Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yau, abin ne ya zo a kurace, don haka a kuracen za ayi, duk wata gayyata na gamata a jiya sai ko ‘yan office din ku su ma ka yi text kawai ka turawa kowa.
Na jika ba a yadda na saba jinka ba, wani abu?”
Hawaye suka ziraro daga idanun Khalipha, sharrrrr..........suke zuba kamar an sunce famfo. Ya ce cikin rishin kuka, “Daddy na gode da kaunarka da kulawarka gareni, da kyakkyawar zuciyarka mai son faranta min a kullum.
Abin da zan fada yanzu don Allah Daddy kada ka yi masa wata fassara daban, ko ka yi tunanin na yi ne don in mai da kai abokin wasana, ko kuma na yi don in tozarta in wulakanta ka, ko don ban gode maka ba, ko don in karya maka zuciya.
Na yi hakan ne domin neman masalaha tsakanina da Ubangijina. Na fasa auren RAYHANAH a daura da Radhiyyah ‘yar Dr. Halima. Ita kuma Rayhanah Allah ya huci zuciyarta ya ba ta wanda ya fini”. Kawai sai yasa masa kuka.
Dr. Mansur ya dade bai yi magana ba, zuciyarsa ke wani irin tukuki na fushi da Mami mai tsanani, fushi irin wanda bai taba yi ba a rayuwarshi ta duniya.
Tabbas Asma’u ce ta yiwa Khalipha barazana da matsayinta na (uwa) domin dankafar da Rayhanah da martaba nata Dan.
“To ai shi kenan”.
Bai san sanda ya gayawa Khalipha hakan ba.
“Ta nuna power dinta a kanka, nima zan nuna tawa da wanda na haifa nake da iko da shi. Dadin haihuwa kenan. Yau da ban haihu ba da Asma’u ta nuna min iyakata ta nunawa duniya BA NI NA HAIFE KA BA!
Babu komai, daina kuka Khalipha, zan mata yadda take so, nima zan yi yadda nake so. All the best Khalipha, yi biyayya ga mahaifiyarka domin samun tsira a gidan duniya da lahira baki daya.
Kada ka damu da bacin raina, wallahi ko kadan baka bata min ba, ban kalleka da matsayoyin da ka lissafa a baya ba, face na yi maka kallon DA MAI NEMAN ALJANNAH a diga-digan mahaifiyarsa.........”
Ihu Khalipha ya saka masa. “Daddy ba kai ka haifeni ba? To wane ne? Shege ne ni?” Kara yake saki da ihu mai gigitarwa saida shi kansa Dr. Mansur ya razana. Da tsoron kada Khalipha yayiwa kansa wani lahani. Bai san sanda ya soma kuka ba shima ya soma kira cikin lallashi da nadamar bacin ran da ya kai shi ga furta abinda yayiwa kansa alqawarin har abada bazai furta ba,
“Cool down Khalipha!!! Ba shege kake ba, da ubanka, ita ta haifi abinta da mijinta na fari, tun auren saurayi da budurwa, bayan haihuwarka suka rabu, kana da shekara biyu ya rasu.
Ni da ita mun hadu ne a jami’ar Trinity din Ireland (Dublin) ta zo karatu nima na zo, tana zaune da Uncle din ta da matarshi tare da kai, Nanny na kula da kai ita kuma tana karatu. Da muka yi aure ne na karbeka muka karasa karatu muka dawo, da shekaru hudu da auren mu ta haifa min Ibraheem.
To ka ji, kwantar da hankalinka har gobe kai Dana ne Khalipha, ba wanda ya isa, ba abin da ya isa ya kankare wannan sunan Abdullahi Mansur Takai, sai wanda ya halicce ni ya halicceka.
Mahaifinka Balaraben Hurghada ne (Egyptian) ya zo Jos kasuwanci ne ya zauna a cikinta tsayin lokaci har ake kiransa (Ba Hurgade Mukhlis), ya kuma bar maka tarin arziki mai yawa wanda iyayensa suka zo suka kwashe, suka kuma ki karbarka, a cewarsu basu san da zancen auren ba tunda bai gaya musu ba, duk da fata ta nuna amma kamanninka da ita ne sak.
Tun daga lokacin na mai da kai Da na Khalipha, kuma har gobe matsayinka kenan. Share hawayen nan Khalipha bana son su and I’ll stand by you..... ina a bayan ka yiwa mahaifiyarka biyayya domin ta sha wahala da kai yadda baka zato a Dublin. Ga karatun medicine ga rashin lafiyar ka ta ciwon hanta har Allah ya baka lafiya.
Tunda ba ta so to ba ta so din ne, ko anyi abin ba zai yi albarka ba, ba kuma za ta bari a zauna lafiya ba. Kyale Asma’u da kafiya a kan abin da bata so, in fa ba ta son abu ba za ta taba son sa ba.
Tana da hakki mai girma a kanka wanda ni bani da shi. Zan kuma nuna mata nima na haifa, kowa ya yi iko da nasa”.
Ya ci gaba da lallashin Khalipha wanda ke kuka mai keta zuciyar duk mai imani, har suka aje wayar Khalipha bai daina kuka ba. Shima Dr. Mansur hawayen yake ta sharewa da hankicinsa. Ya tada motar ya hau kan titi ya karasa Takai.
A kofar gidan Hakimi ake ta sauke huhun goro da alawa da Dr. Mansur ya zo dasu shake a boot din motarsa. Wajen matan gidan ya fara shiga aka gaggaisa da su Haj. Karima, sannan suka kule a falon Hakimi shi da dan’uwansa suna tattauna mai yiwuwa. A take aka soma gayyatar daurin auren da za ayi a gobe Lahadi.
Bayan Khalipha ya yi kukansa har ya gaji, idanunshi sun soma yi mai zafi da wannan sabon al’amari da ya tunkaro shi. Ya girgiza zuciya da ilahirin gangar jikinsa.
Wai Baba Dacta ba shi ya haife shi ba. To shi din wane irin mutum ne mai karamci da kyautatawa ga al’umma? Mutane irinsa tsiraru ne a cikin al’umma.
Mami ya kira, muryarsa sak kamar babu komi a cikinta.
“Alright Mami. It’s done, sai ki sanar da Dr. Haliman Daddy ya ce in gaya miki gobe in sun dawo daga daurin auren da za suyi a Takai za su zarto nan Kano a daura na Radhiyyah. Mami kisa min albarka! Albarkarki kawai nake nema Mami, bayan wannan babu wani abu. Zan samu Mami???”
Hawaye ne suka sake zubo masa, wanda bai damu da ya sharesu ba, suna ta zuba a kan cinyarsa.
Maimakon Mamin tasa mishi albarka kamar yadda ya roka, sai ma ta hau tambayarshi wai daurin auren wa su Daddyn za su yi a Takai?
Khalipha don bakin ciki sai ya sanya kansa cikin gwiwoyinsa kamar karamin yaro ya ci gaba da kokawa kansa-da-kansa. Ita kuma Mamin a can ta gaza sukuni.
Ga dai Khalipha ya haifu ya yi mata yadda take so, ya hakura da farin cikin rayuwarsa domin ya faranta mata, ya samu albarkarta amma zuciyarta ta gaza nutsuwa da son sanin auren wa za a daura a Takai?
Kada zancen Dr. Halima fa ya tabbata, Rayhanah ta zama kishiyarta Dr Mansur ya yi auren huce haushi da ita. Tasan zuciya irin tasa idan ransa yayi mummunan baci bahagon hukunci yake yankewa. Ai sai ta mike ta zari makullin mota ta nufi gidan Dr. Halima a gigice domin maganar ta fi karfin ayita a waya. Dr. Mansur macijin sari ka noke ne, shirunsa a kan al’amari na nufin daukar mataki wanda ba zai yiwa victim dadi ba.
Tana tafe da gudu tayar motarta ta gaba ta fice, motar ta gangara ta bugawa wata katuwar mota duk fitilunta suka kwankwatse, Allah ya sota ba abin da ya sameta, sai buguwa da kanta ya yi a jikin sitiyari, sai dan gilashin da ya yanki goshinta.
A take jami’an tsaro suka cika wajen suka jawo mata bacin lokaci da biyan cin hanci. Ba ta isa gidan Dr. Halima ba sai da magariba.
Dr. Haliman ta ganta afujajan ga jini na zuba duk ya bata tsadadden swiss lace yellow dake jikinta. Ita ta yi mata dressing din wajen ta rufe da plasta, sannan Mamin ta koro mata bayani.
Maimakon Dr. Halima ta tayata jimamin abin da take wa gigita da tsoro a kai, sai guda ta je ta sakarwa Radhiyya a ka, ta kira Babanta a take ta sanar da shi.
To dama shi Alh. Kabir shanyayye ne, take babu bin ba’asin wannan kagararren aure ya soma gayyatar jama’arsa ta waya. Radhiyya ta kunna (Nancy Agram) tana taka rawa a gaban Mamin har ta ji wani bangare na zuciyarta ya yi mata ba dadi, amma ta kasa nunawa ko a fusaka sai dariyar yake take taya Radhiyyah.
Ta kuma ce, “To Radhiyyah kinga dai kokari da fadi-tashin da muka sha ni da mahaifiyarki don samun farin cikinki, kin kuma san Khalipha ba shi ya ce yana ra’ayinki ba.
Don haka (handle him with care Radhiyyah), ki kular min da shi don Allah shima ki yi hakuri da shi sai a hankali, insha Allahu komi zai daidaita”. Radhiyya ta rungume Mami har da hawayen farin ciki a idanunta.
Haka Mami ta dawo gida a salube gwiwa babu nauyi. Don ko cikakkiyar sallama basu yi da Dr. Halima ba, ba ta tofa wani abu a kan damuwarta ba, she is busy calling her people su zo daurin auren Radhiyya da Khalipha gobe.
Idan Mami ta ce ta yi barci a daren yau ita kanta ta san karya ne. Ga azabar ciwon kai, ga radadin ciwo, ga tunani, fargaba da damuwa.
Har sha biyun dare Dr. Mansur bai shigo gidan ba, tana falo tana dakon shigowarsa amma har karfe biyun dare babu ko inuwarsa, wannan ya tabbatar mata a Takai zai kwana.
Ta soma kiran wayarsa ana cewa a rufe. Sai ta koma kiran Khalipha shima a rufe. Tamkar wadda aka yiwa allura ta zabura ta yo dakin ‘ya’yanta mata, kwayar idanunta sun zurma ciki sosai tashin hankali da zullumi.
Abida da Jawahir kowacce na barci a gadonta, sai Azizah a kan sofa take nata barcin. Daga can kusurwar karshe ta dakin ta hango Rahane tana kan sallaya da hijabin da ya rufe dukkan jikinta sai fuska da tafin hannu, amma ko kafafunta ba a gani, tana rike da Alkur’ani bugun Misra tana karantawa amma ba a fili ba.
Dai-dai lokacin da ladanin wani masallaci dake makwabtaka dasu ya kwalla kiran sallar Asubahi. A yadda Mami ta nufota a fusace kamar kurar dake jin yunwa ya sata rufe Alkur’anin da sauri ta aje gefe, tana karanto duk addu’ar da ta zo bakinta, don ta yi zaton Mami rufeta da duka za ta yi.
Bayan ita dinma bata da lafiya, adalilin duk wasu hanyoyin sadarwa tsakaninta da Khalipha sun yanke. Baya neman ta, ita kuma idan abu ya dameta, bata iya gayawa kowa, kawai tasa a ranta Khalipha ya gama yayinta ne dama ba aurenta zai yi ba, yaudara ce kawai irin tasu ta ‘ya’yan gata. Ya samu wata dai-dai da shi, ita kuma ya rufe duniyarta.
Wannan ciwon da Khalipha ya ji mata a zuciya, shi ya kassara ta, ciwo take a tsaitsaye duk da bata kwanta ba. Wani bangare na zuciyar tata kuma sai ya ce, “To ai Khalipha ba shi da laifi, bai yaudareki ba, ke kika yaudari kanki, da kika dauki dukkan amana da soyayyar duniya kika bashi, da saninki kan cewa kina zaman ‘yar karo ne a gidansu amma kika zarme kika wuce gona da iri, wai shine life-mate dinki......”
Wannan tunanin din dai, bai rage komi daga son da takewa Khalipha ba, sai beken kanta da take gani. Ba ta gama tunane-tunanenta ba da mamakin abin da ya kawo Mami dakinsu yanzu da asubahi haka kamar Damisa, ta ji Mamin ta finciko ta babu ko takalmi a kafarta.
Figarta kawai take har a kan step din bene wanda zai sadata da reception din gidan, tana buguwa tana komai amma Mami ba ta fasa janta ba sai da ta dangana da gate.
Ta bude kofar wucewar mutum ta cillata wajen gidan tana cewa,
“Ki tafi gidan ubanki! In ya mutu ne ki nemi danginki. Ba nufina in wulakanta ki ba, amma ke kin dauko hanyar wargaza min rayuwar iyali, kin rabani da mijina da ‘ya’yana da kwanciyar hankalina.
Taimako ba hauka bane, Allah ya gani na yi iya wanda zan iya. Ina rokonki Rayhanah kada ki sake waiwayen inda muke, ki je kauyenku ki yi aure ya fiye miki da ci gaba da zama cikin iyalina kin ji na gaya miki”.
Garammm! Ta rufe kofar. Karar kofar kenan da ta razana Malam Dahiru dake sallah ya fito da gudu ya ga shigewar Mami da kulle kofofin reception dinta da ta yi.
Sai kuma ya ji shesshekar kukan mace a wajen get dinsa. Da azama ya bude ya fita yana haskatata da tocilan dinsa.
“Wace ce a nan?”
Ya tambaya cikin barazana, a lokacin da kwayar idonsa suka shaida wadda ke tsugunne a gefe tana kuka.....
“Rayhanatu?”
Ya ambaci sunanta cikin kokwanto. Hawaye kadai ke zuba ta ce, “Taimakamin da kudin Motar da zai kai ni Takai Malam Dahiru......... don Allah ba don ni ba......”
Ta ci gaba da kuka mai matukar ban tausayi.
A kidime ya ce, “Rayhanatu ba inda za ki, shigo daga nan, sai Dacta ya dawo koma mene ne ba zan barki ki tafi ba don kin yi ma Mami laifi. Ki yi hakuri ki daina kukan ya dawo”.
Tana kuka sosai ta ce, “Malam Dahiru za ka iya bani ko ba za ka bani ba?”
Yadda ta fiddo masa manyan idanunta dake jike jagab da hawaye sun kuma kada sunyi jawur, sai jikinsa ya hau bari.
Ya ce, “Zan shiga matsala ne Rayhanatu idan na barki kika tafi....... ki ceci hanyar cin abincina ni da iyalina kada ki yi sanadin rabuwata da karimin mutum irin Babanku. Ita ma dai Hajiya wane irin laifi danka zai yi maka ka kore shi? Korar ma cikin duhun Asubahi?”
Da ta ga Malam Dahiru ya tsaya ya tsinke mata da surutu mai ban haushi a gareta, ba kuma shi da niyyar taimakon nata. Bakin ciki ya yi bakin ciki a zuciyar Rayhanah, sai kawai ta tattare doguwar jallabiyyar dake jikinta ta yanka da gudu, gudun da ba ta taba zaton ta iya ba kamar filfilwa a lokacin gari ya soma haske.
Ko kabarin iyayenta ne ta yarda ta koma da ta kara kallon ko da get din gidan su Khalipha, Abida da Mami, da suka yiwa zuciyarta rauni mai zurfi da ba zai taba warkewa ba.
Malam Dahiru dai girma ya soma cimmasa, ba zai iya wannan gudun da Rahane ta fyalla ba balle ya kamata. Sai ya dau wayarsa ya kira Dacta ya gaya mishi iya abin da ya gani.
Ga mamakin Mal. Dahiru, Dacta bai wani razana ba, bai yi mamaki ko fadan da ya yi tsammani ba, cewa ya yi da shi,
“Don me baka ba ta kudin motar ba? Hau babur dinka maza ka bita ka ba ta kudin ka yi tafiyarka”.
Ya jefa waya a aljihunsa ya tashi babur aguje shima ya bi hanyar da ta bi wadda za ta sadata da bakin titi.
Unguwar Lamido Crescent unguwa ce a Kano ta wadanda suka san muhimmancin BIRO (‘yan boko). Babu ruwan kowa da kowa, ba cinkoso ba sa-ido kamar kana Abuja.
Don haka ko gilmawar motoci babu a dai wannan lokacin. Sanda Mal. Dahiru ya hawo kan titi ya hangota can gaba da shi tana bin gefen titi sauri-sauri gudu-gudu kamar mai yin Safah da Marwah.
Ita kanta ba ta san ina take jefa kafarta ba, fatanta kawai ta ganta a Takai, koda akan iska ne, kuma hawaye basu bar tsere a kan kundukukinta ba tana ta sharewa da zurmemen hijabinta.
Da ta ji karar babur a bayanta ai sai ta kara artawa a guje, shima kuma ya nuna mata mutum da inji ba daya bane, ya sha gabanta har ya dan bugeta ta fadi a kan titin.
Ya taimaka mata ta tashi ya rike hannunta gam-gam domin kiciniyar kwacewa take tana rokonsa kada ya maidata gidan Dr. Mansur, ya tafi ya kyaleta tunda ba zai taimaka mata ba.
Mal. Dahiru ya ce, “Na rantse da mahaliccina ba zan mai da ki ba. Hau bayana in kai ki tashar Mariri in sa ki a motar Takai”.
Kukan dai bai tsaya ba, amma ta ji sa’ida a ranta. Ta dane bayan babur ya ja suka tafi. Lokacin gari ya fara haske misalin karfe shida na safiyar Lahadi kenan.
A tasha Mal. Dahiru ya sata a motar Tsangaya, ya sanar dasu a Takai za su sauke ta. Ya kirgo kudin da suka bukata ya basu ta shiga gefen taga daga baya ta zauna.
Tana share idonta tana dagawa Mal. Dahiru hannu da godiya. Ya zagayo tagar da take ya mika mata naira dari biyu da kunshin kosai mai zafi. Hannu biyu tasa ta karba, tana gode masa. Ta share hawaye ta ce,
“Sai wata rana...... Malam Dahiru na gode a gai da Sahura”. (Matarsa).
Bai bar tashar ba sai da ya ga tashinsu, bayan motar ta cika. Shima sai ya ji danshi a kan fuskarsa, yarinya-yarinyar kirki, me ya raba ta da mutanen kirki irin wadannan? A fuskarta da yanayinta dai ya nuna ko yatsa kasa mata a baki ba za ta ciza ba, in baka yi mata izini ba. To me ya hadata da Dr. Asma’u haka? Ita ma ai mutuniyar kirki ce”.
Haka ya yi ta sake-sakensa shi kadai har ya koma gida ya jingine babur dinsa ya ci gaba da harkokin gabansa.


****
[12/24/2019, 21:47] Takori: Haj. Karima wadda ta amsa sunanta (Mai Karamci) kuma uwargida abun alfahari ga miji da iyalanta, ta yi sallama dakin da amaryar take a lokacin Inna Juma na faman yi mata fadan ta ki shan jarkar tsumin da Haj. Karima ta kawo tun jiya.
A sanyaye Rahane ta ce, “Inna zaki ne da shi mai yawa, bama shan sukari. Baba Dacta ya ce yana sanya Diabetes (ciwon suga), kuma yana lahani cikin hakora”.
Inna Juma ta ce, “Ciwon sukarin ya ci uwatar, mu da muka shanye fiye da jarkoki dubu ai kin gammu a asibiti”. Ta tsiyayo a kofi.
“Ungo kwankwade ki bani kofin, don kushewar Ubanki.........”
Ita Hajiya Karima sai dariya take da jin muhawarar tasu. Ta idasa shigowa cikin dakin tana ce da Inna Juma.
“Kyaleta Inna, da kanta za ta ce ki bata idan ta san amfaninsa, sanda za ta kwankwade jarka goma ma ba za ta sani ba”.
Rahane ta kyabe baki ta zumbaro shi ga Inna Juma, ta ce, “Don Allah Maman Anty Nabilah mene ne amfaninsa a lafiyar dan-adam? Zaki yana sa basir da….......”
Ai buge bakinta Inna ta yi da mafici har leben kasan ya kumbura. Da sauri Haj. Karima ta kwace maficin Inna na shirin kara mata, ta ce
“Rufa mata asiri Inna kada angon ya ganta da kumburarren baki ya ce ya fi son ki. Rayhanah sha kawai rabu da Inna, ki sa a ranki kawai Inna ba za ta dage ki ci abu ba, alhalin ta san zai cutar dake ba”.
Inna ta ce, “Sanabe a gun Rahane har da na tsiya, komai ta ce yana sa kaza yana sa kaza, komai ka yi baka yi dai-dai ba sai ta kwakulo ma illah”.
Hajiya Karima na dariya ta ce, “Inna rainon likitoci ce fa, ‘yar likita (uwa da uba) matar likita, kinga kuwa ko ba ta shiga aji don ta koyo likitanci ba za ta iya yi miki allura ta baki maganin kowacce cuta, ai ke gaba ta kai ki, wai gobarar titi a Jos, babu ke babu hawa layin ganin likita a asibiti”.
Haka dai suka yi ta barkwanci, Inna da Haj. Karima, Rahane ba ta tsoma musu baki ba. Cewa take cikin ranta; Haj. Karima daban ce cikin matan gidan nan wajen saukin kai da karamci, dole mijinta ya sota fiye da su Haj. Indo. Don ta kama girmanta, ta iya zama da kowa dake samanta ko karkashinta da zuciya daya.
Kusa da Rahanen ta dawo ta zauna, ta ciro wasu tablet din na Indonesia tana cewa, “Rahane maza kora wadannan da ruwa, kinga yanzu za a kai ki gidanki a Kano kafin sati mai zuwa Daddy ya danka ki hannun angonki. A sannan ne wadannan magunguna da muke takura miki ki sha za suyi miki amfani. Ki daina mai da kanki yarinya mana, kin girma fa, aure GIRMA ne, ko shekaru basu kai ba”.
Rahane murmushi ta yi har fararen hakoranta suka bayyana, kanta ya kumbura, don tana son GIRMA. Tana so a ce ta girma, she’s no more a kid now!!!
Ta karbi magungunan daga hannun Haj. Karima tana dubawa, ta kasa karanta rubutun chinese dake jiki. Ta ce cikin ranta, “How can I take drugs without Doctor’s order?” Ta karba ta hambuda su a baki, ta boye su a kasan harshenta ta kora da ruwa.
Haj. Karima na ba da baya domin ta je ta dawo ta yi toilet da gudu ta tofo su cikin masai ta yi flushing ta wanke bakinta. Inna Juma da ta fahimceta ta hau salati da sallallami.
Rahane ta rungumeta tana rokonta kada ta gayawa Hajiya har da ‘yar kwallarta. Ta ce, “Inna ni ba zan sha maganin da ban san na mene ne ba, ba zan sha tablet din da ba likita ne ya yi Prescribing din ta gareni ba”.
Inna Juma ta tureta daga jikinta tace, “Ni da Allah daga ni, ai shi kenan ke kika sani. Ana miki gata kina iyayi. Sai ki je wa mijin salam! Ina ruwan wani”.
Da dan mamaki a fuskarta ta ce, “Inna da da gishiri kike so in je masa?”
Inna Juma ta ce, “Eh mana, ai gara ki je da dandano ko ya so ki, tunda ba kiyo kyawun Yalwati ba, kin dauko bakar fuskar ubanki. Ko da yake yanzu kin dan fara washewa ba kamar sanda kina yarinya ba”.
Rahane na dariya ta ce, “Inna har da cin fuska?”
Inna ta ce, “Har da cin kafafuwa kuwa, idan kika yi wasa in kwace mijin idan ya yi mini. In ta tsuma kaina yadda zai ji ni cau!”
Wadannan languages na Inna Rahane ta kasa gane musu, kuma Innar ta ki fitowa fili ta yi mata bayani sai dukunkune maganar take. Ta je da dandano? Ta yi cau? Sai ka ce wata abinci. May be Inna Juma bata iya Hausa ba.
Barorin gidan Hakimi ke ta shigowa da manyan jakunkuna. Haj. Karima ta biyo bayansu ta zauna sosai tana bude jakunkunan tana fadawa Rayhanah cewa lefenta ne a dinke.
Ta dinga daga atamfofin super da swiss lace kamar debo su akai a kasuwa ba kudi aka sa masu yawa aka saya ba. Takalma da jakunkuna ‘yan Italy abin sai wanda ya gani. Kayan shafe-shafe, turaruka, gyaluluwa, sabulai abin ba’a magana. Ta gaya mata cewa duk nata ne. To abin ya fi karfin Rayhanah ta yi magana sai ido, kuma shi ta zuba mata.
****
RAHANE A GIDAN AURENTA!
A al’adar babban gida musamman irin na sarauta, lokacin bikin aure an saba gwangwajewa a cashe ayi almubazzaranci da dukiya. Amma wannan auren na ‘ya’yan Dr. Mansur biyu (Khalipha da Ibraheem) ya zo da sabon sauyi, ko algaita ba a busa ba, ko kwarya ba a buga ba, haka ko guda babu wanda ya rangada.
Wannan kuma ya samo asali ne da yadda auren ya zo ba cikin shiri ba, ga kuma duka angwayen babu ko daya. Gidan bangaren daya amaryar kam sun cashe sun gwangwaje yadda ransu yake so, an wulakanta naira. Amarya ta daura sittiru na kece raini, anyi hotuna da sauransu.
Amma a bangaren daya amaryar ba ta da wannan gatan, ba ta ma sa-aka ba, ba ta ma kuma da wanda za ta gayyato a duniya idan ba Jawahir ba, ga shi kuma watakila har abada ba za ta koma inda Jawahir din take ba, da aminiyarta Azizah.
Sannan ‘ya’yan Hakimi da yawa da sauran matansa basa farin ciki da aurenta da Ibraheem saboda Nabilah. Don haka ko taron wuni ba kowacce ce ta zo ba, wannan bai damu amaryar ba, balle danginta da suka zo rakata gidan mijinta daga Albasu, Takai da Tsangaya dukun-dukun da su, bayan su a wurinsu sun kure adaka.
Hakimi da kansa yana gaban motar Dr. Mansur wanda ya zo daukar amaryar da kansa, a bayan motar Haj. Karima ce, Inna Juma (wadda za ta zauna tare da ita) da Zinaru da babbar ‘yarta Hansai. Bai tsaya ba sai farfajiyar wani matsakaicin mansion mai rufi ruwan kasa da fenti ruwan madara. Guda biyu ne a jere amma cikin get daban-daban a unguwar ‘Farm Center’ dake bayan shagon Kasa (Country Mall).
Babu yawaitar jama’a a unguwar babu cinkoso, yawanci ma duk gidajen ma’aikatan gwamnati ne da sababbin gine-gine da aka fara ba a karasa ba. Sai kamfanoni da shaguna sababbi wadanda ba a fi shekara da bubbude su ba.
Hannun Rahane cikin na Baba Dacta har dakin barcinta, cewa yake
“Da a Takai gidanki yake, a kan doki zan kai ki Rahane. Shiga gidanki kina mai neman aminci daga Ubangijinki, ta

Please Login or Register in order to submit comment