Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


Downloaded from GNOVELS.COM.NG




This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG
to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/gnovels

Twitter : https://twitter.com/gnovels

Telegram : https://t.me/gnovels

NANA KHADIJA (littafi na daya)


NA

BINTA UMAR ABBALE

(Maman Abdul Wahabu)



NA FARA DA SUNAN ALLAH SARKI BUWAYI ,WANDA YA QAGI SAMA DA KASA SARKIN DA BABU KAMARSHI,

ALLAH KAYI DADIN TSIRA GA ANNABI MUHAMMADU(SLW) WANDA KABAWA YA YADDAR KA ,ALLAH KA KARA TSIRA DA AMINCI A GARESHI DA AHALINSA DA SAHABBANSA TSARKAKA


ALLAH YADDA KABANI IKON RUBUTA LITTAFIN NAN ,LAFIYA INA ROKANKA KASA IN GAMA LAFIYA, ALLAH KA YAFEMIN KUSAKURAI NA NA CIKI.
AMEEN.





WANNAN LITTAFIN QAGAGGE NE DA GA NI MARUBUCIYAR BANYI DOMIN WANI KO WATA BA WANDA YAGA YAYI DAI DAI DA RAYUWARSHI A RASHIN SANI NE




GARGADI



BAN YADDA WANI KO WATA YAYI AMFANI DA WANI BANGARE NA CIKIN LITTAFIN NAN

BA BATARE DA SANINA BA ,DUK WANDA YA TABAMIN WANI SHASHE A CIKI ,ZAMU TSAYA A GABAN HUKUMA





_WANNAN LITTAFIN NA KUD'I MALLAKIN ME SHI NI MARUBUCIYAR TUNDA 1,23,4,5,6 DIN SA BAN MALLAKAWA KOWA BA IN KANA BUKATA SAI KA BIYA KUDIN KARATU ZAKA SAME SHI DAGA FARKO HAR KARSHE HANNUN MARUCIYAR, WALLAHI DUK WANDA YW FUTAR MIN DASHI HAR 'YAN CIMA ZAUNE SUKA SAMU SUKA SIYAR MIN DASHI BAN YAFE MASA BA, NA FADA CEWAR DUK WANDA YACI DA GUMI NA UBANGIJI YAYI MIN SAKKAYA DOMIN BAZAN TABA YAFEWA BA ALLAHI. NASAN ALLAH BA AZZALIMI BANE ZAI BIMIN HAKKINA KAN ZALINTA TA DA AKAYI.




DOMIN SAMUN CIGABAN WANNAN LITTAFIN KAN FARASHI ME SAUKI DARI BIYAR KACAL #500 DAGA 1,2,3,4,5,6 DUK AKWAI A GURIN MARUCIYAR DON HAKA ME BUKATAR KARANTA CIGABANSA SAI YA KIRA WANNAN NUMBAR KAMAR HAKA.

08089965176
07084653262







*BISIMILLAHIR-RAHAMANIR-RAHIM*









Lkace kwabo fada ya rin ca6e tsakanin Dije da indo sai faman ko kawa suke Dije sai faman zagin indo take itako indo sai faman dukan ta take dake dama Dije bata da wani karfi sai aikin tsokanar fada gashi bata da wani jiki indo ta fita jikin girma Sa'a ko sai kokarin rabasu take yi suna hadawa da,ita.

wata irin tsawa! su kaji an ce "kai wannan wane irin iskanci ne kukeyi anan da dabbanci "? cikin sauri Dije ta saki indo sai haki! take ta juyo jikinta sai tsuma ya keyi ganin yaya Ali ne a tsaye a gabansu ,,sai faman zare ido take harara ya banka mata yace "wato ke dan ubanki bazaki daina wannan iskancin ba ko? kitara yara ki ta kokawa a waje dan rashin kamun kai" ya mutsa baki tafara tana kunkuni dashi "to ina ruwanka za kazo ka wani ta kura mana ni banasan a shiga min sabga" duka ya kai mata abakin cikin zafin nama yace "dan ubanki wakikewa haka nisa anki ne " ? cikin sauri ta dafe bakinta hawaye ya na zuba tace "Allah ya isa mugu" cikin kunkunin tayi maganar mari ya kaimata gami da cewa "wato bakin ki bazai mutu ba ko wallahi sai na gyaramiki zama shashashar yarinya kawai stupid " yafada tare da jan hannuta tana turjewa yadaki kafarta ta fadi kasa ya hau janta a k'asa

Su indo kuwa tun lokacin da yaya Ali ya mari Dije suka gudo sabuda sun San halinsa harsu zai hada ya Zane babu abinda ya dameshi,,janta yake yana dukanta da kafarsa itako bakin ta baibar yimai rashin kunya ba Nene, CE azaune a tsakargida tana ta faman gyaran wake ta ji ihun Dije tashi tai da sauri ta tana gyara daurin zaninta tana fadin "wallahi na tsani mugunta irin ta "yayan unguwar nan me kuma marainiyar Allah tai musu suke dukanta" kafin tarufe bakinta ta hango Dije a kasa Ali ya na janta kamar yana Jan tsumma Salati ta tabka tace "kai Ali wannan wane irin abune mai tayi maka dan mugunta "? tafada tare da karasawa tana kokarin kwatar Dije daga hannunsa "wai bada kai nake ba kasake ta mana wallahi ka kiyayeni akan wannan marainiyar Allah sa,arkace ita dazaka dunga dukanta iyi"? ,sakinta yayi yana jan tsaki tare da hararar Nene "yace wallahi Nene ke kike daurewa yarinyar nan gindi take yin abinda tagada ma". "to ina ruwanka da,ita iyi?" cewar Nene. cikin 6acin rai ya kalleta tare da daure fuskarsa yace "samunta nayi fa a waje ta tara yara suna ta faman dan be sai kace wasu dabbobi dan nai mata magana tahau zagina wallahi kija mata kune ta kiyayeni kan in bar garinnan sai na canja za mata kammanni da duka"
Harara Nene ta galla masa tace "ka ki yaye ni Ali nifa ba na San ne man magana taya daga zuwan ka zaka ta kurawa yarinya tana wasa da kawayenta gaskiya in dai zaka zo ka ta kura mana ne gwara ka juya ka koma bana son zuwan naka haba ina dalili." Tak'arashe maganar tana gyara daurin zaninta,

Fuskarshi babu Walwala yake kallonsu yana Mamakin Abinda Nene tace tabbas Nene in dai a kan yarinyar nan ne babu da Wanda baza ta 6ata ba ,cikin yanayin maganarshi yace "ae ba gurin ki nazo ba gurin "yan Uwa da Abokan Arziqi nazo wancan Mara kunyar yarinyar bata isa ta Sani na bar garin nan ba batare da na shirya ba"
Harara D'ija ta galla masa tare da murgude baki tana bayan Nene A la6e
Yana kallonta yana Mamakin Rashin kunyar yarinyar,

Nene tace "to babu ruwanka da'ita har ka bar garin to kaji!!

Bai ce komai ba ya Nufi bakin rijiya domin daukar bota da nufin daura Alwala ganin har an soma kiraye kirayen sallahr magari ba

Ya na sane ya zira kafarshi daya wacce ke sanye da takalmi sawu ciki ya mutsikewa D'ija "yan ya tsu yayi saurin dauke kafarsa ya sakai ya fice daga gidan hannushi riqe da bota


Wata kara D'ija ta kurma tana kallon kafarta guda domin Sam bata lura dashi ya take mata ba

Da sauri Nene ta jiyo tace ke lafiyarki kuwa ?Cikin ihu D'ija tace "Nene kunama ce ta har beni yanzu"


Da sauri Nene n ta kafama kafar D'ijan tana duba wa gami da jan yeta da gurin tana sallalami , ta hau duba kafar


Tace" kefa kin fiye sangarta haka harbin kunama yake, ko dai wani kwaron ne ? Tashi ki bani guri in kara duba gurin"

Da sauri D'ija ta matsa gefe tana jan kafa sai kace wacce tayi targaade

Hakadai Nene takaraci dubanta a gun bata ga komai ba juyowa tai gurin dijan tace" Ai sai ki tashi daga gurin ko kije kiyi alwala lokacin sallah yayi na gaya miki kidai nai wa manya rashin kunya kinki ji idan yaje yaji miki ciwo babu ruwa na Ato,,cikin zumbura baki dije ta tashi da ga gun ta nufin inda butocin Al,wala suke ta dau daya dan duk abunta bata wasa da sallah da lokaci yayi take barin abinda take taje tai sallah

Shi kam Ali yana gama alwala wani yaro ya bawa butar ya mayar gidan ya huce masallaci bai dawo ba saida ya jira lokacin isha ya gabatar da ita yai adu'oinsa sannan ya dawo gidan.

Nene ya tarar ta idar da sallah isha dije kuma tana can gefe itama ta idar da sallahr tana ta faman cin wake da shinkafa wanda tasa nene tayi mata itakam tana bala'in san wake da shinkafa da manja da yaji tai ta zabga yaji tana ci tana zuk'ar baki, ko kallon inda take bai yi bah ya samu gefen Nene ya zauna yana karewa tsakar gidan kallo dan shi kam mutum ne mai tsamtsami abu kadan sai yasayi tashin zuciya yana da bala,in stafta komai nashi a tsare dan baya shiri da kazami gashi da wani irin hali. muskiline sosai sai ya gadama yake magana ko acikin abokansa ma haka dan har suna suka samasa ammafa duk wannan halinnasa bai raina mutum ko mai kankantarshi da iyayansa ya na bala'in sansu da kannansa to suma suna ji dashi sosai sabida ya nai musu abinda suke so Ammafa suna jin tsoransa musaman idan sukasan sunyi wani laifin dan baya musu wasa musamman akan harkar karatunsu, wannnan kenan

Nene ce ta jiyo bayan tagama lazimi tace" to sarki kafi sarki mulki kazo kazaune min yanzu zakafara iyayin naka ko"? tafada tana gallamasa harara
Murmushi ya saki ya kalleta yace " ke ba ayin abin arziki da ke daga zuwa na ko ruwan kirki baki bani nasha ba kina ta wani naiman fada dani" dariya Nene tayi tace" to ai kaine daga zuwanka ka fara halin naka"

Ta shi tai tai nufi madafi wata katuwar kula ta fito dashi ta a jiye a gabansa hade da da faranti tace "gashinan ai mutumin kane nai maka sabida nasan ka ce yau zaka zo" tafada tana kokarin zuba masa tuwon shin kafa ne da miyar taushe wanda taji nama da manshanu sai kamshi ne ke tashi agun tun lokacin da tabude kular ,ta zuba mai ta ajiye a gabansa tace"to gadanga bissimilah"tafada tana murmushi dan in taso tsokanarsa da wannan sunan take kiransa.

Gyara zama yai ya ce "saura ruwa ai cika ladanki uwargidana" gyara fuska tai tace "wannan kuma sai ka tashi ka dauko da kanka wai kai komai sai anyi maka" tafada tana harararsa hade fuska yai yace " sai kiyi ai nikuma bazanci ba indai baruwan kika kawumin ba"/ya fada yana kallonta da murmushi a fuskarsa dan yasan halinta indai baici abinci ba tashin hankalinta zata yi.

Duk wannan abin da suke dije na gefe tana jinsu dan indai da sabo ta saba indai yazo sai sun ta tabkawa da Nene

Nene ce ta kalleta tace" dije na tashi ki dauko masa ruwa a kinji tunda nari ga na zauna bazan tashi"

Wani irin kallo yabi Nene dashi daga ita har dijan yace "har indai wannan yarinyar ce zata d'auko min ruwa wallahi bazan ci abincin ba kina ganin yanxu tagama kazantar ta bayan tagama lashe hannunta ko wanke wa batai ba sabida tsabar kazama ce ita kice ta d'auko min ruwa insha ki kwashe abincinki na fasa ci ya Riga yagama yin sanyi ma" yafada yana Dada gyara kwanciyarsa a gefenta harararshi tai ta tashi tana sababi "wannan yaro halinka sai dai kai matar ka zatasha iyayi da feleke" cikin daki tashige inda firji yake tadauko mai ruwa mai sanyi.

Dije kam tana gefe sai faman harara take aika masa dashi a zuciyarta take fadin " a kwai babban kazami ma irin ka wai kai mai tsafta kadinga wani tsartar da yawu saika ce wata mace"
Harara a duhu Dija take domin shi Ali bai San ma tana yi ba

Nene CE ta,ajiye mai ruwa na roba hade da lemo mai sanyi tace "gashinan to sarkin tsurfa" tafada tana zama a gefensa ,,tashi yai yaje fi ya dauraye hannuwansa duk da cewa ba wani abin ya ta6a ba

Dawo wa yai ya zauna ya jawo plate d'in abinci yai bisimillah ya fara ci ,humm Ali kenan cin abincinnasa ma abin kallo ne cike da tsurfa yake ci yanaci yana ta6e baki yana kallon Nene yana jiran yaji abinda zata ce

Itako kallonsa batai ba sabida tasan Neman magana yake ta cigaba da sabgoginta,,

Dije kam tashi daga gun tana faman zumbure zumburen baki taje ta wanke hannunta ta dawo sai taji tana san taci towan gashi cikinta ya cika ba yadda zata yi haka tashige daki ta canja kaya ta haye gadon Nene tai kwanciyarta

Yana gama cin abinci ya tashi daga gun ya canja guri bayan ya wanke hannuwansa. haka Nene ta tashi bayya da ta iya ta kwashe kayan ta gyara gurin tana yi tana sababi shida yai mata shiru a zuciyarsa yace da rigima kenan idan kikaji da abinda nazo garin kenan duk wanann da kike shafar mai ne

Bayan ta gama gyara gun ta dawo ta zauna tana kallonsa tace "tun dazu nake jiran inji dame kazo min yau kuma ?

Murmushi ya saki yace" Nene mu kenan dame nazo miki kuwa inba da alkairai ba"

Washe hakora tayi tace "dan nema to ina jinka" tafada tana tsare shi da ido gyara fuskar sa yayi Alamar maganar da zaiyi mai muhimanci ce yace " sako ne da ga ABBA,
yace kihada kayanki gaba daya inzan koma in tafi dake dake da waccan marakunyar yarinyar.

Wani irin kallo Nene ta watsa masa tace "wallahi ka kiyayeni Ali ka rainani ko bazanje ba"
Tun yaushe ake magana daya nace bazan jeba ya kyalemu anan ina ce wancan satin shima basiru yazo nace bazan jeba saime zaku takuramin sai nabar daki na inatafi wata abuja ban zuwa tafada tana gyara zamanta"

Kallonta yayi yana kwantar da kai dan ya fuskanci inba haka yayi mata ba da akwai matsala dole sai yai aikin rarrashinta,

"Haba Nene wai yaushe zaki gane ne ba fa cewa akai kitafi kizauna acan gaba daya ba zaki dinga zuwa anan lokaci zuwa lokaci ,,kiyi hakuri mutafi kije kidan huta acan kinji uwargidana" ya fada yana murmushi

Ko kallonsa batai ba yace "kinji Nene ,, tai mai banza

Yace "to shikkenan tunda kinza6i atafi da da dijan taki babu matsala ai" cikin sauri tadago kai tana banka masa harara

Dariya ce ta su6uce masa ya din gayi sai da yayi mai isar sa sannan yace " "ai dama zabi biyu ya bayar Abba yace inkice baza kixo ba to a kawo masa dije zai sata a makarantar boko tunda anan kin hana ta karatu"

Kallon sa tayi tace "to ai sai ka jamu ka kai mu abuja nace ni bazan zuwa ahe"

"To ai shikkenan kin san zan iya ko"? ya fada yana kallonta. Ya cigaba da cewa "wallahi kiyarda kawai mutafi in ba haka ba sai ki wayi gari kiga na tafi da wacan marakunyar inga yadda zakiyi" yafada yana ya mutsa fuskarsa

Harararsa tayi tace "to katafin da ita mugani"

"Haka kika ce"? Yafada idonshi a tsaye a kan ta.

"Eh haka Na ce" tafada tana hararsa a karo Na biyu ,taci gaba da cewa munanan in da mukafi wayo babu wata Abuja da zamu ai nan ma tana karatun To! Kaji"!
kallon ta yake yana ya mutse Fuska Na sabo yace"Shikkenan tunda kin fi son A tafi da yarinyar taki zaki wayi gari ki ga ba ta nan domin ba zamu zauna da Yarinya haka ba babu Arabi babu boko kin sangartata"

Sanin Halin sa yasa na kaifi d'aya domin baya magana biyu, tunda taga yana wannan murmushin nashi tasan zai ai kata Ta kalleshi gami da gyara,zama tace " yanzu yaushe zaka tafi"?
Shiru yayi sai da ta qara maimaitawa ,yace" Nan da kwana biyu"
"To shikkenan zan bika Amma bazan Dade ba kwana biyu kawai zanyi in dawo ,domin bazan tafi in bar dakina ba ,da"yan Uwa da Abokan Arziqi"

Cikin zuciyarsa yace "Ai sai kidawo mugani Nene kenan in kika tafi kin tafi kenan,


Mik'ewa yayi yana kallon Agogon dake daure a hannunsa ,ya kalleta Cike da tsokana yace" Daga zuwana duk kin bi kin rikice sai faman fada kikeyi,kinqi ki barni Na huta"


Dariya Tayi gami da gutsirar goron ta tace"ai kai ne Ali halinka sai kai daga zuwa kafara cikin zalin "yar marainiya Allah."


Yace "zan shiga ciki in Dan huta"

"To to ,cewa zakayi sai da safe kawai ,Ai gwara ka huta nasan A kwai gajiya a tare da kai ,Allah ya bamu Alkairi" Tafada tana kokarin kunna redion ta domin sauraren taskar Labarai A tashar Redio Kano ta bello dan dago.

"To Allah ya tashemu Lafiya Uwargida kuma Amarya" yafada yana nufar hanyar dakinshi Na gidan Wanda idan ya sauka garin yake kwana ciki.

Murmushi Nene tayi ,tabi bayanshi da Kallo ,Afili tace Dan Nema sarki iyayi da Feleqe kai dai naga matarka ai ka tsaya ruwan ido"

Yana jin ta yayi mata shiru domain in ya biye ta tata sai su kwana a gurin gashi shi bacci yake ji ,bayan haka kuma jikinshi yayi masa Nauyi Wanka kawai yake son yi ,
Shi Mutum Wanda baya son zafi ko kadan.



ASALIN LABARI


Malam Ibrahim Haifafen garin Kano ne cikin Karamar hukumar Dan batta ,Mutum ne Wanda Allah yayi masa Arziqi a wancan lokacin ,shararan Manomi ne Wanda Mutane da dama suka ci suka bayar ta dalilinsa ,Asabili da Karamcinsa kwata kwata bashi da ganin kyashi ,in yaga baka da qarfi sosai zai talla fa maka har ka tsaya da kafarka.
To Allah babu ta inda baya jarrabar bawa duk wannan dukiya da Allah ya Azurtashi da shi ,Allah bai bashi haihuwa ba,
Shekararsu goma sha biyu da Aure da Matarshi Hajara,
Wannan Abu sam bai tayarwa masa da hankali ba,tunda yasan haihuwa nufi ce daga Allah ,gashi duk fadin Kano babu Asibitin da basu je ba shida matar tasa maganar dai daya CE ,duk likitocin suke fada lafiyansu lau lokaci ne bai yi ba.

Shiyasa kawai suka tattara suka barwa Allah ikon shi.

Ganin haka ne yasa "yan Uwa da Abokan Arziqi suka dinga kawo masa yaransu ,wai ko zai Aura domin yasamu haihuwa,
Yace"duk su kyaleshi ,yasan haihuwa lokaci ne idan yana da rabon haihuwa a duniya zai haihu ,ko yayi Aure ko bai yi ba,
Su kyaleshi kawai shi yanzu bashi da bukatar karin Aure


Shine fa "yan Uwa suka yi ca! A kan Hajara wato (Nene) cewar ai its ce ta mallakeshi sai Abinda tace yake yi.


To Ashe duk wannan Abinda a ke ciki Hajara Na dauke da ciki Dan wata Uku dukkaninsu basu San dashi ba.
I ta dai tanaji sauye sauye a jikinta Amma bata kawo ciki gareta ba,yau da lafiya gobe babu ,Malam Ibrahim yace su tafi Asibiti kawai a duba ta.

Tashin Farko Likita da ya dubata yayi mata a won fitsari anan ya gano ciki gareta,Dan wata Uku da kwanaki

Ya kalli Malam Ibrahim yace"matarka Na dauke da ciki Dan wata uku.

"Alhmdullihi Alhmdullhi Alhmdullhi"
Shine Abinda Malam Ibrahim yariqa maimaitawa yace"hakika babu sarki sai Allah ,ya Ubangija Na gode maka da kayimin wannan baiwar,
Yafada yana kallon doctor din fuskarshi cike da Annuri

Dr yace"tabbas Allah ne Abin godiya,yanzu zamu daura ta kan Abubuwan da masu juna biyu ya dace suyi da irin Abinci da ta riqa ci ,bayan nan kuma idan cikin yayi wata hudu sai tafara zuwa Asibiti domin a riqa Auna shi"


"In sha Allahu Malam din yafada"

Doctor ya rubuta musu Magani masu kyau sosai da kara lafiya ga mai ciki.
Sannan sukayi masa sallama suka tafi bayan Malam yayi masa Alkairi sosai da sosai


Nene ma tayi farin ciki sosai Amma bata nunawa sabida kunya irin ta fulani ,to haka dai suka cigaba da rainon cikin har lokacin haihuwa yazo.


Cikin ikon Allah Nene ta haihu lafiya cikin Dakin ta in da tasamu da Namiji ,farin ciki gurin Malam Ibrahim babu kama hannun yaro "yan Uwa da Abokan Arziqi suka riqa tayashi murna ,shiko ya din ga fitar da hatsi yana rabawa talakawa,ranar suna yaro yaci sunan Bashir.
Haka Bashir ya ta so gaban iyayenshi cikin kulawa domin Nene macace mai kula da yara gami da tsabta,
Sai da Basir ya shiga pramary 4 sannan Nene ta samu wani cikin lokacin yana shekara goma sha biyu ,wannan karon ma Malam Ibrahim yayi farin ciki haka yayi ta hidima da Nene da cikinta.
Lokacin da Bashir ya fahimci Mahaifiyarshi Na da ciki sai yayi ta murna zai samu qani,domin yana da bala'in son yara


****
Wannan karon ma Allah ya sauki Nene Lafiya a dakinta in da raqara samun da Namiji ,malam Ibarqhim yayi farin ciki sosai da sosai ,ranar suna a ka sawa yaro suna Lawan,


Nene taci gaba da rainon yaranta cikin kulawa,Bashir yana kaunar Dan uwansa sosai ,in babu makaranta shi yakewe Nene raino Dan har makarqntar Allo ya kan tafi da Lawan


Allah sarki mai yadda yaso ,shekarar Lawan Uku a duniya Allah ya karbi ran Malama Ibarahim mutuwar da ta gigita Zukatan Al'uma sosai,Nene tasha kuka daga karshe sai ta danga ga Allah taci gaba da rainon yaranta.


*****
Bashir mutum ne Na jama'a baya zama ,sosai tunda ya kammala scondry skull yafara harkar Siyasa,
A daddafe ,ya tafi ,bayaro univasity dake kano ya samu difoloma ,sai ya watsar da karatun ya shiga siyasa gadan gadan
Tun Nene bata so ,daga baya sai ta dawo tana masa Addu'a.


Dan Uwanshi kuwa Lawan babu ruwanshi domin magana ma bata dameshi ba,
Shima a yanzu yana makarantar gaba da primary


Duk Abinda Bashir ya samu Na jama'a ne ,shayasa a kasa ka masa Bashir Mai jama'a

Ganin girma yazo masa ya
Sa Nene tayi masa maganar yayi Aure domin shine cikar mutum

Nan ya nuna mata shifa yanzu bashi da wata budurwa harkar Siyasar sa kawai yake

Nene tace to yaje yaga Zainab "yar gidan kawun shi wato Kanin Malam ibarahin tace taga yarinyar tana da hankali da nutsuwa
.yace to shikkenan zai je ya ganta


Ko da Bashir ya ga Zainab sai yaji ta kwanta masa,sabida haka ba'a dauki wani dogon lokaci ba a kasha shagali Amarya ta tare nan gidan kusa da Nene dake gida ne girman gaske ,haka Bashir ya yanki guri yayi ginin zamani sosai.


Yawan kyautarsa da tausayin talakawa yasa matasa da tsaffin yankin Nash suka tsayar dashi takarar Craman ,Aikuwa Abin ikon Allah lokacin zabe yana zuwa Bashir ya lashe yazabe.

Zoka ga murna gurin jama'ar gari ,da "yan Uwa da Abokan Arziqi jama'a sun ji dadi domin suna ganin Bashir zai kawo ci gaba a yankin nasu

Lokacin Zainab matarshi tana da tsohon ciki ,Haka tai ta taya mijinta murna,
Nena ma tayi farin ciki sosai tai tayi masa fatan Alkairi gami da Addu'a Allah ya tayashi riqo,ya sauke nauyi da ya dauko


Lawan ko dashi a kai ta fadi tashi ,bakinshi yaqi rufuwa ,Sai murna yake.




A taike dai Alh Bashir yariqe mukamai da dama ta fannin Siyasa in da daga baya yasaki harkar Siyasa yafada kasuwanci ,shida wani Abokinshi Alh Auwalu ,sosai suke shi go da motoci Iri daban daban Na zamani Cikin farashi mai sauqi


i ta iya da halinshi.
Tun yana yaro yake da mugun kyankyami Abu qalilan zai sashi yai ta kwara A mai
Nene tayi kewarsa sosai sabida sun shaqu da juna


Basu jima da komawa Abuja ba Hajiya Zainab tasamu ciki Alh Bashir yayi ta murna
Lokacin haihuwa yazo Allah ya sauke ta lafiya an samu da Namiji
Nene tace A sama jamelu


To haka rayuwa ta tafi Alh Bashir Arziqi yana kara bunkasa sosai da sosai

Yaranshi hudu biyu maza biyu mata

*wanene Aliyu*
yana da bakar zuciya da miskalnci sai kai mai mgn goma bai kula kaba sai yaga dama zai amsa daya yana da bala,in tsafta dan haka ba abincin kuwa yake ciba in kacire nenensa da ummi bai yadda ko ruwa masu aiki subashi ba indai bai daga hannu ummi ya fito ba duk da cewar ruwan roba ne

Yana mutukar san ya ga yazama soja tun yana yaro shiya sa yadage sai da yatafi yai karatu sosai akan aikin yanxu haka ya kammala aiki kawai yake jira ya fara,,,





To lawan ma akwai wata daya so anan bayan gidansu yarinyace mai sanyi hali kamar sa sunanta khadija ,,

Da nene ta fuskanta tace to baza ai jinkiri ba taje ta sami yayan mahaifinsu tace to aje a ne mar mai auranta ,,

Aikam ba,awani dau lokaci ba aka sha shagali bayan duk 6angare biyu sun amince amarya ta tare anan gidan kusa da nene tunda gida ne mai girman gaske bangare bangarene ,,

Idan baku mantaba dama mlm ibarahim mai arzikine a wannan yankin nasu a wancan lokacin gidansa ma abin kallo ne


Nene tana mutukar jin dadin zama da khadija sabida irin matan nan ne masu kirki da saukin kai babu ruwan ta da hayaniya haka shima lawan din yana jin dadin zama da ita ,,

Alh bashir kam yakanzo lokaci zuwa lokaci dashi da iyalinsa yakan dan jima kan yakuma abuja shiyasa yaran sukasa saba sosai musamman Ali mutumin nene tana bala,in sansa ,,shikam Ali bai san tanayi bah
Sai tahana kowa abu tace Ali zata bawa sai yazo tabashi yace bayaci ko ya kar6a ya bayar a gabanta ba yadda zata,yi takari mitarta ta gama yai mata banza ,,

To haka rayuwa taita tafiya lawan Allah bai bashi haihuwa da wuriba sai da sukai shekara sha uku da aure sannan Allah ya a zurta khadija da samun ciki,,

Nene taita murna dan a zuciyarta take cewa shine yagaji irn haihuwata dan har tana ganin ma ko bazai haihu bashi huumm ,,,,,nace nene ai abin na Allah

Tunda khadija

Please Login or Register in order to submit comment