Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


Downloaded from GNOVELS.COM.NG




This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG
to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/gnovels

Twitter : https://twitter.com/gnovels

Telegram : https://t.me/gnovels

๏ปฟ[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ
'YA'YAN MIJI

Na Umm Asghar

Sadaukarwa gareki 'yaruwa rabin jiki Fatima (Uwani) Eshak, Allah ya jikanki ya kyautata kwanciyarki

1
Zaune take akan kujerar gaban madubi tana shafa man body shop. Bayan ta gama ta dauko humra da kulacca ta shafa a jikinta sannan ta dauki doguwar rigar baccinta mai santsi kalar purple ta saka. Hair spray din argan oil(ors) ta fesa a gashinta sannan ta daureshi a cikin ribbon ta kawo hula ta saka. Turaren sandra (al rehab collection) ta fesa, sannan ta daura zani akan kayan baccin ta saka hijabi, wayarta ta dauka ta fita daga dakin tana mai jawo kofar ta rufe.
A daidai corridor da zai sadata da dakin maigidan sukayi karo da Ummi wacce ta fito daga parlour mahaifinsu. Kallon sama da kasa tayi mata sannan ta doka tsaki tare da cewa "maciyiya amana har an fito za'a tafi dakin tsoho, a haka dai zaki kare cusa kai babu kwarjini kuma abinda kika zo donshi ba samu zakiyi ba don kuwa idan har muna nan ruwa ma sai ya gagare ki sha a gidannan. Kai ke kam kwata-kwata ma bakisan halacci ba, banda haka ace ki rasa miji aure sai Daddy, mijin Mami nefa? Idan kin manta na tuna miki". Bangazarta tayi sannan ta wuce ta barta a tsaye a wurin tamkar wacce aka dasa. Tafi minti biyar a tsaye bayan wucewar Ummi ba ta tafi ba. Dakyar dai ta janye kafafun data ji sun mata nauyi ta wuce zuwa dakin daddy. A hankali ta tura kofar tare dayin Sallama, a ciki ya amsa mata. Yana zaune a kan gado yana duba wasu takardu. "Sannu da hutawa daddy" tace mishi bayan ta ninke hijab da zanin data doro akan kayan baccinta don kuwa dokarshi ce idan harta shiga dakinshi baya son ganinta kunshe cikin hijabi. "Akwai abinda kake bukata kafin na kwanta", ta tambayeshi duk da kuwa bai amsa sannun data mishi ba. Kamar bazai amsata ba kuma can sai ya cemata "black tea nake so".
Zaninta ta mayar sannan ta saka hijabin ta fita. Kitchen ta nufa ta dora ruwan tea data saka lipton guda biyu da kayan kamshi wajen dahuwar sai teaspoon daya na strawberry flavour data zuba. Bayan ya tafasa ta juye a cikin flask ta dora akan tray hade da kofi da cokali da zuma don daddy baya shan sugar sai dai yayi amfani da zuma ta dauka ta nufi daki.
A zaune a inda ta barshi anan ta sameshi, akan bedsida drawer ta ajiye tray din sannan ta wuce bandaki ta hada mishi ruwan wanka. Bayan ta fito ne ta sanar mishi sannan ta hau kan gadon ta kwanta. Bata san lokacin daya tashi ba don kuwa har ta fara bacci tajishi yana mata abubuwa, dole ta wartsake daga baccin ta kula dashi.

UMM ASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

'YA'YAN MIJI

Na Umm Asghar

2
Tana yin sallar asuba ta wuce kitchen don kuwa al'adar maigidan ne iyalinshi basa cin abincin masu aiki. Kasancewar tun dare tayi shirin yin waina da sinasir ne yasa tana shiga ta fara haramar suya tare da hada miyar taushen data wadatu da tantakwashi da busashen kifi. Kafin karfe takwas tayi har ta gama shirya abincin a cikin warmers ta dora a dining table sannan ta wuce dakinta tayi wanka ta shirya cikin atamfar jullius holland kalar blue da yellow wadda akayiwa dinkin skirt da riga free fitted. Kasancewar kwalliya ba damunta tayi ba powder kawai ta shafa sai lipbalm data shafa a lebenta ta daura dankwalin atamfar ta nufi dakin Daddy. A gaban madubi ta iskeshi yana makala rank a jikinshi kasancewarshi soja mai mukamin major general.
Tsugunawa tayi ta gaisheshi. A ciki ya amsa kamar dai yanda ya saba amsa duk wata magana tata. Ita dai kam har yanzu ta kasa sabawa da Daddy a matsayin mijinta, tsoronshi data kaji tun fil'azal bai taba barinta ba kuma shima he's not helping matters don kuwa yanda yake treating dinta ada haka yakeyi a yanzu bambancin kawai yanzu ita matarshi ce akwai hakkukuwanshi dake kanta kuma take saukewa da ada babu. Tayi nisa cikin tunaninta har bata san ya fita daga dakin ba sai jin karar rufe kofa tayi. Da sauri ta tashi ta bishi don ta bashi abinci.
Akan table ta iskeshi tare da sauran yaran gidan. "Ina kwananku" tace musu tare da janyo kujera ta zauna. Tana gaidasu ne don tasan cikinsu babu maiyi mata magana idan har ba ita tayi musu ba. Yanzun ma Yaya Khalifa ne kawai ya amsa gaisuwar tata. Plate ta dauka ta sakawa Daddy waina da sinasir din ta zuba miyar a cikin soup bowl sannan ta zuba mishi kunun gyada a cikin cup ta tura gabanshi sannan ta debi nata ta fara ci.
Sunyi nisa a cin abincin ne sannan ta lura Mu'azzam ko taba abincin baiyi ba. Lura Daddy yayi da baya cin abincin ne yasa ya tambayeshi dalilin rashin cin abincin nashi. Budar bakin Mu'azzam sai cewa yayi "Fisabilillahi Daddy ya za'ayi da sassafe mutum yaci wani sinasir as breakfast idan dai baso akeyi cikinshi ya cushe ba, amma na lura matarnan abinda taga dama takeyi a gidannan". Wai maimakon Daddy ya tsawatar mishi akan rashin cin abincin tunda ba'a ranar aka fara yin waina da sinasir a matsayin abin kari ba hasali ma timetable ne dasu na duk abincin da za'a a rana tun daga safe har zuwa dare kuma tun lokacin Mami haka akeyi koda tazo gidan babu abinda ta canja, a'a sai ce mata yayi "meyasa kika dafa abinda kinsan ba kowa keso ba, daga yanzu idan zakiyi girki lallai ne ki tambayi abinda sukeso kafin kibgirka don kada ayi abinda wani bayaso, yanzu ki tashi ki dafa mishi wani abin don bazai yiwu ya tafi school bai karya ba".
Ba karamin kada maganar Daddy tayi ba sai dai ba yadda ta iya bayaga tayi abinda ya sakata. Kallon Mu'azzam tayi wanda fuskarshi ke kunshe da murmushin nasara tace mishi "me kakeso na dafa maka"? A yatsine ya amsata da cewa indomie da kwai. Kitchen ta wuce ta dora mishi indomie din. Lokacin data gama ta kawo babu kowa a parlour sai shi kadai. Wato Daddy ya fita kenan ba tare da ya mata sallama ba. Ajiye mishi tayi akan table ta juya, har takai stairs zata hau sama sai jivtayi yace mata "bakiji ba", juyiwa tayi tana kallonshi tare da sauraron abinda zaice. Murmushi yayi tare da cewa "kadan ma kika gani".
Juyawa kawai tayi taci gaba da hawa stairs din. Dakin Daddy ta wuce ta hau gyarawa tun daga cikin dakin har bathroom da sittingroom din.

UMMASGHAR
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

'YA'YAN MIJI

Na Umm Asghar

3
A yammacin wata asabar ne tana zaune a sitting room tana kallon movie a tashar mbc2. Farida da Ummie ne suka shigo suka zauna. Remote Farida ta dauka tare da canja channel zuwa musicplus. Dagowa tayi ta kalletaganin yadda sukazo suka iske ta tana kallo suka canja mata salon tayi magana suyi mata rashin kunya. "Fadi karta kasheki" shine abinda Farida tace mata. Dauke kai tayi tamkar bata san cewa da ita takeyi ba.
A guje Ruqaiya da Zainab suka shigo suna rige-rigen hawa kanta suka ce "Aunty Aisha mun dawo" da fara'arta ta dagosu tare da cewa "to sannunku da dawowa, sai aje a cire uniform ayi haramar yin sallah magriba ko". A tare suka ce to suna masu wucewa don su canja kayan islamiyyarsu zuwa na gida. "Kai kuzo nan" Farida tace musu "ban hanaku kula wannan matar ba amma shine dayake kunnuwanku na kashi ne ku bakwa ji kullum sai kunje inda take ko, kuna kallonmu amma ko sannu baku ce mana ba kun tafi wurin kanwar uwarku, to wallahi bari kuji na gaya muku daga yauidan na kara gani ko kallonta kunyi sai nayi muku shegen duka, ku wuce ku bani wuri".
Sum-sum suka wuce zuwa dakinsu. Su kam har kullum suna mamakin yadda yayyensu ke yiwa Aunty Aisha tamkar dai ba 'yaruwarsu bace. Ita kam Aisha suna fara yiwa yaran fada ta haya sama ta bar musu parlour. Dakinta ta nufa don yin sallar magriba don kuwa har an fara kiran sallah.
Koda ta idar da sallah bata tashi a wurin ba sai taci gaba da wuridi har aka kira sallar isha ta tashi tayi sannan ta sauka kasa don tayi serving dinner. Akan table ta iskesu sun fara cin abincin kasancewar Daddy baya nan yasa suka fara cin abincin ba tare da sun jirata ba. Tana bude warmers din taga wayam babu komai a ciki, takaici ne ya kamata ganin yadda suka cinye abincin ba tare da sun rage mata ba. Juyawa kawai tayi ta koma daki don bakin ciki bazai barta ta shiga kitchen don neman abinda zata ci ba.
Khalifa ne ya kalli kannenshi dake haramar barin table din yace "ina kuke tunanin tashi kuje ba tare da kun cinye abincinku ba, wannan din wa kuka barwa shi". Turo baki Farida tayi tace "to Yaya Khalifa mun fa koshi ne". Harara ya doka mata sannan yace "come on dawo ku zauna ku cinye, kunsan bazaku ciba kuka kwashe abincin gaba daya ita mai daguwar baku rage mata ba. Idan ma kunyi ne don kuyi mata mugunta to kanku kuka yiwa don kuwa sai kun cinye abincinnan tas ina kallonku".
Haka suka zauna suka tuttura abincin da kyar yana kallonsu har sai da suka cinye tukunna ya tashi ya bar wurin. Tuntsirewa Mu'azzam yayi da dariya har yana rike ciki ganin yadda suke ymutsa fuska kamar masu shirin yin amai. Tsaki Ummie tayi tace "to miye abin dariyar kuma". Wata dariyar ya karayi sannan yace "ai kune kuka sakani dariyar, ai idan kuna son yiwa matarnan tsiya bari zakuyisai Daddy na nan yanda duk abinda zakuyi ba maice muku uffan, amma Yaya Khalifa kam ai kinsan he always has a soft spot for her. Aurenta da Daddy ne ma yasa yaja baya da ita". "Wannan kuma shi ya jiyo, amma mudai ba'a isa a hanamu takurawa yarinya ba tunda dai ta yarda ta auri ubanmu" cewar Farida. Mu'azzam yace "lallai ma Farida bakida kunya, Aishan kike cewa yarinya agemate dina cefa don nasha jin Mami na cewa watanni 2 na bata".
Taking tayi tare da cewa "to shine me don sa'arka ce ko sa'ar Yaya Khalifa ce ai na kirata yarinya tunda kuwa dai a haife Daddy ya haifeta sannan kuma girman da tayi mana bai wuce na shekaru uku zuwa hudu ba. Ni ai tunda ta yarda ta auri Daddy naji na tsaneta ni inaga dama can tana sonshi ta rasa yadda zatayi ne sai kuma ta samu Hajiya ta bullo da maganar aure a tsakaninsu, bakuga ko musu batayi ba ta amince ita a dole ga mai biyayya".

TUSHEN LABARIN.



UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

'YA'YAN MIJI

Na Umm Asghar


4

TUSHEN LABARIN

Ja'afar Bello Danmaliki haifaffen garin kano ne a cikin unguwar gadon kaya sai dai iyayensu asalinsu mutanen karamar hukumar gaya ne. Su biyu iyayensu suka haifa shi da kaninshi Ismail. Daga Ismail mahaifiyarsu da suke kira da Hajiya bata kara haihuwa ba hakanan kuma mahaifinsu bai yi sha'awar kara aure ba ko don ganin ya samu wasu 'ya'yan.
Ja'afar yayi karatu tun daga primary anan kano har ya gama secondary, daga nan ya wuce Nigerian defence academy wato nda a kaduna inda ya karanci engineering a bangaren army ya fito da mukamin 2nd lieutenant. A shekarar daya fito daga nda ne ya auri dadaddiyar budurwarshi tun ta yarinta wato Zainab wacce ta kasance 'yar makotansu.
Watannin aurensu goma Zainab ta haifi danta na farko Muhammad Bello mai sunan mahaifin Ja'afar suna ce mishi Khalifa. Khalifa nada shekaru uku ta haifi Ibrahim Mu'azzam. Bayan Mu'azzam ne ta haifi Khadija (Ummie) mai sunan mahaifiyarta. Tsakanin Mu'azzam da Ummie ma shekaru uku ne. A shekarar da Zainab ta haifi Ummie ne Ismail kanin Ja'afar yayi aure a cikin kuma shekarar ne dai Allah yayi mishi rasuwa a dalilin hatsarin mota, ya rasu ya bar matar shi da cikin wata shida.
Mutuwar Ismail ta kada Ja'afar sosai don kuwa akwai shakuwa sosai a tsakaninsu. Bayan watanni uku da rasuwar Ismail matarshi ta haifi diya mace akasa mata suna Farida. A lokacin da Farida ta isa shiga makaranta nevya karbota ya kawowa Zainab sannan ya sakata a makaranta tare da Ummie. Farida da Ummie sun taso tamkar 'yan biyu kasancewar duk sunyi kama da iyayensu maza ne don sau tari mutanebna dauka 'yan biyu ne.
Tun bayan Ummie Zainab bata kara haihuwa ba sai da aka shekara goma don har ta fara cire rai da haihuwa sai kuma Allah ya kawo. A ranar wata litinin ne da safe tana zaune tana shayar da jaririyar data haifa Ruqaiya Hajiya wato surukarta tayi sallama a tare da wata yarinya da bazata wuce shekaru goma sha biyu zuwa sha uku ba.
Mikewa tayi tsaye tana cewa "Hajiya sannu da zuwa" "yauwa sannu Zainabu sai ke kadai ko yaran duk sun tafi makaranta" tace bayan ta zauna akan kujera. Zaman itama Zainab din tayi tana cewa "wallahi kuwa Hajiya kinji yanda gidan yayi shiru sai sun dawo kuma, barka da asuba Hajiya an tashi lafiya" tace tana mai rusunawa. "Lafiya lau ya kwanan yaran" "lafiyarsu lau Alhamdulillah". "To Masha Allah dama yarinyace na kawo miki, ina take ne ma kame Aisha" tace tana waigawa. Tasowa yarinyar tayi daga inda take a bayan kujera tazo ta tsugunna tacr "Hajiya gani". Gyara zamanta tayi sannan tace "kinaji ba Zainabu yarinya ce 'yar kanwata a kauye uwar ta rasu shine na dauko ta ganin ita kadai uwar ta bari to shine naga gara na kawota nan wurinku tunda dai akwai yara sai ki hadasu ki rike ko 'yan aikace-aikace ta taya ki, amma don Allah Zainab ki rike mini ita amana tamkar 'yarki tunda dai da na kowa ne ladanki na wurin Allah bare ma rikon maraya Allah ne kadai zai biyaki".
Dagowa tayi ta kalli yarinyar. Ba laifi kam yarinyar tsaf take babu wani alamu na kazanta ko kauyanci a tare da ita. Tace "to Hajiya nagode Allah ya kara girma, Allah kuma ya tayani riko yaya sunanta". "Aisha sunanta, abokan wasa muke da uwar ta jima bata haihu ba saida girma ya fara kamata sannan Allah ya bata Aisha daga ita kuma bata kara haihuwa ba". Ta juya ta kalli Aisha tace "kina jina Aisha ga Zainabu nan a wurinta zaki zauna ki dauketa tamkar mahaifiyarki kiyi mata biyayya, da nan gidan da can wurina duk daya ne don haka kar ki sanu wata damuwa kinji, Allah yayi miki albarka"
"Bari na tafi Zainabu idan yaran sun dawo ace ina gaishesu" tace tana mikewa. Har wurin mita suka rakata sannan suka dawo ciki. "Zo nan kusa dani ki zauna" Zainab tace mata. Tasowa tayi ta zauna a darare akan kujera inda ta nuna mata. Dafata tayi tare da cewa "ki saki jikinki dani kinji Aisha, ki daukeni tamkar mahaifiyarki duka abinda kikeso ki gaya mini In Sha Allahu zanyi miki shi idan har baifi karfina ba, kuma daga yau Mami zaki na ce mini kamar yadda 'yanuwanki suke kirana, basanan suna makaranta yanzu amma idan sun dawo zaki gansu".
A hankali ta gyada kai tace "nagida Mami In Sha Allahu zaki sameni mai bin abin da kika ce". Mami tace "to haka ake so yanzu tashi muje na nuna miki dakinku". Tashi tayi ta dauki ledar kayanta tabi bayan Mami suka hau sama zuwa dakinsu Ummie. Daki ne babba yana dauke da gado 6by6 sai wardrobe din jikin bango da madubi. A wardrobe din Mami tace ta ajiye kayanta sannan ta nuna mata bandaki ko tana da bukatar shiga ta juya ta fita.

UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

'YA'YAN MIJI

Na Umm Asghar

5
Ko da su Ummie suka dawo daga school sun iske Aisha ne a dakinsu. Farida ta rike kugu tare da kare mata kallo kafin tace "ke! Wacece ke kuma me kikeyi a dakinmu?" Farida kam akwai tsiwa ba kamar Ummie ba data kasance mai hakuri don sau tari idan Farida nayiwa Ummie tsiwa sai ka dauka itace babba. Aisha tayi murmushi sannan tace "sunana Aisha kuma yanzu a gidanku zan zauna so na zama 'yar gidanku kenan", cikin farinciki Ummie tace "kenan anan dakin zamu zauna dake, kai amma naji dadi wallahi, ko Farida?" "uhm" Farida tace tana yatsina fuska. Uniform ta cire ta zubar dasu a tsakiyar dakin sannan ta debi kaya ta saka ta fice daga dakin tana kwala kiran "Mami mun dawo". Ita kam Ummie ta saka Aisha a gaba tana ta mata tambayoyi, ita dai Aisha murmushi takeyi kasancewarta ba mai yawan magana ba. Shigowar Mami dakin ne yasa suka dago suka kalleta. "Ku taso kuci abinci ke Ummie kin saka Aisha a gaba da surutu ko, wai ko uniform din ma baki cire ba" tace bayan ta karaso cikin dakin sosai. Tashi Ummie tayi tana cewa "yanzu zan cire Mami". Tace "to maza ki cire ku fito kuci abinci don ku kadai ake jira" ta juya ta bar dakin.
Bayan Ummie ta canja kayan makarantarta dana gida ne suka sauka kasa don cin abincin. Ummie taja kujera ta zauna sannan tace Aisha tazo ta zaunaa kujerar kusa da ita. Tsaki Farida tayi don hakanan taji bakuwar da aka kira da Aisha bata kwanta mata ba. Ita kam Aisha duk a takure take jinta don bata saba cin abinci a table kuma a cikin mutane haka ba. Mu'azzam ne ya dago yana cewa "Mami wacece wannan kuma da zata zo ta zauna mana anan bata san nan duka family bane, me ya kawo bare cikinmu"
Cikin kakkausar murya Mami tace "Mu'azzam yi mini shiru anan, Aisha ba bare bace itama 'yar gida ce don haka kar na kara jin makamanciyar magana irin wannan a bakinka, kai gaba dayanku ma hope you understand?", gaba daya suka ce "eh Mami". Bayan gama cin abincinsu ne suka koma daki, suna shiga Aisha ta hau tattare kayan Farid data zubar a kasa. "Ina za'a saka wadannan" tace wa Ummie, "kai mata toilet ki saka a cikin kwandon kayan wanki" ta amsata.
Da daddare ne Mami suna zaune da Daddy a sittingroom dinshi na sama take ce mishi "dazu Hajiya tazo har ta kawo mini yarinyar da zata na tayani aiki tace 'yar wata kanwartace data rasu shine ta dauko yarinyar, to ina tunanin a sakata a school maimakon zamanta a haka ko ya ka gani". Shiru yayai bai amsata ba, ita kam wannan hali na J.B sau tari yana bata mata rai don idan baiso ba duk maganar da zatayi ba amsawa yakeyi ba shine ma ya saka idan ta mishi magana taga bai amsata ba bata maimaitawa sai ta kyaleshi, don kanshi kuma idan yaso saibya dauko maganar.
Yanzun ma ganin bazai amsata bane yasa ta mike don taje tayi shirin barci. Har ta kai wurin kofa taji yana cewa "duk yanda kikayi daidai ne". Murmushi kawai tayi sannan tace "nagode bari naje nayi shirin kwanciya don barci nakeji, akwai abinda kake bukata?" Cikin ginshira yace "yeah, only you". Wata kasalalliyar dariya tayi sannan tace "hmm Daddy kenan" ta juya ta bar parlour cikin rangwada. Hannu yasa ya shafa kwantacciyar sumarshi yana mai lumshe ido, murmushi dauke a fuskarshi. Shi kam Allah ya sani yana son Zainab sosai, after all these years yana jinta a ranshi tamkar yau ya fara sonta. Tashi yayi shima ya nufi dakin din yayi shirin kwanciya.


UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ
'YA'YAN MIJI

Na Umm Asghar

7
A haka dai rayuwa taci gaba da tafiya. Ga Aisha dai ta dada kame kanta daga shiga harkar Farida da Mu'azzam don ta lura akansu zaman gidan zai iya gagararta. Ita kuwa a yanda takejin dadin zama da Mami ga kuma ingantaccen ilimi duka biyu wato na addini da boko da take samu baza taso tayi abinda zai rabata da zaman gaidannan ba.
Ga kuma baby Ruqaiya da sukayi wata irin shakuwa da ita don mafi yawan lokuta idan tana wurin Aisha ko Mami bata yarda ta dauketa sai da kyar. To shima Daddy a nashi bangaren bai kara maganar mayar da ita gidan Hajiya ba, kodayake a yanzu duk fitinar Farida da neman rigimarta ta kyale Aisha ganin bata shiga harkarta.
A yanzu haka Aisha tana ss1 ne yayin dasu Ummie suke jss3. Tun zuwan Aisha gidan sau daya taje garinsu tayi hutu na sati uku. A wannan lokacin ma hutun take son zuwa sai dai kuma kasancewar ciki ne da Mami tsohi yasa dole ta hakura. Ko babu komai tana taimakawa Mami da hidimar gidan don zuwa wannan lokacin babu wani abu da bata iya ba a kitchen.
Mafi yawan lokuta zaka sameta ne a kitchen tare da Mami da sauran ma'aikatan gidan, abinda bazaki taba ganin Ummie ko Farida sunyi ba. Yanzu ma aikin abincin dare sukeyi ita da Mami a kitchen. Yaya Khalifa ne ya shigo kitchen din yace "sannu Mami, mezan samu wallahi na gaji da yawa ga yunwa na kwaso, yau tunda muka fara lectures tun 12 sai six muka gama without any interval".
"Sannu Yay Khalifa ai kana kokari wallahi Allah dai ya bada sa'a". "Amin Aisha nagode, me kukayi ne da rana? Yace bayan ya zauna akan kujerar kitchen din. "Favourite dinka ne wato faten doya bari na zuba maka" tace bayan ta dauki plate ta zuba mishi abincin sannan tace mishi "anan zakaci ne ko na kai maka parlour". "Bari kawai na wuce dashi Aisha nagode" yace yana mai tashi daga kan kujerar. Karbar abincin yayi ya fita a kitchen din. Bayan sun gama hada abincin ne Mami ta fita ta barta a kitchen din ta karasa gyarawa. Sosai take tausayawa Mami ganin duk da tsufan cikinta hakan bai hanata yin hidimar gidanta ba.
A daren ranar suna kwance suna bacci Mami ta shigo dakinsu ta tashi Aisha. "Lafiya Mami?" tace bayan ta tashi zaune. "Saka hijabinki ki taso asibiti zamuje" tace mata a yayin da take barin dakin. A hanzarce ta tashi ta daura zani akan kayan baccinta ta dora hijabi ta fita zuwa dakina Mami. Akwatin da Mami ta hada don zuwa asibiti ta dauka suka fita. Koda suka fita harabar gidan tuni Daddy ya juyo da mota, gidan gaba ta budewa Mami ta shiga sannan ta koma baya ta zauna.
A lokacin da suka isa asibitin karfe daya da rabi ne na dare. Suna zuwa direct labour room aka wuce da Mami, su kuma suka samu wuri anan rwception din suka zauna. Nesa sosai da Daddy Aisha ta zauna, duk sai tana jinta a takure don ita dai hakanan take jin tsoron Daddy bata taba sakewa dashi ba shima kuma bai taba sakar mata fuska ba tsakaninta dashi gaisuwa ce kawai.
Basuyi zaman awa daya ba a wurin nurse ta fito ta fada musu Mami ta haihu diya mace. Gaba daya annurin farinciki ne ya sauka a fuskar Daddy, mamaki ne ya kama Aisha don kuwa bata taba ganin fara'arshi haka ba. Ba'a wani jima sosai ba aka fito da Mami da babynta zuwa wani dakin. Bin bayansu sukayi zuwa dakin da aka kwantar da ita. Daddy

Please Login or Register in order to submit comment