Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

murya mai sanyi amma cikin fada
akace ke haka ake bada abinci a gidanku ko?na juyo da
sauri ga mamakina yana danne danne wayarshi kamar
yanda na sameshi,sai a lokacin ne ma na dan kalli
fuskarshi, kykkyawa ne na ban mamaki don duk gidan
yafisu kyau sak kamarshi daya da hajiya yaya,tsawa
naji in ba zaki zuba musu ba dauki ki tafi,da sauri na
duka jikina na kyarma na zuba musu nan dakin ya bude
da kamshin miyar kajin na mika wa kowa sannan na
mike dayan yace dan bamu ruwa nace to zan fita
dayan kuma yace ga fridge nan na nufi gun fridge ina
tunanin yanda zan bude dan ban taba ganin irinshi ba
cikin sa'a ina dafa shi sa i naji na latsa wani abu sai ko
ya bude kayan shaye shaye ne kala kala na rasa
wanda zan dauko musu sai na dauko musu ruwa a
babban gora na dauko five alive na aje masu da na
duba saman fridge din sai naga kofuna irin na wajen na
dauko tiran kofunan gaba daya na aje a gabansu,ina
kokarin mikewa ne mami tayi sallama suka amsa har
da yayanmu ta shigo dauke da kula da plate da cokali
na fita na dan tsaya a kofar dakin ina jiran mami
labarin abinda yayanmu yayi mani sai na jiyo itama
tana shan nata fadan,muryar yayanmu ne yana ce mata
yar iska haka ake dafa abinci?indomie ne din ba za ki
iya dafawa ba?ina cewa ganin kin danfi su mariya abin
kirki ashe kema useless ce,sam ban ga wani amfani ba
gun mace matsawar bata iya abinci ba,ko aure kukayi
irin abinda da zakuyi kenan ko?sai naji muryar wani
acikin abokan yaya yana cewa to kayi hakuri mana
maska,ai yara ne sai naji muryar yayanmu din yana
cewa no.......
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Nasir kar ka goyi bayan wadannan yaran sam basu iya
komai na mata basu iya girki ba basu iya gyaran daki
ba,sam basu iya komai na mata ba yan iska sai dare
yayi ka gasu suna surutu da samari sannan ace masu
yara?yaci gaba da cewa bari kiji ba za'a yi asarar
wannan abincin ba maza ki dauka kije ki cinye shi ina
nan shigowa har dakinku inci ubanki in baki cinye shi
ba ina nan yanda kuka sanni ban canza ba fita useless
kawai,nan mami ta same ni a kofar daki duk na kara
firgicewa na dubi mami wadda ke zubda hawaye nace
mami yanzu ya zakiyi da wannan uwar taliyar don
Allah?tace zo muje sai da muka isa gun lungun shiga
cikin gida sannan ta dubeni tace don Allah iman ci
wannanabincin kiji nasa hannu na dandana daidai kam
yayi sai dai da ta dam kara wasu abu zai danfi wannan
dadi,nace yayi mana tace to kinji shiyasa ni sam bana
son ya sani wani aiki ga tozartani a gaban abokanshi
nace to ki kai ma masu wanke wanke su tafi dashi gida
mana tace wai in kaiwa su lami masu aiki?nace eh
tace baki san yayanmu bba kenan kar kiyi fata irin haka
ta hada ku kuma duk matar da ta aureshi ta shiga
uku,nace anty mimi zatayi fama muka wuce cikin gida
bansan yanda mami ta kare ba,sai washegari a school
take ce min zubar da rabi tayi ya sameta tana cin
rabin.Washe gari gab da magriba na dawo daga
islamiya da shike ina zuwa sanawiyya na shigo
gida,zaune a kofar dakin yayanmu samari ne su hudu
sai shi yayanmu yana tsaye yana daddana waya,nadan
yi mamakin yanda baya gajiya da danne danne waya
ban taba ganinshi ba waya ba kuma ko da yaushe cikin
danna ta yake tun daga nesa nake kallonshi sanye
yake da dogon wando da riga daga nesa nake kallonshi
sanye yake da dogon wando da riga mai gajeran hannu
masu ruwan bula da ratsin fari an rubuta adidas a
jikinsu,gsky yafi yan gidanmu kyau,maza da mata dogo
ne yana da dan fadin ga kwarjini gashin kanshi a
nannade ina tsammanin yana sanya mai ne akan ko
kuma haka gashin nashi yake?oho ban san dalili ba duk
sanda na ganshi sai gabana yayi wani mugun faduwa
bana raba daya biyu don ina jin tsoronshi ne,na iso daf
dasu kanshi a duke yana danna waya amma sai naji
yace ke in kin shiga kice Sa'a ko Bilki su kawo mana
butoci,to ba ma magana dasu Sa'a ko ince basa min
magana kuma ban ga mami ba sai naje dakinmu na
dauko butoci guda biyu na kai masu shi baya gun ina
zaton bayinshi na daki zaiyi sagir na tura sagir ya
kwaso mana butocin,wata rana asabar zan tafi
islamoya don yanzu bana jiran kowa a yan gidanmu dan
ba lokaci daya muke karatu dasu ba sai dai na biya wa
Amira mu tafi,sanye nake da hijab har kasa nasa safa
da nikab yayanmu na gani yana kulle dakinshi sanye
yake da gajeren wando da yar rigar nike kafarshi da
safa da takalmi but na kwallo da alama zai motsa jiki
ne,nazo zan wuce ya dan dubeni ina jin yana son ya
gane kowacece kamar na gaishe ahi sai kuma na fasa
ina zaton bai gane ni ba,na gota shi kadan sai ya juyo
yace ke gabana ya fadi dama cikin faduwar gaba
nike,na dawo kaina a kasa nace gani baiyi magana ba
ya gama rufe dakin ya matso gab da ni sannan yasa
hannu ya dage nikab din idona ya firfito don tsoro yace
ooh na dauka mami ce,ya cigaba da magana fuskarshi
a daure ke na lura sam baki gaida mutane ko?na dan
saci kallonshi fuskata yake kallo na kali kasa sannan
nace ina kwana?yace wuce bani so sai da na roka
kenan dubeta ,a raina nace masifaffe kar ka amsa din
na tafi abina.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Zama da Amira yasa yau da gobe nima na soma
karanta littafi kuma sai da na tambayi mama tace
amma na dinga karanta masu kyau kuma masu amfani
sannan in har zan karanta to ya zama bani da aiki ko
na makaranta ko na gida shi yasa ma nafi yin karatun
da daddare kasancewar bana fita ko ina ko samari
sunzo kirana mama bata matsa mani ba don tace in kr2
nake son nayi to na tsayar da hankalina gun
karatun.Yau monday muna hutun easter bani da wani
aiki duk na gama kwance nake bisa gadona ina karanta
wani littafi mai suna auren kisan wuta ina jin dadin lbr
banji sallamar mami ba sai dai naji an fisgw littafin
daga hannuna cikin sauri na tashi tana dariya tace kai
iman,ke dai kina krt nan baki jin komi,nace lbr ya
hadu,tace hala na soyayya ne?nace eh tace ai na sani
nace kin san me?ai ku ne kuke soyayya ni kin ganni da
saurayi ne?naci gaba da cewa wallahi ni banma yarda
akwai wata soyayya da kuke cewa ba,mami ta soma
dariya tace lallai yarinya da sauranki ke da kike karanta
littatafai ai ke zaki ba wani lbr yadda ake soyayya,nace
suma duk jinsu nake sai kiji an ce wai tana tuna shi
tana mafarkinahi,don Allah da gaske ne?mami tace aa
karya ne randa baku iya nutso a cikin soyayya ba ba
zan yi magana ta katse ni da cewa ke ni ba wannan ya
kawo ni ba an sa ranar su a anty Mariya wannan
Alhajin kin ganeahi?nace mai katon cikin nan?tace eh
shi ita kuma Hadiza wannan Sanusin mai jar motar
nan,nace na ganeahi wanda ya taba cewa na kirata,don
ya bata kudi ta bani shine ake cewa kar na kuma
gaishe da saurayinta,don mu duk wanda ya dafe mana
ya dafe mana kenan mami tayi dariya tace to shi. Yaya
a
Abubakr yana zuwa gidanmu haka yaya ibrahim
dukkansu suna min hidima sannan yaya Sulaiman
shima yana zuwa sai dukkansu sun daina shiga wurin
mama sai dai su gaishe ta waya,wani abin mamaki
kuma yaya Abubakar shi kadai yake zuwa haka ma
yaya Ibrahim din duk babu wanda ya taba min maganar
soyayya ina ganin take takensu kuma bana jin zan iya
amince ma dayansu.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Yaya Kabir ya gama bautar kasarshi ya dawo gida,to
shi dama muna shiri dashi rannan na fita da safe zani
shagon mal Sani dan sayan sabulu naga yaya Kabir
yana tahowa daga bakin kasuwa na jira ya iso nace kai
kam ka cika yawo daga ina? Na duba wani abokin bab
can da bashi da lfy nace ko Alhaji isa naji mami tana
maganar zuwa duboshi yace yea shi ne,muka jero
muna tfy har gida na tsaya daidai kofar dakinshi zai
bani kwanukan dana kawo mishi abinci da daddare ya
fito dasu kenan yayanmu shima ya fito daga dakinshi
cikin sauri na gaisheshi sau daya wato ina kwana yace
lafiya dama shi gaisuwarshi bata wuce haka in ma ka
kara to ba zai amsa ba na amshi na wuce sai naji
yayanmu na cewa kice mami tazo tayi mani shara kan
nayi magana sai yaya Kabir ya riga ni yace ai yaya
Abdulrahim dama wannan din kasa da kafi ganin daidai
dan ta kware yacw to gashi in kin gama ki rufe mani
dakin kiba brother key din,nasa hannu biyu na karba
gami da cewa a dawo lfy bai amsa ba yayi gaba,na dubi
yaya Kabir nace don Allah shi yayanmu baya amsa
gaisuwa ne?Kabir yace yayanmu kenan ai shi daban ne
duk yanda kika so ki san halinshi ba zaki iya ba mutum
ne mai ban alajabi na wuce ina dariya,na sanar da
mama aikin da yayanmu ya sani tace to na bar wankan
naje na gyara mishi dakin zatayi ma su jamila in na
dawo sai nayi nima nace to na shiga dakin yayanmu sai
yau na yima dakin kallon tsaf,leather sit ne kujerun shi
bakake ne masu girma setinau sai kayan wuta kafet da
labulaye jajaye dakin sai kamshi yak nan na soma da
bedroom din katuwar katifa irin wadda ba asa ta a gado
din nan ce sai hanga na kayan sakawa a saman hangar
akwatuna ne saiti biyu na dubi hangar rataye da kaya
jibge a kan katifar ma duk kaya ne dai dai ko ina
kwashe masu datti nayi a cikin wani dogon kwando irin
na zuba kayan na gyara uwar daki tsaf sannan na koma
falo shima nayi mishi aiki sosai na goge electronics din
komai yayi tsaf sannan na dauko turaren daki na feshe
ko ina na kulle dakin,na kaima kabir,wanan shine silar
fara sani aikinshi na zama mai gyara mishi daki har ya
zama dayan key din dakin ma a hannuna yake kullum
da safe sai na gyara nake tafy makaranta wata ranar
laraba na isa dakin da sauri dan in gyara na tura naga
dakin ya bude a raina nace yau yayanmu bai je training
bane?na shiga ban ganshi ba na cire hijabina na ninke
na ajiye a saman kujera kaina tsaye na shige uwar
dakin kayan barci ne a jikina doguwar riga da
wando,sam ban san yana bedroom ba na shige toilet na
gyara tsaf na fito bedroom din sai a lokacin na kula da
mutum kudundune cikin bargo nayi sauri na duba kan
gado dan na tabbatar yayanmu ne a kwance,ya
kudundune da sauri na juya zan fita sai naji yace zo
nan muryarshi irin ta marassa lfy nazo na dan duko
yacw ki dafa mani ruwan lipton nace to na fita zuwa
dakinmu mama na samu tacw har kin gama?nace ban
ma gyara ba don yana nan ne yace akawo mashi ruwan
lipton inaga bashi da lfy ne,mama tace ga wannan dibar
mashi a ciki na baban sagir ne da yasa na dafa mashi
dan yana fama da mura sai dai nasa kayan
kamshi,nace zaisha ai yana shan na gida kuma yana
sawa na diba na kaimashi na rusuna na bashi da kyar
ya mike ya zauna akan gadon ya amsa duk naji banji
dadi ba nace yayanmu baka da lfy ne?yace eh nace
sannu,haka na koma naci gaba da gyaran falon har na
gama na kara lekowa nace sannu na gama ko za'a
kawo maka wani abu ne?yace ki shiga ki sanar da
hajiyata sannan in ba zakiyi latti ba to ki dafa min
indomie nace to cikin mintuna da basu fi biyar ba na
dafa mishi hadaddiyar indomie na kai mishi....
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Afalo na sameshi zaune kan doguwar kujera yana
sanye da singilet da gajeran wando naja dan karamin
table din glass din dake tsakar dakin na dora cooler fin
a kai na zuba mishi a cikin plste nasa cokali nace a
baka ruwa?ya girgiza kai a raina nace yau dai ba danne
dannen waya ba tare da ya dubeni yace kin fada ma
hajiyata din ne?nace bata bude kofa ba,yace bani waya
a cikin bedroom na shiga na wayar na kan katifarshi na
dauko na duba fuskar wayar gabana yayi wani
mummunan faduwa sakamakon ganin hoton anty mimi
a fuskar wayar na kai mishi sañan nace bari na gyara
cikin,na shiga na gyara na fito yana cin abinci yace
bani abinsha a fridge na bude coke na gwangwani na
dauko mishi dan ina yawan ganin gwangwanayen coke
din a cikin bolarshi na hado mishi da ruwan Cway na
aje na wuce ban wani karya ba shiryawa nayi kawai
nasha ruwan tea kadan don kar mama tayi min magana
na fito su mami sun jima da shiryawa shi yasa ma ban
tsaya saka safa ba,haj yaya mukayi karo da ita ta dawo
daga dakin yayanmu ta dubi bilkisu tace yayanku bashi
da lafiya ku shiga ku gaishe ahi keda saa da mami
sukace to sun shiga ni kuma na tsaya daga waje ko
yaya akayi ya ganni sai ji nayi yace ba zaki shigo bane
ke? Na shiga da sallama na ce sannu bai amsa mani ba
ya cigaba da cewa in kin dawo makaranta ki dafa mani
wani abu ,karfe nawa kuke dawowa?nace biyu yace to
zan je na ga likitane sai ki samar mani wani abu nace
nace me zaa dafa yace komai ma,muka fito su bilkisu
sai wai hararata suke yi ni ko tausayin halin da yake
ciki shi ya dameni ko a mota sam na kasa sakewa duk
tunanina yana can gunshi sai kuma abin da yafi tsaya
mani a rai hoton anty mimi dake cikin wayar yayanmu
tana sanye da jar riga kanta ba dankwali tana ta faman
murmushi duk sanda na tino sai gabana ya fadi a ranar
sukuku na yini ko yan ajinmu sai da suka tambayeni
nace banjin dadi haka a mota da muna dawowa na kifa
fuskata kan jakata ban da tunanin yanda yayanmu ya
yini da jiki bana tunanin komai har naga karfin halina
irin wannan daga hankali haka,mami ta dafa bayana
tace iman wai yau me yake damunki ne?nace banjin
dadi ne tace sannu na amsa muna isowa gida kowa na
kokarin leka dakin don naga an karo kofar saa ta
harareni tace neman suna shishigi babu kwarjini ban
kula ta ba na shige dakin da sallama yana kwance
sambal a kan 3sitter barci yake amma fuskarshi a sake
tamkar yana murmushi don ko idonshi biyu bai cika
faraa ba,wayarshi a ajiye kan kirjinshi ina mamakin irin
son da yake ma waya na dubi fuskarshi gsky yana da
kyau sosai cikinshi a dame tamkar baya cin abinci na
kuma duba sa amma shi dogo ne don kanshi a hannun
kujerar yake taga ba ma kafar shi ya dora amma duk da
haka kafar sai dai karfinashi ne ya haukan hannun
kujerar farin gajeren wando da yar tshirt itama fara
sune jikinshi,na juya da niyar in fita sai naji ance me
kike so?gabana ya yi mumunan faduwa nasa hannu na
dafe kirjina jakata ta fadi kasa na kuma kasa juyowa
jikina sai rawa yake yi nayi waje da gudu a firgice na
shiga daki Allah yasa mama bata falo don haka sai na
shige dakinmu,sai da na nutsu sannan na fito na shiga
dakin mama ta dubeni tace ya sauran yan uwanki suka
rigaki shigowa?nace yayanmu ne ya kirani yace na dafa
mashi abinci kuma yaki fada min wane zan dafa yace
wai kowanne na dafa,mama tace tunda bashi da lfy ne
to ki dafa mashi wake da alayyahu ki sa kayan ciki
akwai a fridge ki mishi hadi sosai yanda zai mishi dadin
ci nace to.Da yake tun a makaranta mukayi sallah sai
na shiga aiki kawai uku da kwata na kammala aikin sai
da na watsa ruwa sannan na aiki sagir ya gani ko kofar
dakin yayanmu bude take bayan ya duba ina sanye da
riga da siket na farin lesi na shiga da sallama shine ya
amsa gaba na na faduwa na shiga abinda na gani shine
ya tsorata ni,anty mimi zaune a gabanshi a kan kujera
shi kuma yana kwance tana rike da hannunshi bansan
dalili ba sai naji duk banji dadin ganin haka ba sannan
ga wani abu da ya tokare mani kirji wata tsawa da anty
mimi ta dakan ita ce kuma silar rudewa ba zaki ajiye
abin da ke hannunki bar nan ba?useless kawai kin wani
tsaya akan mutane,na ajiye kan table zan juya sai
sannan yayi magana yace baki zuba mani ba zaki
tafi,,Najuyo da sauri ban dubesu ba na dauki plate daya
da na kawo don haka na zuba mashi cokali ma daya na
kawo na sa mashi na tura table din gabanshi dan ya
tashi zaune,dakin ya dauki kamshin abinci yace ki kawo
wani cokali da plate din tace no ba zan ci ba barshi,na
bude fridge na fito mashi da coke da ruwa na ajiye
tunda na fito nake mamakin yayanmu iya kwanakin da
na dauka ina mishi aiki ban taba jin yace mani sannu
ba haka ban taba jin yace abincin nan ko dakin nan
baiyi daidai ba sam.Wasa wasa na zama baiwa,gyaran
daki nice girki nice aike yanzu duk inda naje sai ya
jirani na dawo sannan zai aiken abinda ke ban mamaki
bai taba nuna min yana jin dadin abinda nake mashi ba
sannan uwarshi da kannanshi sun kara sani a gaba wai
mun shanye mata da kabir ma ya kan sani nayi mashi
aiki amma ba kullum ba kwana biyu uku hakan ya kan
ce a share mashi daki kuma idan na dafa ma yayanmu
abinci shima ina zuba mashi to a cikin satin nan ya
soma aiki shima aikinshi ya ragu,
Kwanaki sun shura ana saura sati ukku bikin su Anty
Mariya mami take bani lbr komawar yayanmu in anyi
biki da kwana biyu nan duk naji ba dadi nace mata sai
ya dade zai dawo?tace a'a yace duk bayan wata shidda
zai dinga zuwa saboda zancen bikinshi da mami da
zaran ta gama HND dinta nace Allah ya kaimu.....
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
Baba shine yayi mana ankon bikin gaba daya ko da
yake kala biyar suka fitar shi kuma biyu yayi mana, ana
sauran kwana goma biki da misalin karfe uku na
yamma ina tsaye bakin kofar yayanmu ina sanye da
atamfa sai karamin hijabina mai less fari takalmina fari
yayanmu yace nazo zai aikeni kafin ya fito daga daki
sai ga wasu abokanshi suka min sallama na amsa
sannan na gaishesu suka amsa min gami da cewa mai
dakin yana nan?nace yana ciki suka ja fararen kujerun
roba da yayanmu ya zuba a gurin suka zauna,sai gashi
ya fito guna ya nufo da leda an rubuta SI super market
a jiki,yace ga wannan ki hau mashin ai kinsan gidan su
mimi ko?nace e yace to ki kaimata kuma ki yi sauri
yanzun nan,ga wannan ya miko mani dari biyar na fita
ba wai don nasan gidansu anty mimi ba bana dai iyayi
mashi musu ne,bansan dalili ba na dai san malali
suke,gidansu Amira na shiga sannan nace don Allah ta
kira mani mami da wayarta mami tace gata nan ma
zuwa gidansu Amiran dana soma mata bayanin cewa ta
min kwatancen gidan su Anty Mimi sai tace min me
zan je inyi?nace yayanmu ne ya aikeni,suka rakani su
da Amira don na hau mashin tayi ma mai mashin din
kwatancen inda zai saukeni muka tafi yanda Mami tayi
mani kwatance haka nabi bayan na sauka a mashin nan
da nana sai gani a gidansu anty mimi na shiga
kannanta na samu suna wasa a harabar gidan sune
suka yi min jagora har ciki nan na sami Haj Laura da
wata kawarta suna hira na gaishesu da farko bata
ganeni ba sai da na gaya mata daga inda nake sannan
ta murtuke fuska tace zauna nan na zauna.Ta daga
murya ta kwala ma Mimi kira kan Mimi ta fito sai
wannan kawar tata take tambayarta wannan yar gidan
wacece?maman tace yar gidan kishiyar hajiya ce
yar'uwata itama ta yatsuna baki tace ai har ta haifi yar
da takai girman haka?ko ba amaryasu ba?tace itama
mana amma ai wannan agola ce sai shegen kankanba
kan ta kuma cewa wani àbu sai ga Anty Mimi ta fito
tace gani Mumy, Hajiya ta dube ta sannan ta nuna
mata ni tace ga mai nemanki nan muna hada ido
gabana ya fadi tace meye kike nemana?nace yayanmu
ne ya aikoni tace yace me?na isa gunta nace gashi
yace na baki ta dubi kayan tace duk gidan ba zai aiko
kowa ba sai ke ko?shegu mayun asiri ni dai nayi shiru
na kasa magana,Haj laure dake zaune can gefe tace to
ko bata kayan ta maida mashi mana,tace tabdi ai shi
momy daban yake in har na bari aka maida kayan nan
ai sai nayi dana sani,ta fincike daga hannuna tace ai
zamu hadu ni dashi,a raina nace kamar zata iya mashi
wani abu,ina jinsu sai faman masifa suke nace ai sai
kuyi a raina,ina fitowa daga gidan na soma raba ido ko
zan ga mai mashin amma ban gani ba na soma tafiya
sai naji ihu ban juya ba naci gaba da tafy mai motar
yaja ya tsaya ya fito ya biyoni yace ke yan mata ina
magana,na juyo cikin dardar don ban taba tsayawa da
wani ba nace lfy?ya ce kalau in har ba zaki damu ba
ina son sanin sunanki nace don Allah mallam kayi
hakuri,nacigaba da tfy ganin yana ta bina gashi ban
sami mashin ba ko wane yazo sai ka ganshi da mutum
akai nace sunana Amira yace to ina ne gidanku nan dai
nayi mashi kwatancen gidansu Amira muka rabu dashi
lfy,da kyar na samu mai mashin na isa gida in da na
bar su yaya nan na samesu na dan rusuna nace na
kaimata yana sanarshi(wato danna waya)ba tare da ya
dubeni ba yace ki shiga daki ki dauki wata leda ke ma
kije kiyi amfani dashi nace to nagode kwarai,bai amsa
ba na mika mashi kudin hanuna nace ga canjin kai
kawai ya girgiza mani na nufi dakinshi,irin ledar da ya
aike ni da ita ce akan kujera don haka nasa hannu na
dauka na nufi cikin gida ni da mama muka duba less ne
me shegen kyau kala biyu sai wani yadi mai santsi
shima kala biyu takalmi da jakka kala biyu mama tace
kin gode,nace mama ki bani da na kamu dana su
Jamila sai na kaima yaya Sulaiman a tudun wada tace
sai dai gobe nace mata dama ai.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai masu
nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?
_e_pi_=7%2CPAGE_ID10%2C737012347
A ranar yaya Abubkr yazo da daddare kofar gida ya
tsaya ya aiko Kamal wai nazo,na fita muka gaisa muka
shiga hirar duniya can ya ce kanwata yau nazo da
alamurra masu girma nace to yace zancen na zama ne
na isa kofar dakin yayanmu ganin baya nan sai na
dauko kujerun shi na robana aje mana a kofar dakin
yaya kabir muka zauna ya dubeni yace lman nace
na'am yace ya kamata ace tuntuni kinsan inda nasa
gaba,nace kamar yaya kenan?yace yau dai na gaji ina
son in fadi maki cewar ina sonki kuma da aure ba da
wasa ba,nayi shiru don banyi wani mamaki ba don na
kula da hakan shima yaya Ibrahim kwana hudu kenan
da yazo min da irin wannan maganar,yace sister naji
kin yi shiru,nace to me zance?gasky yaya ni bazan
boye maka ba karatu zanyi har sai naga karshen
biro,ya tsura min ido sannan yace in har zaki yarda ki
aureni to ni kuma na miki alkawarin zan jira ki,na dan
bata fuska nace gsky kar katsaya jirana don ni sai nan
da shekara ashirin zanyi kai kuma kila a lokacin kace
na tsufa ko ni naga tsufanka,yace inda so ai tsufa ba
matsala bane nayi shiru ina tunani shi ma fa haka
mukayi dashi (wato yaya Ibrahim)sam wai jirana
zaiyi,yaya abubkr yaci gaba da matsa min nace yaya
mubar maganar nan in lokaci yayi sai ayi na sako
mashi wani zancen muna cikin hira yayanmu ya dawo a
motarshi na raya a raina cewa daga gidansu Mimi yake
sai kawai naji banji dadi ba kuma wancan abin dake
samani nauyin kirji ya taso,sau daya ya dubi inda muke
ya shige dakinshi sai naji ma duk hirar ta gunsheni
nace da yaya Abubkr zan shiga gida yayanmu ya dawo
kuma fada yake mana ya dubeni yayi shiru sannan
yace har yanzu bakida waya a hannunki ko?nace eh
amma mama tace ina gama secondary zata sai mani
ya juya gefenshi ya dauko wata leda yace min gashi
wannan ni na sai maki ba Baba bane bare mama tace
ki maida,nace to bari sai na fara fadi mata in ta yarda
sai na amsa yace dole sai na amsa ko ya kwana a
gidan nan,dole na amsa yana tfy na dauki kujerun
yayannu na nufi kofar dakinshi cikin sanda na ajiye zan
tafi naji yace wanene a nan?nace nice yace me kike
nema?nayi shiru sai gashi yazo bakin kofa fuskarshi a
murtuke yake magana wayace ki daukar min kujera?
nayi tsuru tsuru yace wannan shine na farko kuma
inason ya zama na karshe kar ki yarda ki kuma daukar
min kujera ko ni sa'anki ne?nace a'a na durkusa nace
yi hakuri bai min magana ba ya wuce daki ni kaina dari
dari nake bansan yanda zanyi da waya ba. Washe gari
nayi kuru da safe na nuna mata tace ke bakya jin
magana ko?nace miki sai kin kammala karatunki
sannan zaki ci gaba sai na sai maki waya amma kinje
kinsa Abubakr ya sai maki ko?to shi kenan,na soma
hawaye ina cewa wllh mama bani na sashi ba tace ki
maida mishi in yazo nace to har tara na safe ban daina
kukan

Please Login or Register in order to submit comment