Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

su kafin wani lokaci sai su daina ji.
In har ba a nemi magani da wuri ba, yana hana kunnen da ya kama ji. Bayan rashin ji mai dauke da wannan cuta kan ringa yin magana kasa-kasa, (ta yadda in har baka saurara bama ko ka saba da shi bazaka ji shi ba), sannan ga juwa da hajijiya”.
Dr. Mansur ya ce, “Duk wadananan alamomi Rayhanah na fuskantarsu. Sau tari sai na saurara sosai nake jin me take cewa, to amma Dr. ta wace hanya jin Rayhanah zai dawo daidai ta daina amfani da hearing aid?
Likitocinmu sunyi iya kokarinsu amma abin da suka tsaya a kai dukkaninsu shine babu wata mafita sai ta amfani da na’ura mai kara karfin ji (hearing Aid)”.
Dr. Philips ya nisa ya ce, “Da farko in jin mutum ya fara raguwa, ba lallai ne sai an dau wani mataki ba, na ba da magani ko wani abu makamancin haka. Amma in cutar ta tsananta, na’urar kara ji ta kan taimaka kwarai da gaske. Amma kuma a kan kai matakin da cutar kan yi tsananin dama na’urar kara karfin ji ba za ta iya taimakawa mai matsalar ba.
A wannan matakin a kan yi aikin fida. Fidar da aka fi yi ita ce wadda ake canza dodon kunnen dan Adam da wani kashi da ake yi da dafaffiyar roba ko karfe. A kan kira wannan fida a Turance ‘Stapedotomi’.
A mafi yawan lokuta a kan ci nasara, inda matsalar ji kan kau. Mutum ya dinga ji rangadadau, ya kuma ba da kariya ga can cikin kunnen mutum.
Amma fa wannan aikin fida yana bukatar taka-tsan-tsan, don idan aka yi rashin dace, to fa jin mutum kan dauke dungurungum a kunnen da aka yi aikin. Bugu da kari akwai hadari na lalata jijiyoyi masu kawo sako da gurbata jin sauti.
Don haka kafin a yiwa mutum mai wannan lalura wannan aikin, a sanya zuciya karbar kaddarar samu ko rashi. Duk da a mafi yawan lokaci a kan dace da yin nasara a wannan aikin fidar kunne, amma akwai wahala wajen yanke hukuncin yinsa farat daya da matsalolin da ake samu idan aka yi rashin dace.
Saboda haka ne yasa wasu ke gwammacewa da yin amfani da na’ura mai kara ji cikin kwanciyar hankali har jinsu ya zo ya zama ya tabarbare, inda wannaan na’uraa kan daina yi musu aiki kwata-kwata.
Hakan yasa wasu kan zabi ayi musu aiki tunda wuri, wanda hakan zai sa su zama basu da bukatar wannan na’ura in an zabi yin aiki, ka ga in aiki ya yi nasara to an samu waraka kenan, in kuma an sami matsala ka ga ya zama cewa kunnen da yake da kyau sai mutum ya ci gaba da amfani da shi. Wato an jefi tsuntsu biyu da dutse daya.
Masana a fannin ENT (Ear, Nose & Throat) sunyi muhawara a kan cewa ko da nan gaba a iya yiwa wancan kunnen da ya rage. Wasu daga cikin su sun yarda kan cewa gara mutum ya hakura ya ci gaba da amfani da na’urar kara ji saboda risk hatsarin dake tattare da yin aikin na samu ko karasa kashe kunnen gaba daya.
Madallah da kuka kawo yarinyarku tun kafin na’urar kara karfin ji ta daina yi mata amfani, wato kafin lalurar ta tabarbare da yawa. Akwai shaida takaitacciya wadda ke da’awar cewa kwayoyin magani na flouride za su iya hana ji, kuma za su iya taimakawa wajen kyautata jin. Da ragewa mai lalurar juwa da hajijiya. Amma dai a nan Sikotilan ba’a cika amfani da kwayoyin maganin na flouride ba.
Don haka zabi yana gareku, ci gaba da amfani da na’ura, fida ko kwayoyin magani. Akwai bukatar in baku lokaci zuwa gobe don ku yi tunani da kyau ku yi zabi cikin ukun don samun lafiyar Rayhanah.......”
Har suna hada baki wajen katse shi da cewa, “Babu wani tunani da zamu yi mun dogara ga mahaliccinu, wanda ya saukar da kowacce irin cuta tare da maganinta. A yiwa Rayhanah fida a dukkan kunnuwan guda biyu. Sauran al’amarin (nasara ko rashin ta) mun barwa Ubangijinmu”.
Murmushi Dr. Philips ya yi, yana gyada kai cike da gamsuwa, haka nan shima ya ji ya samu kwarin gwiwa. Ya tura musu takardu cikin folder suka sanya hannu.
Zunzurutun kudin aikin Dr. Mansur ya tura masa cikin jakar dake gefensa (in cash) ba ta banki ba, kamar yadda Philips ya bukata. A yayin da ya dauki biro don rattaba sa-hannu cewa ya yi.
“TAWAKKALTU ALAL-LAH!
LA’ILAHA ILLALLAH!!!”
Wato
“Da Allah muka dogara! Babu sarki sai Allah!!!”


Bai yi barci ba, kwana ya yi nafila, zikirin Ubangiji da neman dacewa daga Allah. Tun Dr. Imam na jan carbi a gefe, har bacci ya kwashe shi a kan sallayarsa bai san tsahon lokacin da Dr. Mansur ya dauka yana sallolinsa da ambaton Ubangijinsa ba.
Yana mamaki cikin ransa, wane irin so Dr. Mansur ke yiwa patient dinsa haka? Da ba shi ya haifa ba? ‘Yan boko da yawa basu da wannan akidar. A wajen gogaggen dan Arewa a boko kowa ya yi ta kansa. Naka shine naka, basu da irin wannan zuciyar. A ganin Dr. Imam mutane irin Mansur, tsiraru ne a cikin al’ummah. Wannan haka yake (Takori)


****


ALKAWARIN ALLAH YA CIKA......
Kamar daga nesa take jiyo kiran sallah, don haka ta yi hanzarin kai hannunta ta shafo na’urarta, don dai ta san bata kwanciya da ita, kuma gabanin alluran da Philips ya yi mata ta tabbata ta cire su.
Da gaske babu su a tare da ita, hakan kuma bai hanata jin kiran sallar Asubar ba. Ta yi saurin juyawa don ganin ta inda sautin ke fitowa. ‘Yar rediyon Dr. Mansur ce dake kan dirowar gadonta ke fitar da sautin kiran sallar. Daga masallacin Qubah.
Wata sassanyar iska kuma ta ji tana ratsawa ta cikin kunnuwanta zuwa cikin kwakwalwarta. Ba ta ko haufi jinta ne ya dawo! Rasss!! Kuma rangadadau!!!.
Sai ta yunkuro da karfi daga kwancen da take, sai Daddy ya yi saurin maidata kwancen sakamakon na’urorin dake lullube da kanta.
“Rayhanahtu aikin bai yi ba ko???” Dr. Mansur ya fada muryarsa na dan rawa jikinsa na dan karkarwa.
Ta dago ido a hankali ta dube shi sai kwallar farin ciki ta ciko idanunta. Ta kurawa Daddy ido kawai ta kasa cewa komai. Ko uban da ya haifeta iyakar kaunar da zai yi mata kenan. Ita kuwa da me za ta sakawa Daddy a fadin duniyar nan? Babu, ba ta da shi ban da ta yi masa addu’a a bayan kowacce sallar farillah kamar yadda take yiwa iyayenta da Iya.
Dr. Mansur ya gaji da kallon da Rahane ke masa babu ko kiftawa hawaye na zuba a idonta, ya karaso jikin gadonta yana tambaya “Rayhanatu........Rahane.......Rayhanah.......kina jina???”
Cikin kukan farin cikin da ya kwace mata ta ce, “Ina jinka Daddy, sosai, ba tare da hearing aid ba!”.
Sai ya juya baya ya yiwa Allah Sujjadah. Dai-dai lokacin da Dr. Philips da Dr. Imam suka shigo. Suka nufeta da azama suna ciccire na’urorin domin allon kwamfutar dake makale a sama ya nuna komai na Rayhanah ya dawo normal.
Kwanaki bakwai suka kara bayan nan duk cikin treatments din ne, da shan magani, sai da komai ya zama dai-dai sannan suka taho. Suka sauka da asubahin safiyar Litinin mai albarka a filin jirgin Malam Aminu Kano.
Daddy bai yi mamakin ganin cewa Mami ba ta zo taryarsa ba, ya san ba ta sani ba, kuma ko ta sani ba za ta zo din ba. Don ko sallamar kirki basu yi ba, wannan ne ya hanashi kiranta a waya har suka je suka dawo.
Matar Dr. Imam ta zo ta dauke su, suka aje Daddy da iyalinsa a gidansa dake Lamido Crescent sannan suka wuce nasu gidan a Badawa lowcost.
Malam Dahiru maigadi shi ya biyo su da kayansu. Daddy ya yi amfani da mukullin shi ya bude kofar reception suka bi matattakala zuwa sama.
Jawahir da Abida na barci Zizah ta fada musu a kai tana ihun murna, “Tashi Yaya Jawahir, Yaya Abida tashi, Rayhanah na ji (with out aid), it is successful...... ku tashii ku gani....”
A gigice Jawahir ta mike da gudu ta rungume Rayhanah, sai ga kwallar farin ciki. Abida kanta ta mamakantu, ta kasa komawa barcinta ta rasa cikin yanayin da take ciki, tana taya masoyan Rayhanah murna ko tana bakin ciki ne ba ta sani ba. Abin da ta sani shine jikinta ya yi sanyi, ta kasa hassala komai.
Rayha wanka ta yi, ta dauro alwala ta bada faralin Asubahi, ta yi addu’o’i na godiya ga Gafurun-Rahimun, neman Rahamar Allah ga iyayenta da Baba Dacta ba don ya mutu ba. Duk hirarrakin da Azizah ke zuba musu labarin kauyen Braemar ne da basu sani ba.


****








Sanda Daddy ya shiga bed room dinsa, ga mamakinsa sai ga Mami ta biyoshi fuskarta a sake kamar ba abinda ya faru.
“Maraba da bakin Scotland, duk da dai tafiyar da dawowar duka babu waya..... da fatan an samu nasarar abin da aka je nema”.
Ta fada tana loosing tie din wuyansa. Bai ce komi ba kawai kallon ta yake. Sai ta fada jikinshi tana kuka a hankali tana ba shi hakuri da cewa, ta zauna ta yi tunani ta ga cewa abin da ta yi bai kamata ba, kishi ne da sharrin shaidan, wanda baya so a zauna lafiya.
Tsakanin mace da mijinta sai Allah. Balle Asma’u da Mansur, wadanda suka gina rayuwarsu a kan soyayya, kauna da fahimtar juna.
Ya ce, “Ni me za ki ce min kuma Mamina, tunda kin daukeni dattijon banza, wannan furfurar da ta fara baibaye kaina duk ta banza ce. Ban taba zato ba Asma’u, ban taba zaton za ki iya zargina a kan komai ba balle Rayhanah! Zan dauki komai, amma ban da a taba mutuncina da gemuna da furfurata.
Zan iya rabuwa da komai a kan hakan Asma’u.......... Rayhanah ‘yata ce, ki sa wannan a ranki, ina jin wani abu daban game da ita a jikina da zuciyata mai kama da kaunar jini a kanta. Allah shi ya fi kowa sani. Amma kin bani mamaki Mami, mamaki sosai, wanda ya sanya ni cikin kokonton anya ke ce? Asma’u ina hankalinki ina tunaninki? Ina yardarm da muka yiwa juna........”
Ta yi saurin kai hannunta ta rufe mishi baki tana girgiza kai hawaye na zuba a idonta.
“Na tuba Dactana, na tuba likitan zuciyata. Tun ranar da wannan al’amari ya faru ban kara samun nutsuwar zuciyata ba, bana isasshen barci saboda nadama. Na yarda lallai lokacin hankalina ya tafi, ka yi hakuri Dactana, don Allah ka yafe mini.......”
Irin rikon da ya yi mata kadai ya isa amsar cewa ya yafe mata ko bai yafe mata ba. Tabbacin shima ya jigata da rashinta.
Da safe ne yake gaya mata duk abin da ya faru a Braemar da nasarar da aka samu. Ta mamakantu kwarai, kuma a lokacin ta tafi dakin su Rahanen.
Fuskarta da murmushi ta dubi Rayhanah ta ce, “Congratulation Rayhanah, Allah ya kara lafiya”.
A sanyaye ta ce, “Amin”. Tana son ta yi kuka zuciyarta cike da kaunar Mami da tsoron kada ta komo irin Mamin da ta koma mata a baya.


To haka rayuwar Rayhana ke tafiya a gidan Dr. Mansur, cikin dadi ko akasin sa. Dama rayuwar ta gaji haka. Watarana zuma, watarana madaci. Mami ta daina kyararta, amma fa bata shiga sha’aninta kamar da. Girman da yake bayyana a tare da Rahanen yana bata tsoro, yarinya ta koma kamar black American, kirar jikinta da yanayin tsayinta mai sa maza su kasa dauke ido a kanta ne.
Ga zigar Dr. Halima wadda ta fi komai yamutsa mata lissafi. Ta kan ce idan ba ta raba yarinyar nan da gidanata ba, to kuwa ta shirya shan mamaki a gaba. Asiri kuma ko ta ina Halima bankawa Khalipha take don ya yarda da maganar Radhiyyah, shi da ma kwata-kwata babu wanda ya san halin da yake ciki.
Su ba kudi ne basu da shi ba, ba kuma wani abin hannun Khalipha ko iyayensa suke hange ba, kawai tana son samawa ‘yarta abin da take so ne, don ta samu kwanciyar hankalinta.
Cikin wannan tsukin Khalipha ya dawo Morocco, ya kammala kwas din da aka tura shi, ya samu karin girma a ofis dinsu. Kowa ya sha tsaraba amma ta Rayhanah (is special).
Kaya ne na matan Morocco zabga-zabga, wasu lafiyayyun dogayen riguna kala-kala guda goma sha biyu, da Pakistan da Abayat suma kowanne dozen guda. Ya yin da kannensa suka tashi da guda shida-shida, doguwar riga biyu, Pakistan biyu da Abayoyi guda biyu.
Wannan karon kam Mami ta kara karfafa zarginta, ta kuma sa ido sosai a mu’amalar Rahane da Khalipha.
Da Khalipha ya dawo ya samu wannan labari da bai taba samun mai dadi kamar shi ba, wato warkewar Rayhanah. Daki ya shiga ya gabatar da sallar nafila raka’a biyu ya yiwa Ubangiji godiya, ya yiwa Baba Dacta addu’a, ya roki Allah ya ba shi karfin zuciyar fuskantar iyayensa a wannan lokacin a kan bukatarsa.
Sai dai abin da ke bakanta mishi rai kwarai shine, sabuwar mu’amalar da Mami ta tsiri yi da Rahane, na rashin sakar mata fuska, haka ko magana take yi da Khalipha idan Rahane ta shigo wajen sai ta yi shiru.
Sannan idan Rahanen ta gaisheta ko ta yi mata magana, amsawa take a ciki kamar ba ta so. A sati daya da Khalipha ya yi cikin gidan yana hutawa kamin ya koma ofis Monday ya lura da hakan.
Ba ta da zancen da take yi masa sai na Radhiyyah, and he is not interested at all. Ta kasa ta tsare ta hana shi kebewa da Rahane da yake tana cikin hutu.
Ko yaushe tana tare da shi, abinci tare suke ci, fita ma in ta kamata sai ta ce shi zai kaita, a haka dai har ya cinye satin shi da Rahane sai dai ya hango ta daga nesa ko in sun fito cin abinci.
Ranar Lahadi da yamma ya koma Abuja ya shiga sabon ofis dinsa, wanda bai sa shi farin ciki ba ko kadan, don tunaninsa da zuciyarsa basa kai, sun yi nisa cikin zuzzurfar soyayya marar misali.
Khalipha baya da zabi banda ya kara kauracewa gidan su, baya son bayyana abin da ke zuciyarshi yanzu, amma zuciyar ta ki jurewa. Ya kan kira iyayen a waya su gaisa a kai a kai ya kuma ba da uzirin rashin samun zuwa da aiki ya yi yawa.
A wata Seminar likitoci na federal govt. da Dr. Mansur ya je Abuja ya yi tunanin bari ya kai ma Khalipha ziyara gida tunda Asabar ce baya zowa ofis. Gidan Khalipha da ma’aikatar su ta ba shi yana nan a (Maitama). Daddy ya yi horn maigadin ya bude mishi yana barka da zuwa. Daddy ya tambaye shi ko maigidana yana nan?
Ya ce, “Eh, yana nan, amma gaskiya a tsukin nan baya ganin kowa, ya kuma yi umarni gare shi cewa ko waye ya zo neman shi ya ce baya nan ko ya same shi a ofis. Yanzun ma don ya ga Daddy ne shi yasa ya bude”.
Daddy ya faka motarshi a gefe cikin rumfar adana motoci a kalla guda uku, ga ta Khalipha nan guda daya kirar (Cadillac Srx) da canzo daga Morocco, daga ita ba wata.
Ya fito ya doshi (door-bell) ta falon yana dannawa. Jibril da ke wankin kayan Khaliphan a bayan gidan ya zo ya gaida shi, sannan ya ce,
“Oga bai da lafiya Alhaji, kuma ya ki yarda cewa ba shi da lafiyar balle ya je asibiti, ni dai na yarda ba shi da lafiyar ko abinci ban yi zaton yana ci ba, don ya hanani yi mishi girki sai dai kullum ya yi ta aikena siyen abinci, kuma yadda na kawo haka nake fiddashi abin da ya taba ba yawa. Ba zai bude ba, da dai ka kira shi a waya”.
Da sauri Daddy ya dauko wayar yana kiran Khalipha sannan ya yiwa Jibril inkiya da hannunshi alamar ya tafi.
Anyi sa’a wayar Khalipha tana kunne, kuma ya sanyata a caji nesa da shi kadan, yana kwance gefen gadonshi da ruwan tokan (pjs) a jikinshi, ya tasa kwamfuta a gaba yana shigar da sakonni.
Sarai ya ji kararrawar amma bai yi niyyar budewa ba, sai kuma ga kiran waya dole ya mike zuwa gareta, ga mamakinsa kiran Daddy ne. Da sauri ya amsa wayar.
Daddy ya ce, “Ina kofar falonka”.
Cikin rashin kuzari ya bude kofar. Daddy ya tokare hannayenshi jikin kofar falon yana kallon shi. Gaba daya ya zube ya yi jajir, idanuwansa manya masu sheki sun zurma ciki, hakan bai hana shi bayyana a kyakkyawansa ba.
Yana shirin russunawa Daddy ya yi saurin kama hannunshi suka idasa shiga cikin falon, ya zaunar da shi a gefensa cikin bakaken (leather seats) din da suka yiwa falon kawanya.
Kafin Khalipha ya furta gaisuwa Daddy ya katse shi da cewa........ “Me ya faru? Me ya same ka, ka kulle kanka kai kadai cikin gida? Me ya zabgar da kai haka? Mece ce damuwarka Khalipha? Gaya min maza, wannan ba Khaliphana da na sani bane”.
Sai ya fada jikin mahaifinsa shi kuma ya rungume shi sosai, ba kuka yake yi ba, ajiyar zuciya yake yi. Ji ya yi zuciyar tana sanyi daga zafi da suyar da take yi.
Wani bangare na zuciyarsa na karfafa shi da cewa, ka yi amfani da wannan damar da Allah ya kawo, ka fadawa Daddy abin da ke neman kwantar da kai ya salwantar da ci gaban rayuwarka.
Daddy uba ne mai fahimta, da akida daban da ta Mami. Babu haufi zai fahimceka, ya mallaka maka abin da rai da zuciyarka ke so. Walwalarka da kuzarinka su dawo, ka dauko Rayhanah ku rayu tare har abada, ku haifi ‘ya’ya masu albarka har zuwa karshen rayuwarku.
Duka wannan tunani Khalipha ya yi shi ne cikin ‘yan dakikan da basu wuce goma ba. Daddy bai katse shi ba, ido ya zuba masa yana sauraren amsar bakinsa.
Khalipha ya dago ya kalli Daddy idanunshi sun kada sun koma brown dinsu masu sheki dake cike taf, da kwalla, wadda babu alamun za a ba ta damar zubowa saboda dauriya irin ta namiji da rashin son nuna karaya.
Ya maida kai ya sunkuyar, sakamakon kwarjinin da idanun mahaifin nasa suka yi masa. Amma fa wani bangare na zuciyarsa na cewa da shi, “A kul! Ka bari wannan damar ta subuce maka...”
Cikin rawar murya da sarkewar harshe ya ce,
“Daddy… Rayhanah…. Rayhanah nake so ka aura mini”.
Dr. Mansur bai tambaye shi wace Rayhanah ba, tunda Rayhanah daya suka sani a duniya dukkansu, basu san wata mai wannan sunan bayan ita ba.
Dr. Mansur bai yi mamaki ba, shi kansa jikinshi na ba shi akwai wani boyayyen al’amari game da Rayhanah a kanshi da ‘ya’yansa tun ranar da ya fara ganinta jikinshi ya ba shi hakan.
Wannan yarinyar rayuwarta cikinsu na nuna al’amura da dama wanda Allah kadai ya sani. Sai dai kuma kash!
A inda ya yi fatan al’amarin ya kasance ba a can ya kasance ba. Anyway a hakan ma baya da ja, kuma yayi farin ciki, amma yadda yasan yunwar cikin sa haka yasan cewa Mami ba za ta taba amincewa ba, musamman da yake ta fishi power a kan Khalipha.
Tabbas Khalipha ba wani abu ke damun shi ba sai soyayya, irin soyayyar da ya yiwa Mami mai azabtarwa, wadda ba a lokaci daya take faruwa ba, a hankali take shigar mutum ta yi masa kisan gilla batareda ya sani ba, tayi masa babakare a zuciya da gangar jiki. Ta hana shi sukuni da nutsuwa har sai ya mallaki abin da take so.
Wannan shirun da Daddy ya yi ba karamin kada Khalipha ya yi ba, tsoron shi Allah, tsoron shi kada Daddy ya ce ba zai ba shi Rayhanah ba ko ba zai yi mata aure yanzu ba. At 34, yana cikin wani mataki na tsananin bukatar diya mace, amma fa Rayhanah kadai.
Ga dimbin mamakinshi Daddy murmushi ya yi ya dafa kafadarsa ya ce, “Wannan shine abin damuwa Babana? Har a sanya zuciya cikin takura? Baka tsoron hypertension kake wasa da aiki da lafiyarka?
Rayhanah ai ‘yata ce kamar yadda kake Da a gareni. Idan har kana so ita ma tana so me zai hana in mallaka muku juna? Ni ai abin farin ciki ne a gareni in aurar da Rayhanah a hannun da na tabbatar ko bayan raina ba za ta wulakanta ba.
A da, na yi niyyar ba zan aurar da Rayha da su Abida ba sai sunyi zurfin karatu, amma tunda har haka ta faru, bani da ja da yin Allah. Abdallah jeka nemi so wajen Rayhanah, idan ta baka ni mai daura aure ko gobe ne. Alas! Babu sauran damuwa ko?”
Hawayen farin ciki suka zubowa Khalipha, ya rungume Daddy yana kuka sosai. Daddyn na share masa da hankicinsa yana cewa,
“Haba Babana, tsakanin uba da dansa ai ba godiya. Duty na ne as a father in tabbatar da farin cikinku in har bai sabawa addini ba. Hakkina ne in yi muku aure, saboda kun kai munzali, amma sabgogin neman duniya suka sha’afar dani ga yin hakan, har sai da ka ankarar dani. Nima na gode Babana. Ya isa kukan nan bana son shi, ya isa!”
Haka ya ci gaba da share mai hawayen har kunya ta kama Khalipha. Daddy da kansa ya je kitchen ya dauki tray ya bude firij ya debo tuffah, inibi, fresh milk da cake da sandwitch ya dawo falon, ya ja tebir a tsakiyarsu ya daura tray din, ya dau tambulan mai garai-garai yana tsiyaya tatacciyar madarar Oldenburger mai sanyi yana cewa,
“Ni bako ba a tareni da komai ba, to bari in yiwa kaina maraba. You donno how hungry I’m”.
Dariya Khalipha ya yi, shima wata azababbiyar yunwa ya ji ta taso masa. Ya karbi tambulan din da Daddy ke mika masa cike da madara mai sanyi ya shanye, ya sake cika masa ya kwankwade. Zai karo masa yana dariya ya daga masa hannu. Sai shi ya cika ya shanye.
Khalipha ya mike ya je kicin din, ya debo dambun nama mai yawa da Mami ke ba shi in zai taho da coconut-cake mai yawa da ta ke sawa ayi mishi da kwalin Exotic ya zo ya kara musu a kan tray din, suka yi shiru dukkansu sai ci suke, da alama kowannen su tsohuwar yunwa ce a jikinsa.
Daddy na bai wa Khalipha labarin zuwansu (Braemar Village), da yadda komai ya wakana, a lokacin shi Khalipha yana Morocco. A nan ne Khalipha yake gayawa Daddy shima ya taba yin wannan tunanin, amma sai ya ga cewa tafiyarsu shi da ita ba za ta yiwu ba. Shi yasa ya bari a ransa sai sunyi aure.
Daddy murmushi ya yi yana tuno artabunshi da Mami a kan tafiyar, amma bai gayawa Khalipha ba kada mutuncin mahaifiyarsa ya zube a idonsa.
Shima ya dade yana mamakin wai Mami ce ta yi masa haka? Zargi a kan shirme? To dai ya yi mata uziri da matantaka. Ai mace ce ita ma. Tunaninsu ragagge ne. A wani fannin kuma yana cikin damuwar yadda za su karke da ita a karo na biyu idan ta ji bukatar Khalipha, sannan in ya tuna alkawarin da ya yi mata kafin ta yarda ta karbi yarinyar.
Amma ai ba ta fi karfin addu’a ba, Allah ya sanyaya zuciyarta don ya san ba ta iya fushi ba, shima bai iya ba. Musamman a kan Rayhanah.
Khalipha wanda ke cikin farin cikin da Daddy bai taba ganinsa cikin kwatankwacinsa ba ya katse tunanin shi da cewa,
“Daddy zan iya kiran Rayhanah a waya da amincewar ka? Daddy zan iya ba ta waya?”
A sanda ya fadi hakan kansa na sunkuye ne. Daddy sai ya mika masa hannu ya ce,
“Bani in kai mata. Amma da wajewar cewa za a bani salalar kaiwar, ka san ba a aikin banza a Kano”.
Dariya Khalipha ya yi, ya zaro wayarsa ya cire layin (MTN) wanda kowa ya san shi da shi ya sanya sabo na Etisalat ya mikawa Daddy.
Daddy ya karba ya zura a aljihun coat dinsa, ya sake mika masa hannu ya ce, “To bani salalar”.
Ba yadda Khalipha ya iya don tsananin farin cikin da yake ciki ya fi gaban biro ya rubuta, ya dauko credit card na layin da Daddy ke amfani da shi na naira dubu daya ya dauki wayar Daddy ya loda a ciki. Daddyn ya karba ya mike yana cewa, “To ai kaga haka ya fi, yanzu zan san na zama dan aiken soyayyah da hujjah”.
****
[12/24/2019, 21:47] Takori: Daddy na gudu a kan titi zuciyarsa kamar takarda don haske, Allah yana cika masa

Please Login or Register in order to submit comment