarta,na dube ta cikin tsoro nace kinji
ko?tana ce mishi ya koreni zai koreni ko dai ma in tafi
ne?mami sai dariya take yi min,Kamal ne ya shigo ya
sanar da mami mamansu na kiranta.Bayan kwana biyu
ya raba tsaraba har su jamila da sagir ya basu,mama
ma ta samu less da shadda da takalmi sagir din ma
harda Jc shi da kamal,su mami english wax ya kawo
masu ni dai banje ba kuma bai sani dani ba don ban
yarda ya gani ba,ran da ya yi kwana ukku da dawowa
mama ta amshi girki da rana ina tayata aikin burabisko
mami ta same mu a kicin tace yaya yace a kai mishi
abinci,nace yana cin birabisko ne?tace oho nace to
inbazaki laifi ba kije ki ce mishi burabosko ne don kar a
yi mishi laifi,tayi musrmushi sannan ta fita,anty yagana
tayi sallama ta shigo na fito daga kicin na amsa,sannan
na gaisheta gami da tambsyarta saudat tace tana gida
sannan ta wuce ciki tana ce min maman naki na ciki?
nace eh,mami ta dawo tace yace akai ma abokanshi
shi kuma a dafa mashi indomie amma ke zaki dafa ko?
tace eh nace to don kar inyi kuskure mami tayi dariya
tace kai ke kam kin cika tsoro,sababin kuloli mama ta
bani na zuba masu birabisko da miyar kaji yaji curry sai
kamshi yake,na dauka na tafi nayi sallama a kofar
dakinshi aka amsa mani cikin faduwar gaba na shiga
nace sannunku mutum uku suka amsa kaina a kasa ban
kalli kowa ba nace a ina zan ajiye?cikin dauriya nake
magana gabana sai faduwa yake wani daga cikinsu
yace maska tana magana,da sauri na dan dubi wanda
aka kira maska yana ta faman danne danne waya
tamkar ba dashi ake magana ba,dayan yace ke ajiye
kan wancan table din,na dubi table din sai naga akai
yayanmu ya dora kafarshi ,na dubi mai maganar nace ai
yasa kafa a kai yayi murmuahi sannan yace ajiye ko
ina kinsan halin yayan naku sai hakuri na ajiye a
gabansa don mami tace dama su ne zasu ci na juya
zan tafi sai naji

Please Login or Register in order to submit comment