Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

motivate the mind of readers




Na
Maryam Ismail
Muhphat



Page2⃣7⃣to2⃣8⃣





A ranar batayi isashen bacci ba,ga dai tsananin ciwo ga kuma kewar iyayenta uwa uba da mijinta ya juya mata baya,har safiya tayi Sarena bata kara sanin inda kanta yake ba,donko tasha amai dukta galabaita ciki ciki take numfashi.




Da misalin karfe11 na safe,Mama dukta damu tun jiya rabon data saka Sarena a idanunta amma ba halin tambaya,suko gasu a parlo sai sheka dariya suke suna fira,karaurawar dakin ta shiga kara alamar damai shigowa,yunkurawa yayi yana fadin"Manab harya karaso kenan".yana budewa kuma zatonsa ya zama gaskiya musabaha sukayi sannan ya shigo cikin gidan a parlon suka zauna,Nabila kuwa kara matsewa a jikin Jawad take ko kunyar fingilallun kayan dake jikinta batayi tana wani narkewa a jikinsa.



Wani bakin cikine ya ziyarci zuciyar Manab a kufule yace"friend ina Sarena?"


Wata faduwar gaba ta ziyarci zuciyar Jawad dandanan ya daure fuska yace"oho ka duba part dinta zaka wani dameni".



Mikewa yayi ya isa part din nata buga kofan yake amma shiru babu ko motsi kasada kawai yayi ya tura ,parlon a gyare sai zuba kamshi yake ko ina tsab,jiyo nishinta da yakeyi a hankali a hankali yasa ya kara isa kusa da bedroom nata aeko itace zaro ido yayi ,da sauri ya karasa ya tura kofar,yadda ya ganta ya masifar tada hankalinsa da sauri ya dawo main parlo yana kwalawa Jawad kira,


Yatsine fuska Jawad yayi a hankali ya furta "Menene kuma".



" lallai Jawad,ka kosan me kake aekatawa da iliminka zaka kashe y'ar mutane,Sarena ba lafiya sosai ko tashi bata iyayi "cewar Manab



" to mezan mata ko yarinyace karama da batasan hanyar asibiti ba,goyata kakeso nayi,nifa malan ba cewa nayi ka daman ba"Jawad ya fada.



Wani far da idanu Nabila tayi sannan tace"haba Habibi nah,ya kamata ka dubata,sannan ka kaita asibiti pls mana"



Tsaki yaja yace"Hada ke za'a tursasani wify gaskiya bazan iyaba ,aetanada hankali karki kara saka kanki a irin wannan don Allah".


Duk yadda Manab yaso Jawad yazo ya dauko Sarena fafur yaki saima ya tashi yaja Nabila suka wuce daki yace inya fita yaja masu gidan.sosai ran Manab ya baci waya ya ciro ya kira Salim ya tambaya ko yana hospital, ya amsa da eh,cikin hanzari ya koma wurinta a lokacin ko motsi batayi,babu yadda ya iya a dole ya dauketa ya fito yana gudugudu ya sakata bayan mota yaja da gudu sai hospital din salim.


Cikin gaggawa aka shiga da ita emergency a rude Manab ya rike hannun Salim yana fadin"pls Salim do ur best ,banaso Sarena ta mutu wallahi ina jinta tamkar ciki daya muka fito banaso na rasata".


Dafa kafadarsa Salim yayi ya daga masa kai ya shiga ciki.



Safa da marwa ya shigayi yana tunanin shinwai meya shiga kan Jawad wannan wanne irin cin zaline haka,yafi awa hudu a nan yana jiran Salim sannan ya futo suka wuce office.



"Wai aekin me Jawad yakeyi yakeson kashe y'ar mutane da ranta" cewar Salim.



"Hm inako zan sani tsohwan Dan iskan ya biyewa wannan y'ar iskar yarinyar ita ke juyashi fuska kamarta biri". Manab ya fada.



" to gaskiya Sarena tana bukatar kula,kagadai ya ciwan zuciyar data samu da ba'a kawota Asibiti ba at anytime zata iya rasa ranta,uwa uba ga cikin dake jikinta tana fama da laulayinsa".



Da sauri Manab ya dago kai yace"Ciki ,kuma da Cikin sa a jikinta yabarta tana wahala gaskiya Jawad ya canza ban taba tunanin zewa Sarena haka ba inka duba irin son da yake mata amma bari mu gani"
Waya ya Ciro ya fara kiransa ,harya fitar da rai akan zai dauki wayarsa sannan ya dauka ajiyar zuciya Manab yayi sannan yace"Jawad wai meke damunka kanaso ka gama da duniya lafiya kuwa?,ka sakawa yarinya ciwan zuciya har yana baraza a rayuwarta,ga Cikin daka dirka mata kuma ka barta cikin wannan halin".



"Dakata Manab tadai sakawa kanta me nake mata,nifa ko sunanta banaso kana ambatamin indai kanaso muci gaba da zama wuri daya,sannan ni tunda aka kawota so d'aya na rabeta sannan kacemin tanada Ciki,toni ban karba ba ba Cikina bane,taje ta nemi Wanda yayi mata shi" be jira ansar Manab ba ya tsinke wayarsa.



Murmushi Salim yayi yace"karka damu Manab wannan bayin kansa bane mudai muyi masa addu'a mu kula masa da matarsa har Allah ya sauketa lafiya shine kawai".




Dakin da aka kaita Manab ya shiga,Sarena yakebi da kallo tayi fari tas abunta ta kara kyau drip ne like a hannunta ,hankalinta kwance tana bacci sai fitar da numfashi takeyi.



Salim ya saka masu kula da Sarena dare da rana,bata da matsalar komai a asibitin ta murmure tayi kiba abunta,kullun Manab da Salim suna tsaye a kanta kwananta biyar aka sallameta,Manab ya dauketa ya maida ita gida yayi mata fada sosai akan tayi hakuri kuma kada ta saka damuwa a ranta.



********



Parlo ta fito dama tunda ta dawo take dakon ganin Jawad ,zaune ta samesa har kasa takai ta gaeshesa tayi masa banza.


A hankali tace"idan bakaji tausayinaba ae kodan D'anka da yake Cikina ka tausayamin my Love ".



Tsawa ya daka mata wacce tasa ta firgicewa lokaci daya tana kyarma.sannan yace" karki kara kirana My love ,Cikin Jikinki ba nawa bane,kije ki nemi Uban danki karuwa kawai,kuma daga yau kin daina zaman banza a gidannan duk wani aeki ke zaki rika yinsa bance ki zauna ki hutaba ,inko naga akasin haka zaki gane kuranki,wannan kadan daga hukuncin Cikin shegen da kika kawomin ne"kafa yasa ya halbeta harta fadi ya wucewarsa.




*ALKALAMIN MARYAMA* ✍🏻



Gaisuwata a gareki kawar alkairi masoyiyar Asali na,Khadija Haruna Abdulkadir alkairin Allah yakai maki inayinki irin sosai dinnan.





Share and comment


Muhphat luv
[01/08, 8:54 PM] Cweet Mrym Mhphert: *ASALI NA*




🌈kainuwa writer's association


United we stand and succed:our ambition is to entertain & motivate the mind of reader's




Na
Maryam Ismail
Muhphat



Page2⃣9⃣to3⃣0⃣




Wani irin kuka ke shirin kubuce mata,da sauri ta toshe bakinta ,sai wasu zafafan hawaye da suka kwaranyo daga idanuwanta ,bakin ciki cike da zuciyarta ,kallon Jawad kawai take harya bacewa ganinta,kasa mikewa tayi daga inda take saida Mama ta kamata sannan dishi dishi ta soma gani a haka tabi bango zuwa dakinta a kan chair ta kifa kanta ta fashe da kuka.




Nabila kuwa duk abunda yake faruwa tana ta window tana lekensu ganin tahowar Jawad yasa tad'anyi baya ,yana shigowa suka rungumi juna kallonta kawai yake ,sannan ya hada bakinta da nashi ya soma tsotsa kamar ya samu sweet daga nan wasa ya sauya,na jawo kafafuna nayi waje😀




*AMERICA*



Zaune take a chair iskar garin na ratsata ,yanayin yayi dadi ga Wanda yake kwanciyar hankali,hango fuskarta nayi idanuwanta rufe suke cikin bakin glass tayi kyau sosai ,saidai hawayen dakebin gefan fuskarta kallo daya zaka mata ka tabbatar tana cikin tashin hankali sosai .



A hankali Mr Samol ya karaso gareta kamata yayi yana goge mata hawaye yace"meke damunki wify".



Bakin Lissa na rawa ta furta"Sarena ,inason y'ata anya banyi kuskuren barinta a Nigeria ba,gashi inata kiran wayarta bana samu".



Murmushi kad'an yayi yace"ki daina damuwa,kinsan mijinta na sonta sosai zai kula da ita,kuma muma zamuje ganinta kada ki damu"
Da kalamai masu dadi ya shawo kan Lissa harta daina kuka ta dauki tunani irin nashi.




Some months later.



Cikin Sarena ya shiga wata na tara a kowanne yanayi zata iya haihu,bayan hanyoyin da su Hajiya sukabi wurin kasheta ita da cikin Amma basuyi nasara ba,hakan ya basu dama suka maisheda Sarena cikakkiyar baiwa a gidan,ko kadan idan bakayi mata mugun saniba bazaka taba ganeta ba tayi baki, ta rame, ta fita daga hayyacin ta koma kazama don a sati so daya take wanka,ga wasu kaya da basu da maraba da tsunma su take sakawa,daki daya suka bata a part din masu aeki wata guntuwar tabarma CE shinfide a dakin sai gefe kullin kayanta na sakawa,rayuwa kenan.




Zaune take a gefan tabarmarta kanta a gwaiwarta hawayene kebin fuskarta daduk ta koje .



Banko kofar dakin Nabila tayi tana yan harare harare tare da toshe hancinta ,wankin dake hannunta ta watsa a jikin Sarena tace "ke dallah tashi ki wankemun kayannan sannan ki wankemun Mota zan fita".


D'ago kanta tayi tanabin fuskar Nabila data gama konewa da mayukan kara fari na kanti" tace haba,wai bakya tausayina kiji yadda nake amma ko'a jikinki kamar kema ba y'a mace ba".



Saurin dakatar da ita Nabila tayi sannan ta kwashe da dariyar mugunta tace"tausayi aeni ban sanshi a kanki ba,na tsaneki yadda na tsani mutuwa ta,dama nace zan sakaki kukan wuya tunda har kikayi kuskuren had'a hanya da abunda nikeso".



Mikewa Sarena tayi sannan tace"tir da irin wannan rayuwa taki,sai naji ke keyi nikejin kunya shin baki girmama addininku ,kobashi ya basu damar auran mace fiye da d'aya ba,amma ke kike jayayya,kodayake ae addinin ba kama jikinki yayi ba"
Dukawa tayi ta kwashe kayan wanki tana tafiya da kyar ta soma wankin kayan tanajin kunar rai a tattare da ita.



Jawad kam ya zama saniyar ware banda Hajiya da Nabila babu mai rabarsa su kadai ke morarsa harta Manab da Salim sun rabu dashi donko kadan bazasu iya daukar halayyarsa ta yanzu ba ko sallah bata damesa ba ,saidai daga gefe suna masa addu'a





Zagaye kawai Umma take tsakar d'aki abun duniya ya dameta ace d'anta na cikinta ko kadan yanzu be damu da itaba yau kusan wata biyu bata sakashi a idonta ba,bazai yiwuba dole tasan abunyi gaskiya ,dole Jawad ya dawo gareta.



Da sallama Momyn Manab ta shigo gidan cike da fara'a mata meson mutane,cikin mutunci Umma ta taryeta suna murnar yaushe gamo,part din Ummu suka shiga a bed suka zauna



A hankali cike da nazari Momy tace"wai meke damunki ?,kika wani fita hayyacinki".



"Ba dole ba,yaufa wata biyu banga Jawad ba,kuma yana cikin garin nan ,an rabani dashi ko ta waya baya iya kirana gaba daya ya koma bashiba" cewar Umma.



Murmushin takaici Momy tayi tace"haka nikejin labari donkoni ya daina zuwa wurina,ya kuma rabu dasu Manab, dama idan na gansa yake d'an debeman kewar *MINAD* to nima ya gujeni,ki tashi ki kama addu'a babu abunda yafi karfin Allah d'anki ze dawo gareki.


Haka Momy tayita bata shawa ta gari,sannan suka rabu akan cewa zasuje gidan jibi.



Flowers duksun cika gidan and'an jima ba'a gyara wuriba,me kyara aka kirawo yazo yayi masu aski,a lokacin kuma Nabila ta fita zuwa wurin bokanta akan ya kashe mata Sarena tunda hartayi bakin maida mata magana.




Askin yake Mama da Sarena suna Sharar flowers din dake zubewa a kasa,sauri Sarena tayi ta dago a firgice har cikin kwalwarta abun ya ratsata ga wani irin mumunar faduwar gaba,a hankali ta dago kafarta daga tudun data taka.

Riketa Mama tayi sannan tace Bari na tona wurin naga menene a ciki,tsab Mama ta tone ramun,wani irin ihu suka rigaji yana fita faga ramin, hannunta na kyarma ta kwaso kayan dake ciki,layune iri iri ,ga katon abu gunki sak sai wani gashi,ga kuma rigar Sarena data Jawad an dauresu wuri daya.



Duk abunda ke cikin layun saida Mama ta karantasu tasan makarar asiri bata nunawa kowa ba facce Sarena ,wuta ta hada ta konesu kurmus tare dayin addu'o'i har suka cinye sannan tasa ruwa ta wanke tokar tas.




Bacci yake tare da mafarki,hannu taketa miko mashi daga cikin bakin ramun da take,tana kuka tana fadin ka tai makeni,zuwa yayi cetonta ya mika mata hannu sai aka janyeta kasa,ga jarirai har biyu sai binsa suke suna kuka,suna kiransa da Abba.
Firgigita ya farka yayi zufa sharkaf a hankali ya furta *MINAD* ina kika shiga kika barni ,zumbur ya mike jikinsa ko kadan ba kwari ga jiri yana gani,tunani yakeyi yaushe rabon da yayi sallah Alwala ya dauro ya soma jero salloli.




Nabila kuwa bokanta ya tabbatar mata saiya sadu da ita maniyinsu shine mahadar gubar kisan Sarena,bako musu ta bishi suka shige bukkarsa suka soma masha'arsu dukda warin da bokan yakeyi haka ta daure har sukayi ya samu maniyyin ya hada maganin a kwalba ya bata tare da sharadin ta tabbatar Sarena tasha wannan maganin cikin ruwa ko abinci.cike da farin ciki ta dawo gida hankalinta bekai kan wurin ajiyarta ba ,ta wuce part dinta tayi wanka don tsabtace jikinta bayan ta gama take shedawa Hajiya yadda sukayi.



Umma kuwa ko kadan taki bacci yanzu ko ta fara saluda zaune take a sallaya tanata yiwa danta addu'o'i,addu'ar uwa akan danta.


Typing ba dadi kuyi hakuri da wannan pls



Comment
Share
Like



Muhphat luv
[01/08, 8:54 PM] Cweet Mrym Mhphert: *ASALI NA*



Na
Maryam Ismail
Muhphat




🌈kainuwa writer's association


United we stand and succed:our ambition is to entertain & motivate the mind of reader's





Page3⃣1⃣to3⃣2⃣





Cike da kisisina Nabila ta mike ta nufi dakin Jawad tana zuwa kai tsaye ta tura kofa,ta shige ciki ,kan sallaya ta hangosa,gabanta yayi wata mumunar faduwa tuni kyarma ke shirin kwace mata,daurewa tayi ta karasa garesa zata kwanta a jikinshi,wata iriyar tsawa ya daka mata Wanda yasa sora kadan ta zubo fitsari.



Binta yayi da mugun kallo sannan yace"uban waye tsaranki da zakizo ki kwanta a kaina,kuma daga yau karki kuma shigomin daki babu sallama tashi ki fita ki bani wuri Jaka kawai".




Kallonsa kawai take tana hawaye a zuciyarta tana fadin na shiga ukku ni Nabila ya akai haka ta faru,mikewa tayi ta fice da gudu tana isa daki waya tayi saurin dauka tana kiran number din hajiya,bugu daya ta dauka baki na kyarma take fadin"Hajiya na shiga ukku na,Yaya Jawad ,duk abunda nayi masa Hajiya ya warware sallah fa yakeyi yanzu kumani yake kora daga dakinsa tsantsar tsanata tananan kwance a zuciyarsa"kuka ya kwace mata.



"Rufe bakinki kinji,daina damun kanki bazamu gaji da bannatar da miliyoyi ba akan farin cikinki,kije kiyi aeki akan wannan mayyar kafurar yarinyar,ki fita harkar Jawad ni kuma zanje wurin malam karki damu"
Da irin wannan maganganun gurbatattu Hajiya ta kwantarwa Nabila hankali harta Dan daidaita sannan sukayi sallama.




Fitowa tayi don duba ajiyarta kamar yadda ta saba ,ganin an tone wurin batasan lokacin data kurma uban ihuba,tare da zaro ido ta dafe kai,ba damar tayi tambaya a gane da saka hannunta a abun da suka gani wurin,rai bace ta juyo zuwa part dinta.



Duk abunda takeyi akan idanun Mama da Sarena take yinsa suna kallonta ta window,numfasa Mama tayi tace"Allah ya shiryi mai hali irin naki,ke kuma Allah ya juyo da hankalin mijinki a wurinki".



Murmushi kawai Sarena tayi tace a gurbatacciyar hausarta"na gode,Amma ni kasarmu zan koma Mama ,na fasa auran dashi".




Ko kadan Jawad bayajin karfin jikinsa kwance yake rufda ciki hankalinsa tashe,abubuwa da yawa sunata dawo masa akai,ji yayi daga kwance kamar ana juyashi ga tashin zuciya,da gudu ya fada toilet ya soma kwarara amai,bakinkirin dashi ga wari,ya dade yana yinsa,kamar fitar wani abu take a lokacin yajishi ya koma sawat har wani karfi yakeji a jikinsa,wanka yayi ya fito ya shirya cikin kananan kaya,ya feshe jikinsa da turaruka masu dadin kamshi yayi matukar kyau cikin wando black da riga red ,wayarsa ya dauko ya soma kiran layin wayan Manab.




Shiko Manab zaune yake gaban Ammi sunata fira akan matsalar Jawad din tana fada Masa anjima zasuje gidan ita da Ummansu suga meke faruwa.



Karar wayarsa yasa yakai dubansa garesa cike da mamaki ya furta Jawad,dauka yayi a sanyaye jin muryar Jawad a sanyaye yasashi sakin ajiyar zuciya yace"friend ya kake".



"Nrml kana ina ,zanzo yanzu" Jawad ya fada.


Murmushi Manab yayi yace"Angon Nabila da wuri haka,ina gida".


Wani irin tsaki Jawad ya saki sannan yace"banza kawai ,dallah ka daina fadamun haka"be jira amsa ba ya kashe wayarsa ya dauki key din motarsa yayi waje.




Gefe take tsaye ita da Mama ya fito hankalinsa bekai Kansu ba,Mama zata gaeshesa Sarena ta rufe mata baki ,kallonsa kawai takeyi yayinda wasu zafafan hawaye kebin kuncinta.harya ja Mota ya fita akan idanuwanta.





Nabila ganin ba kowa da gudu ta shiga dakinsu Sarena ganin kwanon abincinta a gefan katifarta da alama shizataci ,cikin sauri ta warwaro kullun maganin ta zuba ta motse abinci ta rufe,ta fito da sauri ta koma part dinta.



Kallon Sarena Mama tayi, tace"har yanzu kina son mijinki,amma kuma kince zaki rabu dashi".



Goge hawaye Sarena tayi tace"ina sonsa,Amma bazan zauna dashi ba,baya sona"


"Kinga kada kiyi kuka,kinga kinada ciki banaso kina damuwa,muje kici abincinki kada yayi sanyi kinji y'ata".



Kai tsaye dakinsu suka shiga ,zaunar da ita tayi ta jawo kwanon ta mika mata ta dauka spoon ta bata,ta wuce waje don ida aekace aekacenta.ita kuma ta soma cin abincin.





Jawad yana isa gida ya gaeshe da Ammi,sannan yake fadawa Manab mike faruwa kuma shi yanzu besan yazaiyi da Sarena ba harta saurareshi,sannan ya roki Ammi dasuje gidan,wucewa sukayi suka dauki Umma,suka wuce gidan Jawad.





Sarena kam ta cinye abinci tsab,kai tsaye taji cikinta ya soma juyowa kamar zai fito kai tsaye jini ya soma bin kafarta wani azababban ciwan ciki ya taso mata,Mama ta soma kwala ma kira,Amma bazata jitaba kasancewar tana kasa,a hankali ta soma rairafe tayo hanyar waje.




Da Sallama su Jawad suka shigo main parlor din,Mama ce kadai gaesawa sukaci gaba dayi sannan Ammi tace"ina Sarenan takene".



" tana ciki abinci takeci bari na kirata"kafin Mama ta rufe baki,suka hango Sarena tana fito da rairafe a hankali ta dafa kofa ta mike bakinta na rawa tana so ta furta sunan Mama.




A razane Ammi ta dago tana kallon cinyarta dake dauke da wani bakin tabo a jiki ,bakinta ta kyarma ta fada da karfi"Minad".



A razane kowa kebinta da kallo suna maimaita sunan data fada Minad.



Cikin Sarena ya kuma murda mata ta saki wani razanan ihu ta tafi zata fadi,dukansu sukayi kanta,kafin kowa ya isa gareta Ammi harta isa ta riketa,tana kuka tana fadin"Ku taimaka mun kada Minad dina ta mutu don Allah",tuni Sarena ta some a hannun Ammi,Nabila na gefe tana kallonsu .



Cikin sauri Manab ya fizgeta yayi mota da ita,da gudu suka rufa masa baya.




Comment
Share
Like





Muhphat luv
[01/08, 8:54 PM] Cweet Mrym Mhphert: *ASALI NA*



🌈kainuwa writer's association


United we stand and succed:our ambition is to entertain & motivate the mind of reader's



Na
Maryam Ismail
Muhphat


Godiya gareku masoya TABON D'A NAMIJI,ina bada hakuri na jina shiru kwana biyu da kuka jini naji dadi sosai wasu sun kirani,wasu sunman text,insha Allah ranar Sunday zaku rika jina kullun Alhmdllh yanzu shine gabana.





🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚
Last page
🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚


Sadaukarwa ga kainuwa writers Allah ya kara hada kanmu.






Mota Manab ya shiga suka rufa masa baya,kowa da abunda yake fada sabanin Jawad da tunda aka ambaci Minad ya rasa gane komai yanaso yasan tayaya Sarena zata koma Minad dinsa wannan wanne irin rudadden Asali ne a tattare da ita.


Da kyarma Manab yake kiran Salim yana fada masa ga Sarena ba lafiya su taimaka mata,kai tsaye Emergency suka shiga da ita yayinda kowa ke safa da marwa a wurin suna jiran saka mako.





Su Mr Samol kuwa yaune jirginsu ya sauka Nigeria saboda rigimar Lissa kullun kuka take tace wai tayi mafarki Sarena na cikin damuwa da kunci hakan ya tilasta masu tahowa don duk jiya basu rintsaba,kai tsaye gidan Jawad suka nufa nan Mama ke sanar musu Sarena na asibiti,tun kafin su isa Asibitin Lissa ke kuka suna isa ko parking basuyi ba ta bude murfin mota ta fito tana tambayar sisters din wurin,a rude suka isa da ita wurin hakan yayi daidai da turowar da akayiwa Sarena a Bed an fito da ita daga Emergency zuwa wani dakin na daban,wani irin ihun kuka Lissa ta saki lokacin data gama bin jikin Sarena da kallo duktayi baki ta lalace kwatakwata batayi kama da Sarenar data bari ba,kai tsaye Jawad ta nufa tana dukansa tana fada masa mugayan kalamai da nuna masa irin tsanar data masa,dakyar Mr Samol ya riketa ta fada jikinsa tana fadin"I will never forgive u inhar Sarena ta mutu,kaima ka jera sunanka a matsayin matacce I promise u this".



Kallonsu Salim yayi yace muje Office,Manab da Jawad sai Mr Samol suka bisa nan ya masu bayanin gubar da aka bata,amma Allah ya taimaka sunkaita asibiti da sauri gubar batayi tasiri a jikinta ba Alhmdllh ita da abunda ke cikinta suna cikin koshin lafiya.


Wata sanyayyar Ajiyar zuciya Jawad ya saki yana godewa Allah ,sannan suka fito,a dakin da aka kai Sarena suka shiga har Daddy da Abba sun iso rigima na neman ta balle tsakanin Ammi da Lissa.



Cikin kuka Ammi tace "wannan tabon na cinyarta akwaishi tsakiyar bayanta,kuma Ku duba wannan Minad ce,".


Nanfa ido ya soma raina fata ana bude bayan Sarena saiga tabo ya bayyana.


Matsowa dab da ita Ammi tayi tace" ki tashi Minad,yauga mahaifiyarki a gabanki tana cike da kewarki da soyayyarki dama ban taba sakawa raina kin mutu ba,ina matukar sonki nasan zaki dawo gareni"


Wani irin nishi Sarena tayi a hankali ta bude idanuwanta da suka lumshe ta fara bin kowa na dakin da kallo baki na rawa take mikawa Momy hannu tana fadin"Momy na,ki tafi dani banason nan ".




Matsowa kusa da ita Momy tayi ta dafata tace" share hawayenki gatanki ya dawo Mind ki kalli wannan itace Mahaifiyarki bani ba ki bude kunne ki saurareni".




Lissa bata jira neman Shawar mijinta ba ta fadi komai ke faruwa da tun ranar da suka dauki Sarena har kawo yau,gaban Ammi taje tace"kiyi hakuri bama da zabin daya wuce wannan,komun dawo da ita,zasu iya cutar da ita kumani Soyayyar ta ta shiga raina, amma kuyi hakuri".



Kowa na dakin hankalinsa tashe yake masu kuka nayi ,Abba ko da Umma sunyi sufa sharaf suna faman kamekame,ananme kuma Mama ta shigo dakin ta kalli Nabila da Hajiya kai tsaye ta mika video din dake hannunta kowa ya kalli duk abunda ke faruwa,ganin ba sarki sai Allah yasa Nabila saluda tana Neman afuwa da fadin abubuwan dake faruwa.




Da sauri Abba da Hajiya sukayi waje kankice me suka shige Mota suka fita da gudu be kallon ina yakeyi da mota horn wata babbar Mota ke masu, basuji ba kafin motarsu Daddy ta iso motarnan ta murjesu tas jikinsu yabi kwalta dakyar aka tattarasu aka sallacesu zuwa kabarinsu,tashin hankali da sauyin yanayi yasa Sarena shiga labour room bata shirya ba ta haifo yaranta yan Maza guda biyu masu masifar kama da Jawad sosai .




Nabila kuwa kai tsaye ciwo ya sakota gaba ta kamu da HIV ga wasu kuraje da takeyi suna fitar da ruwa mai wari duka jikinta ta rame tayi baki ta lalace,a cikin mabaratan asibiti suke zama,



Umma ko ta dade da saluda,ta zauna tana istigfari ta koma ga Allah,sosai Ammi ke tausaya mata kullun cikin sadaka da ibada take.



Alhmdllh Sarena ta koma Minad a ranar sunan yayanta suka karbi musulunci ita da Daddy da Momynta,yaranta kuma sukaci sunan Abba da Daddy suna kiransu da Ashman da Ashwan,Mama ke kula dasu.



Some years later




Farin ciki ya dawo wa family dinsu,hankali kwance tuni Minad tayi sauka,yaranta sunyi wayau sosai Alhmdllh sun zama yan uwa dasu Mr Samol, soyayya tsakanin Jawad da Minad ta kara karfi hankalinsu kwance duk wani damuwa ta yaye masu Minad tayi kyau tayi fari yar gata a wurin iyayen ta da yayanta ga kuma mijinta rayuwata hankalinsu kwance.



Godiya ga sarki Allah daya nunamin karshen wannan littafi.





Muhphat luv
Downloaded from GNOVELS.COM.NG




This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG
to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/gnovels

Twitter : https://twitter.com/gnovels

Telegram : https://t.me/gnovels


Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4
Chapter 5

Please Login or Register in order to submit comment