Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

canji a tare da ita sai ya sota ya mutunta ta a idon duniya kamar yadda yake yiwa matarshi. Zata zame mishi tamkar yadda Aisha ta zamarwa Daddy, zata zamanto mai sonshi mai tattalinshi da farin cikinshi. Zata yi hakuri da duk wani batanci da zata gani daga gareshi ne ko matarshi duk zata jure har sai ya sota tamkar koma fiye da matarshi don ta lura ba wani sonta yake yi ba tafi danganta shi da sha'awarta yakeyi, idan ma kuma akwai son to sha'awar ta rinjayeshi don haka zata koya mishi yadda zai sota ya kuma kaunaceta.




Dole ne ta sauke girman kai ta nemi taimakon Aunty Aisha (rana ta farko da Farida ta yardarwa zuciyarta cewa ta cancanci ta kirata da Aunty) wurin koyon girke-girke da yadda zata kula da muhallinta da mijinta dama wasu abubuwan. Don Ummie ta gaya mata irin problems din data fara fuskanta a wurin mijinta da taimakon Aunty Aisha komai ya zama normal.




Tasan cewa mijinta yafi na Ummie wadata don komai da suke bukata 'yan aiki ne keyi musu, hatta da girki cook ne dasu da yake yi musu shi yasa ita bata samu matsala irin wacce Ummie ta samu ba. Amma yanzu dole ne ta tashi ta koyi abubuwan da ada take ganin ba komai bane tunda tana da masu yi mata, dole ne ta fara ciyar da mijinta abincin da ta dafa da hannunta don bature ma yace the way to a man's heart is through his stomach, to kuwa zata shiga zuciyar mijinta tayi kane-kane ta hanyar ciyarda shi daga abincin da ta sarrafa da hannunta.




BAYAN SHEKARA DAYA

Sanye take cikin leshi daya amsa sunanshi na lace mai matukar kyau da tsada. Kalar cream ne sai akayi mishi ado da zare kalar coffee da golden. Golden costumes tayi amfani da sai dai anyi musu kwallaiya da kananun pearls kalar coffee da cream. Sai mayafi, takalmi da jaka da tayi amfani da kalar coffee. Dinkin rigar buba ne da zani, cikinta dan kimanin watanni shidda ya turo ta cikin rigar.




Taku take yi daidayharvta isa wurin motarta kirar hyundai (elantra) dake ajjiye a harabar gidan ta shiga ta bata wuta sannan ta fita. A bakin gate ta tsaya suka gaisa da maigadi har tayi mishi kyautar dubu daya sannan ta wuce.




Duk da ba nisa ke tsakaninsu da gidan sunan ba amma hakanan taji bazata iya tafiyar kafa shine ma yasa ta fito da mota. Tafiyar 'yan mintuna ce ta kawota gidan. Horn ta danna maigadi ya bude mata gate ta shiga ta samu wuri tayi parking motar.




Cikin takunta na nutsuwa ta nufi cikin gidan. Da sallam a bakinta ta shiga parlour gidan, Farida dake zaune tana bawa yaronta nono tace "oyoyo Mummy, gaskiya munyi fushi tunda sai yanzu kike zuwa sunan ga alama dai bakayi da wannan Daddyn namu". Cikin dariya tace "to me zanzo nayi muku, ai na zauna a gida nima na kula da nawa mijin . Nida ba yanzu ma nyi niyyar zuwa ba Ummie ce ta isheni da waya, tana ina nema?" ta fada tana keken ta inda zata hango Ummie.




Bata zauna ba har sai da ta shiga ciki suka gaisa da maijegon sannan ta dawo ta zauna a parlour. Duk wani nau'i na abincin da akayi a wurin sunan sai da aka kawo mata. Kallon abincin tayi ta cewa Farida "kwashe abincinnan ki maida snacks din kawai sun isheni sai ko alala".




Bayan ta kai abincin ne ta dawo take cewa "Mummy kin kawo mana sakon (suna kiranta Mummy ne yadda su Zainab ke kiranta) don wallahi bakga yadda na matsu kizo ba don kamar na biki gida haka nayi taji".




"Yana mota sai na tashi tafiya sai ku bini ku karba". Daidai lokacin Ummie ta shigo, kusa da Aisha tana cewa "Mummy sannu da zuwa , wallahi ban san kin zo ba ina can Inbtisam ta hanani sakat da rigima, Allah yasa dai kin kawo mana sakon".




"Kai ku dai Allah ya shiryeky wallahi, ji yanda kuka bi kua dameni akan sakonku, to duk me son kayana sai ta ajjiye kudi". "Kai mummy kefa uwace idan ba ke ba wurin wa zamu muce ayi mana, ba girmanki bane kice sai mun biyaki" ta fada tana mai rungumo Aisha.




"Ina su Ruqaiya ne Mummy, da naga ban ganzsu b na dauka tare zaku zo" Farida tace. "Umhh kunsan halin Daddynku cewa yayi baza suzo ba tunda yau akwai islamiyya, ransu a bace suka tafi makarantar".




Bata wani jima ba ta tashi tayi sallama da maijegon (matar Khalifa ce ta haihu, yaron yaci sunan Daddy wato Ja'afar) sannan su Ummie suka rakata har wurin motar, bayan sun karbi sakonsu ne suka yi sallama taja motarta ta koma gida.




A kullum cikin godiyar Allah take idan taga yadda my'amalarta da 'ya'yan mijinta ta canja daga marar kyau zuwa mai kyau. Don a yanzu sosai suke bata grmanta na matar ubansu itama kuma ta rike girmanta da Allah ya bata tana hulda dasu cikin mutunci da mutuntawata kuma yi sa'a Daddy ya kauda idonahi daga harkarsu, komai ya gani a tsakaninsu baya magana don yasan bazata taba cutar dasu ba.

TAMMAT BIHAMDULILLAH
*****

Anan na kawo karshen takaitaccen labari na da nayi wa laqabi da 'YA'YAN MIJI. Ina rokon duk wanda na batawa yayin rubutunnan da ya yafe mini, a kullum dan adam ajizi ne nimakuma na yafewa kowa duk da dai babu wanda ya bata mini.
Har Kullum sadaukarwar ta 'yaruwata ce Fatima (Uwani) da Allah yayi wa rasuwa ina barar addu'a ga duk wanda ya karanta littafin nan a gareta da fatan Allah ya jikanta yayi mata Rahama ya kai hasken Rahamarshi kabarinta ya tasheta a inuwarshi ranar tashin Alqiyama. Mu kuma idan tamu tazo Allah yasa muyi kyakkyawan karshe.
Jinjinar ban girma ga daukacin members na groups din Umm Asghar Novels, Dakin Hausa novvels, Dandalin Hausa Novels, Khaleesat Hydar Novels a facebook da kuma Hausa Novel.


UMMASGHAR.
Downloaded from GNOVELS.COM.NG




This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG
to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/gnovels

Twitter : https://twitter.com/gnovels

Telegram : https://t.me/gnovels


Please Login or Register in order to submit comment