Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kyarma take gaishe shi


Kallonsu yai yana nazarin su sai kace wasu marasa gaskiya


Hararar Na'ima yai yace "wannan rawar jikn da kike nameye?

"Babu komai ta fada hade da sunkuyar dakanta yace " ina Ummi ne?


Cikin sauri fa,iza tace " ta hau sama yanzu ina jin sallah za tayi"


Bai ce komai ba ya Ciro wayarsa daga aljihu n jins din daya ke jikinsa sakamokon jin kira da yaji ya shigo wayar


Nene kam tace "mutum sai kace wani mala,ika daka zuwan ka Guri yara sun yi wani tsuru!,tsuru" tafada yayinda take mikewa daga inda take bayan tagama cin abincin


So take taje tai sallah itama ganin lokacin sallar yana neman wucewa,



Faruk ne ya kira shi
Cikin jin haushi yace "wai dallah malam mene wai daga da wiwa kaki barin mutane su huta sai faman kiran waya kake,iyi?


Daga daya bangaran
Shima faruk din cikin fusata yace" an dame ka din kai dan rainin hankali ne wallahi ya zai,ai in dinga kiran wayar ka kaki dagawa sabida tsabar baka da mutumci "


"An ki daga wayar me zakamin to zaka da me ni da kiran waya" yafada yana dan murmushi sabida yasan ya gama kunna faruk din


Cikin hayaniya faruk din yace "ubanka zanma dan isa kawai"


"Dallah malam kasan wannan takardun suna wajanka kasamu muna ta faman ne masu ehe?


Dan dariya Ali yasaki kasa kasa yace " wane takkadu kuma?


"Bayan ka zo ka kar6a saga hannuna" yana sane so yake ya kular da faruk din ta kaddun suna hannunsa


Tsaki faruk din ya ja yace "ni zaka mayar wani shashasha ko

Ai ganin zuwa kafito dasu dan raini wayo kawai "


Kashe wayar yai ya mai da ita aljihunsa


Ummi ce ta sakko.bayan ta idar d sallahr


Tace "kaida waye ne kuke magana naji kamar magana sama sama. Ya mutsa fuska yayi yace "faruk ne


"Au ko danaji. Yana ina tafada tana kallon falon,,


"Bai zo ba waya mukai mybe kin ganshi yanzu ai akwai wasu takkadu da muka cike zai zo ya karba su"


"Ummi mun same ku lafiya ?


"Kalau muke" yace " wai ina jameel ne ?


Ummi tace " bai Dade da fita ba kasanshi kayan bol yasa yafice ai yau sai an ganshi kuma"



Shiru yai bai CE komai ba domin dai bayadda zaiyi da jameel kasan cewar sa tun yana yaro kwallo tashiga ransa yana masifar son kwallon kafa shiyasa ko wace irin bol za,a buga kallonta baya wuce shi ga musu acikin abokai sunayan "yan kwallo kuwa Babu wanda bai sani ba



"Ummi.Mai kika girka min ne ?

Yafa da yana marai raicewa harararsa tayi tace Babu abinda na dafa "


Dariya yai yace "nasan wasa ne Ummi na CE fa,,



Nasan tayi min girkinta mai dadi da gamsarwa"





Shiru Ummi tayi bata ce komai ba


"Kinji Ummi na wallahi wata irin yunwa nake ji please "yafada da yanayin shagwaba



Su dija dake gefe kam kallon ikon Allah take ganin irin tabarar da Ali yakewa ummi sai kace wani yaro,,


Ta6e baki tayi aranta tace dube shi abin ma ko kyau bai mai ba


Ummi tace " ni kam Ali wanann larurar taka ta isheni wanann wane irin abu ne to in kayi aure yazakai iyi? dole dai kaci abincin matar taka domin dai kasan mu nan mun sallama ka ato"!


Mikewa tayi ta nufi kchin


Dija ce takewa fa,iza magana kasa kasa tace "wai dama haka wannan ya Alin yake sai yaita wani abu wai shi maitsafta yai tacewa mutane kaza mai "


Da sauri fa,iza ta kalli inda yake zaune. ta kalli dija tace "ke wallahi Babu ruwa in yajiki tam"


Shikam bai San me sukeyi ba domin air pic ne a kunnashi yana jin kira,a tare da shek malam sulaiman ya na masifar son kira'arsa, idanoshi a lumshe,,



Ita ma dija kallo gun tai tana ya mutsa fuska bata cekomai ba ,,


Tace "wai ina Nene ne?

Fa,iza tace" " ta tafi sallah tashi muje muyi muma "



Ummi CE tashigo da Abinci cikin wani plete
Ta ajiye a gabashi "gashinan ai "

Tafada tana zama cikin kujera,,

Bude idanowanshi yai yace " iluv ummi na godiya nake"


Kallon Cikin plete din abincin yai wata lafiyar yiyar waina ce ta shinkafa taji miya sai kamshi take gefe lemo wanda yake bala,in so da ummin take masa shi kadai zo6o ne ake mai wani irin hadi wanda ummin ce ta,iya shi



Sauko wa kasa ya yi ya tankwashe kafafunshin yai bissimillah ya fara ci



Sallamar faruk yai tare da shigowa sabida ya saba babu wani shamaki da gidan sabida yazama dan gida abotarsu da Ali tun da kuruciya karatu ma tare sukayi komai na su irin daya sai banbancin hali da kowa ya ke dashi ,,


Shi faruk yana da sakin fuska da fara,a sabanin Ali da yake miskili na ,ajin karshe


Shigowa yai yace "ummi wanan mutumin ya dawo zai farasaki wahala ko?


Yafada yayin da yake zama shima a gefen Ali,,


Murmushi ummi tayi tace"kai ma kafada ai faruku"


Yace" ummi ke ce kike wani damu wa dashi yai zuciya ya nemo mata ai mai aure kowa ya huta sai ka wai yazo ya dinga saki wahala wallahi kidaina bashi abincin ki yayi girma da cin abincin gida,ehe"


Dariya ummi tayi tace "wai baka mai fada ne shi baya ganin kai har ka haihu ko zuciya bayayi ba shima ,,


Yace "ummi kuka tsaya wani lallabashi me ake jira wai tunda da matar a hannu mun she da sai kawai a shafa fatiha in yaso takarasa karatun a dakin nata ita siyama n,,


Wani irin kallo Ali yakewa faruk din yana faman harararsa


Shikam faruk dariya ya kara kecewa da ita sabuda yasan ya gamma kunna Ali ,,a sabili da yasan ya tsani ai mai magana siyama,n



Faruk yace "kinga bamu gaisa ba ma

Antashi lafiya" tace "lafiya lau ya hjiya binta " yace "tanan lafiya lau wallahi,,


Nene ce ta fito daga wani daki acikin falon bayan ta,idar da sallah kwanciya tai tana lazimi sai taji surutu yai yawa ita a tunanin ta ko jameel ne



Zama tai da carbin a hannunta tana kallon faruk tace "au! ummaru kai ne ka zama haka" tafada tana rike bakinta dariya faruk yayi yace "me nazama kuma nene,, dan sun saba da nene sosai tunda shi mutum ne mai yawan wasa da dariya shiyasa duk sanda nene tazo garin sun dunga fafatawa kenan,,



Tace "kazama wani burgujeje haka aikin sojan ya mai dakai iyi"


Dariya yai yace "nene kenan wace irin tsaraba ki kawomin ne?


"Wace tsaraba, wancan yabari mukayi yabi yadaga mana hankali wai ana neman ku gurin aiki ,,


"Aikam dai wallahi kinsan yanayin aikin namu wani aiki zamu fita muyi gobe shine dalilin da nai mai waya yatawo"


Nene tace "ai kuna kokari aikin ku akwai hadari sai dai muyi ta tayaku da ado,a Allah ya tsare mana ku


"Ameen ,Ameen yace "nene kunzo lafiya

Ya aka baro "yan uwa "??

"Kowa lafiya lau wallahi ya iyalin naka"? murmushi yai "yace sunan lafiya lau ai zan kawu su ku gaisa kan ki koma "


"Ai da ka kyauta kuwa ". yace " insha Allah"



Ummi ce tace" ai nazata bacci ki kayi da naji shiru ,,

Nene tace "ko daya baccin yaki zuwa kwanciya nai ina hutawa wallahi , wai ina jameel ne"?


Ummi tace "ai bai dade da fitaba yagama zaman jiran zuwanki ganin har daya tayi baku karaso ba shi ne ya fita kuma
Bai dade da fita ba kuka karaso,,










"AF ko da naji" Nene tafada tana kallon Ali da yake cin Abinci tace "kai kam haka ake babu tayi kayiwa mutane shiru iyi?


Banza yai mata faruk ne yasaki dariya yace " nene kenan ki rabu dashi ai akan an mai magana shine yake ci wa mutane magani

Aure kuwa mutum sai an masa, ko yaki ko ya so"


Nene tace " au ! maganar aure ne baya so tafada tana rike baki


Ummi da tun fara maganarsu bata samu su baki sai yanzu tace "ke ma kyafada nene"


Kallon Alin nene tayi tace "ina ce akwai matar a hannu to me ake jira ehe"


Shidai bai ce mata komai ba cin abincin sa yake cikin kwanciyar hankali,


"Ko akawo ma abincin ne faruk "?


"A,a ummi alhmdulilah wallahi kinsan da zanci bazan tsaya wani sai an tambayeni ba"


"Tace nasani ai naji kai shiru ne ai shiyasa na tambayeka"



Ali kam tashi yai daga gun bayan ya kammala cin abincin,,

Canja gurin zama yai ya zauna yana dan ciccin magani fuskar sa a hade


Da kallo nene tabishi dashi tace" haka dai sai dai aci a bar kayan a gun aci ai tusa kai ko kunya bakaji abokin ka har da da kai ka zauna kana faman iyayi "


Wallahi kamar kinsani duk cikin abokanmu shikadai ne yai saura amma duk muna d aure,,



"Rabu da shi ummaru nasan abinda zanyi bari abban nasu ya dawo in ya so sai inji me ,akatsa Ya jira "


Kansa dake sunkunye yana faman latsa waya ya dago yana hararar Nene fuska a ya mutse yace "mezakiyi to?


"Sai kaji abinda zanyi "

"To wai ke ina ruwan ki ne iyi" ya fada ya na kallon ta


"Da ruwa na ehe me kake nufi sai muzu ba maka ido ko to baka isa ba tunda kungama sasanta kanku kai da siyamar to gwara ai a gama"



Kallonta yai yace "wayace miki mun sasanta kanmu ehe?



"To wai ma ni nataba cewa ina son siyama ne da kuke ta wannan abin ya fada yana kallon ta



Baki nene tasaki tana kallonsa tace "au! Mu zaka kamayar kananun mutane iyi Ali"



Dariya faruk yayi yace" karya yake nene. Yana sonta yana san dai yai wasa da hankalinku ne"


Wani duka Ali yakaiwa faruk yace " wallahi zanci ubanka mara mutumci "

Cikin sauri faruk ya kauce yace "au dan nadafadi gaskiya shine har da duka"



Cikin Hayaniya Ali yace "dallah malam kai mana Shiru wallahi ko,in ballo ma ruwa kai kasan a inda zan je inyi dan iska kawai"



Tsaki ummi tayi tace" kana da aiki Ali wa kake so ka mayar karamin mutum iyi"? tafada tana kokarin tashi d ga gun



Umm !! "ke ma dai kya fada inji nene" itama tana kokarin barin gun ganin lokacin sallahr la,asar yayi tace" ai kamar ka auri siyama kagama. tokaji"!!



Wani Kallo Ali yakewa faruk bayan nene tabar gun,yace "wai kai wane irin dan iska ne ehe. Haka kawai za kazo ka 6allo min aiki"


Dariya faruk Yayi "yan isa ka biyu dai ni da kai nizaka kashewa waya dan rainin hankali kawai "


"Malam ina takkadunnan Iyi?

Banza Ali yai masa sai da ya kara maimaitawa sannan yace "sai katashi kaje kaduba d kanka "


"Wallahi sai Nafisa taji labarin Mufida tunda baka da mutunci "


"To taji mana angayamaka tsoranta nake yi ko an ce maka ita kadai zan aure"


Ali yace "haka kace ko?

"Eh man"

Wani murmushi Ali yasaki yace" zakaga aiki da cikawa wallahi banza mayen mata aure ko shekara biyu bakaiba har ka soma hange"


Cikin sauri faruk yadawo ya zauna yace. "Rufan asiri wallahi bana iyawa da masibar Nafisa don Allah kar kafada mata wallahi inta ji shikkenan na dai na bacci kishin bala,i ne da,ita"



Dariya Ali yai yace "me kagama cewa dazu iyi"?











Faruk yace " me nace kuwa ai bakarya nayi ba yaza,ai kadinga yaudarar yarinya alhalin tasaki jiki zaka aure ta kowa ya shaida sannan kace bakasan zancan ba"


"Nida bakina na ta ba ce maka zan aure ta?"

"Sai kafada meyasa tun farko abun ba kafada ba sai yanzu d magana tai nisa kace bakasan zancan ba ai kasan wa sane"


"To dan ubanka sai ka aura min ita tunda kai kahaifeni"


Dariya faruk ya kece da,ita yace "to wai mekake nufi ne da kaketa wani hanya hanya ne ,,kasan dai yarinyar nan bakowa take kulawa ba sabida kai sai kafadi dalilin da yasa zakace bazaka aure taba"





Cikin yanayinshi kamar koda yaushe yace "ba taimin ba shine dalilina" ya mutse fuska


"Baka,isa ba wallahi" inji faruk,

Cikin mamaki Ali ya kalli faruk yana mamakin rantsuwar da yayi yace " au rantsewa kake"?


"Eh inji faruk banga dalilin da yarinya zata bata lokacinta ba sannan daga baya wata magana ta faru bayan kasan wannan zai zubarwa da Abbah kima da mutunci acikin abokai dashi kansa maihaifin siyamar wannan zai iya jawo zumuncin nasu yayi rauni
Dan haka wannan maganar ma ka,ajiyeta a gefe Sam bata,taso ba" yakare magana yana mai da nuffashi.


Kallo sa ya ke yace " to dakake wani tada jijiyar wuya dole zakaimin ne ehe" yafada fuska a hade


"E dole za,ai maka tunda kai bakasan daidai ba"


Wani murmushi Ali yayi yace "na bar maka kaje kai tabiyu da ita tunda da ma amatse kake da mata dan iska kawai"



Harararsa faruk yai yace "eh naji laifine dan naso mata ai su ababen a so ne"


"Kar kai tunani bansan halin dakake ciki ba da irin magungunan da kake karba a gun Dr Hashim dan iska jarabbabe ai kai mata Biyu ne suka dace dakai domin mace daya bazata iya daukarkaba "



Duka Ali yakai mai yace "wallahi zanci ubanka har nakai ka "



"To kar ya aikai maka" faruk yafada yana barin gun yace "dallah zo ka dauko min takkadun inkama gabana"

Banza Ali yai mai yacigaba da duba wayarsa "wai ba magana nake ba bafanasan raini hankali kasan nawa halin inyatashi "


Mukulin shashin nasa ya jefa masa yace "malam kar ka isheni kadauka kaje kadauko da kanka mana "


"Daba a hannunka suke ba meye na da womin da su iyi kabi kazo kadamu mutane"




Kwafa faruk yayi bai ce komai ba ya dauki key din dakin yai fita sabida yasaba da halin sa a zuciyarsa kuwa shima shiyasan abinda zai kyokyoyamishi na rashin mutunci




Shiru falon yayi inbanda Ali da yake zaune yana fama d waya,,



Su Dija ne suka fito itada fa,iza suna faman kyalkyala dariya kwata,kwata ba su lura da mutum a gun ba sai da suka zo tsakiyar falon sannan dija ta ankara ,,tsaya wa tai tana gyara fuska fa,iza kam kai tsaye tibi ta je ta kunna tace " yanzu za,afara amma maimaici ne sai kokarin neman tashar a rewa 24 take ,,


Ita dai dija batace komai ba tana nan atsaye a gun,,


Jiyoyawarwa da zatai bayan tagama kunna musu kallon me zata gani ya Ali ne a zaune yana kallonta da fuska a murtuke


Cikin sauri tace ya ali anyi ni lafiya? "zo nan" ya fada batare da ya amsa gaisuwar ba jiki na kyarma taje ta zauna a gefenshi yace "me nagaya muku iyi"?


Shiro fa,iza tai tana zare ido yace" badake nakeba dan ubanki "


"Imm dama kace mudaina yawan kalle kallen da muke"


Wani rankwashin ya kaima ta cikin sauri fa,iza ta rike kanta


"Bayannan fa? Iyi " yafada yana kallon dija dake tsaye har yanxu a,inda take ,,hararar ta yai yace "tsayuwar uban mekikewa mutane anan gun?


Cikin tsawa yace "zo nan"


Kallon sa tai babu digon tsoro ko kadan a fuskarta ita mamaki mata tsaya tana yi ganin irin rawar jikin d fa,iza take yi,,


"Bada ke nake ba ko sai nazo nayi kulikulin kubara dake anan "



cikin rashin tsoro taje itama ta zauna kusa da fai,za tana dan zumzum bura baki itafa bazata yadda da haka ba ya bar ganin anzo gidansu ta fada a zuciyatta



Kallon ta Ali yai yace "ina dan kwalinki" ? sai sannan dija ta tuna ta cire dan kwalin ta tun a dakinsu fai,za


"Yana daki" tafada idanonta atsaye a kansa,


"Tashi dallah kije ki dauko nan bagidan ar'na bane ,,kika yadda na kuma ganinki babu dan kwali sai nayi miki aski wallahi"



Zare ido fa,iza tayi tana kallon dijan tana dan zungurinta da kafarta alamr tatashi taje ta dauko dan Ali zai iya yi mata asikin bakaramin aikin shi bane


Itakam in yaiwa dija aski ai ya cuceta a yanda take da gashinan a,zuciyar ta take cewa ina ma ita take da gashin da dija take da shi da an ga iyayi,



Tashi dija tayi ta nufi dakin tace "wallahi bazan dawo ba ai ba ubana bane kai sai kadinga ta kurawa mutane



"Je ki kiramin Na'ima" yafada yana kallon fa'iza bayan dija tashige

Tashi tai jiki a sanyaye tace yau mun shiga uku dakin nasu tashiga ,,


Na'ima na kwance bacci take yi "yaya Na'ima kitashi "ta hau bubbuga gadon cikin bacin rai Na'ima ta bude ido " wai meye ne "tafada tana hararar fa,izan


"Ya Ali ne yake kiranki "

Kallon fa,izan tace" me ye ?

"Nima bansani ba ya ce ne kizo" tashi tai tana fadin "wallahi kika jawomin duka akan kin zan rama domin dai ni nasan ba abinda nayi tun tafiyarsa a to"


Zumbura baki fa'iza bata cekomai ba ta kalli dija dake zaune tana duba hoto nan su tace "shine kikaqi dawowa ko?


"To me zanyi in nadawo iyi" tafada tana tabe baki


Bata ce mata komai ta fita daga dakin Na'ima ma barin dakin tai sukabar dija ita kadai


Yana zaune inda yake sabanin dazu shida jameel ne yanzu shima da wowarsa kenan


Kallonsa Ali yai yace" wato kai bakaji ko"?


"Bro menayi" inji jameel din


Hararasa Alin yai yace " ban sani ba yanzu a war mu nawa da shigowa garin ehe kafita tun safe ,,wai kai a kwallo zaka kare ne"?


Sun kuyar d kai jameel din yai ya ce "wallahi bro wannan mezafi ce shiyasa kasan mune shugabbani shiya sa gobe ma zamu fita,,


Kallon sa Ali yake shi ga maganar da yakeyimasa amma yana sako wani zancan daban kwafa yai yace " lallai jameel yayi nisa "


Kallon su Na'ima yai yace " ke Na'ima mena fada mu kafin inje kano?


"Wato ba kwajin magana ko"?


Cikin inna,ina Na'ima tace "wallahi bama fita in dai ba makaranta zamu ba ko gidasun siyama katambayi ummi ma kaji"



"Wallahi ku kiyayeni, ban hanaku kallon ba amma ku tabbatar babu wani abu wanda yashafi harkar karatun kar kusa shi a cikin shirmenku wallahi uban mutum zanci ni"


Nene ce ta fito daga dakin tace " kamar maganar dan gida na nake ji"



Dariya jameel ya ke yace " a,a uwar dakina barka da zuwa"


Kafin takaso har yatashi yaje ya rungometa. Yana dariya

Ita ma dariyar take tace "mai gida babu awo babu ce fane wai kai haka ake auran ne"



Tafada tana zama a daya daga cikin kujerun da suke falon

Yace "kece ai ba ai miki gwannita ,,yanzu me kike so?


"Babu amma jeka nemo min fura da nono " to jameel yace kin samu yanzu za,a kawo ".ya fada yana kokarin barin gun wanka yake so yai har ya fita ya dawo yace "wai ina wannan "yar kauyan yarinyar ne ko bada ita kikazo ba "?


Harararsa nene tayi tace "e"


Dariya yai ya fita dan yasan fada tai kawai yasan nene bazata iya tafiya mai nisa irin wannan batare da dijanta ba



Kallon su Na'ima tayi wa "yanda sukai tsorutsoru a gaban Ali ko motsin kirki bau wacce take


Shikam Ali hankalinsa baya kansu kallon sa yake bayan ya canja tashar da Fa'izaa ta kama


Labarai yake saurara a tashar aljazeera,,


"Ku kuma meye haka , sai kace wasu masu nai man gafara " tafada tana rike ha6a



Shirou sukai babu wacce tayi maganan acikinsu,,


Kallon Alin nene tayi tace "miskili kafi mahaukaci ban shaushi kenan,,

"Wai me suka yima ne" ?



Banza yai mata haushinta yakeji yasan tunda tace zata gayawa abba maganar siyama sai tafada yasan halinta da tada zaune tsaye kawai zatazo ta dama mai lisssafi,,


Sai da ta kuma mai maitawa sannan yace
"Meye ruwanki to " yafada still idansa na kan tv



"Da ruwa na wannan cinzali ne ai , ya zaka zaunar da yara guri guda ka hana su motsi sabida mugunta, ai ba sojojin ne su ba ko masu laifi ballanta kai musu irin wannan horan"



Kallon Fa'iza nene tayi tace "ina dija n take ?


"Tana dakinmu " " tashi kije ki ki ra wu min ita


Kallon Alin tayi yana kallonsu ta gefen idon sa bai ce ko mai ba




A darare ta tashi ta nufi dakin nasu











tare suka shigo ita da dijan kai tsaye inda nene take ta nufa ta zauna kan hannun kujerar da take kai



Fai'za ma kusa da nenen ta zauna dija tace "baki baccin ba nene "?


"Yau she zan iya bacci yanzu ai yamma tayi "


Kafin ta rufe bakinta ummi ce ta sakko daga sama tana kwala a sabe mai aikinsu kira ,,


Kallon Alin Ummin tayi tace "au kananan ashe ba ka fita ba?


"Eh nadan tsaya sauraron labarai ne"


Bata ce komai ba tane mi guri ta zauna tana kara gaida Nene



Asabe ta shigo cikin sauri tace "gani hajiya"


Ummi ta kalli Nene tace "meza,a da fa miki ne?


"Da ni kuke tambaya iyi"?

Nene tafada tana kallon ummi


"A,a nene wai ko kina sha,awar cin wani abin "


"A,a duk abinda aka dafa zanci bana son tsurfa daga zuwa za,tsiri tambayata "


Dariya ummi tayi tace" Nene kenan"

Kallon asaben tayi tace "kije ki shirya abincin yadda ya kamata"


"To" asabe tace ta bar gun


Canja tasha ummi tayi zuwa mbc,maxx

Wani shiri suke nunawa na kiwon lafiya ,,


Na'ima tace "don Allah ummi mayar mana arewa mukalli dadin kowa duk da cewa sun kusa gamawa"


"Ba maimaici suke ba yau"?


"Eh ummi ai bamu kalla ba duka ba"


Ba tace komai ba ta mayar musu da shi arewa


Tsaki Ali yayi kasa kasa ya mike yace " ummi nafasa fita sai anyi magariba zanje in dan kwanta" yafada yana kokarin barin gun



"Aikam dai da yafi tunda faruk din yazo gwara ka huta zuwa an jima "tafada tana kallonsa,


Yace "ai haka za,ai sai yanzu gajiyar take damuna wallahi ,,


"To ai dama dole "


Kallonsa nene tayi yayin dayake kokarin barin falon


"Ai gwara daka tashi daga gun kazo ka kankane kamar wani kai ne mai gidan sai faman mulkin mallaka kakewa mutane,,


Dariya yayi kadan "yace kanki akeji "


Ya fita daga falon shashesa ya nufa yattada key din jikin kofar budewa yai yasan. Faruk ne ya barshi yana ganin asarar mayar mai dashi



Zama yai gefen katuwar katifar dake dakin yana kokarin balle botoran rigar dake jikinsa ,,


Kwanciya yai rigingine ya daura hannayenshi saman goshinsa



Tunanin. Maganar dazu yake dasukai da faruk gaskiya shi kwata,kwata siyama ba taima sa ba bayajin sonta ko daya a ransa sai irin na addini isilama


To amma maganar faruk abin duba wace tunda hakikanin gaskiya siyama da iyayenta sun saki jiki zai aureta dasu kansu Su Abbanshi da ummin


To amma babban abinda suka kasa ganewa game da shi baya ra,ayinta tunda shida bakinsa baita6a gaya musu yana sonta ba ita take haukanta har suka fuskanci hakan ta bangaranta



To shikam mutum ne da yake girmama mai kaunarshi baya ga hakama bashi da ra,ayin wulakanta mutum ballanta me kaunarsa shine abinda yake dubawa yakasa furta wa da bakinsa baya ra,ayinta ,,


Shiru da yayi shiya basu karfin gwiwar kamar shima yayi na,am da abun


Gaskiyar lamari babu wannan a ransa ,,shifa har yanzu bai ga macan da tai mai ba wacce tatara abubuwan da yake so ba



Duk da cewa akwai tarin "yan matan dasuke karakaina akansa to amma su dun ma akwai matsala dan duk macen da tayi ma tallan kanta to tabbata bata da kamun kai



Shiyasa yake musu kallon dai-dai



Shikam bashi da mafita a wannan lamari zai iya auran siyama sabida irin kaunar da take nunawa a gareshi to amma kam. Zai yi aure in yasamu dai dai dashi,,


Wannan shine hukunchin da ya yanke ,,



To a can falo kuwa yaran samun sakewa sukai sabida dodon su ya bar gun ,,kallon su suke cikin raha suna dariya ,,nene ma takan sa mu su baki cikin surutun nasu



Abbah ne yai sallama
Hannu shi rike da wa yoyinsa bayanshi kuwa salmanu ne rike da jakar abban da sauran ta muhiman takaddunsa ,,



Cikin ihu Fa'iza ta tashi taje ta dane shi "abbana sannu da dawowa "shima cikin dariya ya rike ta yace Fa'iza n abbah ya gida?


"Lafiya kalau abbanmu" Rike hannusa tayi suka jera har inda nene take



Zama yai a kujerar da take fuskantar nene


"Sannu da zuwa nene kunsha hanya ko"?


"Yawwa sannu aikam dai mun same ku lafiya?"


"Lafiya kalau nene yaya su baba malam da sauran "yan uwa?"


Nene tace " kowa lafiya

Please Login or Register in order to submit comment