Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

╨╧рб▒с>■  b■   АА                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                                ¤   _    

 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~БRoot Entry         └Fc WordDocument    .ж0Table        Data
            ■   ье┴ЙИ P┐j[KSKSд.ж╡*      д╪╪11111эДqм1А▒l>╪111111[н1[1[111 Bismillahi Rahamanir Raheem!!! =╪N▐ 'YAR BAIWAH=╪N▐
Maman Ussee

Yau yakasance jumma'ah yayinda kowa ke hada hadar zuwa masallaci garin yayi haske gwanin sha'awa kowa lamarin gabansa kawai yake tafe take tana yan wake wakenta dauke da tulu akanta zataje debo ruwa rafi kasancewar yau kasuwar garin nasu so take taci kwalliya Dan zuwa kasuwa Sameera kenan YAr BAiwa ahankali kawarta indo ta lallabo tabayanta tace Keee, hava indo meye haka nihar kin tsoratani wallahi ohh wadda aka kira da indo tayi =╪▐ tace kekuma gaki da tsoro kamar kura ko samira tayi murmushi tace to sai kawai naganki kwatam toya akayi kawalliya naje gdnku banga ki ba eah wllhi Inna ce ta aikeni sayen omo kinga sauri ma nakeyi tace karna Dade to sa himma nima kinga danakai wan nan din nakare sai mun hadu kasuwa ko taimata sallama suka wuce.
Kai tsaye gidansu ta nufa da sallamarta ta aje tulun washh wallahi umma nagaji ke banason shashanci Dan wan nan diban ruwan ne wai kingaji rafin nisa gareshine daxakice wai kin gaji sa himma kiyi wanka kinga ankusa tasowa daga masallaci, kije kasuwar ki yo mana sayayya ta amsa da to tashiga daki ta kwabe kayanta tafito da daurin kirji tashiga bayi tai wanka ta fito tana Shafa mai da hoda nidai gefe nakoma ina kallon ikon Allah anata cika fiska da kwalli da digo digo ohhh dariyace ta kusa subucemin nadai gimtse INA kallon Samira an takarkare ana Shafa Jan =╪D▄ takare takoma fannin sa kaya wasu kaya atamfa ce ba laifi kam a wurin samira da ita a ganinta yau Zata goge sosai.
Sameera yarinya ce yar kimanin shekara goma sha Biyu farace ba Sol ba irin chocolate colour din nan Allah yamata baiwar kyau bakinta Dan karami dashi dauke da siraran labba ga hakora farare Sol kanana Jere gwanin sha'awa tanada idanuwa masu kayatarwa irin na mejin bacci sexy eyes ba laifi kam batada jiki kuma baxa asakata layin maras kiba ba masha Allah da ita son kowa kin Wanda yarasa ga tada shaf brain shiyasa ake kiranta da yar Baiwa duk abinda aka fada mata bata mantawa ga hankali uwa uba hakuri batada kiriniya ga basira sai dai kash abu dayane samera batadashi iyayenta talakawane ga samira nason boko kamar me intaga Dan birni cewa take Dan koyamini turaci Allah yayi sameera mai son abu duk abinda tasa kanta to ta rike kenan kuma da an fada mata so daya ya shiga kanta
Umma na fito bani sakon so nake nadawo da wuri so nake naje wurin Dan birni kinsan yau yadawo Ohh kekam da naci kike to Allah Bada Sa'a ungo ki sayo min kayan yaji da sukari kinji tace to innna ta amsa tafito tana tafiyarta a hankali ba abinda ke damunta har takai kasuwa tana sayayarta saiga garbati shida tawagarsa suka tareta ke yar Baiwa sunanda kowa ke kiranta dashi kenan. Tin dazu ina jiranki kin shanyani mekike nufi itadai bata ce komai ba ta sadda kanta kasa tana wasa da yatsunta can sai ga Indo ta isu takallesu ta watsar wai kai wanne irin bawo nekai ana soyayya dolene kunbi kun takurawa yarinya kun hanata sakat duk Inda taje sai kunbita kamar wasu mayu. Ke yarinya ki iya bakinki mtseew indo taja karamin tsaki kukan dai anyi shashashai wllhi ilu na tare da garbati yadaga hannu zai mareta sai iro yace kai Narabaka gidansu basa yafiya wllhi kumuje tunda uwarta tazo indo taja hannun samira suka wuce kekam dai kinji haushi su wadan nan banzayen zaki tsaya suna garaki to indo yakikeso nayi dasu kinsan halin garbati zai iya kullamin sharrin da banjiba bangani to ki tsaya sokonci har a Rena ki in anmiki tsiwa xakiyi kinuna bakya tsoronsu inba haka. Ba kinatare dajin haushi to Inda banxoba fa sai yaya kenan sai ya kuwa illa in rokesu mtseew kinji haushi wllhi yar Baiwa nidai muje kiraka ni nasayowa innata magarya tam muje.
Suna tafe suna tadi abinka da kawaye har sun manta Indo kawar sameerace tun suna yara sa'an ni. Juna ne gidansu ba wani nisa dagidansu sameera indo akwai tsiwa ga iyayi batada hkr kuma bata daikar raini shiyasa ake shankunta ko a cikin gari uwa uba tanada yayu masu shiga mata gidansu duk Wanda ka taba ka tsokalowa kanka basa Barin kota kwana.
Sallamu alaikum inna nadawo xanje gidansu Dan birni akoya min boko to yar Baiwa saikin dawo kardai ki Dade kinji ta amsa da to ta fito da azama zuwa gidansu kabeer duk da tana shakkun Hajiyarsa Dan ta tsaneta hasalima batason yana zuwa gidan baxata manta ranar da takirata da mayya kekam kullun sai kin likewa Dana to ahir dinki sameera bata kawo komai aranta ba ita burinta kawai akoya mata turanci ta iya zata jure duk wani fada na Hajiya matsawar za'ta samu abinda takeso wan nan kenan.
Tana shiga gidan saida gabanta yafadi tadai danne ta Shiva cikin gidan kai tsaye falon Hajiyar ta nufa suna zaune ita da 'ya'yanta husnah da yusrah sai kamal kanin Kabeer da Sallamarta tashiga su yusrah naganinta suka washe baki suna dariya ohh Yar Baiwa sarkin son karatu har an iso kenan cewar kamal Hajiya Kareema najin an ambaci sunanta ta hade rai kamar bata taba dariya ba Samira na shigowa ta gaida Hajiyar INA wuni lafiya atakaice San nan taja tsaki mtseew da dawowar tashi baza'a barsa ya huta ba kuma zaki wani zo kidamesa haba Hajjiya meye laifinta nine nace tazo ai dalibata ya kk ya kwana biyu hpe dai kinzo dashiri danyau akwai sababin darussa ta murmusa tace eah uncle to shigo ki zauna kamin naci abinci sai mu fara Husnah kuma Ku shirya musamman ma ke yusrah naga bakya maida hankalinki sosai sunka turo baki hva yaya week end nefa yakamata mu huta kai bana son shashanci kutashi maxa Hajiya kareema hararar samira kawai take itadai ta tsani yarinyar nan nacewa ne da ita to dolene saita iya turanci itada take ba yar kowa ba tashin kauye ko ubanme iya turancin zai tsinana mata oho yarinya kamar mayya tabi ta ha nata sakat itada danta inyazo week end said a dare da rana yana tare da shegiyar yariyarnan sai Yarbaiwa cewar Hajiya acikin zuciyarta.
Itadai sameera ta takure gefe jiran fitowar uncle Kabeer kawai take yazo yafara koya mata abinda zata karu tabar gidan yana kamalawa tafito da book rike a hannunsa yace to daliba muje garden ko ta mike su yusrah ma suka biyota suka biyo bayanta suna isa kowa ya zauna a kujera yafara gabatar musu da lesson yayinda yar Baiwa da yayi tambaya take amsawa itada batamada lesson book amma yusrah sai a hankali gara ma Husnah tana Dan ja haka da haka har suka kare kasancewar ba lokaci dayawa 'Yar Baiwa tai godiya takoma ta ma Hajiya sallama ta wuce zuwa gidansu tana zuwa ta rungume ummanta tana murna take Bata labarin abinda aka koya mata haka rayuwar samera takansance har karshen sati itadai burinta tasamu ilmi Dan ta taimaki mahaifanta!!!

2 be continued
Maman ussee

=╪N▐ 'YAR BAIWAH=╪N▐2у

Maman ussee


Rukayya 'ya CE ga malan sa'idu ita kadai Allah ya azutarsu da ita bayan sunsha wahala matuka kamin su sami haihuwa shekarar su 10 da aure ko batan wata ba'a taba yiba a gidansa kwatsam sai ga cikin Rukayya ansamu karkuso kuga murna a wurin malan sa'idu ya dauki burin duniya yasaka akan cikin nan mai dakinsa har mamaki take duk da itama tana burin taga kwanta a duniya Dan baxata manta ba ko haihuwa akayi idan taje barka ba'a. Bata jariri wai batasan zafin haihuwa ba Dan haka.Baxa a bata ba tasha kuka amma dayake mijinta na matukar kaunarta sai ya lallasheta da kalamai masu dadi yana kwantar mata da hankali yana lurar da ita haihuwa ta Allah ce kuma Allah yana sane dasu karta damar da kanta wata rana suma Allah zai basu nasu rabon haka ne kam gashi hkrinsu yabasu yau Allah yabaiwa salamatu ciki haka sukayita renon cikin har Allah ya ingantashi Rayuwa kenan(mai hakuri mawadaci) malan Sa'idu mutumin garin Raba ne asalin su fatakene sukanje fautaci gari gari anan ne Allah yaha dasa da salame sunana da ake kiranta kenan jinisu ya hadu sosai Dan ita yar dagacin garin Damagara ce kuma duk bako a gidansu yake sauka suke basa masauki anan me Allah ya hadasu har aure ya shiga duk da dagaci. Baisoba a cewar sa bayason ya baiwa.bako yar sa Dan su danginsu auren dangisukeyi haka salame ta dage sai sa'idu aka wanke aka kaita garin raba duk da sun raina da arxikin sa'idu haka suka baro yar uwarsu suka koma damagara haka kuma rayuwarsu takansance itada masoyinta gwanin sha'awa malan sa'idu marayane su biyu mahaifinsu ya haifa malan sa'idu shine babba sai mai bi masa atine wadda bayan haihuwar tane mahaifinsu yarasu duk nauyin gida yadawo akan Maman sa'idu duk da lokacin. Bai wani girma ba sosai atine na karama itama haka dai sukaci gaba da rayuwa yau da dadi gobe da ciyo har Allah ya tashi kafadarsu Atine kuma tayi aure ta auri Habu Wanda shi a birni yake zama da akayi aure yadauki matarsa suka koma can da zama sai dai insunxo ziyara

Haka rayuwa tasance gwanin sha'awa salame da sirikarta bamai jin Kansu har aka wayi gari ta haifo santaleliyar yarta mai ban sha'awa kowa sai santin 'yar yake kamar kasace ka gudu daranar suna ta zagayo aka saka mata Rukayya sunan mahaifiyar Maman Sa'idu suna kirantada 'yar baiwa kasancewar Allah yamata hkr tun tana karama batada hayaniya ko wanason Rukayya haka ta taso cikin kulawa ga takwararta na sonta bataso taji kukanta ko wasa ake aka doketa yanxu nan zakaga Baaba ta daura ta yafa wai sai taji mafarin dukan yar lelenta abinka da yara kowa shakkar taba Yar Baiwa yake Dan kar yajaxama kanshi mita a wurin Baaba Dan har gidansu mutun takanje idai game da yar Baiwane

Luv u all my fans
Maman ussee




=╪N▐ 'YAR BAIWAH=╪N▐5у
Maman Usman

Haka suka ci gaba da ratsa sabara har suka cinma titi sukaita tafiya tun Rukayya na kallon gari gari har ta gaji tai Bacci tasake farkawa kuma basu kaiba.

Ai kuwa basu suka isa garin sokoto ba sai misalin karfe 6 na yamma suna isa suka dauki hanyar arkila federal lowcost adai dai saitin wani gida ma dai daici yayi faking kamin nan ya umurci Rukayya data fito bayan ta fitone ya bude both ya Ciro mata yar Jakarta ya CE shiga mana ai nan gdnku ne ta dauki jakar ta shiga cikin gdn shi kuma ya bude get yasaka mortar a cikin gida San yabi bayan Rukayya.

Da sallamar sa ya shiga cikin gidan yana kwalawa Atine kira maman sajeeda maman sajeeda kin gammu sai yanxu ko oyoyo Abba cewar Abdallah yaxo da gudunsa mahaifin nasa yadaga sa sama yana dariya sweet boy ya ina mamanku da Auntynku suna kitchen cewar fadil daya fito da niyar zuwa masallaci ya gaida Abban nasa yaja hannu Abdallah suka wuce Atine tazo ta rumgumeshi sannu da zuwa my Dear kunsha Hanya ya INA yar tawa banganta ba au ai na zata tashigo tin dazufa nace da ita tashigo Dan zanshigo da mota kila ko bata gane kofar bane oho bari in dubota daga nan na wuce masallaci da an fara kiraye kiraye ko ta amsa da to.

Yar Baiwa kuwa tunda tashiga gidan takasa gane hanya kawai sai kalle kalle take ta Shafa nan ta taba can tanata mamakin ikon Allah can dai ta tsaya a wurin flawers tanata mamakin wai yau itace a birni muryar mutane datajine ya fargar da ita sai ta kewayo ta Inda ta biyo daga farko Rukayya INA kika shigane ko baki gane hanyar bane ta sadda kanta kasa shima murmushi yayi ya ja hannun ta ya kaita har cikin gidan kamin ya koma zuwa sallar magrib,

Yarta barka da zuwa ya su yaya da Baaba ta amsa suna nan kalau sunce na gaidaku harma da abu akace na kawo muku tau Rukayya bari yanxu kiyi sallah sai kiyi wanka kici abinci kinji ko bara na kira sajeeda taje dake dakinta saita nuna maki komai kinji ki saki jikinki kinji nan ma gidankune munan iyayenkine ki daukini a matsayin ummanki ki dauki Abban Abdallah a matsayin mahaifinki bakida matsalar komai kinji ta ammasa da to,

Kallon falon ta farayi Wanda aka kawatashi da kujeru masu kyau sai kayan kallon da dining area sai kuma dayan gefen store da kitchen sai dakin yara dake kusa da store gefe daya kuma room& falor ne sai dakin me gidan dake kusa da na sajeeda cikin kankani lokaci takarewa gidan kallo a ranta fadi take aljannar duniya dankari Ashe akwai ire iren wadan nan Abubuwan more rayuwa haka tab gaskiya maganar hausawane da sukace nazaune baiga gari ba.

Murya Sajeeda CE ta dawo da ita a duniyar tunanin da ta Lula yar uwata zomuje kiyi sallah kinji ta amsa da to yayinda tabi bayan sajeeda dauke da Jakarta a ka suna shiga dakin wani sanyine ya doki fuskar Rukayya tare da daddadan kamshin air fresh sajeeda taja hannunata sukashiga bayi ta muna mata komai kamin nan ta fito ta barta me Rukayya zatayi inba sake baki ba ta fara tabe tabe ba abinda yafi Jan hankalinta irin gani. Kanta datakeyi a mirror sai murmushi take can dai sajeeda taji shuru ba labarin fitowar ta gashi ita har ta gama sallah amma Rukayya. Bata fito. Ba ta kwankwasa kofa yadai Ruky naji ki shuru koda matsalane a San nan ne yadawo haiyacinta ta tuna nan wai bayan gidane ta kunna tap tayi alwala San nan tafito tana fitowa sajeeda ta bata sallaya da hijab ita kuma ta fada toilet Dan tahadawa Rukayya ruwan wanka.

Bayan ta kamala sallah ne sai ta karewa dakin kallo ba komai bed ne kawai sai drower sai dressing mirror ba laifi kam gidan ya tsaro sosai bayan tayi wanka ta fitone sai ta Shafa mai kawai sajeeda CE tabata. Body spray tashafa Dan sajeeda akwai son kamshi zata girmi Rukayya kadan Ruky cewar sajeeda kidaukeni a matsayin yar uwarki kuma kawarki nasan bamu wani saba ba Dan ko munje can Raba ba wani dadewa mukeba su mummy sun muna bayanin komai bakida wata matsala kiyi sallar isha sai muje muci abinci kinji =╪
▐ murmushi tayi hadi da yin sallah tana idawar itama sajeeda sallar tafara yi bayan takammala ne suka fita tare suka fito zuwa wajen cin abinci anan suka tarar da iyayesu har sun fara cin nasu sai Abdallah ne yace daddy wan nan CE new Sister dinmu ko ai na Santa a Raba take itace Baaba take cewa yar Baiwa ko aikuwa kowa ya fara dariya kai son ka cika surutu dayawa eah sunanta Rukayya daga yau sister Ruky kunjiko fadil yes momi suka amsa Abin yabaiwa yar baiwa sha'awa a ranta tace lallai inbaka mutu ba zakasha kallo haka akaci abinci cike da raha ana kamalawa sai kuma aka fara labarai anan ne kuma Daddy yafara yiwa Rukayya tambayoyi. Ba laifi tasan wasu wasu kuma bata amsawa sai kuma fadil da Abdallah suka CE su bacci sukeji Sajeeda ma taja Ruky sukabar mummy da daddy a falo.

Daddy yanisa gaskiya da ace Baaba bata amince ba da an cuci yariya kinga yanda takeda brain kuwa Dear Mummy tayi murmushi Allah dai yabamu ikon rike amana ameen ta amsa nimafa azo asan yanda za'ai dani Dan ah gajiye nake ya kashe mata ido daya ta murmusa da tasan halin Mijin nata,

A bagaren su Sajeeda kuwa banda tadi ba abinda akeyi sun Dade suna fira kamin nan su kayi addu'a suka kashe wuta suka kwanta Rukayya kam godiya takeyi ma Allah wai yau itace a. birni dasunan boko.

Muje zuwa kuna tare da Zeenat Yusuf maman ussee


=╪N▐ 'YAR BAIWA =╪N▐6у

Maman ussee

Tun da asuba mommy tashesu daga bacci Dan su yi sallah bayan sun idar ne kuma suka sake koma wa bacci kasancewar week end ne ba makaranta,
Basu suka tashiba ba sai kusan 10:am wanka suka farayi kamin nan sajeeda ta ja hannun yar uwartata domin suje cin abinci Dan tasan yanxu kowa ya tashi dayake al,adar gidan ne atare ake cin abin suna fito gaida iyayensu sunka farayi kamin. Nan Abdallah da Fadil suka gaidasu suma mommy CE tace 'yata bawata matsala saiki Rukayya tace ba komai insha Allah daga nan kuma akayi saving din kowa yafara cin abinci amma banda Rukayya dantakasa cin abinci itasam bata saba dashi ba tafi son dumamen tuwo ko koko da kosai ko waina amma INA ita in cin wan nan kwamacalar,
Daddy ne ya kula da ita sai yakira sunanta Ruky ya.bakya cin abinci ne ta sadda kanta kasa cikin in INA tace a gida koko nakesha ko dumamen tuwo ai ko mexasuyi inba dariya ba Mummy CE tace ki Dan Dana mana kiji ai da dadi inbaxaki iya shaba to kici doyar mana tadai daure tayi spoont daya na damar miyar typeyocer din ai kuwa saita hau sha Sajeeda dariya kawai take kasa kasa ,

Bayan sun kammalane daddy yace dasu su shirya aje islamiya yaushi da kansa zai kaisu Dan ya mika Rukayya nan danan kowa yahau shiri kowa tafito cikin uniform din Islamiya Daddy yafito suka fice gabaki daya mommy kawai suka bari agidan,

Abakin get yayi fakin yayinda su Sajeeda suka nufin classes dinsu shi kuma ya nufi office din malamin makarantar yaga batar da Rukayya a matsayin daliba akayi mata tambayi ba laifi kan Dan ko a can Raba tana zuwa makarantar allo bayan an kamla aka bashi takarda yasa hannu yabiya kudi sai suka CE yakoma da ita gobe sai ta fara zuwa kuma da uniform suka sake fadamai dokokin makaranta yayi musu godiya ya ja Rukayya suka tafi a mai makon subi hanyar gida sai taga sunbi wata hanyar mexatayi in ba kallo ba ido ya samu abinci dai dai wata yar plaza taga Daddy yayi parking yace ta jirasa batasan meyaje yiba bai jimaba sosai taga yadawo da Iedoji biyu a hannusa ya. bude set din baya daba kowa yasa su a ciki sa,ilin da yadawo yatada mota suka nufi hanyar gida,

Mummy suka tarar harta kammala komai na gyaran gida da Inda sukaci abinci sannu da aiki mommy yara ga kaya nasiyowa Rukayya da yadin uniform saiki bada dinki ayimata iri biyu iri. Nasu Sajeeda Dan gobe zata fara zuwa sauran kayan sa wane nixan fita sai nadawo aff ana manta kinsandai makarantar Boko suna jarabawa ne sai nadawo Hutu zan kaita zadai aci gaba da koya musu extra lesson kamin da dawo hutun Dan naga ba wani Hutu mai yawa bane murmushi tayi hadi da yimasa godiya da fatan alkhairi,
Rukayya kuma tana zaune ta kurawa TV Ido ko kyabtawa batayi mummy ta dafata tace muje kitayani gyaran daki sai mu Dora girkin rana Dan su sajeeda sai 4:pm zasu dawo ta fice yayinda Rukayya ta rufa mata. Baya tana nuna mata abubuwa da yakamata ta kula dasu wan nan kenan,

A cikin yan kwanaki n da tayi a gida. Bata fuskantar komai sai farin ciki ga soyayya da yan uwanta ke nuna mata suna debe mata kewa sosai sun shaku da sajeeda inka gansu gwanin sha,awa komai tare sukeyi Dan ko a Islamiya tare suke komai sajeeda itace take koya wa Rukayya wasu Abubuwan da bata gane ba cikin sa,a kuwa da am fada ta rike shikenan malamansu har mamakin irin Baiwar da Allah yayiwa Rukayya suke gashidai bawani dadewa tayi ba amma inka ganta saika rantse ta shekera a cikin islamiyar gida kuma ga lesson ana musu badama tana kawo wuta sosai Daddy yasan bayada haufin inya kaita skull za,a sakata aji daya da Sajeeda dayake ita jss 2 take, Tun tanajin kunyar saka wando da Riga harta saba Dan kuwa yanxu Rukayya ta goge dama can ita kai waye ne da ita batada matsala in basuda lesson itada Sajeeda suke taya mummy aikace aikacen gida dayake anyi Holiday.

Maman ussee=╪▐ Ina Alfahari da Ku my fans


=╪N▐ 'YAR BAIWAH =╪N▐7у
Maman Ussee

Haka Rayuwarsu taci gaba da kasancewa gwanin sha,awah har holiday ya kusa karewa yau ya kasance Sunday kowa da kowa na falon gidan anata firar duniya gwanin dadi fuskar kowa cike da annashuwa da anuri Abdallah ne yace Daddy gobe Holiday zai kare kuma kasan kamuna alkawarin zaka mana shopping yau ko Fadil ya amsa eah little bro Mummy tace harda ni kenan za'aje shopping din Daddy yace OK to Ku shirya sai muje tare kunji yes Daddy suka mike Dan shiryawa Rukayya an zama yan gida yanxu kowannen su yafito cikin shiri Rukayya da Sajeeda jalabiyace a jikinsu dark blue sukayi rolling abin yayi kyau fadil da Abdallah kuwa Riga da wandone suka sa mummy itama Doguwar rigace ta shadda taji kwado kai familyn fa sun birgeni haka suka fito suka shiga mota Mummy dasu Sajeeda a Baya fadil da Abdallah a gaba asu zarce ko inaba sai a Zabira shopping mall nan kowa yayi ta zabar abinda yakeso Rukayya dai kasa daukar komai tayi Dan ita kunya takeji Sajeeda CE kedaukar komai Biyu inta dauka saita daukar wa Ruky bayan sun karene sukaje wurin bill akayi bill Daddy yabiya suka sake fitowa kowa sai kallon su yake nusamman Ruky da Sajeeda kamar yan biyu ba karya Allah yayi Halitta Dan ko Sajeeda ba bayaba a fagen kyau, Daddy bai zarce dasu ko,ina ba sai Daddy's smart anan sukaje suka ci abinci suka zaga gari sosai kamin nan suka dawo gida.

Gab da magrib suka dawo zubewa sukayi a fallo kowa ya gaji Dan yau sunsha yawo sun more sosai gsky bayan su hutane Daddy yaja su Fadil da zuwa masallaci Mummy kuma ta wuce zuwa dakinta yayinda da umurci su Sajeeda dasuje su yi sallah suma kuma su shigar da kayan ciki haka suka kwashi kayan zuwa Inda yakamata su adanasu. Bayan sun idar da Sallar Isha suka fito bayan aka ci gaba da hira can Daddy Yakira sunan Rukayya, Rukayyatu ki shiryafa gobe zaki soma zuwa skull insha Allah saboda haka saiki shirya kinji murmushin jin dadi tayi yayinda da ta CE nagode Daddy Allah yakara girma bakomai ai kidage dai kinji ko to 'ya ' yan Daddy aje ayi bacci saboda a tashi da wuriko kunji yes Daddy af na manta Ga uniform din Ruky can a bed dina Sajeeda jeki kidauko mata gobe sai a shirya da wur wuri kinji tau Daddy bakida wata matsala Rukayya. Nariga nayiwa principal magana interview kawai za a maki su zasu baki komai da komai saboda haka kidage kawai inkiyi kokari za a sakaki class daya da 'yar uwarki Sajeeda tam ta amsa suka fice dakin su kowa yayi addu'a ya kwanta yayinda 'YAR BAIWAH take farin ciki sosai mafarkin ta yakusa yazama gaskiya.

Maman Ussee


=╪N▐ 'YAR BAIWAH =╪N▐ 8у
Maman Ussee

Monday morning tun 6 suketa shirye shiryen zuwa skull Sajeeda CE ke nunawa Rukayya yanda zatasa kayan skull din ,kai gsky fa kinyi kyau tawan kinga yanda skull uniform din nan suka karbeki ta kashe mata idon daya Ruky ta kaimata duka ta goce suka fito falor sunata dariya yayinda su Fadil ma su. Shirya tsaf Daddy kawai suke jira bai wani jima ba ya fito sanye da kayan shi dagani shima aiki zaije daya aje yaran, ba bata lokaci Mummy tai musu addu' a suka fice dukkansu suna daga mata hannu,

Bayan sun shiga mota Daddy ya tuka zuwa skull din dake dai dai Bafarawa east, garin yacika sosai da mutane kasan cewar yau Monday masu zuwa skull na fita yayinda masu zuwa aiki ke kama ga bansu da zuwa aiki kai tsaye daddy cikin makarantar ya danna motarsa wato KEY SCIENCE ACADEMY, bawani bata lokaci Sajeeda dasu Fadil suka nufi assembly yayinda Daddy ya nufi principal office da Rukayya bayan yagabatar da ita a fadamai rules din makaranta ya amince kamin nan aka bashi takarda

Please Login or Register in order to submit comment