Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


Downloaded from GNOVELS.COM.NG




This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG
to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/gnovels

Twitter : https://twitter.com/gnovels

Telegram : https://t.me/gnovels

. *************************⬇**********************
************* Ai Hausa Novels ****************
*************************⬆ **********************

DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.

Visit > https://www.aihausanovels.com.ng

Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post.

Email > aihausabooks@gmail.com

******* FOLLOW US ******

Facebook: Ai Hausa Novels

Twitter: Ai Hausa Novels

Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels



Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu.

********************** ⬇ **************************
*************** Ai Hausa Novels ****************
********************** ⬆ **************************

[7/10, 10:34 PM] Bintu: *'YAR BANGAR SIYASA!!*
🌺 romantic love story🌺
*NA:*
*BINTA UMAR ABBALE 🍒*
*🌍Manazarta Writes asso*
_'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_
~~~~~~~~
*NA KUDI NE.......!*
_Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_


_*'KIRKIRARRAN LABARI NE, BA'AYI DAN ACI ZARAFIN WANI KO WATA BA WANDA YAGA YAYI DAI-DAI DA YANAYI NA RAYUWARSA TO A RASHIN SANI NE!*_
~~~~~~~
_Pegen farko naki ne_
*_Ummi 'yar bare bari na gaisheki kanuri kina 'kamshi ina binki da humra 'yar dakina Allah ya bar 'kauna ta dan Allah!_*
~~~~~~~~
_Bisimillahi_


Free Pege
*1*

*'DORAYI*
Wani rugujajan gida na hango na jar 'kasa duk katangar gidan ta zaizaye ta dur'kushe ta zama 'yar 'karama saboda tsabar wahala 'kofar gidan hanhai!! yake masu wucewa ma suna kallon cikin gidan .....Wani tattararran buhu na hango wata budurwa ta saki tana fad'in"Haba wannan wace irin masifa ce ace kullum gida a bud'e saboda tsabar mutunci duk kuna zaune a rasa wanda zai sakaya 'kofar ko kishin kanku ba kwayi meye amfanin talauci Allah ubangiji kayi mana katangar 'karfe dashi."

"A'a aunty Wasila kyalemu mu sake mu sha iska yo wannan gidan in ba abude shi ba me za'ayi masa gida a ru'be da jar 'kasa ai wallahi ko ta halin 'Kaka sai nayi kudi in huce takaici nayi dakace dana fito ta tsatson babanmu duk shine ya cuce mu aikin banza kawai." Ta 'karasa maganar tana jan dogon tsaki!

Uwani dake sunkuye a bakin rijiya tana wanki tace"Kya fad'a Rashida ni kaina da kace nakeyi da auran babanku gashi ya mutu ya barni da wahala da 'kailulu kafin zuwansa gidanmu akwai manyan mutanan da suka fito zasu aureni nace shi nake so saboda naga fari kyakkyawa sai da tafiya tayi nisa a tsakaninmu na gane kyau bashi bane kawai ka auri mai kudi ka huce bakin cikin duniya."

Rashi da turo daurin dankwali gaba tace"Ai wallahi Uwani nayi alkawarin sai nayi auran kece raini dan ba zan auri 'karamin mutun ba sai na za'ba na durje sannan dan wannan kyawun nawa ba zai tashi a banza ba."


Uwani tace"Yawwa 'yar gari kiyi komai ba komai nice Uwarku nice Ubanku babu shegen da ya isa ya sanya ido a kanku tunda babu wanda yake taimaka mana to kuwa banga dalilin da zai sanya ace dole sai kunyi aure ba ko wacce tayi abunda take so kwalliya kuwa ko wace iri ce kuyi ku futa ku samo manyan maza masu abun hannu ni kaina wannan kyawun da Allah ya baku bana so ya tashi a banza a wofi."


Wasila dake tsaye tana sauraransu tace"Yanzu dai Uwani idan na fahimce ki kina so kice mu tafi yawon karuwanci ko."?

Uwani tace"To meye idan karuwanci kukayi? ai halak dinku kuke nema da kuje ku dauki na wani gwara ku mika jikinku a biya bukata sai me waye zai gani abunda ba fitowa yake a saman goshi ba."

Wasila tace"To sai dai in Rashida amma ni na fad'i miki kome zakiyi wallahi bazan zubda daraja ta da mutunci na ba, na yarda zanyi ko wace irin sana'a ce amma banda karuwanci."


Uwani tace"Kece babba kuma kece mara wayo yo mara wayo mana duk wata sana'ar da zakiyi a yanzu ba takai ta karuwanci ba itace yanzu yanzu zaki mi'ka kiji dumus! a hannunki yanzu sai kiga kina murza sitiyarin mota yanda kike da zubi ai nasan manyan mutane da sarai ne za suyi karakaina a kanki."

Wasila ta harari mahaifiyar tata tace"Wallahi Uwani kinji kunya kwarai komai hud'ubarki ba zanyi wannan sana'a ba ina da ilimi dai-dai gwargwado sannan kuma ni babu abunda na tsana a duniya irin iskanci, wallahi da in mi'ka kaina gurin wani gardi gwara na kwana banci ba, Sana'a kam nace zanyi ko wace iri ce banda karuwanci."


Rashida tace"Wallahi aunty Wasila baki da wayo kin fini fa zubin jiki mai kyau da daukar hankali wallahi kina fad'awa wannan harkar maza zasuyi caaaa! a kanki shikkenan mu da talauci munyi hannun riga."


Ashar! ta lailaya mata tace''Kika sake mun irin wannan maganar sai ranki ya 'baci! kema bana fata kiyi wannan sana'a in dai kudi ne ku bari ku gani ku dai ku taya ni da addua."

Uwani na shanya kayan wankau din mutane tace"To shikkenan muna zuba ido mu gani a 'kasa uwar tsari yau ki shigo mana da gassasun kaji da lemo nan zamu gane kin zama "yar kasuwa."

Wasila tace"Uwani dan girman Allah da Annabi kar kuje yawon bin gidajan jama'a sannan kar ki tura Rashida tayi wannan sana'a wallahi bata dace damu ba a matsayinki na mahaifiyarmu ki kare mana martabarmu insha Allahu yau zan fita a sa'a za'a dace."

Uwani tace"To tunda kince haka shikkenan Cin mu da shan mu duk ya rataya a wuyan ki." Tace"Eh naji insha Allahu Allah zai bani ikon d'aukar nauyinku."


Har ta d'aga buhun zata futa sai ta dawo tana kallon mahaifiyar tasu tace"Ko na futa dan Allah karku daga buhun nan ku barshi a haka yafi mutunci." Uwani tace"Shikkenan Allah yq bada sa'a."
Wasila ta amsa da "ameeen" tasa kai ta fice daga gidan.





_Muje zuwa_
*BINTA UMAR ABBALE*
[7/10, 11:29 PM] Bintu: *'YAR BANGAR SIYASA!!*
🌺 romantic love story🌺
*NA:*
*BINTA UMAR ABBALE 🍒*
*🌍Manazarta Writes asso*
_'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_
~~~~~~~~
*NA KUDI NE.......!*
_Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_

*Free Pege2*
Wasila na fita ta nufi gidansu Hadiza 'Yar camas! 'kawarta ce sosai amma kuma halinsu ya bambamta! Camas! tana bin maza kuma tana d'an ta'ba shaye shaye sa'banin Wasila da bata shan komai na maye sannan kuma bata bin maza kawai dai ku barta da tsiwa da rashin kunyarta.

Camas! na zauna a tsakar gidansu suna hira jefi jefi da mamanta Wasila tayi sallama ta shiga gidan Mahaifiyar Camas mai suna Asabe ta amsa tana fad'in"Wasila kece a gidan." ? Tace"E wallahi ina wuni." Suka gaisa a mutunce har Asabe na tambayarta Uwani tace"Tana nan lafiya.

Camas! Tace"Ke 'yar iska ina zuwa kuma nagan ki da mayafi yau ina hijab din."? Wasila tace"Dauko mayafinki muje." Camas ta mike a hanzarce ta shiga dakinta ta dauko wani karamin mayafi ta yafa suka fita Asabe ta bisu da kallo tana girgiza kai al'amarin na 'yar tata sai addua dan a zahiri ma gwara Wasila kanta komai ma Hadiza ya lalace har karatu duk ta watsar gwara Wasila nayin asha ruwan tsintsaye gurin zuwa makarantar.

Sai da suka kusa futa daga layin sannan Wasila tace"Ke Camas! yau fa a shirye nake wallahi! Gidan gwammanti zamu je yanzu."

Camas! tace"Kai! Wasila me zamuyi a gidan gwamnati kuma."? Wasila tace"Muje kawai ina so in fara harkar Siyasa ne." Camas! tace"Harkar Siyasa kuma lallai Wasila kina so ki jefa rayuwarki a rud'ani Siyasa masifa ce duk ga sana'oi nan da zakiyi ki rufawa kanki asiri sai kice siyasa za kiyi."!

"Kinga Camas! idan zakije to ni bana son wata doguwar magana anan gurin harkar Siyasar ma idan ta kar'beka sai kaga ka samu kudi sannan kuma duniya ta san da zamanka."

Camas! tace"Kuma fa hakane wallahi hausawa nacewa matsoraci baya zama gwani kawai mu afka ba'asan inda rana zata fad'i ba.'' Wasila tace"Ashe kin gane 'kawata."


Bakin titi suka fito suka samu a dai-dai ta sahu kai tsaye sukace ya kaisu gidan gwamna. Mai d'an sahu ya kallesu da mamaki sosai a tare dashi gidan gwamnati to me zai kai wad'annan yaran can? bashi da mai bashi amsa kawai ya ja babur din sukayi gaba.....Yanda suke hirar ne ya fahimci inda suka dosa yace''Yaya na ni dai shawarar da zan baku shine ko zakuyi wannan harkar dan Allah ku tsare mutuncin ku kar ku ku watsar da martabar da Allah yayi muku."

Wasila tace"Insha Allahu baba zamu kiyaye." Yace."To nagode da kuka dauki magana ta." Ana kiran sallahr magariba ya sauke su a bakin titi Wasila ta ciro dari biyu a bayan condem din wayarta ta bashi yace."Ai saura dari dari uku ne kudin."

"Haba Baba kayi hakuri da wannan d'in ita kenan muka baka ka gani ko na dawowa ma bamu dashi." Yace"Shikkenan." Babur din yaja ya barsu a gurin.

Camas tace"Shiyasa sam bana son shiga babur! din dattijai duk 'yan buri ne gwara in shiga na samari masu tara suma su kunna maka kad'e kad'e in ta kama ma suce ka bar kudinki."

Wasila hankalinta na kan wata mota dake kokarin shiga rukunin gidan gwamna tace"Wallahi haka maganarki take Yawwa kinga wata mota zata shiga bari na tsayar da ita sai ta hau d'agawa mai motar hannu.

A hankali motar ta tsaya inda take kana gilashin motar ya sauka a hankali mamalakin motar ya bayyana.....Wani 'kosashen mutun ne bayan motar a hakimce kana ganinsa kasan yaci ya tada kai da nera yana hada ido da Wasila ya had'iya wani yawu zuba mata ido yayi har suka 'karaso gurin.........Manya manyan idanunta ta juya kana ta dafa motar da hannunta guda ta lankwasar da mirya ta tace"Barka da wuni yallabai ya gida ya fama da jama'a."?

Alhaji Ma'aruf ya amsa yana washe baki sosai yace."Lafiya 'yan mata jama'a kuma ku za'a tambaye."

Ta saki wani shu'umin murmushi tace"Yallabai kenan, Dama muna neman wata alfarma ne." Yace."Ko wace alfarma ce ku fad'eta mutukar ta shafi gidan gwamnati to zanyi kokarin ganin kun sameta."

"Yawwa Yallabai muna so mu fara harkar siyasa ne shiyasa muka dacewar muzo muyi tambaya akai." Alhaji Ma'aruf yayi mirmushi hade da shafa sajensa ya dan tura hular sa 'keya yace"To ai kaya ne suka tsinke a gindin kaba, babu matsala ku shigo mota muje zan shiga gurin mai girma Governor idan na fito sai muje daku guest hause dina in yaso sai muyi maganar.

Ba tare da wata fargaba ba suka bude mota suka shiga suka zauna dravar yaja motar suka bar gurin.





_Muje zuwa_
*BINTA UMAR ABBALE*
[7/11, 12:37 AM] Bintu: *'YAR BANGAR SIYASA!!*
🌺 romantic love story🌺
*NA:*
*BINTA UMAR ABBALE 🍒*
*🌍Manazarta Writes asso*
_'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_
~~~~~~~~
*NA KUDI NE.......!*
_Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_


*Free Pege3*
Kunnanshi ma'kale da waya ya fito daga bedroom din shi ya zauna daya daga cikin shirga shirga kujerun dake palon ya wani d'ora kafa d'aya kan d'aya yana masifa!....."Khalifa wad'annan mutanan fa babu Allah a tare dasu ni wallahi tuntuni na dawo daga rakiyarsu shin wai mulki hauka ne!? duk wannan kashe kashen da akeyi da sace sacen yara kananun mun san daga ina ne kawai saboda ana jin tsoronsu sai ayi shiru to wallahi daga yau na shirya d'amarar ya'ki! dasu mulki suke so nima shi nake so Allah ya bawa mai rabo sa'a haba! wannan al'amarin ya ishi talakawa wuya tayi wuya mutane sai mutuwa sukeyi gobe ka fito da wuri zamu fara yawon kamfen insha Allah." Khalifa dake daya bangaran yace."Insha Allahu zan fito da wuri amma yana da kyau ka tanadi matakan tsaro kafin fitar tamu.'' Yace."Kar ka damu da wannan insha Allah Allah zai karemu tunda domunshi muke." Sallama sukayi da juna ya kashe wayar tare da ajiyeta saman tevur din dake gabanshi.....Zuba masa ido nayi ina kallo wai! Allah yayi hallita a gurin kyakkyawa ne ajin farko fari gaggausa yana da dogon hanci da manya ido da gashin gira kewayayyiyar fuskarsa na dauke da sisirin sajensa wanda yasha gyara ya zauna das ya kawata fuskar tashi......Ya wuce ka kirashi yaro gaskiyar magana kenan domin idan ka tsaya ka kalleshi da kyau zaka fahimci shekaru sun d'an tura masa a 'kalla yanzu shekarunsa ar'bain da biyu zuwa da uku........
*Ahamad Musa (Ba iya ka!)* ainin sunansa kenan Matashin saurayi mai jini a jiki mai tashen kudi wanda bai san iya adadinsu ba, shi ya sanya jama'ar gari suke kiranshi da wannan suna *Ba Iya ka!* shima ya samo shi gurin mahaifinsa *Alhaji Musa (Ba iya ka)* wanda ya shahara yayi shura a zamaninsa Allah ka ji'kan maza.
Ahamad kawai ya haifa shima kuma kafin ya haifeshi din sai da ya futar da rai! da haihuwa lokacin duk girma ya baibayeshi ya auri wata 'yar filani ashe rabon a jikinta yake haduwarta ta farko ta dauki ciki.......Farin cikin da ya shiga a lokacin Allah yayi yawa dashi ya dinga sadake sadake yana kai mutane saudiya suyi wa matarshi addua Allah ya sauketa lafiya.

Allah babu yanda baya tsara lamarinsa gurin haihuwar Ahamad mahaifyarsa ta rasu sosai iyalin Alhaji Musa sukaji mutuwar daga bisani suka barwa Allah lamarinsa.....Sai suka dawo kan Ahamad suka dinga nuna masa so da kulawa mussaman mahaifinshi Allah ya jarrabeshi da kaunar yaron nashi ashe ba zasu dade da juna ba Allah ya dauki rayuwar Alhaji Musa....Mutuwar da ta girgixa zu'katan al'ummar gari suka dinga kuka da fadin"Bango majin ginar talakawa ya fad'i!! Jama'a sukayi dafifi a harabar gidan suna masa addua da fatan Allah ya kai rahama kabarinsa.

Tunda Ahamad ya taso yaga yanda mahaifin shi ke taimakon al'umma sai ya dora a inda ya tsaya tun yana dan shekara ashirin a duniya sunanshi ya 'bace a gari mutukar baka kira
*(Ba iya ka)* ba to babu in zaka kwana kana kiran Ahamad babu wanda zai gane wanda kake nufi....


Ahamad jama'ar gari ne suka kwadaita masa sha'awar mulki da sam ba tsarinsa bane ya fiso yayi harkokinsa to shima kuma da ya zauna yayi nazarin yanda al'amuran siyasar ya ta'bar'bare sai kawai yayi sha'awar fantsama kansa a harkar domin ya taimaki al'ummar da suke galabaita a jahar mussaman talakawa sune dama abun tausayi.


Kallo guda za kayi masa ka gane yana da fuskar Salihai! a zahirinsa kenan a bad'insa kuwa mutum ne shi mara hakuri kuma sam baya barin ta kwana kamar zawo yake mutukar kayi masa abu idan bai rama ba sam baya jin dad'i....bayan wannan halin nasa bai da wani mummunar hali dama ance adan adam tara yake bai cika goma ba Ahamad nada tausayi da taimako sai nace muku ma duk rabin neman kudinsa yanayi ne kan jama'ar gari marasa galihu da na kasassu gami da marayu.......Dalili kuwa bashi da nauyin kowa a kanshi tunda shi ba aurene dashi ba ballanta ayi maganar yara, Jama'ar gari duk sun dauka yana da aure da iyali shiyasa duk adduarsu a kan iyalinsa take 'karewa sai dai kawai amsa da "ameeen"

Nasan zakuyi mamakin namiji kamar Ahamad mai jini a jika sannan uwa uba kudi! ga kyau da kwarjini da haiba da yake dasu amma me yasa bai aure ba? Yana zaune hakane ba wai dan bashi da lafiya ba ko kuma rashin matar aure akwai 'yan mata bila adadin dan ba zasu lissafu ba, kawai duk cikinsu bai ga wacce ta kwanta masa a ransa bane ya ajiye maganar aure a gefe saboda yasan cewa lokaci ne idan Allah ya kawo masa matar lokaci guda za'ayi a gama.

'Daya daga cikin masu tsaronshi ne ya shigo palon....Ya d'aga kanshi yana kallonshi A nutse yace."Ya akayi."? Garba yace."Kana da bakuwa tana dakin 'baki mun sauketa."

Jim! yayi yana nazari wace 'bakuwa yayi kuma yanzu karfe goma na dare! Ko da yake ai tunda ya fara wannan harkar kuma yayi ta ganin jama'a ya mike a nutse Garba ya bashi hanya ya wuce kana ya take bayanshi.





_Muje Zuwa_
*BINTA UMAR ABBALE*
[7/11, 9:41 PM] Bintu: *'YAR BANGAR SIYASA!!*
🌺 romantic love story🌺
*NA:*
*BINTA UMAR ABBALE 🍒*
*🌍Manazarta Writes asso*
_'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_
~~~~~~~~
*NA KUDI NE.......!*
_Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_



*Free pege4*
Cikin takun girma gami da 'kasaita ya shiga d'akin, lokaci guda 'kamshin turaransa ya karad'e hancinta, ta d'ago shanyayyun idananunta ta zubasu a kansa, tun kafin ya 'karaso inda take zaune ya 'kare mata kalau black beauty mara tsayi sosai da cikar kirji dauke kansa yayi daga kanta ya had'e fuska sosai wannan bakuwar tashi ba ta arziki bace duba da yanayin suturar dake cikinta.

Tana sanye da wata matsatstsiyar t_shart da dogon wandon jins wanda ya fitar mata da zahirin hallitarta ta sanya karamin hijab wanda ko kirjinta bai rufe ba tsakiyar kanta yayi tozo da tsayi da alama tana da gashi sosai tunda ga alamunsa nan ya nuna saman goshinta.


Hannunsa cikin aljuhu ya isa inda take, ta mike tsaye da sauri tana marmar da shegun idanunta masu rikita lissafin da namiji......Ya kura ma jikinta kallo tayi sosai dan bai hango makusa a tattare da ita ba ta cika har ta batse kuma tana da abubuwan da yake bala'in so a jikin 'ya mace sai dai kash! ba wannan ne a gabansa ba abunda ke gabansa a halin yanzu shine ya za'ayi talakawa su samu walwala da farin ciki.

Fuskarshi ya sake tamkewa tamau! yace."Baiwar Allah daga ina? ance dani nayi bakuwa na dauka ta arziki ce sai a ka samu akasi."

Wasila taji ciwon maganarshi kasancewar ta macen da bata daukar raini mussaman ga da namiji basarwa tayi ta matsa kusa dashi cikin salon janye hankali tace"Daga duniya na fito nazo ne in d'ebe maka kewa nasan namiji lafiyayye kamar ka na bukatar lafiyayyar mace ka mata.

Tsawa ya buga mata yana nuna ta da hannu"Ke! cikin gidana kika shigo kina min wannan maganar? ashe dama zargin da nake miki gaske ne okey get out from my house. "! Maimakon ta fita sai ta durfafeshi tana so ta rungumeshi, ya kai mata wani wawan mari! yana ya tsine fuska sai karkad'e jikinsa yake kamar wanda ya ra'bi motar daukar kashi.....Ya mutsa fuska yake yana korar shaid'an, yace." Za kici Ubanki yanzu yanzu zan sanya a xane miki jiki har gida zaki shigo ki kawo min iskanci ni ba'irinku bane." Fita yayi yana 'kwalawa Garba kira.

Wasila ta dauke hannunta dake fuskarta gaskiya yana da taurin kai ta lura ba zai bari ha'kansu ya cimma ba ruwa ba d'an iska kawai tayi irin wannan shigar ya dinga kauda kai yana ya tsine fuska anya ma kuwa lafiyayye ne? bata da mai bata amsa sai tayi maxa ta dauki jakarta zata futa suka buga karo dashi yazo zai shigo kirjinta ya daki kirjinsa yayi saurin ja gefe guda yana kallonta sai wani gumi yake kamar wanda yayi tsere.

A ya tsine ta kalleshi tace"Na d'auka ai lafiyayyan namiji ne ashe hotiho ne har kana zagina 'kato da kai baka kunyar zagi anzo a jiyar da kai dad'i kana gudu Allah ya kyauta kaje ka nemi magani."

Wata sha'ka ya kai mata ya matse ta a jikin bango (garo) ta dinga kakari idanunta sunyi jajawur!!! Cikin kaushin murya yace."Idan za'a had'a min iri-irin irinki guda dari duk zan gama musu aiki ba tare da nagaji ba, 'karyar iskanci kike yarinya da ina da bukatar mace a yanzu dana fatattaka ki kuma in kwana lafiya 'yar iska mara galihu."

Hannu tasa tana 'kokarin 'bam'bare hannunsa dake sha'ke da wuyanta duk ta muzanta sai kyarmar jiki take tana cizan le'banta.....Sai da ya gama galabaitar da isa sannan ya saketa aikuwa ba tayi wata-wata ba ta kai hanni gabanshi zata d'amka! yayi gaggawar ri'ke hannunta yana kallonta da mamaki a tare dashi.

Sun jima suna kallon juna ita dashi mugun mamakin 'karfin halin yarinyar yake wato shammatarsa take so tayi ta nakasta shi....Ido jawur! tace"Sake min hannuna."! Ya 'kara rike hannun tamau! yana sakin wani killer smile yace"Kina so ki ta'ba ne."? Wasila tayi tsuru-tsuru tana kallonsa sam ba tayi tsammanin guy zai samu galaba a kanta ba.

"Wannan kayan aikin da kike gani yafi 'karfin irinku 'yan iska! na kamilar mace ne mai addani ba irinki mai yawon ta zubar ba." A fusace! ta fuzge! hannunta ta watsa masa kallon raini fuuuuu!! ta kama hanyar fita......Taku uku yayi ya cimmata tare kofa yayi yana me bin jikinta da wani shu'umin kallo.

"Sosai kikayi babu wata makusa a jikinki duk inda 'yan mace ta kai kin kai yarinya sai dai sam baki burgeni ba idan ma turo ki akayi to sai kije ki sake sabon shiri ki sani Ahamad ya wuce tunaninki." Yana 'kare maganarshi ya 'kwalawa Garba kira.

Ya shigo da sauri yana fadin "Yalla'bai! gani.'' Yace." Maza rakata da bulala idan tayi gardama ka zane 'kafafunta." Garba Ya kalleta, "Wuce muje." Yafada cikin bin umarnin Ubangidansa.

Wasila kamar ta hadiye zuciya ta mace tunda take a rayuwa ba'a ta'ba tozarta irin yau ba lallai guy bashi da mutunci amma babu komai sun d'aura idan kere na yawo zabo na yawo watarana za'a had'u.
Kallon uku shaura kwata tayi masa kana ta gyada kai ta wuce shi.....Garba ya bita a baya da zabgegiyar bulalarsa....Harbar gidan ya fito ya tsanya tare da zuba hannuwansa cikin aljuhu yana kallo Garba ya tasa 'keyarta har bakin gate yanayi yana caud'a bulala a 'kasa kamar zai daketa hakan ya sake kular da ita ta sake 'kullatar guy girgiza kai kurrum take tabbas maganar da chamas! tayi gaskiya ne babu abunda yake cikin harkar Siyasa sai tozarci da wulakanci, Garba na ganin tayi nisa da layin sai ya juya ya koma cikin gidan.





_Muje Zuwa_
*BINTA UMAR ABBALE*
[7/12, 8:39 AM] Bintu: *'YAR BANGAR SIYASA!!*
🌺 romantic love story🌺
*NA:*
*BINTA UMAR ABBALE 🍒*
*🌍Manazarta Writes asso*
_'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_
~~~~~~~~
*NA KUDI NE.......!*
_Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_

*Free Pege5*
Yana tsaye a inda yake Garba ya shigo ya sanya masa ido har ya 'karaso inda yake tsaye.....Kai a 'kasa Garba yace."Sir tayi nisa da layi sosai amma fa ina zargin wani dan gane da wannan yarinyar." Ido ya sanya masa a nutse yace."Kamar name kenan." Garba ya 'kara risinar da kanshi a kasa yace."Anya kuwa ba turo ta akayi ba kuwa kasan fa mutanan babu abunda ba zasu iya ba."

Murmushi yayi yace."Garba idan ma turo ta sukayi tayi min sharri ko abu makancin wannan to insha Allahu ba zasu samu nasara ba ni nafi karfinsu tunda bana nufin su da sharri sai alkairi harkata ta siyasa kuma yanzu na fara babu gudu babu ja da baya ni dasu Allah ya bawa mai rabo sa'a."
Garba yace."Ka gama magana Yallabai Allah ya baka nasara

Please Login or Register in order to submit comment