Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

na rike da baby sai faman fara'a yakeyi yana ce mata "sannu Zainab", ya dade a asibitin kafin yayi sallama da Mami ya tafi gida don a lokacin kausan karfe uku da rabi ne na dare. Daga Mami har Aisha basu wani samu yin barci ba saboda baby bata barsu ba. Sauki daya suka samu ma shine da safe da likita yazo ya dubasu ya basu sallama. Anyi sallamar babu dadewa Daddy ya shigo dakin hannunshi rike da kwandon kayan abinci. Da sauri Aisha ta tashi ta karbi kwandon a hannunshi sannanta gaisheshi. Yana amsawa ya karasa kan gadon ya zauna yana yiwa Mami sannu tare da amsar baby a hannunta. Breakfast kawai sukayi suka koma gida kasancewar anyi discharging dinsu tun kafin zuwan Daddy. Da isarsu gida yaran gaba daya suka fito suna ihun Murna. Rige-rigen karbar baby sukeyi, Mu'azzam ne ya karbi babyn a hannun Aisha ita kuma ta fito da kayansu suka shiga cikin gidan. Cikin kankanin lokaci gidan ya cika da baki 'yan barka don haka nema hutun da Aisha take bukata bata sameshi ba saboda hidima da tayi mata yawa.


UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

'YA'YAN MIJI

Na Umm Asghar

6
Washegari suna kan table suna breakfast Daddy ya sauko daga sama a bayanshi Mami ce rike da briefcase dinshi. Kujera taja mishi ya zauna sannan taja kujerar dake gefen damanshi ta zauna. Yaran duka suka gaisheshi ya amsasu cikin kulawa. Itama Aisha gaisheshi tayi tana mai tsugunawa. "Lafiya" kawai yace ya cigaba da magana da yaranshi. Gaba daya sai taji ta muzanta, anya kuwa maigidan yana maraba da zamanta cikin iyalinshi. Duk sai taji abincin ma ya fita daga ranta. A haka dai ta daure ta tuttura. Bayan kowa ya gama ne suka tashi suka fita, yaran suka tafi school shi kuma Daddy ya tafi office. Ya rage daga Aisha sai Mami sai ko baby Ruqaiya. "Mami kawota" Aisha tace tana mai mikawa hannu don karbar Ruqaiya. A baya ta sakata ta goya sannan ta haya sama ta nufi dakinsu ta hau gyarawa. Kayan Farida ne duk a barbaje a tsakar dakin ga alama dai Farida bata san ta cire kaya ta adanasu ba. Daga zuwanta jiya zuwa yau ta lura Farida sakaltacciyar yarinya ce saki yayi mata yawa.
Bayan ta gama gyaran dakinsu ne ta shiga dakin Mami don ta gyara. Nan kam a gyare yake tsaf don haka juyawa kawai tayi ta sauka kasa. A parlour ta iske Mami tana kallon the doctors a mbc4. "Sannu Mami" tace a yayin da take zama a kasa. "Yauwa sannu Aisha, me yasa kike son zama a kasa ne, tashi ki koma kan kujera", tashi tayi ta zauna akan kujerar. Mami tace mata "su Ummie sun tafi makaranta sun barki ko, kema inaso ki fara zuwa ina fata daikin fara karatu acan garinku". Tace "eh Mami na fara ina jss2 yanzu haka". Mami tace "Masha Allah, akwai wata makaranta a kasan layinnan zanje na duba In Sha Allahu zuwa wani satin zaki fara zuwa". Durkusawa tayi tace "nagode Mami Allah ya saka da alkhairi".
Dariya Mami tayi tace "tashi da Allah daga durkuson nan, baki daukeni uwa har yanzu ko, miye abin godiyar to ai dolenmu ne muyi miki hidima tunda dai ke amana ce a hannunmu. Jeki kwantar da Ruqaiya sai kizo mu shiga kitchen ki tayani girki ko".
A cikin satin aka gama yiwa Aisha komai na makaranta anan wata private school dake cikin unguwar sun dauketa a jss2 din da take kasancewar sun gwadata sunga tana da kokari sai dai rashin samun ingantaccen ilimi yasa turancinta yake da rauni, ganin haka nema yasa Mami ta shirya da malamarsu ta english zatana yi mata lesson akan turancin. Duk da makaranta da Aisha ta fara zuwa, wannan baisa ta daina yiwa Mami hidimar da takeyi mata ba kamar gyaran dakinta da nasu dakin da kuma wankin kayan Ruqaiya. Hakanan kuma rainon Ruqaiya na cikin aikinta idan ta dawo daga makaranta.
Sosai Mami take jin dadin zama da Aisha don kuwa yarinyar bata da kyuiya duk abinda ta sakata shi takeyi. Itama kuma Aisha tana jin dadin zamanta da Mami don kuwa Mami mutum ce mai alkhairi da kuma son mutane, gashi kuma a komai bata yin bambanci tsakaninta dasu Ummie da suke 'ya'yanta komai tayi musu itama shi takeyi mata. Ko tana da matsala a zamanta a gidan to da Farida nel data takura mata ta hanata sakat don ko wasa sukeyi da Ummie idan tazo wurin to ta barshi. Sai ko Mu'azzam shima yana takura mata amma ba kamar Farida ba, shi kam Yaya Khalifa babu ruwanshi don baya na shiga harkarsu.
A yammacin wata lahadi ne bayan malamin dake yi musu karatun islamiyya ya tafi ne suka nufi filin wasansu. Kowa da kalar wasan da yake yi, Ummie da Aisha dai lilo suka hau Ummie tana tura Aisha. Farida da Mu'azzam kuma wasan guje-guje sukeyi. Abin tsautsayi Ummie tana shilla Aisha ne ita kuma Farida ta taho a guje Mu'azzam na binta kawai tayi karo da kafar Aisha ta hantsila ta fasa hanci.
Wata irin razananniyar kara ta saka. A guje duk sukayi wurinta suna mata sannu ganin yadda jini yake fita daga hancinta duk sai suka rude. Gaba daya suka nufi cikin gidan in banda ihu babu abinda Farida takeyi. A rude Mami ta taso tana tambayarsu lafiya. Mu'azzam ne yace yana mai nuna Aisha "gatanan itace ta hankadata ta fadi ta fasa hanci". Cikin daga murya Ummie tace "laa bafa haka akayi ba, Mami ina tura Aisha ne a lilo su kuma suna wasan guje-guje sukayi karo da Aisha ta fadi ta fasa hanci", "ke yi mini shiru da bakya magana a hankali" tace da Ummie. "kai kuma matsa ka bani wuri naje na wanke mata ciwon, ai duk laifinkane don kuwa na hanaku wasan guje-guje amma bakwa ji".
Mami taja Farida zuwa bathroom ta wanke mata jinin daya bata mata fuskar sannan ta bata paracetamol tace ta kwanta ta huta. A ranar kam da Daddy ya dawo ya tarar da abinda ya faru yayi fada kamar me har yana cewa Mami shifa idan rikon bazai yiwu ba sai a maida Aisha gidan Hajiya din bazai lamunci ganganci akan yaranshi ba. Shi Daddy wani irin mutum ne mai son yaranshi hakanan baya son wani ya rabeshi, ko rikon Aishacma abinda yasa baiyi magana ba saboda Hajiyarahi ce ta kawota gidan amma da babu abinda zai sa ya karbeta. Ita dai Mami hakuri kawai take bashi don kuwa tana matukar jin dadin zama da yarinyar.


UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ
'YA'YAN MIJI

Na Umm Asghar

8
Tun bayan da Mami ta haihu gidansu bai rabu da jama'a ba. Don Aisha ma ko makaranta bata samun zuwa saboda hidima da tayi mata yawa. Ga aikin jego ga kuma hidimar Ruqaiya da kacokam ta dawo hannunta.
A ranar da akayi kwana biyar ne da haihuwar da safe Aisha na zaune a dakin Mami tana shirya kayan baby data wanke Mami ta shigo cikin dakin dauke da baby. Kwantar da ita tayi akan gado sannan tace da Aisha "idan kin gama shirya kayan kawo mini kunu sai kizo ki janyo mini wancan akwatin". Bayan ta gama shirya kayan ne taje kitchen ta damowa Mami kunun gyada sannan ta kawo mata. Akwatin data ce ta janyo mata tare da budewa ta fito da kayan ciki. Laces ne guda uku sai atamfar super holland guda hudu da voiles guda uku. Mami tace "miko mini na gani" tashi tayi ta mika mata kayan. Dagawa Mami tayi ta kalla sannan tace "wai nan kayan fitar suna ne Daddy ya mini sai kace wata yarinya, nikam ai na gaya mishi babu wani taron suna da zanyi".
Aisha ta kara daga kayan ta kalla sannan tace "ai kuwa dai Mami kayan sunyi kyau, Allah ya sakawa Daddy da alkhairi, amma Mami meyasa bazakiyi taron suna ba". Dariya Mami tayi tace "kayya Aisha taron suna ai na yara ne, haihuwa ta biyar ni kuwa wani suna zanyi, don wani abu irin na Daddy ma wai baby sunana ya saka mata nayi-nayi dashi ya saka sunan Hajiya yace a'a".
Cikin fara'a sosai Aisha tace "Allah ya rayata, kuma Mami me za'ace mata?" "Zainab dinta zaku kirata don banason boye sunannan" a cewar Mami. "Ina Ruqaiya ne duk yau ban ganta ba" Mami ta tambayeta. "Tana wurin Lami tun bayan dana mata wanka ta dauketa ta goyata to inaga bacci takeyi tunda kikaga shiru bata kawo taba". Aisha ta amsa mata.
A ranar suna ne baby taci sunan Mami wato Zainab. Kasancewar Mami ba taro takeyi yasa gidan bai cika da mutane ba amma duk da haka 'yanuwa na jiki duk sunzo don haka aiki yayi wa Aisha da sauran ma'aikatan yawa don sai faman dora abinci sukeyi suna saukewa. Ita dai Aisha har ta matsu dare yayi ko ta samu ta kwanta ta huta.
Bayan suna ne da kwana biyu suna zaune a parlour gaba gayansu yaran gidan suna hira Mami kece mata idan anyi hutu sai ta shirya taje garinsu ta kwana biyu. Sosai taji dadi sai dai kuma tana tunanin udan har ta tafi yadda hidima zatayiwa Mami yawa, bata dai yi magana ba don kuwa tana kewar Babanta zataso taje ta ganshi.
Murmushi tayi sannan tace "to Mami nagode Allah ya kara girma". Kallonta Ummie tayi sannan tace "umh Aunty Aisha sai murna kikeyi zaki tafi ki barmu ko tausayinmu bakya ji bayan kinsan zamuyi missing dinki sosai". Tsaki Farida tayi hade da tabe baki tace "kedai zakiyi missing dinta nikam da zamanta da rashinshi duk daya ne a wurina don rayuwata nakeyi tamkar babu ita a cikin gidannan".
Murmushi kawai Aisha tayi ta dauke kai. Ita dai ta rasa abinda ta tsarewa Farida a cikin gidannan don ko magana idan har ba ita tayi mata ba batayi mata shima kuma ba lallai ne ta amsa ba. Wannan kuma baisa ta daina yi mata magana ba koda kuwa kullum ta mata bazata amsa ba.
Tun bayan da Mami tayi mata maganar zuwa gida ta fara shiri don ta fitar dakayanta da yawa da zata bayar a garinsu wa 'yanuwanta haka ma kuma Mami ta hada mata kayan bayarwa nabyara da yawa da zata rabar acan. A daren da zata tafi ne tana zaune a tsakar dakinsu tana shirya kayanta a cikin akwati Mami ta shigo hannunta rike da bakar kedar viva. Zama tayi a bakin gadon sannan ta mika mata ledar , jarba tayi tana kallon Mami da alamar tambaya a fuskarta. " Na Babanki ne da kuma goggonki wato matar Babanki ga kuma wannan ki kaiwa babanki inji Daddy sai kije kiyi mishi godiya" ta mika mata envelope.
Russunawa tayi hadi da karbar envelope din tace "nagode Mami Allah ya saka da alkhairi ya kara budi". Bayan data gama hada kayan ne ta nufi parlour Daddy don tayi mishi godiyar alkhairin daya yiwa mahaifinta. Daga bakin kofa ta tsaya tayi sallama, sai bayan an amsa ne tare da bata izinin shiga sannan ta shiga. Durkusawa tayi ta gaisheshi sannan ta mishi godiya ta tashi ta fita. Ruqaiya dake wasa a parlour ta taso ta biyota tana rigimar sai ta goyata. A daren ranar dai baccin Aisha rabi da rabi ne don dokin zataje taga Babanta.


UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ
'YA'YAN MIJI

Na Umm Asghar

9
Tun bayan da Aisha tayi sallar asuba sai bata koma bacci ba sai ta shiga wanka ta fito ta shirya cikin atamfar mediym holland dinkin riga da zanu. Koda ta shirya sai ta hau gyaran gidan inda duk tasan ita ke gyarawa. Bayan ta gama ne ta shiga dakin Mami. Bata sameta a dakin ba don haka sai ta shiga gyaran dakin. Tana cikin yin shara ne Mami ta fito daga bandakin ga dukkan alamu wanka tayi.
"A'a Aisha har kin shirya" tace a lokacin da take zama a kan stool din dressing mirror. "Eh Mami, ina kwana" "lafiya lau, kin ma kuwa yi bacci irin wannan sakko haka" dariya tayi tace "nayi bacci Mami kawai dai tunda nayi sallah ban koma ba. Me za'ayi as breakfast naga kwana biyu ba'a bin timetable"? Mami tace ai kuwa dai, sabon timetable nakeso nayi har yanzu kuma ban samu lokaci na zauna ba. Ki bare doya a dafa sai ayi doya mai kwai hade da farfesun kayan cikin da mukayi jiya yana cikin fridge warming kawai za'ayi sai tea. Kije ki fara kafin na gama shiryawa na fito kitchen din".
Tattara sharar tayi sannan ta nufi kitchen don tayi aikin da Mami ta sakata. Sai dai ta kusa gama hada breakfast din sannan Mami ta shigo ta tayata suka karasa. Karfe goma batayi ba su Aisha suka dauki hanya ita da Mallam Adamu driver. Sosai Ruqaiya tayi kuka ganin Aisha zata fita babu ita. Ita kanta Aisha sai da ta zubar da hawaye ganin yadda Ruqaiya ke kuka.
Sun isa garinsu wurin karfe sha daya. Basu sami Babanta a gida ba har ya fita kasuwa sai Goggo kawai suka samu da 'yan jikokinta suna wasa. Karba sosai akayi mata. Ruwa kawai Mallam Adamu yasha ya juya ya bar Aisha sai bayan sati biyu zai dawo ya dauketa. Bayan taci abinci ta huta ne ta fita gidajen makwabta fon ta gaishesu. Duk gidan data shiga suna mamakin girmanta da wayewar da tayi. Ba ita ta koma gida ba sai goshin magriba, koda ta koma gida Babanta ya dawo. Sosai yaji dadin ganinta. Sai bayan anyi isha'i ne sannan ta fito musu da tsarabarsu suna ta murna tare da saka albarka. Bayan nanne suka zauna da Babanta suna hira, sai tambayoyi yakeyi mata akan zamanta dasu Mami ko tana da matsala duk da dai baiga alamar hakan a tare da ita ba amma zaiso yaji hakan daga bakinta. Sai da ta tabbatar mishi bata da wata matsala sannan suka shiga hirar duniya.
Anan nema yake ce mata shidai zaiso ace data gama secondary school idan har ta samu miji ta kawoshi gida ayi mata aure don mutuncin diya mace shine dakin mijinta don anan garinsu har an fara surutun rashin aurenta don ma ba ganinta akeyi ba.
Sosai Aisha taji dadin zuwanta gida don ta zagaya 'yanuwanta na wajen uwa da uba ta sada zumunci don haka ne ma taga sati biyun tayi saurin karewa. Koda safiyar da zata koma kano tayi ta gama shirinta tsaf kafin lokacin da Mallam Adamu yazo daukarta. Duk wani tsaraba da zata tafi dashi an hada mata shi wuri daya. Babanta ma bai fita kasuwa ba din yana so yaga tafiyarta kafin ya fita. Kafin karfe sha biyi Mallam Adamu har ya iso, babu bata lokaci tayi sallama da duk mutanen gidan ta fito tana sharar kwalla ta shiga mota suka dauki hanyar kano.
Suna hawa titi ta fara bacci wanda ba ita ta farka ba sai da suka iso gida taji Mallam Adamu nace mata ta tashi sun iso gida. Farkawa tayi da salati a bakinta ta kalli harabar gidan sai taga tamkar yaune ta bar gidan gashi har taje ta dawo. Da sallama ta shiga cikin parlour babu kowa a ciki don haka ta wuce kitchen don tasan a wannan lokacin acan zata samu Mami. Sosai Mami tayi murnar dawowarta. Bayan sun gaisa ne ta haya sama don ta ajiye kayanta. Data sauko ne take tambayar Mami inasu Ummie tace mata suna gidan Hajiya acan zasu yini. "Kuma Mami har Ruqaiya sukaje gidan Hajiya"? "A'a tana dakina tana bacci bata dade da kwanciya ba kika shigo".
Koda Ruqaiya ta farka taga Aisha ai sai ta makale mata ta hanata sakat duk inda ta saka kafa nan take maida tata. Ko gani takeyi zata kara tafiya ta barta ne. Su Ummie basu dawo gida ba sai wurin takwas na dare. A lokacin Aisha ce kadai a parlour don Mami tana sama tare da Daddy. Ganin Aisha a zaune da gudu Ummie tazo ta rungume ta tana murna cewa takeyi "Wallahi Aunty Aisha munyi missing dinki sosai kullum Ruqaiya sai tayi mana kuka ita akaita Aunty Aishanta gashi komai akayi mata sai tace sai ta gayawa Aunty Aisha idan ta dawo".
Ita kanta Aisha taji dadin ganinsu don kuwa tayi kewarsu sosai. Farida ce ta kalleta a sheke tace "huh lallai zaman kauye dai baiyi ba, Allah nagode maka da ban hada komai da kauye ba da ko yaya mutum yaje kauye ya dawo sai ya canja". Dariyar shakiyanci Mu'azzam ya saka sannan yace mata "ai wannan uwar kibar da kike narkawa kamata yayi a kaiki kauyen ko kya sabe, wuu wa yaga Farida a kauye" ya kyalkyale da dariya har yana rike ciki. "Amma dai wallahi Yaya Mu'azzam ka cuceni, aini ko ace daga kauye nake idan na samu na rabu da zaman kauye babu abinda zai maidani ballantana ma mi yayi gamin jirgi da mita" tace tana murguda mishi baki. Haka dai sukayi ta shakiyancinsu Aisha na jinsu tayi tamkar bata san ma sunayi ba.


UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ
'YA'YAN MIJI
๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

Na Umm Asghar

10
A haka dai rayuwa taci gaba, gashi Aisha har ta gama secondary school ta samu cigaba a makarantar Sa'adatu Rimi college of Education tana karantar catering wato fannin girke-girke.


A yammacin wata alhamis ne Aisha na kitchen tana taya Mami hidimar abincin dare, Mamin ce ta shigo kitchen din tace "sannu Aisha na tafi na barki da aiki ko, wai ina wajen Daddy muna maganar tafiya Umrah da zamuyi tunda yara suna hutu, inaga ko wajen jibi sai ki shirya ki koma wajen Hajiya kafin mu dawo tunda tafiyar zata kama ranar lahadi ne".


"Ashe tafiyar tazo, Allah ya kaiku lafiya ya dawo daku lafiya. Mami ayi mana addu'a, In Sha Allahu zanyi shirin. Har kwana nawa zakuyi? "Inaga sati biyu ne" inji Mami.


Tunda Farida taji batun tafiyarsu Umrah taji kuma babu Aisha a tafiyar take ta faman yada mata da habaici. Ita kam Aisha ko kallonta batayi ba. Wani abu da Farida bata sani ba shine bata taba hada kanta dasu ba. Tasan matsayinta a gidan na 'yar cin arziki ta kuma san nasu matsayin na 'ya'yan gidan.


Wannan nema dalilin da yasa bata taba daga ido ta kalli wani abu da akayi musu da ba'ayi da itaba duk da dai Mami na kamantawa mawuyacin abu ne tayi musu wani abin batayi mata ba amma wasu lokutan tana yi din ita kuma Aisha hakan bai taba damunta ba.


A kowanne lokaci ta kasance mai godiyar Allah da bais ta zama mai kwadayin abin wani ba. Banda haka da tasha takacin Farida don kuwa sau tari Daddy yanayi musu kyauta ita da Ummie ba tare da ya hada da ita ba. Idan irin haka ta faru Farida ta dinga iyawa tana kafafa kenan duk don ta kular da ita.


Bata manta wani lokaci da Daddy yayi wata tafiya zuwa ingila ya kawowa su Ummie wayoyin hannu a matsyin tsarabarsu. Firirita da iyawar da Farida tayi mata a lokacin don ta kular da ita nada yawa. Ita kam ma dariya abn ya dinga bata don ganin ita dai wayar ma ba damunta tayi ba kuma ba wanda zata kira a waya gareta ba bare ta damu.


A yammacin asabar bayan ta gama hada kayanta zata tafi gidan Hajiya ne ta suka kasa don su kara yin sallama da Mami kafin ta wuce. Kowa na tambayarta abinda takeso su saya mata harda Zainab sai abinma ya bata dariya.


Da zata tafi ne Mami ta kawo kudi ta bata koda zata bukaci wani abu ba sai ta tambayi Hajiya ba. Godiya sosai tayi mata sannan ta dauki jakar kayanta ta kara yimata sallama ta fita. Har mota su Ummie suka rakata, ganin ta shiga mota sai Zainab ta fashe da kuka wai sai ta bita. Da kyar Ummie ta janyeta suka koma cikin gida.


Ta sani itama zatayi kewar Ruqaiya da Zainab sosai domin kuwa ta shaku da yaran ba kadan ba. Duk wata hidima tasu itace tun daga kan wankansu, cin abincinsu, shirinsu zuwa makaranta, kitsone da koya musu homework duk ita keyi. Mafi yawan lokuta ma tare suke kwana a dakin yaran.


Da sallama ta shiga cikin gidan tana janye da akwatinta. Baaba Indo mai aikin Hajiya na tsugune a bakin famfo tana wanke-wanke. Dagowa tayi tare da amsa sallamar tana cewa "maraba da takwara yanzu da yammannan kike tafe".


Cikin fara'ar da bata yankewa a fuskarta tace "eh Baaba Indo mun sameku lafiya" tace "lafiya lau hala dai zaki kwana mana biyu na ganki harda akwati". Aisha tace "eh sati biyu zanyi muku" tace "kai madalla kice muna da babbar bakuwa".


Murmushi kawai tayi ta wuce dakin Hajiya. Bata sameta a parlour ba sai ta wuce cikin dakin. A zaune akan sallaya ta tararda ita tana karatun AlQur'ani don haka akwatin kawai ta ajiye ta fito parlour ta zauna. Tayi kusan mintina goma a zaune kafin Hajiya ta fito daga dakin. Zamowa tayi daga kan kujerar ta gaisheta.


Bayan sun gama gaisawa ne Hajiya ke cemata taje kitchen ta debi abinci. "Wallahi na koshi Hajiya sai dai ko zuwa anjima" tace mata. Jefi-jefi suke hira da Hajiya har aka kira sallar magriba suka tashi don yin sallar.


Aisha dai bata tashi akan sallayar ba sai bayan da tayi sallar isha. Ko a gida ta saba bata tashi bayan magriba zama takeyi tayi tilawar karatun Alqur'ani har sai an kira sallar isha tukunna ta tashi tayi.


Bayan ta Isar ne ta fito ta debi abinci tana ci suna hira da Hajiya. Sallamar da Daddy yayi ne ya katse musu hirar da sukeyi. Yana zama Aisha ta gaisheshi ta tashi ta koma cikin daki taci gaba da cin abincinta.


Sallama ya shigo yayi wa Hajiya don jirginsu da safe zai tashi. Sun dade suna hira irinta tsakanin da da mahaifi.


Sosai yanda yake bawa Hajiya girmanta yake burgeta din kuwa kudinshi da mukaminshi basu saka ya banzatar da mahaifiyarshi ba, komai na jin dadin rayuwa ya wadata dashi.


UMMASGHAR.
[11/26, 22:16] Umm Asghar (Fatima Eshak): ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ
'YA'YAN MIJI
๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘ฉโ€๐Ÿ‘งโ€๐Ÿ‘ฆ

Na Umm Asghar


11
Sosai takejin dadin zamanta da Hajiya. Ko babu komai tana karuwa da ita sosai ta fannin ilimi don kuwa mawuyacin abu ne kaji Hajiya ta zauna tana sakin zance barkatai. Duk wata magana da zata fito daga bakinta mai ma'ana ce ko da kuwa a cikin hira ne.


Suna zaune a parlour suna kallon tashar Sunna TV wayar Hajiya dake ajiye akan tv stand ta dauki kara. Tashi Aisha tayi don ta dauko wayar. Intetnational number ta gani akan screen din.


Mikawa Hajiya wayar tayi sannan ta shige daki don ta bawa Hajiya wuri ta amsa wayarta ga alama mutanen saudia ne suka kirata.


Tayi kusan mintuna goma da shiga dakin sai ga Hajiya ta shigo ta mika mata wayar tace mata "karba Maminku ce akan layi". Da sallama ta amsa wayar sannan tace "Mami ina yini, ina Zainab da Rukieta?" "Lafiya lau Aisha, ya gida" Mami ta amsa mata. "Gida lafiya lau Mami, yasu Ummie da Farida dasu Ya khalifa. Wai yaushe zaku dawo ne Mami wallahi sosai nake cikin kewarku". "Muma muna kewarki Aisha, ga yaranki nan sun hanani sakat ni kaina na matsu mu dawo ko na huta kullum cikin rabon fada nake".



Dariya Aisha tayi tace "ayya Mami kice idan kuka dawo sai na basu purnishement tunda suka wahalar mini da Mamita".


Sun dade suna hira da Mami kafin sukayi sallama. Tashi tayi ta kaiwa Hajiya wayarta sannan ta zauna suka cigaba da kallon da sukeyi. Ji tayi Hajiya na magana don haka ta dawo da hankalinta gaba daya wurin Hajiya. "Na'am Hajiya me kikace" tsaki Hajiya

Please Login or Register in order to submit comment