Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

dauki ihu,Mazan gidan Suka yo kaina,Umma ta fito da Sauri, Fu'ad kuwa cikin Malam masu karatu ya taho da babban malamin,Islam ya fito da gudu,Ina ganin Malamin na Fadi kasa Ina birgima Ina wani irin Nishi,yatsan kafata ya rike babba ya shiga rero karatun Qur'ani,Wani Ihun nakeyi Ina birgima,Daga can malamin yace Kai waye?
Aljanin dake jikina ya fara magana Yana cewa sunana Salahu,Laifi tayi Mana me girma,Dan me zata kwara Mana ruwan zafi muna kwance muna Hutawa a makwararar gidansu,nazo Bara gidansu ta kwala min kwano tare da korata shi yasa Ni Kuma na shigeta na rigada na aureta Kuma wallahi sai Naga karshenta bazan taba fita ba.

Malamin yace yaushe ta zuba muku ruwan zafin? Aljanin yace tana shekara goma sun dafa taliya sun Tace Bata Bari ruwan ya huce ba ta zubo Mana Muna kwance dama Yan Adam Mata da yawa suna Mana Haka Basu San wajen hutawarmu bane sai Kawai su dinga sheko ruwan zafi Basu Bari ya huce,Nazo Ina Bara a gidansu na fito a siffar mutum yaro ta karbi kwanon ta kwala min a kaina shi yasa nace sai Naga karshenta Kuma wallahi bazan barta ba,duk Wanda ya aure ta ya auri masifa har danginsa ta Zama tawa,Nine na Sadu da ita,Islam najin Haka ransa ya baci kishi ya taso Masa yace Malam yanzu ko an daki Rumaila wa aka duka? Malam yace Aljani ka daka,Zumbur na Mike da Muryar Aljani nace au fada zakayi da Ifritu to Bismillah,Islam kishin Aljani ya sadu da matar da zai aura Fu'ad Yana rike shi Yana Karfa ka dake ta Islam,Malam Yana Kai Islam saurara Amma Islam Iya karfinsa ya samu ya zage ya Kai min Uban naushi sai da na tashi sama Zan fado kasa Fu'ad yayi sauri Allah yasa kusa da shi na taho Zan Fadi ya cafeni a jikinsa,Lokacin da Islam ya Kai min duk tunaninsa Aljani ya daka lokacin Kuma Aljani tuni yayi tafiyarsa ya barni aci ubana,Ina faduwa Aljanin ya dawo jikina ya shige abinsa yayi luf yasan Wanda ya aureni ya aurarwa Kansa masifa,Ni kuwa Suma nayi jini ta Hanci ta Baki,Dan rashin Imani su Khaleesat murna sukeyi,Suka kwashi mamansu sukayi asibiti,Islam ko ta kaina baibi ba yayi tafiyarsa wajen Momy dinsa Yana Bata Hakuri Yana cewa na fasa aurenta Momy bazan auri Aljana ba,Momy data Suma Nan take ta wartsake tana Jin dadi.

Abbi Yana dawowa Islam yaje yace ya fasa aurena,Abbi ya kada ya Raya Amma yace Sam baya so na yanzu,Ni kuwa Ina can Tuni Fu'ad yayi Hospital Dani Yana ta shara gudu,agajin gaggawa aka bani,Abbi ya bimu Asibiti daga baya shi da Umma,ba abinda likitoci Basu Yi ba akan na farfado Amma babu alama,Umma tana kuka Tace Kaine duk ka jawo wannan abin Fu'ad da ka amince da tashin hankali Bai samu Rumaila har aljanunta sun tashi ba, Fu'ad Hawaye ya zubo Masa karon farko yace Umma wallahi Ina sonta,Abbi ya kalle shi yace shashan banza,na fasa aurawa kowa Rumaila ko ta warke ta samo wani Mijin da kanta ta kawo, Fu'ad yace Please Abbi Zan haukace,Abbi yace ka Dade baka hauka ce ba ka dage ka nemi soyayayyarta,tana sona Abbi,Inji uban wa? Sai ka Bari na gani da Ido na, Fu'ad yace to zaka gani Abbi, Umma Tace Dan Allah karku damemu da wata Soyayya Rumaila tana wani Hali kana ji Doctor yace sai tayi kwana biyu ko Uku Bata farfado ba Kuma zata iya wucewa Kiyama, Fu'ad yace Wlh idan ta mutu sai na daure Islam har abada ya dakar min Mata
Abbi Yana takaici yace rufe min Baki.







Karshen Free page.





AsmaBaffa
[7/13, 8:42 AM] Sis Asma: 🎈🎈🎈🎈
DANGIN RABI
🎈🎈🎈🎈







NA KUDI NE

DUK WACCE TA FITAR MIN DA NOVEL DINA ZUWA WASU GROUPS ALLAH YA ISA BAN YAFE BA, A MADADINA DA DUK WACCE TA SIYA TSAKANI DA ALLAH AKA CI AMANAR FANS DA WRITER NI ASMABAFFA AKA FITAR MIN TO
ALLAH YA ISA
KUMA DUK WACCE TA GANSHI TA KARA TURA SHI ZUWA WASU GROUPS DA WANDA TA GANI BATA SIYA BA TA KARANTA KUMA TASAN NA KUDI NE AMANA AKA CI BAN YAFE BA,
SABO DA DUK WACCE TA SIYA BA IYA KUDI BANE SAI DA AKA AJIYE YARJEJENIYA KAN BAZA TA FITAR BA,TASAN DOKA TA KARYA,KO ADMINS MASU SON BIRGE MEMBERS NA GROUPS NASU SAI SU SIYA SU DINGA TURA MUSU,KU SANI AKWAI CIWO DA HAUSHI KUMA BAMU YAFE BA WALLAHI.






DANGIN RABI IS DEDICATED TO AIDA MAMAN TASNIM.
















41-45


















Official









By
AsmaBaffa











Page naku ne

Maman Dee
Fatimamusasamaru
Balkisu
Mmn Saddeeq
Dr Zainab Abdullahi
Maryam Yamai Aliyu
















A zaune Fu'ad yake gefen gadon da nake kwance ya tsura min Ido Kamar zai Hadiye Ni,sai yau ya taba min kallon tsaf a Nan ya gano lallai ba karamin kyau ne Dani ba, Allah yayi baiwa a Nan haka ya furta a ransa,a hankali ya furta Allah ya tashi kafadu Yar gidan Iyanta,Umma Tace me kake cewa? Istigifari nayi ya furta Kawai,Sallah ma da kyar ake tashin Fu'ad yaje yayi,har dare Yayi Umma Tace to ya kamata ka hakura Haka kaje gida sai gobe ka dawo,abinci Kuma su Tasalluwa zasu kawo da komai munyi waya, Fu'ad yace kije dai Gida ke Umma ai Ni ke nake Shirin fadawa ki tafi gida Har na Kira Driver zai maida ki gida,Kaga ban son shirme Ina ka taba ganin Namiji yayi jinyar mace? Gashi Zaki fara gani Umma,Abbi ne ya shigo da kayan shaye shaye na Lemuka da Fruits yace Kai Fu'ad taho mu tafi,Zaiyi magana Abbi ya daka Masa tsawa tashi nace baka da kunya ko? Kabi ka Raina mutane,Mikewa yayi Yana turo jajayen labbansa Yana tafiya Yana kallon inda nake a kwance Haka yabi Abbi dole Suka fita,Key din mota Abbi ya Mika Masa gashi ka tuka, Fu'ad ya kalli Abbi yace Ashe Allah yaji kan mu Allah Zan Shiga cikin Trailer Abbi gwara ka tuka Kawai idan Kuma kana so mu tashi gobe a kabari to na tuka mota,Abbi Baki Bude yace Bani mukulli tunda Kai ka haukace ma naga alama.

Tunda Abbi yake tuki Yana ta yiwa Fu'ad hirar business da zai tafi Italy,Uhm... Kawai Fu'ad yake Iya bada amsa har ga Allah hankalinsa baya jikinsa,Yana wajen Rumaila har Suka koma gida Haka ya fita ya manta ko motar Bai rufe murfin ba yayi gaba abinsa sai Abbi ne ya Rufe Masa,Islam ne ya tari Fu'ad yace Yaya Fu'ad ya jikin Rumaila? Harara Fu'ad ya watsa Masa ba tare da ya bashi amsa ba ya shige part dinsa, Baba Jummai ce ta taho da gudu tana Murna a ranta Dan munafunci tana cewa shike Nan nasan ma Rumaila ta mutu ko Dan Momy Fu'ad?,ai nasan dukan da Tasha da kyar zata tashi baza ma ta tashi ba,Allah sarki gobe Muna da babbar janaza, Fu'ad ya kalle ta yace kece dai Zaki mutu tsohuwar banza ya banko kofarsa ya Rufe ya bar Baba Jummai tsaye a bakin kofa tana jinjina rashin mutuncin Fu'ad.

Tunda Fu'ad ya shige part dinsa Wanka yayi tare da dauro Alwala yazo ya gabatar da Sallar Isha tare da nafilfili Yana ta min Addua Allah ya bani lafiya sai wurin 1am ya samu ya kwanta a saman gadonsa cike da tunanin halin da nake ciki da Kuma rayuwa ta a gidansu ta Shiga dawo Masa tun farkon ganina a gidansu,tunowa yayi ranar da ya fara gani munzo daga Kauye yana rungume Yan Uwansa na wara Hannaye Ina cewa muma ayi Mana,Dariya ce ta kwace Masa ya murmusa Yana cewa Allah sarki da na sani nayi mata,part dinsa Dana gyara Masa yace sai na maida Masa kurarsa ya tuno,Juyi yayi a saman lallausan bed dinsa yace Ban kyauta ba,Haka ya dinga tunano Rayuwata a gidansu wani wajen yayi Dariya wani wajen ya tausaya min har yazo lokacin Dana fadawa Abbi na amince Ina sonsa,shi Kuma yace Bai shirya ba,Nan take yasa Hannayensa biyu ya Shiga yamutsa gashin Kansa me santsi yaja tsaki Yana Jin haushin Kansa,ranar da kyar ya samu bacci ya dauke shi.

Da sassafe Yana Idar da Sallar Asuba tare da Azhkar wanka yayi ya shirya tsaf cikin jallabiya Brown Yana bulbula kamshi tun da sauran duhu duhu a gari ya shiga mota ya bar gidan sai asibiti,lokacin Umma ta Idar da Sallah tana Azhar Kawai sai Sallamarsa taji ya shigo,da mamaki Tace Fu'ad kaine? Ae Umma Ina kwana ya me jiki? Lfy Alhmdllh ta amsa tana cewa Wai Kai Fu'ad meke damunka ne?ko gari Bai Gama wayewa ba,Shuru yayi ya nemi waje a gefen gadon da nake kwance ya zauna,sai da ya tabbatar Ina numfashi sannan ya samu bacci ya fara daukansa sai gyangyadi yakeyi a zaune Umma Tace karka fadawa maralafiya a kanta ka karasata kana gyangyadi tashi ga Empty Bed can kayi baccinka a can,Bedsheet Umma ta shimfida masa a gadon da ba kowa dake private Hospital ne Kamar wani Hotel sabo da kyau ko Ina Yan kamshi da sheki,Kwanciya yayi kamar marar lafiya sai bacci ya kwasheshi,Likita ne ya shigo Yana shigowa yayi tunanin Fu'ad wani patient aka kawo yace ya akayi aka hada patient biyu a room daya Hajiya kina kallo baza kiyi magana ba,ki sanarwa masu kula da su,Umma Tace Dana ne fa tare muke Doctor Bai Jima da zuwa ba bacci ne ya dauke shi baka kula sosai ba Fu'ad ne fa, lokacin Doctor ya lura yayi Dariya sannan yace ai ban sani ba Ashe Oga ne,Murmushi Umma tayi,Doctor ya Isa kaina ya dubani tare da zare min Drip ya min wata Allura ya fita.

Bacci Fu'ad yake Yi sosai wanda sai da ya gaji Dan Kansa wurin 12pm sannan ya tashi lokacin an kawo abinci iri iri,Masallacin dake Hospital din yaje yayi Sallah sannan ya dawo Umma ce ta takura Masa sai yaci,Haka ya zabi abinda zai Iya ci yaci,Basu Dade da Gama ci ba Na fara motsi a hankali na motsa tare da Bude idanuwa na a hankali Ina bin dakin da kallo,Basu san na farka ba sai da suka ji Nace Salamu'alaykum Umma sannan suka juyo da sauri tare da rige rigen zuwa ida nake,ban San me ya faru da Ni ba Ina iya tuna Lokacin da Islam ya Naushe Ni sabo da lokacin hankali na Yana jikina,Kafin nayi tunanin komai Umma ta Kama Ni na tashi toilet ta raka Ni Brush nayi sosai tare da yin wanka na fito Fu'ad ya tafi Kiran Doctor,Har Umma ta bani wata doguwar Riga me siririn Hannu Yar kanti Bata da nauyi,Bayan na saka nace Yunwa Umma,Abincin ta zuba min tuwon danyar shinkafa miyar Egusi ga farfesun kaji a gefe,Ina Ci ya Fu'ad suka shigo tare da Likita,Doctor yace lallai jiki yayi kyau,Ya tambayeni Ina ke min ciwo nace Babu lafiya nake jina,Kawai wajen makoshi na Inda Islam ya nausa ke min ciwo, Wasu magungunan ya ru buta Mana, Fu'ad ya karba yaje ya siyo ya dawo lokacin na Gama cin abincina na wanke Baki na,Umma Tace to Alhmdllh Rumaila Bari naje gida nayi abinda zanyi ga Fu'ad Nan zuwa Yamma Zan dawo,To Umma na furta Ina Wasa da yatsu na gaba daya kunyar Fu'ad ce ta hanani sakewa,mugun kwarjini yake min ga kamshi ya gama tafiya da Imani na,a hankali nace Islam Allah bazan yafe Masa ba,ace Mijin da mace zata aura tun Ina budurwa Yana dukana Haka Ina ga anyi aure sai kace a film din China,wani kongfu ya min sai kace ya samu Jettly,Umma tana hada Kaya Tace kiyi hakuri shima bada saninsa yayi ba.

Kayan Dana cire Dana abinci Umma ta tattara ta kwashe Driver ya dauketa Suka tafi,daga Ni sai Fu'ad,ko kallon inda nake baya Yi sai latsa wayarsa yakeyi Yana murmushi shi kadai Ni Kam Kallonsa nake Yi kamar Zan cinye shi Haka nake ji,Uwar kallo Daina kallo na Haka,naji ya furta ba tare da ya kalle Ni ba,da sauri na dauke kaina gefe Amma ban San Sanda na sake dawowa da kaina dai dai ba Ina ta Kallonsa,Ki Fadi soyayyarki ki daina Bata lokacinki,Murmushi nayi nace ai Ni sai Islam,da Alama Baki San meke faruwa ba ai tuni Islam ya fasa,Da Sauri nace dan Allah da gaske ya fadawa Abbi ya fasa? Fu'ad yace da gaske,Dariyar farin ciki ce ta kwace min nace siyo Mana Lemuka muyi partyn Murna yanzu,Gasu Nan Abbi ya kawo kala kala,To a jera su,Empty Bed din da yayi bacci a Kai ya jawo Gaban mu ya shirya Lemuka da ruwa kusan kala goma,yace saura abin ci,Waya ya Kira tare da yin Order Abinci na Yan gayu,15mnt sai gashi an kawo abinci kala Uku masu shegen dadi na turawa Nan ma na jera su Muka zauna a gefen bed daya gadon Yana Gabanmu da kayan ci da Sha.

Abbi ne ya turo kofa yaga abinda Muka shirya Mun saka a Gabanmu,da sauri Fu'ad ya shiga cewa Happy Birthday to you,ku Kuma lafiya wannan tarkacen fa? Ina Ina na fara uhm....B... Birthday na ne yau,Allah ya kyauta ya jikin? Abbi ya tambaya,da sauki Alhmdllh,Ina wayancewa Ina kwashe Lemuka da sauran kayan ci,kwana biyu nayi a Hospital aka sallamemu,Duk abinda ya faru lokacin da Aljanuna suka tashi akwai a Wayar Khaleesat ta dauka a waya har dukan da nayiwa Momy,a garden suna Zaune da Safna sai Momy,Khaleesat Tace Momy kinga komai na Yarinyar Nan akwai a wayata da shi zamuyi amfani mu Kira Mata Yan Sanda,Kamowa tayi ta nu na musu,Momy tace kinga yanda tayi cilli Dani kamar Buhun auduga lallai Yarinyar sai ta ci malafar Ubanta har yanzu kugu na ciwo yake Yi saura kadan Lakata ta tsinke,Suna zancen Fu'ad yazo ta wajen Yana jinsu,Sai ya share tare da kwalawa Khaleesat Kira,Da Sauri ta nufi Inda yake,muga wayarki Zan dauki number Fadila,Bata kawo komai ba ta Mika Masa,Yana karba ya lalubo video din data dauka Ina Aljanu ya tura a wayarsa sannan ya goge na Wayarta gaba daya tare da Mika Mata Wayarta,harda tambaya kaga number din? Ae Kawai ya furta ya wuce abinsa,Ina zaune a Palo Ina kallo sannan ga littafin English a gaba na na Gama Assignment Dina,Yana shigowa saman 2seater ya zauna tare da yin wani Zama kana kallo kasan kudi ya ratsa shi,Muryarsa na tsinta yace zo ki ga wani Abu, Carbin dake Hannuna na ajiye naje inda yake zaune ,zauna ya furta,gefensa na zauna ya danno min video din da na daki Momy,Ina kallo na zaro Ido har Adduar da Malam yayi min da Maganar Aljanin,Ina kallon Dukan da nayiwa Momy na kyalkyale da Dariya tare da tafawa kaina nace Wow Wallahi na godewa kaina,Weldone Rumaila Weldone ,Sabo da murna ban San Sanda na sakalo hannu na a wuyan Fu'ad Rabin jikina gaba daya a jikinsa,na shako shi sosai tare da lankwaso wuyansa Ina ta dariyar dukan Momy da nayi.

Duf nayi ganin yanda Malam yake min Ruqiyya suna magana da Aljanin dake jikina naji tsaf duk Abinda Aljanin ke furtawa,Tashi nayi da sauri Raina a bace na dauki carbi na tare da Zama na kalli gabas na Shiga Jan carbi Ina cewa Allah ya Isa Aljani Salahu,Allah ya Isa Salahu,Allah ya Isa Salahu Haka nake ta fada Ina Jan carbi, Fu'ad Dariya ce ta kamashi yace karki damu Yan Mata zanyi manage da ragowar Salahu,Duk da ya rigani Jin dadin wajen ya za ayi,Ashe Dan Iskan Nan ne ya fito Miki a suffata ya cuceni duk ya Bata min suna a wajen mutane,Kai Nima nace Allah ya Isa Aljani Salahu,Dariya nakeyi nace munafuki harda laulayi na dinga sheka amai da yawu,To Kira Iya a fada Mata ko ta hakura ta yafe miki cewar Fu'ad,Nace tsaya na Gama jawa Aljani Allah Isa ko cikin carbi ce,Ki lallaba shi kina ji yace duk Wanda ya aure ki ya auri masifa,Ni kuwa Haka zanyi ta maza a daura Dani mu Kara Dani da shi,Wayata na dakko na lalubo number Iya tare da kiranta,naci sa'a naji ta daga sabo da kar ta kashe idan taji muryata,ban Mata bayani yanda zata Gane ba kawai nace Iya Salahu
Ne ya min ciki,Kya fito ma ki Fadi gaskiya ai sai kije wajen Salahun ya aureki,ba mutum bane Iya Aljani ne,Karyarki tayi yawa Ni Zaki dinga rainawa hankali kince babu ciki yanzu kin dawo kince Salahu ne,Tsaki Iya ta ja tare da kashe Wayarta Ina cewa Iya ki tsaya kiji Amma Ina.

Baba Jummai ce ta shigo tana Galla min Harara ta ganni kusa da Fu'ad Tace Ashe kin dawo Baki mutu ba,ai nayi tunanin wannan dukan da kika Sha sai dai ki farka a lahira,Nace to kwana na Bai Kare ba sai ki kashe Ni da kanki,kar dai ki min rashin kunya dama Sannu nazo na Dan Miki Kuma tunda ke fitsararriya ce na fasa tayi tafiyarta,Nace Lallai tsohuwar Nan duk mutuncin da na Mata Bata gani ba Ina kallon take takenta tun da dadewa haushi na take ji, Fu'ad yace kyaleta Watarana korarta zanyi da kaina daga aiki,yawwa kayi Mata sanadi abincinta ya Kare.

Bayan Sallar Isha Ina kitchen Fu'ad ya shugo sanye cikin Riga Armless sky da wandonsa dogo yayi kyau sosai,Kamshinsa yasa nasan yazo Amma ban juyo ba,Hannayensa ya ware Kamar zai rungume Ni harda tsayawa daf da Ni kamar zai rungumeni ta baya,A hankali yace kamar na rungumeta a haka,da sauri na juyo naji kamar Yana magana kafin na Kai ga juyowa cikin zafin nama ya juya tuni ya kalli kofa kamar Bai San Dani ba,Aiki na naci gaba da Yi,Jelar gashi na ya taba da yatsansa Guda daya yanda bazan ji ba, Hips Dina ya kalla tare da cije lebensa na kasa,kafin na juyo sai Naga ya juya Yana latsa waya kamar Bai ganni ba.

Sake matsowa yayi daf Dani nayi sauri na juyo Dan na kamashi Amma sai na hade da jikina da nashi, da sauri ya matsa gefe harda masifa tun dazu kike so sai kin rungume Ni na matsa kin matso na matsa kin matso Haba dole sai kin Sa na dauki zunubi me yasa kike so nane da yawa Haka? Ance ki fadi gaskiya kinki,Baki na saki Ina Jin sharrin da ya Yi min, Palo ya koma ya kwanta Kamar Wasa bacci yayi gaba da shi dama sarkin bacci ne,Fitowa nayi dauke da plate din Fruits,a gefe na ajiye plate din a hankali Ina Sanda na karaso gabansa tare da tsugunawa a saitin fuskarsa Ina Kare Masa kallo Ina wani murmushi,Gashinsa na taba kadan a Raina na furta laushi,wuyansa na karewa kallo wani lumi lumi a hankali na shafa wajen,a hankali ya bude idonsa Wanda cike yake da bacci,na kalle shi da kunya nace tururuwa ce take maka yawo a wuya shine na cire maka,Idanuwansa ya maida ya rufe yace maida min da tururuwata dadin yawonta nake ji a wuyana,ya Riga ya ganeni,naci gaba da Masa tafiyar tsutsa Ina cewa tururuwa ki sauka idan ta maka Kashi a wuya ba ruwana,Umma ce ta shigo da Sauri na koma cewa ka tashi na yanka Fruits din tun dazu nake ta tashinka,Umma ta harareni Tace kya Gama gulmarki marar zuciya, shi kuwa harda yin shuru Wai yaci gaba da baccinsa.

Iya a zaune take saman kujera a tsakar gidansu sai fushi takeyi Taki kula kowa ko Baki ne suka shigo Bata musu magana,Ali Shagali ne ya shigo Iya ta bishi daki Tace Ni fa na fada maka ko Tv ko saki,Nima kayan kallo nake so ka siyo min,bani da kudi bani da inda zan samo su,idan na siya Miki Kayan kallo ita abokiyar zamanki Kuma tayi ya?dole sai na siya muku tare,to ba kayi kudi ba Ni Kawai ba ruwana Malam TV Kawai,Me shayi bakin cikin Halayen Iya sun dame shi yace Jeki gida sai neme ki kin dame Ni na gaji,naji Kuma Zan tafi gidanka din banza mene ciki Banda talauci, me kake da shi,Naji kije sai na nemeki,Zaka zo neman Nawa ne wlh baza ka ganni ba,Iya kayanta ta kwasa da yawa kishiyarta tana kallo tana ta Mata Dariya,Iya Tace kin wa Uwarki Dariya,Uwarki me Dambu ita kika yiwa Dariya ba Ni ba,me Shayi Iya ta gallawa Harara ta fisge dubu daya a hannunsa wacce ya fito da ita zai Aiki yaro ya siyo musu kifi soyayye zasu ci abinci Amma Iya ta fisge kudin tace sai dai ka dakko wata tayi tafiyarta gidanta ko gidan yayanta Malam Haruna bata nufa ba,gidanta Wanda ya kusa ruftowa Nan Iya ta koma da kayanta.

Baba Jummai ce ta fito kitchen dinsu na masu Aiki tana cewa Tasalluwa kije bangaren Umma kiga Yan Wutar Sakata suna can suna ta bariki a bainar mutane Rumaila da Fu'ad,ai gwara su da ke tunda ke ma cewa kika Yi Hotel Zaki Kama idan kina da kudi Daki permanent ki samu Ana kawo Miki gayu kina biyansu kudi,ba gwara su dake ba cewar Tasalluwa Baba Jummai Tace ke dama Tasalluwa ai munafuka ce Wai ke ta Allah ko? Zaki gani,Ana Haka sai ga Fadila Niki Niki da Kaya tare da Rabi,Ni na manta ma Rabi tana Abuja Ashe gidan Fadila aka tura Rabi ta tayata aikace aikace,sai ga Fadila ta rike Rabi tam ta shigo tana rusa kuka,Itama Rabi tana kuka ko me ya faru oho,Momy dasu Safna sune Suka fara damkar Rabi tare da rufe Rabi da duka Tim Tim Rabi tana Ihun kuka tana bada Hakuri,Momy Tace kin kashewa 'yata Aure shegiya bakar jaraba,gashi Nan kin jawo ya saketa biki ko shekara ba a ayi ba har an sako ta ji kake tas...tas Ana ta kashe Rabi da Mari,sai da suka yiwa Rabi dukan kawo wuka sannan suka fatalo ta tsakar gida tare da kayanta, Bangaren Nene tayi tana rusa kuka,Nene Tace lafiya me ya faru? Rabi tayi mukus tambayar duniya Rabi Taki fada sai Momy ce tazo Tace ai baza ta fada ba munafukar banza Wai Haka Kawai ta fashe da kuka Tace Mijin Fadila ya mata fyade,shi kuma ransa ya baci yace ta kawo wata tayi masa sharri sabo da Haka ya saki Fadila su tattara su bar masa gida,Nene Tace Subhannallahi ke Rabi ya Haka? Rabi tana shesheka Tace na Rantse da Allah Fyade ya min lokacin ta tafi unguwa gidan biki ya bani lemo na Sha shike Nan nayi bacci sai Farkawa nayi na ganni a dakinsa ya min Fyade,kwana Uku Ina fada Mata ta bincika sai tayi son zuciya Tace Zanwa mijinta sharri......Rabi ta sake rushewa da kuka,Sanda taga kullum sai nayi kuka shine ta tambaye shi ko da gaske ne shine yace ya sake ta anyi masa Sharri.

Ni Wallahi da na sani bazan taba zuwa birnin Nan ba gaba daya tsinannu ne na cuci kaina,dama zuwa nayi Nima na samu wani Saurayin a gidan Nan ya aure Ni kamar yanda Rumaila ta samu Ina bakin ciki ace ba Ni bace za a aura tunda nice ma Yar Uwar gidan Nan Momy tace naje na dinga Taya Fadila Aiki,dama tunda naje mijinta sai yayi ta kallon duwawuna Yana mintsina min Ido daya,ko idan tana daki sai ya fito inda nake yayi ta shafa min kafata,dama wallahi kwarto yarki ta aura Kuma ba Dan Allah ya aure ta ba Dan ya biya bukatarsa ne gashi Nan idan da Dan Allah ne ai bazai saketa ba,Kuma wallahi Alo tsiya Alo Danja wallahi sai kin biya Diyyar fyaden da aka min ai kece kika jawo,Rabi ta furta tana nuna Momy da yatsa.

Momy Tace kashe ki akayi da Zan Biya Diyya,Diyyar Ubanki Zan Biya?kwadayi da bakincin Rumaila shi ya kawoki ga shi kin jawa kanki Hassadarki ta jawo Miki,Rabi ranta ya baci dama Rabi Bata da kunya ko digo ga masifa,kirji ta turo gaba ta hade kirkinta Dana Momy sabo da Momy ba tsayi Rabi akwai tsayi

Please Login or Register in order to submit comment