Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yawa yake da gani kasan ba Basira a Nan an toshe min ita.

To Rumaila ko kin warke ko Baki warke ba Oho,nace Ni dai Ina Jin na warke Iya tunda naji canji a jikina sayau nake jina lafiya Lau,a daure a karasa maganin kaf,nace to,Ni yanzu fushin da Fu'ad keyi Dani shine damuwa ta,nayi Kiran duniya na tura text Shuru,na bashi Hakuri a text Amma yaki magana har na hakura na zubawa sarautar Allah Ido,damuwa Kam Ina cikinta.
Su Umma duk Ina Basu labarin magani Abun da mamaki Ashe har da Iya a ciki shi yasa malamin yace ayi maganin a garin,shima Malam Abbi ya sanar masa komai yace Inshaallah idan ta Gama ko jifa ko Shafar Aljanu ita da su sunyi Hannun Riga,Shima Mijin nata Haka.

Yau Sunday Yar kawar Momy ta sauka gidan da Trolley dinta katuwa tana ja,Yusra kenan ansha gayu anzo za a tallatawa Fu'ad Kai ko za a samu shiga,Ni Kam na Matsu na dawo Abuja na bawa Fu'ad Hakuri,na gaji da Rashin sa,shima ya kasa jurewa sai ya dauki waya zai kirani sai ya fasa,idan ya fara rubuta min sako sai ya goge ya fasa.

Ni Kam tun Ina zuba Ido har na hakura Nima Kawai,har na Gama maganin kaf ya Kare,Iya Tace to sai ki fara shirye Shiryen tafiya Zan sanarwa Umma sai muje mu maida ki gidan, Iya ce ta dinga bani kayan tsumi na Mata Ina amfani da su sosai,har kiba nayi da kyau sabo da na samu lafiya gaskiya ko a jikina garau nake ji na,Umma Bata fadawa Fu'ad Zan dawo ba sabo da tana Kallonsa duk ya rasa sukuni,Fara'a ma ya daina,Yana cin Abinci Yusra tana palon Umma tana ta kallon Fu'ad da kallo irin na so, Umma ta kalli Fu'ad sai juya cokalin yakeyi ya kasa cin abincin Tace lafiya dai ko? Tsaki ya dan ja tare da furta lafiya Lau Umma,Umma Murmushi tayi Tace ko Kai da mutuniyar taka ne? Yusra ta tabe Baki Tace yo Dama Allah na tuba auren Yara Yan 16-17 ai masifa ne,Umma ta kalle ta kawai,tashi Fu'ad yayi ya bar palon ya Fisgi mota ya bar gidan zuwa wajen abokansa gidan Khaleed,su Khaleed sunga kwana biyu kullum a damuwa yake ko sun tambaye shi baya fada musu dama sun San shi da zurfin ciki.

Ni kuwa Bayan mun Gama duk wani shiri Iya,Affa da matarsa,Kawu Haruna da Yar Uwar Iya Yafendo,sai Aunty Rukayya da Haleesa yarta Muka tafi a mota Sharon Drop na daukar Mana karamar mota Amma me cin mutane da yawa,atamfa na sa baka me adon golden,takalmina Goldin me Dan tudu da jakata me tsada kayan Lefe nace ban taba sata ba sai yau, Umma da Abbi sun San da zuwanmu,duk munyi shiga me kyau ba Wanda zai wulakanta mu,Iya a Hanya Tace bazanyi ko gyangyadi ba Ina kallon gari abina,Ni nasan gidan nice jagora,sai wurin 4pm Muka karasa gidan,Direct Tace na wuce da su masaukin Baki,Su Affa duk zaucewa sukayi da ganin gida irin wannan,Iya Tace Uhmmm kudi suna magana da kansu a wannan gida,ai sun zarta yanda nake zato Rumaila,ko dai ya taba yin shugabansa ne me gidan? Nace a'a,Iya tace to zallan Iya kasuwanci ne Haka?Kai gaskiya Ina yinsu Iya wuya ko Dan kudin Nan Ni sun Gama Dani,Affa yace me Hali baya fasawa dama ciwo ma Yana tadda Hali sai ya Dora daga inda ake,Allah yasa babu kowa sai masu Aiki a compound,Ta garden nabi dasu,Iya Tace kaga guri Kore Shar shi yasa idanuwansu farare tas to kullum Ana zuwa a kafe shuke shuke da Ido ana Shan Madara Ana kallo Ana gyangyadi.

Iya ta sake cewa wannan ma'aikata Haka Kamar gidan sarauta Kuma duk biyansu akeyi? Nace ae,Iya Tace ai kuwa gasu Nan Bulbul dasu,Kawu yace a koshe suke ba yunwa wallahi,Affa yace ku ai Baku zaga duniya bane Amma Ni Dana Yi zaman Lagos na Saba da wannan,Yafendo Tace to sarki Shugaban wayayyu,Matar Affa Tace gaskiya mu nutsu,muyi Ubanki idan mun nutsun da hauka mukeyi ba a nutse muke ba? shegen Baki kamar bututu cewar Iya,Ina ta dariya sai da na zage gidan Nan da su kaf gida gari Guda Suka Sha kallo,Kawu Haruna yace gidan Yan gayu kowa yayi luf a bangarensa,da mune kuwa Yara na ihu,can suna Wasan kasa,can Ana dambe ga mahaukatan samari,To sun koshi me zasu Yi cewar Affa.
Sai Dana kaisu masaukin sannan na gwada musu yanda ake amfani da toilet da sauransu na nuna musu gabas,bayan munyi Sallah kowa ta ajiye Jakarta a Bedroom,Yafendo da Iya,Matar Kawu da Aunty Rukayya da Haleesa,Affa da Kawu na Nuna musu nasu wajen a kebe, Wanka Muka Yi kowa ya huta,na Kira wata me Aiki ta kawo musu abinci Iri iri Dama Umma ta Gama komai,Iya kasa magana tayi tagumi Kawai ta zuba.

nace Iya lafiya? Kudi Rumaila suna magana a Nan gidan,Hhh Dariya Mukayi, tare da su na zauna Muka ci abinci kowa ya nutsu, Ina yin wanka Na canja wata sabuwar Abaya Golden ce ta hadu karshe ga tsada kamar zanje party,Powder na shafa da lipgloss na fito wani fes Kamar daga Engine aka fito Dani na fita a kayan,turaruka na shafa sama sama masu dadin kamshi,Takalmina da handbag Dina na dauka Ina tafiya a nutse na taka har part din Umma.

Sallama nayi Fu'ad ya juya baya Yana Shan ruwa a glass cup da Remote a hannunsa,yaji muryata nayi Sallama zo kuga saurin juyowa wajen Fu'ad,Ido Biyu Mukayi ya kafe Ni da Ido Yana kallona Nima Haka Ina murmushi na Shiga ciki,sallamar ya amsa Bai ma Sanda ya amsa min ba duk fushinsa sai ya neme shi ya rasa,Ina yini Yaya Fu'ad na Furta kallo na Kawai yakeyi kamar zai hadiye Ni Bai amsa ba,Wucewa nayi da sauri Zan haura saman Umma ya riko Hannu na da sauri,na fisge Hannu na nayi sama,Sallama nayi Umma tana daga ciki Tace Rumaila shigo Mana,Shiga nayi Muka gaisa Umma Tace wannan Irin gayu Haka Rumaila kin samu lafiya kinyi wata Yar kiba Dariya nayi Ina Jin kunya na durkusa tare da gaisar da Umma ta amsa tana jikin mirror tana gyara daurin dankwalinta ta atamfa super,Kinyi yanda nace ko nace ae Umma sun Gama komai ma ke Kawai suke jira, Fu'ad ne ya shugo dakin,Umma Tace da su Iya fa suke suna bangaren Baki kaje ku gaisa, Fu'ad yace to zanje Amma ke Umma fara zuwa zamu zo daga baya,Umma ta Gane shi tsaf Tace to da Rumailan zamu tafi ai, Fu'ad ya Bata fuska yace Umma Wai me nayi Miki ne? Share shi tayi ta Mike ta yafa Mayafin ta fita na bita a baya ya rike Hannu na kam,Mur na Sha nace ka sake Ni na tafi Mana,Yace kwace ki tafi Mana idan Zaki Iya,Ba yanda banyi ba Amma na kasa kwacewa,yace Zaki dawo baza ki fada min ba? Kana daga wayata ne? Ko idan na tura maka text kana gani? Ni Dana dinga kiranki kin San an hanani zuwa Garinku kin dauka ne? Wanne wulakanci ne Baki min ba Dan Kinga na damu dake,Baka San bani da lafiya ba lokacin?na fara magani Ina ta rashin lafiya ai baka tambayi dalili ba,ai sai ki fada min Baki da lafiya ko a text,ince bani da lafiya ka zo garin Kuma bayan Umma sunce karka zo,Shuru yayi Yana Bina da kallo yace ban sani ba ai Fushi nake Yi dake I'm so sorry,ya jikin? Ai Naga kiba ma kika Yi ke kina ta Kara kyau kullum,Naji su Iya ma Ashe harda su Salahu ya hada Haba shi yasa abin akwai mamaki Ashe ba yin kansu bane,nace Uhm Allah ya taimake mu,yace naji dadin hakan,kin barni Ina ta Shan wahala Ni daya duk na rame,Dariya nayi nace Ni banga ka rame ba,Kiji Tsoron Allah Baby nace to Ni dai banga ka rame ba kiba kayi ma,Yana murza yatsu na a hankali yace muje to wajen su Iyan tamu, Rungumeni yayi sosai a jikinsa,Nima na kankame shi zai min kiss na zille Muka fita,Mun sakko Kasa Naga Bakuwa Yusra ta Sha gayu an hakimce Ana canja Chanel da Remote, Fu'ad Yana rike da Hannu na Muka wuce Yusra,Yusra ta kafe Ni da Ido sai ta Raina kanta Kuma,ko kallonta Fu'ad baiyi ba Nima ban kulata ba haushi ma ta bani ta wani fito da kirji Ana hango shatin Breast dinta,Nace Wannan fa itama Yar gidan Nan ce? Yar kawar Momy ce tazo hutu Wai yace,nace Kuma shine take wannan abin kamar gidan Ubanta ita Wai balagaggiya zata ci Ubanta ne Bari na dawo wajen Allah yasa ta kulani ko ta min Shishigi sai dura mata ashariya,gantalalliyar banza Haka akeyi kizo palon mutane ki saki jiki wani sharab taje can wajen Momy din mana, Fu'ad Yana jina Ina ta masifa har muka karasa wajen su Iya na kwace Hannuna Muka Shiga da Sallama.

mun Iske Abbi da Umma,naje kusa da Iya na zauna,Iya ta kalli Fu'ad Dake gaida su harda rusunawa,Iya Tace dama kana gidan ne? Yace ae Iya,Umma Suka ji Hira ta barke tsakanin Iya da Fu'ad,ya Iya biyewa Iya.
Iya Tace yaro ya bayan saduwa?ya akaji da mutuwar Nan ta zamani ta farar daya? Fu'ad yace Alhmdllh,dan kuwa ita ake fama yanzu wannan yanzu zakaji an kwanta dashi lafiya sai a tashi sai dai gawarsa,Iya Tace wallahi fa Kawai mutane a koma ga Allah yau mune gobe ba mu ba,wani Haka Rannan Dan makwafci na a gona suna noma Kawai sai gani akayi ya fadi,aka zo Kansa Ana Haladu Haladu Shuru kake ji Ashe har mala'ikan zare Rai yazo ba a sani ba, Fu'ad yace da Iya Eyyya Allah ya Masa Rahma Iya Tace ameen,ai Mata suna cikin wani Hali musamman Yan Mata Ana ta tsince mazajen Daya Bayan daya, Fu'ad yace Wanda sukayi saura sai su dinga auren Uku Uku biyu biyu hudu hudu,Iya Tace Kai Dan Nan Uwaka Fu'ad da 'yata a ciki bance ba to,Dariya aka dinga a palon Har Abbi da Umma Iya Bata so ayiwa yarta kishiya.

Iya sai ta daina zancen mutuwar mazaje ta koma wani zancen,Tace Fu'ad Ashe Haka Allah ya wadata ku? Dariya yayi yace Iya Ina ta fada Miki idan kin ganni Kinga kudi kika ki yarda,Iya Tace na yarda yanzu Naga zahiri Ina garin Nan sai ka cika min Alkawari na anyi min jiniya da motoci yanzu fara kunna min kallo ga Tv, Fu'ad ya kunna katuwar Plasma Chanel din Ball akeyi Wato kwallon kafa Ana ta Kokawa,Iya Tace Kamar zaka dakko mutum da Allah ji garau Kamar na shige ciki.

Yan Ball Ana ta Kokawa tace kayyasa Kai maza kauce Nan to Dan Ubanku Wai a Basu kwallon da yawa Mana kowa ya dauki tasa Dan jaraba akan kwallo Daya zaku kashe kanku,Da yatsa Iya ta nuna wani bature da Alama shine couch Iya Tace Kai Dan Ubanka ka zubo musu kwallaye da yawa kowa ya dau tasa banza dakiki,Dariya muke tayi Iya taga wani yaje har Gaban raga ya kasa ci,Iya Tace Amma wannan yayi asara ku cire shi,Haka akeyi Dan Ubanka ko Ni naje Gaban raga nayi wannan bugun, Fu'ad kaga wani buga kwallo Dan Allah wani shafal Shafal....aka nuna wani siriri Iya Tace da ganin wannan baturen matarsa Bata bashi abinci Yana koshi banza Mijin Tace,Fu'ad yace kamata yayi a daina biyansu Albashi,Iya Tace wallahi kuwa musamman wannan masu fararen kayan,kaga wani dai wannan da gani bazai tarbiyya ba,wannan Uwarsa da Alama fama takeyi da shi,wani ma yaje ya samu dama Amma ya kasa cin ball Iya Tace Dan Allah canja Mana Tasha wannan ba Yan kwallon kirki bane duk jakai ne,ko Ni na samu damar wannan sai na zura kwallo a raga,Dariya Mukayi.

Fu'ad ya Kai American film Ana ta harbi Kawu yace yawwa bar Mana Nan,Iya Tace karyar zaka kalla kai Canja min Tasha, Fu'ad ya kamo Hausa film Iya ta gyara zama Tace yanzu Naga dai dai,Umma ta kalla tace Ina abokan zaman naki Basu zo mun gaisa ba ko bakwa zaman arziki ne mu shirya cin ubansu muma? Umma Dariya tayi Tace haba zasu so ne,Abbi yace ai na Kira su,Suna Haka sai ga Momy da Mama tare da Yan matan su harda Yusra suna Yanga,Momy tana yatsina Kamar taga Kashi,Iya a ranta Tace lallai za a yita sai na tabbatar na gyara muku Zama zaku ci Ubanku,a fili kuwa Iya Hijab dinta ta gyara, Abbi tashi yayi ya tafi abinsa, Fu'ad yace Iya yau Zan tafi dake yawo,Tace na gode Dana ai nasan baza ka bani kunya ba,Zama su Momy sukayi Mama ta ja tsaki,Iya tana jinsu Amma ko kallon inda suke Iya Bata Yi ba,Momy Tace barkanku ya Kauye?,Babu Wanda ya amsa bare tasa Rai za a kulata.

Mama Tace ya Ana magana Kuna Jin mutane,Iya ta kalleta shekeke Tace au damu kuke ne?Affa da Kawu Mikewa sukayi Suka koma bangarensu Suma ko kulasu Basu Yi ba, Fu'ad ba karamin farin ciki yaji ba da su Iya Suka Yi Haka,Rukayya da Haleesa Suka Mike tare da cewa Bari mu huta daga ciki Suka Yi bedroom,saura Iya da Yafendo da matar Kawu sai Kuma mu da su Momy,Umma ita kanta su Iya sun birge ta,Tsaki Momy taja,Iya a ranta Tace zanyi maganinki Bari na warware daga bakunta, ta Mike da matar Kawu Suka Yi ciki,Umma ta tafi Itama, Fu'ad Hannu na ya rike Muka Yi waje muma saura su Momy su daya da su Khaleesat,Naila dama tana Kano ita,Momy Tace kan uban Nan Kinga Yan Kauye? Mama Tace kyale su zasu ga wulakanci sun zunguri sama da Kara,Umma Su Iya kaf matan ta tafi dasu bangarenta a can Nene ta same su Suna kallo.
Ni kuwa Fu'ad ja na yayi part dinsa na gidan ba kowa a ciki,kullum Ana gyara part din ko Ina Neat.








Masu Sharhi Ina matukar Godiya.



AsmaBaffa
[7/13, 8:42 AM] Sis Asma: 🎈🎈🎈🎈
DANGIN RABI
🎈🎈🎈🎈







NA KUDI NE

WACCE TA FITAR DA SHI ZUWA WASU GROUPS DA WACCE BATA SIYA BA TA KARANTA ALLAH YA ISA.












DANGIN RABI IS DEDICATED TO AIDA MAMAN TASNIM







86-90










Official








By
AsmaBaffa











Page naku ne

Auta
Mmn Ummee
Aeesha
Dr Zainab Abdullahi
Alhusnah Mrs Idris
Balkisu
Ummu Arfat
Farhat Mrs Mj
BK
Basmam Glam
Muneerah










A palon na tsaya Ina Kare Masa kallo Wani Yadi ne a jikinsa ruwan Zuma me tsada yayi kyau,Saman 3seater Muka zauna,kallona Kawai yakeyi ya zuba min kyawawan idanuwansa,Kunya ce ta kamani na murguda Masa Baki tare da dauke kaina daka Kallonsa Ina murmushi duk na rasa inda Zan sa kaina sabo da kunya Kuma da farin ciki yau Ina kusa da shi,Hancina na Sosa tare da shafawa,Duk Bai dauke idanunsa ba,Mayafina na gyara sabo da rigar wuyanta me wani raga ne naga kuma shatin Albarkatun Kirjina sun Dan Yi Showing,Mene Haka ya Furta tare da bankade Mayafin ya maida shi baya, Dan tashi na gani ya Furta nace Sabo da me? Umarni na bayar yace Yana kashe min Ido daya,a kunyace na Mike tsaye na Danyi Taku biyu na juya na juyo sannan na zauna s kunyace,yace dama Haka kike? Nace me? Da sigar Rada yace kin hadu,Labbansa na karanta Kawai,Hannunsa ya saka cikin Nawa tare da shigar da yatsunsa cikin Nawa saman Cinyarsa ya Daura Ni tare da zame Mayafin Nawa Gashina da yasha gyara ya warware Yana shafawa,Gashin ya tattara tare da hade shi a hannunsa ya maida shi Bagare daya ta saman kafadata ya Shiga bin bayana da kiss,juyo Dani yayi a cinyar tasa Muna facing juna Bakina ya laluba muka fara Kissing kamar zamu kashe kanmu.

Munyi nisa mun Lula wayarsa tayi Kara Yana ganin Umma yace to fa ya daga kiran Ina Rungume a kirjinsa Wanda da sai da ya saita Muryarsa sabo da tana rawa,Yace Umma Tace turo min Rumaila yanzu akwai abinda zata Yi, Fu'ad dama yasan abinda zata ce kenan,Gani nayi ransa ya baci ya canja lokaci daya,Nace lafiya? Lfy Umma ke neman ki,Hannayena na sakalo ta wuyansa nace shine kake fushi? Shuru yayi,Murmushi nayi nace Kayi Hakuri komai zai wuce soon,Kiss na Shiga manna Masa a jere na gangaro tun daga goshinsa zuwa kumatunsa na sauka a lips dinsa.

Rigata ya gyara min ya gyara shima kamar bamuyi komai ba Sannan Muka fito a tare muna Hira,Yusra ce take leken mu ta saman Momy tare da Farida ko me suke cewa oho, har part din Umma muka Shiga Umma tace zo muje kitchen,Binta nayi Fu'ad ya zauna kusa da Iya, Fu'ad yace Iya yaushe Zaki ga gidana Ni? Iya Tace au Wai ba a Nan gidan sashen Rumaila yake ba Wani gidan ne daban naku? Fu'ad yace ae Baki sani ba? Iya Tace kan Uba lallai Allah ya yarda,Ashe mu muna Kauye Muna karbar Kebur (Cable) Zane mu Kawai akeyi da Kebur,Fu'ad Yana murmushi Ana labarai aka nuna kasar Switzerland Iya Tace wannan wanne gari ne haka? Fu'ad yace Switzerland kenan Iya a Nan ake buga kudade har na Nigeria,Iya Tace na rike sunan,wannan kasa abar zuwa ce Ina son su,shegu sai sun Gama kwashe kudin su Aiko da ragowar kasar mu,ga Inda Yan Kidnapping zasu je can su dinga dauka ba ruwansu da ciniki ko Nawa Suka fada Basu za ayi hankali kwance.

Iya Tace Amma gobe zaka kaini yawon ko? Fu'ad yace Inshaallah,ganin Iya ta kankane Rumailan tasa sai Kawai ya Dan fita compound daga can ya wuce masallaci sai da yayi Sallar Isha sannan ya dawo lokacin naje zanyi Sallar Nima naga na fara period ma gashi Banda pad Kuma kunyar Umma nake ji,Wayata na jawo a saman Mirror na Kira Fu'ad,Yana dagawa nace kana gidan Nan ne? Yace ae Ina part din Abbi,Da Shagwaba nace yanzu naga na fara period Kuma bani da pad ko daya,Wani haushi da bakin ciki ne ya lullube Fu'ad yace Innalillahi Ni Kam na Shiga Uku Kawai a kaini kabari a binne Ni na huta,Wai kwana Nawa ma kike Yi ne? Nace 3days,Yanzu har 3days Ina laifin 1-2 days ma,kice Umma ta baki,Ni kunyar Umma nake ji Kawai kaje ka siyo min,Da Kansa ya fita Kofar gida kusa da gidan akwai wani Chemist katon gaske a Nan ya shiga,Yace pad nake so me kyau,yace ga wacce take hade da Maganin Infection,ita ya siyo me tsadar kana gani ba sai an fada maka ba, a Bedroom din da nake ya shigo ya bani yace muje na gani ko karya kike Yi ban sani ba,Dariya nayi nace akan me Zan maka karya,Toilet na shiga sai Bai iya Bina ba baya son ganin kazanta,na leko nace shugo mana,fuska ya yatsina yayi kwanciyarsa a saman bed din Yana latsa waya har nayi wanka tare da shirya kaina na fito daure da towel Ina goge ruwan jikina da karamin,Mikewa yayi zaune yace kawo na tayaki Yana bin cinyoyina da kallo har na karasa bakin gado inda yake zaune.

Murmushinsa me tsada ya saki tare da furta kin Zama Yar Lukuta wannan cinyoyi sun Tara tsoka me Iya ke Baki Haka? Dariya nayi kadan na Mika Masa karamin towel din ya karba Yana goge min gashi na Yace Bari a dakko Handrier Umma,Me Aiki ya leka ya fada Mata inda zata dakko tana kawo wa tayi knocking ya Bude kofa ya karba ya rufe ya dawo ya jona tare da kunnawa da hannunsa yake barbaza Gashina Yana busar da shi,cikin kankanin lokaci ya bushe yayi Amfani da cumb ya taje harda shafa min mayukan gashi iri iri karshe ya fesa min Hairspray kaina Yana saman cinyoyinsa,nice na Kama gashin da Ribbom ya wanke hannunsa a toilet,Yana fitowa yace kawo lotion din a shafa Miki Baki da sauri ke kin fiye Nawa,Ni dai na Mika masa,yace Ina face Cream din? Nace ai duka shi nake shafawa yace Haka aka ce kiyi? Baki gansu ba set Guda kowanne bangaren akwai nasa shine Zaki na shafa kowanne a fuska idan kuraje Suka fito fa Bai karbe ki a fuska ba,karki lalata fuskar Nan tam,Ni dai Shuru na Masa nasan tsurfar masifa ce da shi,Harda sawa kofa key Yana shafawa sai faman lailaya min wuya yakeyi wani Dadi naji kamar ana min massage,na wani lumshe Ido shi kuwa wani dalla dalla yake bin ko wacce gaba Yana murzawa,kirji na ya gangaro Ina ji nace a tsalle nan,Harara ya watsa min nayi Shuru Ina ji Ina gani ya janye Towel din ya barshi a Hips Dina,zan Kare kirji na da hannu yace Don't...Fasawa nayi ya haye saman Bed din tare da wani sani a tsakiyar kafafunsa Kamar wata Yar yarinya,Albarkatun Kirana ya Shiga shafawa lotion da Hannu biyunsa,Ido na sake lumshewa tare da zaro Harshena na lasi labbana,Maitar ta motsa kenan? Naji ya tambaya,Dariya nayi ba shiri Ni ban ma San nayi ba,Mai Kawai nake shafa Miki ba abinda nake yi,Yana magana Yana Sarrafa Albarkatun Kirjina yanda ya ga dama,sai da yaga dama sannan a gangara cikina zuwa bayana,Mike tsaye ya Furta na sauka na Mike yazo ya shafe cinyoyina tare da lailaya su har ya Gama sannan yace na Gama,da sauri na Daura Towel dina, Zan fita Ni na manta ma nayi hanyar toilet zato na kofa na bi,Dariya ya dinga min,Hankali na ya tashi,yace baza ki sa Kaya ba Haka Zaki tafi? Sai lokacin na tuna,Dawowa nayi na duba jakata na Dauki wata doguwar Riga me Hannun bra maroon me adon fari digo digo,yace ajiye rigar Nan sai Mun koma gida,doguwar Rigar lace na saka Brown,Shiryawa nayi shi Kuma ya Mike yace Zan tafi gida Sarkin santi daga shafa Mai kin wani rikice,Fuska na kwabe yace bacci nake ji,Nace tun yanzu ko goma Bata Yi ba,Me Zaki bani? Nace ba komai,to Good Night yace tare da kissing Dina a lips sannan Muka fito tare ya wuce Ni koma na koma part din su Iya sunyi Shirin bacci,Nima dakin da Iya take na Shiga ita daya ce zata kwana,Nima Shirin bacci nayi na kwanta kusa da ita,Iya Tace Wannan matan Haka Umma take zaune da su?nace Ae,Iya Tace yo kishi hauka ne?

Baki na tabe nace Iya ki rabu da su duniya ce ai Allah Yana kallo,Shuru ma magana ce kana zamanka Zaki ga allonsu ba Rubutu Allah da Kansa zai Yi maganinsu,Ni Wannan Yusran Kawai na tsana Yar Kawar Momy jira kawai nake ta kulani inci ubanta,Dariya Iya tayi Tace sabo da kar ta aurar Miki miji? Mu Wato mu kyale su Momy da Allah ke Kuma kici Uban Yusra ko? Ni ba kishi nake da ita ba,sai dai ki gayawa wani Rumaila Amma Ni Iya ban iya jurar wulakanci ba,anyi Daya biyu to na Uku bazan Iya Shuru ba.....wayata ce tayi Kara Iya Tace Tashi ki fita baza ki Hani bacci ba da Baby Baby Abu yaki karewa ki koma dakin Haleesa ita kadai ce dama sa'arki ce sai kiyi a can,Wayar na daga tare da Mikewa na koma dakin Halisa ita daya ce Bata Yi bacci ba kallo ma takeyi,kwanciya nayi a gefenta Ina waya kasa kasa, Ina ta fadan kalaman soyayya Wanda suke susuta me gida,Haleesa tana ji Tace wlh ba Wanda ya Isa ya hanani soyayya da saurayina Kuma aure kamar nayi,na samu Dan mijina za a hanani,Ina jinta bace Dan Uwarki Ni ba Mamanki bace kike ce min ba Wanda ya Isa?Shuru ta min,Nima na share zancen.

Washe gari da Yamma Umma ta Kai su Iya gidana Suka Sha kallo,Iya Tace yanzu nanne gida yata Rumaila? Umma Tace ae,Ai Iya sai ta fashe da kuka Tace na tuna Sanda nace bazan shayar da Yar Nan ba sai da Ubanta ya biya kudin

Please Login or Register in order to submit comment