Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

abinci waja waja. Ita Anty Wasila goɗai goɗai da ita gata yaya ce amma haka take shafe kwanaki a gidan in tazo garin, shiyasa Zayyad har ya fara rainawa 'yan uwanta saboda yadda suke nuna kwaɗayinsu a fili, ƙarin haushinsa muddun in suka zo haka Rashida take banzatar da lamarinsa ta mayar da hankalinta kacokan kansu bata damuwa da buƙatunsa.


Mahaifinsu Zayyad mai suna Ahmad ya rasu sai Hajiyarsu Halima wacce 'yarsa ilham taci sunanta, Aslam kuma yaci sunan babansu Ahmad, yana da yaya mace Bilkisu suna zaune a Abuja da mijinta Kamaluddeen yaransu huɗu, sai Zayyad sannan Asiya wacce itama tana aure a malali yaranta biyu, sai Mukhtar da yake karatu a KASU.


Ɓangaren Rashida kuma ita ce ta biyu a gidansu, tana da wa Salis, sai Rashida, sannan Haruna sai Anisa sannan Zaliha, ita Wasila yarinyar yayan babansu ce amma a gurin mahaifiyarsu Rashida ta tashi shiyasa suka taso tamkar uwa ɗaya uba ɗaya.


Zayyad da Rashida auren soyayya suka yi kuma Alhamdulillahi a wancen lokacin sun samu fahimtar juna, yaransu biyu Halima (Ilham) 'yar shekara bakwai sai Ahmad (Aslam) ɗan shekara Huɗu. Babban saɓanin da suka fara samu shine yadda Rashida take da mugun kuiya musamman a gurin yin girki, ta mayar da Zayyad tamkar gauro mara mata kullun abincinsa yana waje, dan sai yafi sati bai ci abincin gidansa ba saboda sakacinta, musamman in ya dawo bata gama ba zai fice yaje rastuarant ko yaje gidan mahaifiyarsa yaci saboda baya ƙaunar jira dan ba yi da juriyar yunwa. Idan kuma aka ce watan azumi ya kama to dama baida abun buɗe baki a gidansa, saboda kwata kwata Rashida bata mayar da hankali ta fara aiki da wuri balle a samu ta gama aci akan lokaci, hatta yaranta tana horar dasu da yunwa tsabar kuiya da yayi mata yawa, ga rashin bawa shinfidarsa muhimmamci saboda shegen saurin barci gareta duk inda aka ce goma tayi to tana nan ta hangame baki ta soma barci, sai ya dawo daga inda yaje bata san ya shigo ba, haka yake yawan azumin litinin da alhamis yana ragewa kansa zafi saboda marabarshi da mara mata abu kaɗan ne. Tarin matsalolinta ya sashi soma kule kulen mata a waje musamman waɗanda suka haɗu a shafin sada zumunta na facebook da Instagram, badan yana sha'awar ƙara aure ba sai dan kawai ya riƙa samun in da sai rage lokaci kafin dare yayi ya shigo guda, ko kuma in ya dawo haka zai ɓata lokaci yana chart da 'yan mata kala kala tun baya kauce hanya har ya fara biyewa suna irin hirar nan na batsa, duk da shi mutum ne mai matuƙar tsantseni da aikata zina, sharholiyarsa a iya waya yake yi shima bai yarda da tura hotunan tsiraici ba sai dai zantukan batsa dan ragewa kansa zafi. Hakan yasa ya haɗu da wasu natattun 'yan mata su biyu Zubee da Seema, da yake su yan hannu ne babban burinsu shine su samu damar da Zayyad zai kwanta dasu, duk da suna kawaye amma basu damu ba ko kishin junansu ba tunda rayuwa ce ta bariki.


Matsalolin Rashida sune suka jawo rashin jituwa a tsakaninta da 'yan uwan Zayyad, tun yana ɓoye damuwarsa har sai da Hajiyarsa tazo ta sani, ita da kanta tasha zuwa tana bawa Rashida shawarwari akan zamantakewa dan ta gyara, saboda tana son Rashida kuma ita irin surukan nan ne masu sauƙin kai da hali sam ba tada takurawa matar ɗanta, amma baisa Rashida ta karɓi gyara ba sai tayi biris da shi taga kamar ma takura mata take son yi, gata sam ba tada kunya bata tauna magana kafin ta yi shi wannan yasa zamansu ya koma zaman haƙuri duk kuwa da irin son da Zayyad yake yi mata bai taɓa tunanin ƙara aure ba a ganinsa har da ƙuruciya zata gyara.


Sai dai kuma tun sa'ilin da yayi tozali da Safna ya kamu da zazzafar soyayyarta yaji yana buƙatarta a cikin rayuwarsa, shiyasa ya yi ƙoƙarin samun zuciyarta har suka kawo gaɓar yin aure, hakan yasa shi ya ja baya da 'yan matan da yake kulawa a shafin sada zumunta ya mayar da hankalinsa kan Safna kawai. Batun gidansa kuwa dama tuntuni yaƙi mayar da hankali ya gyara side ɗin dake cikin gidansa, wanda a da niyyyarsa zai saka 'yan haya in kuma ƙaninsa Muktar ya kawo munzalin aure ya tayar da 'yan haya ya aje matar a ciki, sai gashi ashe da rabon Amaryarsa ce zata tare a ciki, shiyasa ya mayar da hankali har sai da ya kammala gyaran.


Lokacin daya nunawa Rashida zai ƙara aure sam bata ɗauki lamarin da gaske ba, dan tasan yana matuƙar son ta saboda da zai yi mata kishiya da tuntuni yayi irin yadda mutane ke zugashi, amma data ga da gaske ne sai ta kwantar da kanta bata ɗaga masa hankali ba dan tasan tunda yayi niyya sai yayi, kawai dai fargabanta kar ya auro wacce zata kwace mata shi, shiyasa tayi yadda zata yi ta shigewa Safna a jiki dan tasan wacce irin mace Zayyad zai auro mata, tayi sa'a Safna tana da sauƙin kai tana matuƙar girmamata, suna yin waya da chart a tsakaninsu, wannan yasa sosai Zayyad yake ganin zasu samar masa da zaman lafiya a gidansa kuma ba ƙaramin farin ciki yake yi da haka ba, shiyasa yake ƙara kyautatawa Rashida duk abinda tace tana so sai yayi mata domin ya sata farin ciki, amma kuma duk a banza dan har yau ba sauya halinta tayi ba tana cigaba da yi masa riƙon sakainar kashi wanda hakan ke ƙara tunzurashi da ya auro Safna.


***


Gidansu Safnah.


Zayyad yana isa gidan yayi parking yana fitowa sai ga Yaya Mudan ya fito zai je siyo abu, ya isa gabansa suka gaisa kana yace ya shiga cikin gida bari ya kira masa ita, Zayyad yayi masa godiya tare da bin bayan Mudan daya nufi cikin gida, sai da ya fara ɗauko masa tabarma ya shimfiɗa a simintin tsakar gida daga gefe, kana ya shiga kwalawa Safna kira ta amsa daga cikin falo.


To ki fito ga mijinki ya zo, gashinan a tsakar gida.


To tace masa kana ya fice ya nufi inda zashi, ba jimawa Safna ta fito cikin dogon Hijab riƙe da tire a hannunta da jug da kofi biyu akai sai gorar ruwan swan da kuma plate an rufe shi da ɗan uwansa plate.


Rahma Ce.


_Ban yarda a juya mini labari ba ko ayi afmani da wani ɓangare na labarin ko kuma satar fasaha, ko a mayar mini da shi Audio a ɗaura min shi a wata kafa na media ba tare da izini na ba, sannan ina gargaɗi ga masu cire sunana a cikin labarina su saka nasu tare da sakinsa a shafinsu, ban hanaku ɗaura labarina ba amma a barmin sunana tare da barin rubutuna yadda yake, da fatan za a kiyaye_
[05/09, 7:12 pm] null: https://chat.whatsapp.com/D5ISXoMOGGR9PPoswkybsj


ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH WABARAKATUH KUNA INA NE MUTANNAN ARZIKI KUHANZARTA KUSHIGA WANNAN GROUP MAI ALBARKA KADA AYI BABU KU , MUNA ARHA MUNA HANA BASHI💕MUNA TURA KAYA KO INA DA YARDAR ALLAH CIKIN AMINCI. DA MUTUNTA JUNA , MUNA KASUWANCI DA AMANA , ZAKUJI DADIN KASUWANCI DAMU .

Ga abubuwan da muke siyarwa kamar haka 👇🏻:
KAYAN KITCHEN
WRAPPERS
JAKUNKUNA
TAKALMA DA KUMA SUPPLEMENT.


MASU KYAU DA INGANCI , YAR UWA ME KIKE JIRA? MAZA HANZARTA KI SHIGA LİNK DON SAMUN KARIN BAYANI KO KUMA KU TUNTUBENI TA WANNAN NUMBER DAN SAMUN KARIN BAYANI . 08033938993 .


UA_ENTERPRISE suna maraba da masu siyan d’ai d’ai ko sari 🤗🤗🤗


*AMARYAR ZAYYAD*


Na


©®Rahma Kabir MrsMG.
Wattpad @rahmakabir


Page 3


Safna ta aje tiren a gabansa kana ta zauna nesa kaɗan da shi tana cewa.


Amincin Allah ya tabbata a gareka Sirrin Zainab.


Ameen Wa Iyyaki. Ya mutanen gidan.


Alhamdulillah duk kalau suke.


Masha Allah! Amma kafin mu kai ga hira, ki fara gabatar mini da abinda kika tanadar mini cikina ya ɗauka tukuna.


Murmushi tayi wanda yasa kumatunta lotsawa dimple, tare da matsawa gabansa ta buɗe plate ɗin Samosa data soya shi ɗazun, Zayyad tun kafin tace masa gashi yayi saurin zura hannu a ciki ya ɗauka ya kai bakinsa ya fara ci, yana irin santin nan da mirgina kai dan yayi masa matuƙar daɗi, Safna dai murmushi kawai take zuba masa kana ta ɗauki kofi ɗaya ta shiga tsiyaya masa kunun madara, Zayyad ya yi saurin katse ta da cewa.


Meye wannan kuma ko yoghurt ne?


Sha dai kaji?


Ta faɗa tana miƙa masa, Zayyad ya amsa tare da kai kofin bakinsa ya kurɓa, wani irin garɗin daɗi ne ya shammaci maƙogoronsa bai san sanda ya kafa kofin a bakinsa ba ya shiga kwankwaɗa, sai da ya shanye kafin ya cire kofin yana sauke ajiyar zuciya mai ɗumi, ya kalli Safna cike da tsantsar ƙauna.


Allah yayi miki albarka, yadda kika faranta mini ubangiji ya faranta miki sannan ya cika miki burinki na mallakar Zayyad.


Wannan karan dariya ne ya kubce mata ta shiga yinsa a hankali sautin yana fita.


Ya baki ce Amin ba kina min dariya.


To ai gani nayi kamar sai an sanya maka waigi, wannan irin santi kamar ance maka ga Safna a cikin gidanka an baka halak malak.


To me ya rage nan da wasu 'yan kwanaki ƙalilan ne komai zai tabbata har abada. Amma batun gaskiya ko miye wannan abun ya mini zallar faɗi, na dai san an saka madara dan ƙamshinsa ke dukan hancina, amma me kyau ki faɗa mini me kika bani ne haka mai daɗi?


Wannan shi ake kira da kunun madara, kuma shi kasha.


Wow amma gaskiya ya kayatar da ni, ban taɓa shansa ba amma ki tabbatar in kinje gidana zaki cikani da salo salon girkinki Ruhieee.


Ya yi maganar yana jan ƙarshen tare da lumshe ido yana saka hannu a gefen zuciyarsa, sosai Safna ta saki dariya, nan dai suka cigaba da hirarsu gwanin sha'awa har misalin ƙarfe tara da rabi kafin suka yi sallama, amma fa saida Safna ta kakkaɓe masa duk wani damuwar da yazo dashi kafin suka rabu ya nufi gidansa cike da bege da ƙosawar son kasancewa da ita.


Ko da Zayyad ya isa gida ya tadda kayan kallo a kunne kitchen a buɗe amma ba kowa a falon, ga plate ɗin abinci da suka ci suka barshi a falon banda ƙamshin taliyar manja babu ƙamshin dake tashi, haka ya kashe soket ya jawo ƙofar kitchen kana ya wuce ɗakinsa, ya cire jallabiyar ya rage ƙananun kaya ke jikinsa ya kwanta tare da jan bargo ya rufe ƙafafunsa, Safna ta riga ta cika masa ciki baida buƙatar abinci, kuma da yake yasan halin matarsa bata girka masa komai ba, da zai kirata ya tambayeta zata ce ta manta, guntun tsaki yaja ya kunna data ya fara duba WhatsApp domin ganin saƙonninsa, dama time ɗin chart ɗinsa kenan dan inya fita aiki ba yida lokacin waya saboda hidima da mutane, nan saƙon Safna ya shigo tana cewa.


Allah yasa mijina ya sauka gida lafiya.


Sai da ya saki murmushi kafin ya bata amsa da lafiya lau sai dai yaga bata online, nan ya fito ya shiga duba saƙonni nan ya samu Seema tana online, sai suka fara chart daga nan kuma suka cigaba da hirarsu na sakin layi, haka ya shagala har kusan sha ɗaya da rabi, ya ce mata zai sauka barci zai yi suka yi sallama tana yi masa mitar itafa ta gaji da ja mata rai da yake yi ya kamata yazo su haɗu su jiyar da juna farin ciki, bai bata amsa ba ya sauka dan yasan ba zata taɓa samun wannan damar ba yana matuƙar kyamar aikata zina, wannana chart ɗin da suke yi shima so yake ya yakice shi ya huta tunda Safna tana gabda shigowa gidansa, Zayyad barci yake ji amma kuma cike yake da buƙatar mace a wannan lokacin musamman yadda yasha kunun madara ya tada masa da maitarsa, dan shi da zarar yasha madara da dare ko yogot to tabbas sai ya motsa masa buƙatarsa, ya duba agogon wayarsa sha biyu saura nan ya shiga wajen kira ya lalubo number ɗin Rashida ya soma kiranta sai dai kash tasa wayar a silent ta saka a jikin chargy a wuta, sannan ma barcinta take yi hankalinta kwance dan tuni tayi nisa dan koda ya dawo tayi barci Anisa ce keta danne danne a waya tana chart, Zayyad sauke ajiyar zuciya yayi mai ɗumi ga mace har mace amma sam hoto ce bata damu da buƙatarsa ba sai nata, dan in abin ya motsa mata tasan ta jira shi ya dawo duk inda yaje, kota dinga kiransa a waya tana jiransa. Zayyad ji yayi kamar ya fashe da kuka ko hakan zai sama masa kwanciyar hankali amma koda yayi kukan ba zai yi masa maganin halin da yake ciki ba, sai ya sauka daga gado ya ɗiba ruwan flaks a marfinsa ya shiga shansa yana kurɓa a hankali har ya shanye farin ruwan ya rufe ya koma ya zauna yana mayarda gumi, daga haka kuma yaji sauƙin ƙullewar marar, sai miƙe ya kashe wuta ya koma ya kwanta ya rufa da bargo ba jimawa barci da ɗauke shi.


*****


Washegari Zayyad sai da ya makara sallar asubahi dan wajen shida da kwata ya tashi, ba ɓata lokaci ya juye ruwan flaks ɗinsa yayi wankan tsarki dan jiya yayi makarfi bar katai kuma ikon Allah da Safna yayi saboda ya kwana da ita a ransa, daya fito wanka ya shirya ya gabatar da sallar asubahi a ɗaki ya cigaba da zama yana jan lazumi har gabanin ƙarfe bakwai, kafin ya kwanta a gado ya kunna data yana duba shafinsa na Facebook, bayi da sauran yin barci dan zai kai yara makaranta ga kuma yana so ya biya gidan mahaifiyarsa ya gaisheta kafin ya wuce shago. Yana a kwance yana jin hirarsu Rashida sai hidimarsu suke yi dan ba tashi take ba, yana matuƙar mamakin sakarcin Rashida tare da ganin wautar yayarsu da ba zata iya ɗaurata a hanya ta gyara ba, ya kula haka rayuwarsu take tun daga gida tarbiyyar da suka samu kenan, tsaki yaja yayi Allah ya kyauta a ransa kana ya sauko daga gado ya shirya cikin ƙananun kaya ya kimtsa ɗakinsa kana ya fito lokacin wajen ƙarfe bakwai da Rabi.


Ina kwana.


Anty Wasila ta ambata.


Lafiya kalau Alhamdulillahi kun tashi lafiya.


Ta amsa da lafiya lau, sai ya wuce zuwa kitchen dan can yaji motsin Rashida, Aslam ya isa ga Abbansa da gudu ya rungume shi yana cewa.


Abbanmu.


Na'am Aslam ɗin Abba, ya naga ba kuyi shirin makaranta ba ina Momynku?


Momy tace uniform ɗinmu yayi datti kuma bamu karya ba.


Ran Zayyad ne ya ɓaci sai ya saki hannun Aslam ya nufi kitchen ya shiga ya tsaya yana ce mata.


Rashida ya naga yaran nan basu shirya ba?


Abban Ilham ashe ka tashi, ina kwana?


Lafiya lau, ina tambayarki baki bani amsa ba.


Rashida ta shiga sosa ƙeya.


Dama uniform ɗinsu yayi datti ban samu damar wankewa ba na manta, amma yanzu nake shirin naje na duba in zai yuwu su saka haka in sun dawo na haɗa na wanke.


Amma nasan uniform ɗinsu kala biyu ne, kuma sun saka ɗaya shekaran jiya monday da jiya talata, yau laraba ya kamata ace ɗayan yana wanke sawa zasu yi tunda sau bibbiyu suke saka kayan friday su saka sport wear.


Wlh ranar Lahadi guda ɗaya na wanke da tunanin washe gari zan wanke ɗayan shiyasa.


Ta faɗa a sanyaye, Zayyad daga hannu ɗaya yayi ya dafe goshinsa dan tsananin takaici, ya sauke hannu yana hura iska mai ɗumi daga bakinsa ya girgiza kai ya fice, a nan ƙofar Kitchen ya tsaya ya shiga kwalawa yaran kira nan suka zo da sauri, ya dubesu.


Kunyi wanka?


Ba muyi ba dama sai mun dawo makaranta muke yi.


Ok kuje yanzu ku sauya kaya masu kyau ku ɗauko jakunanku na makaranta ina jiranku a mota.


To suka ce masa suka isa ɗakinsu da gudu, Zayyad ya koma kitchen ya duba lunch box ɗinsu yaga an aje a gefe ba a jima da wanke su ba, ya isa ya haɗasu cikin kwandonsu ya ɗauka ya fice ya isa ƙofar ɗakinsa ya saka key ya juya ya fita daga falon, a mota ya jira yaran har suka fito suka shiga sai ga Rashida ta fito da gudu.


Abban Ilham basu karya ba ga arish ɗin na gama soyawa yanzu zan haɗa musu tea.


Bai kulata ba ya tayar da motarsa ya ja baya tare da buga hon mai gadi ya buɗe masa ya cilla motarsa waje ya hau hanya ya wuce, Rashida taɓe baki tayi tana jan tsaki ta koma ciki anty Wasila tana cewa.


Wai ke haka kuke rayuwa a gidan nan gabaɗaya bai ɗaukeki a bakin komai ba, anya amaryar da zai aura bata nima shiga tsakaninku ba.


Ke dai anty kya faɗa amma kuma yadda na karanci yarinyar tana da hankali da ilimi bana tunanin zata yi wani abu, halin namiji kawai yake gwada mini.


Amma wlh ke shashasha ce an gaya miki masu ilimin basa shagala ne to su suka fi iskanci ma, dan haka bana tantama yarinyar nan tana niman shiga tsakaninku Allah.


In tayi wani abu ma to kanta ta yiwa ba ni ba, dan Zayyad ɗin ban ɗauke shi a bakin komai ba, bai isa ya wulaƙanta ni ina kallonsa ba ni da shi kar tasan kar.


Allah ya kyauta ni in kin gama haɗa abin karyawa ki kawo muci dan cikina karta yake yi.


Anty Wasila ta faɗa tana yamutse fuska, Rashida tace.


Ai na gama bari na ɗauko.


Sai ta shiga kitchen ta cigaba da aikinta.


**


Zayyad rastaurant ya wuce da yaran ya yi parking suka shiga ciki, yasa aka haɗo musu breakfast mai kyau soyayyan arish da kwai tare da miyar albasa, sai ruwan lipton da kayan ƙamshi, nan suka ci suka ƙoshi daga bisani ya bada lunchbox ɗinsu aka zuba musu abinci jelop ɗin shinkafa da nama duka su biyun ya biya kuɗi suka fito suka shiga mota ya wuce dasu makaranta, ya kashe kusan dubu ashirin a wannan abincin da suka ci. Suna isa makaranta suka ɗauki kajunansu da kwandon abincinsu suka wuce ciki, office ɗin headmaster ya kaisu sun samu ba kowa a ciki sai shi kaɗai, yana ganin Zayyad ya miƙe suka gaisa dan sun saba da juna sosai, suka zauna sai Headmaster ya dubeshi yana cewa.


Ya naga ɗalibanmu da kayan gida Allah yasa lafiya.


Malam kayan nasu ne an wanke musu basu bushe ba, shine naga da suyi fashin makaranta gwara na zo dasu na siya musu wasu, Allah yasa akwai uniform a ƙasa.


Akwai su ai bama bari su yanke saboda masu siye da sabbin shiga. Ina zuwa.


Headmaster yace tare da miƙewa ya shiga cikin wani ƙaramin ɗaki dake cikin office ɗin ya duba uniform ya ciro musu size ɗinsu, nan ya miƙa masa yana cewa.


Gashi nasan zasu yi musu ita bata wuce shekara takwas ko? shi kuma biyar.


Basu ma kai ba, tsayin ƙafa garesu amma wannan zai yi musu.


Cewar Zayyad yana ɗaga kayan yana dubawa, nan ya umarci yaran su cire kayansu su saka uniform ɗin, ba musu suka yi tuɓe suka saka yace su ɗauki jaka da abincinsu su wuce class, suka yi masa bye bye suka fice nan Zayyad ya biya kuɗin uniform suka yi sallama da headmaster kana ya fito ya shiga motarsa ya nufi gidan Amminsu.


Yana shiga falon gidansu ya samu Hajiya zaune a carpet tana ta aikin ɗura dambun Nama a robobi, ta amsa masa sallama tana cewa.


Dan halak kaƙi ambato, yanzu nake zancen Muktar dole ya jira na gama sakawa ya kai muku shago daga can ya wuce makatanta.


Ai tunda nazo sai yayi tafiyarsa. Ina kwana Ammi kun tashi lafiya.


Lafiya kalau Alhamdulillahi ina mutane na su Ilham da fatan kowa lafiya.?


Alhamdulillah yanzu na sauke su a makatanta.


Haba Zayyad meyasa kuke barin yaran nan suke lattin zuwa makaranta, wannan zai iya saka karatunsu yayi ta baya.


Ya zanyi Ammi kema kinsan halin Rashida ba sai na faɗa ba.


Nan ya kwashe komai daya faru da safen ya faɗa mata, Ammi ta girgiza kai tana cewa.


Allah ya kyauta ya shiryata, dama shi mugu bazai cika mugu ba sai yayiwa kansa mugunta, gashi duk abinda take yi ya fara shafar rayuwar yaranta. Shiyasa nake fatan Safna ta shigo ta kula da kai kota fannin Abinci ka huta da zaryar Rastuarant.


Allah yasa mu dace, ashe kinyi dambun naman, kwana biyu masu saye suna ta tambaya.


Ai jiya nace bari na ɗaure nayi nasan za ayi ta tambaya, to jikin namu ne na tsufa yau lafiya gobe ba dama.


Hakane Allah ya ƙara afuwa, Ina Salame mai aikinki bata nan ne?


Ta tafi kula da 'yarta data haihu, shiyasa aikin ke mini yawa amma tace cikin kwanakin nan zata dawo.


To Ammi ko za a sake samo wata ne su zama su biyu.


A'a itama ta wadatar kuma ai yanada kyau ina motsa jikina. Matso kusa ka zuba dambun a leda roba saba'in ne ba sai ka sha wuyar ƙirgawa ba.


To yace mata ya matso yana sakawa a katon leda.
[06/09, 8:54 pm] null: https://chat.whatsapp.com/D5ISXoMOGGR9PPoswkybsj


ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAH WABARAKATUH KUNA INA NE MUTANNAN ARZIKI KUHANZARTA KUSHIGA WANNAN GROUP MAI ALBARKA KADA AYI BABU KU , MUNA ARHA MUNA HANA BASHI💕MUNA TURA KAYA KO INA DA YARDAR ALLAH CIKIN AMINCI. DA MUTUNTA JUNA , MUNA KASUWANCI DA AMANA , ZAKUJI DADIN KASUWANCI DAMU .

Ga abubuwan da muke siyarwa kamar haka 👇🏻:
KAYAN KITCHEN
WRAPPERS
JAKUNKUNA
TAKALMA DA KUMA SUPPLEMENT.


MASU KYAU DA INGANCI , YAR UWA ME KIKE JIRA? MAZA HANZARTA KI SHIGA LİNK DON SAMUN KARIN BAYANI KO KUMA KU TUNTUBENI TA WANNAN NUMBER DAN SAMUN KARIN BAYANI . 08033938993 .


UA_ENTERPRISE suna maraba da masu siyan d’ai d’ai ko sari 🤗🤗🤗


*AMARYAR ZAYYAD*


Na


©®Rahma Kabir MrsMG.
Wattpad @rahmakabir


Page 4.


Sai ga Mukhtar ya fito daga ɗakinsa yana ganin Zayyad ya washe baki yana cewa.


Yauwa shikenan ma bari nayi fijo na wuce inda nafi wayo. Yaya Zey zan samu wani 'yan chanji a gunka? kasan gaye ba kwabo yawane.


Nan kafi auki ai, kana gama karatun nan shago zan buɗe maka ka fara sanin yadda ake kasuwanci kasan muhimmamcin kuɗi.


Dako ka kyauta Zayyad, dan kam wannan shiryayyen in ba anyi masa da gaske ba malalaci zai zama.


Haba Ammi jifa yadda na tara kwanji, ai ko yanzu zan iya saɓa yaya a wuya nayi yawo dashi saboda ƙarfina.


Zayya ya ɗauki ludayin da Ammi ta gama amfani dashi ya wurga masa, Mukhtar yayi tsalle ya koma gefe yana kwasar dariya suma dariyar suke tayashi, Zayyad yace.


Allah ya shiryeka kowa ma ka mayar dashi abokin wasanka. Ga dubu biyu nasan zata isheka fafa.


Yasin tayi mini kaɗan, ina laifin ka bani dubu biyar a matsayina na autan marigayi Alhaji Ahmad da Hajiya Halima mai dambun nama, ƙanin Bilki da Zayyad da kuma Asiya.


Innalillahi! Muktar Allahu yahadika.


Cewar Ammi tana murmushi, Zayyad ko murmushi shima yayi yana girgiza kai dan ƙanin nasu in dai wajen barkwanci ne lamba ɗaya yake, ya ƙara masa dubu uku ya zama dubu biya ya amsa yana godiya.


Zaka yi Albarka dan gidan Ammi In Sha Allah, Allah ya kawo Anty Safna gidanka lafiya muci rayis.


Yana gama faɗar haka ya fice yana kwasar dariya, suma dariyar suka yi suna yi masa fatan shiriya.


Ammi ta miƙawa Zayyad wani robar takeway.


Ga naka sai ka aje kaci abinka a hankali harya ƙare.


Yauwa nagode, a office ɗina zan aje shi dan inna je da shi gida sai dai naga robar a bola, amma wannan baiyi mini yawa ba? kar in karya jalin.


To Zayyad in ka cinye kaine mai bayarwa, sannan ma Alhamdulillahi na fidda uwar kuɗi da riba. Ɗazun nayi waya da Kamal yace mini jibi Juma'a zai zo.


Eh munyi waya jiya, amma kinyi magana da Yaya Bilki yaushe zata zo ita.


Wai in biki saura sati biyu, zasu fara sauka a gidansu can daga baya su dawo nan ayi bikin.


Allah ya kaimu.


Zayyad ya ambata, Ammi tace amin suka cigaba da tattauna yadda suke fatan bikin ya kasance.


*****


Safna.


Tana zaune a ƙaramar kujera tana wanke wanke sai ga Haajara ta shigo gidan da sallama, da murmushi kan fuskar Safna tace.


Sannu da zuwa ƙawalli na ɗauka sai anjima zan ganki.


Ke gwara na fito kafin rana tayi zafi na kasa fitowa, kin san na fara zama ajebo.


Eh ba shakka ɗan baba ya fara mulki dai, ya nauyin jiki.


Alhamdulillahi, umma fa?


Cewar Haajara tana waige waige, Safna ta sanar da ita taje islamiyya ita ce kawai a gidan kowa ya fita sabgarsa, nan ta zame hannunta a ruwan wanke wanke ta shiga kitchen ɗin tsakar gida ta ɗauko mata kujera ta aje a innuwa tana cewa.


Bisimillah, ina kwana

Please Login or Register in order to submit comment