Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

nama ya sungumi É—aya'n yayi É—aki.

Dawowa yayi ya kai wanda ya fashe tare da Sunkuyawa yana kwashe wadda ta zube.

Fararan ya tsunshi yasa yana tattarawa yana tsaka dayi Saiji yayi an takemai su da ƙarfi da tsinin takalma.

Wanda hakan yasashi saurin juyowa da karfi ya sauke kwayar idon shi cikin ta Amnah.

Bin dogayen yatsunshi take da kallo ganinsu wasu irin farare tass har wani jaja sukeyi ga tsintsiyar hannu A yalwace da galgasa..

Ido takashe tanamai kallon kurullah tare da kara É—aro idonta a murzazza fatar shi datayi lumi.

""Kai ÆŠan Dako ne kuwa? In har takasance haka miyasa kamuna asara? Kana aiki da hankali kuwa? Kai da kake Talakka kai ya kamata ace kafin kowa iya tattali, Amma saboda ba gidan Tsoho bane sai a wifintas?

Shuru yayi har lokacin kanshi a sunkuye yake sai hannunshi data danne da takalma da yake kallo wanda still tana akai taki É—agawa shima bai motsa ba..

Mamy takaraso wajen tare da dakamata tsawa da ta sata matsawa.

Kuɗi mai yawa Mamy ta ƙilgo tabashi tare da cewa.

"Dan Allah kayi hakuri kaji ko,Yarinta na damunta ,Ƙarɓi wannan maza katafi kaga am'fara yayyafi wannan kabarshi ba damuwa ko Baba ya ba tsuntsaye.

Mikewa tsaye yayi tare da Ƙarɓa kudin ya kilga ya dauki dubu biyar yace.

Ga sauran nan na kilgi abunda ke hakkina .

Mamaki sosai yaba Mamy wanda ta bishi da kallo na ganin yanda yabata maƙudan kudin da ita kanta batason adadinsu ba.

Murmushi ta saki tare da cewa" ka rike nabaka ai.

Kai ya gilgiza alamun a'a...

Tsawa Amnah ta dakamai tare da faɗin basu kazo nema ba? Kuma zaka tsaya kana ja'inja da ita munafuki ka Ƙarɓa ka wuce daga nan ka cikamu da warin talauc....

Tass!Tass!Tass!!!

Haka Mamy ta wanketa da kyawawan maruka guda ukku wanda sukasata Tuntsirawa.

Kamin mamiu ta juyo har yakai get cikin sauri tare da kwance rawanin kanshi yafara tafiya.

Kiranshi mamy keyi ko tsayawa baiba.

Cikin ikon Allah yana fita yaga mai Machine ya. Haye tare da" faÉ—in ya kaishi kasuwa.

Ganin mai machine na kallon shine ya sashi tunowa da ashe fuskarshi ba É—aure take ba, Da sauri ya naÉ—e fuskar yabar kwayar idon shi.
Cikin rawar jiki da son samun shiga mai machine yace
"Wallahi Dan uwa kaman kama da wani Soja mai suna Sadeeq daya ƙasance Ɗan Gidan Matawalle...

Tsawa sosai ya daka mai tare da faÉ—in saukeni! Dan na hau machine É—inka shike nuni da kasamu damar da zakamun tambayoyin da Ranka keso ?Maza saukeni anan kamin in maka abunda bakai tinani ba, Duniya ba akamane da zaka tsareni da tambayar banza yakarasa cikin sauti da rawar jikin da ta furgita Mai Machine.


Cikin Rawar ɗari mai machine yace "Kayi hakuri Wallahi nima cewa nayi kamace saboda na taɓa ganin shi so ɗaya gidan da nike kai yaransu makaranta Lokacin ma da kek....

Kan ya ƙarasa ya saki wata gigitatta tsawa da tasanya mai machine saurin yin parking tare da direwa ya yanka da gudu..

Tsaki sosai ya saki tare da sauka yafara tattakawa da sauri dai-dai lokacin ne kuma aka tsuge da ruwan sama sosai.

Babu abunda yashamai kai tafiyar shi yake cike da zafin nama sa hannayenshi da yasa ya tare Duka aljihun shi saboda wayarshi da kuma kudin Baba daya karb'o.


Abangaran Mamy kuwa afusace ta kalli Amnah tace ke da kinson Asalina da naki da kuma wahala rayuwa danasha Wallahi da baki kyamaci talaka ba , Saboda...Sai kuma tayi kwafa tare komawa ciki tana share Kwallah a fakaice.

A ɓangaren Amnah kuwa.

Kyarma sosai jikinta ya É—auka akan talakka yau aka mareta aka kaskantar da rayuwar ta agaban wanda baida matsayi.

Jin ruwa ya kaule da karfi yasata tashi jiki asanyaye tayi É—akin ta tare da É—aga waya ta Daddana.


"Please Abbah ka dauka"

Tafada tana yarfe hannu tare da matse Kwallah.

Jin ta kase bai ɗaga ba yasata hakura sai kwanciya da tayi akan makeken gadonta ta saki wani mahaukacin kuka mai tattare da ƙunar zuciya..

Aɓangaran Mamy kuwa tana shiga ɗaki ta dyauki ƙaramar wayar ta tare da kiran Mijinta Alhaji Isa mai Zinarai da number shi ta sirri da bakowa yason shi da itaba sai amintaccen shi.

Bayan ya É—auka suka gaisa .

mamy take tambayar yaushe zai dawo sunyi kewar sa?

Murmushi ya saki tare da faÉ—in nima haka amma next week ina nan dawowa insha Allah ina Yara na?..
Farin ciki sosai Yakamata inda tace" To Allah yakawoka lafiya zanma tarba ta mussam man .

Murmushi yasaki mai sauti yaire da faÉ—in nasani matata nason zakimun fiye da haka .

Dan jim tayi batace komi ba dan gane da yabon da yamata.

Daga cen ɓangaran yace. "Are you ok Sweetie?

ÆŠan nisawa tayi kana cikin raunatata murya mai haÉ—e da roko tace Hubby wallahi alfarma nike nema awajenka.

Ajiyar zuciya ya sauke tare da faɗin Alhamdulillah da awajena kike nemanta ba awajen kowa ba, indai har kinsanni kinsan waye ni to kinson babu Abinda zan gagara yimiki, Dan haka faɗi buƙatunki kai tsaye nida abunda kikeso duk mallakainki ne ...

Wani irin sanyi ya ratsata cike da kwarin gwiwa tace "Hubby agasjiya ina da bukatar sabon mai aiki , Saboda Baba ya manyanta, Ga rabon nan da zanyi bazan iya cewa komi sai su Amnah zasuyiba kadai son halinta zamuyita samun matsalane da ita.


Shikenan Tsadadda "Matata duk abunda kikeso haka za'ayi insha Allah zanyi ƙoƙari sosai wajen samo miki wanda ya dace.

Da sauri tace ''Am nace ba ...

Nan ta kwashe duk abunda ya faru game da wanda yama su Amnah Dako tare da jaddada mai cewa zai iya dayuke duka ragamar gidan baki É—aya, Fatan ta dai ya bata izinin zuwa nemanshi wajrn mahaifinshi dan taga alamar yayi fushi da abinda Amnah ta mai duk da ba komi ta fad'amai ba tana ganin sirri ta ne tsakaninsu da Yar ta. ..

Cike da fahimta haÉ—i da kwarin gwiwa yace "Na amince miki Hajiyata duk abunda kikeso ina sonshi, Ke kinson matsayinki awajena sannan kinson burina da farin cikina inga kinsamu abunda kikeso.


Fira suka shiga yi cike da shauki kana ya kashe wayar.

Ganin babba wayar shi Amnah ta kirane yasa da sauri ya maida mata kira.

Cikin shagwaɓa take faɗin
"Abbana bakasona yanzun kwana nawa banjika ba?

Murmushi yasaki tare da cewa "Amnah nah in bansoku ba wazan So?

Cikin jin dadi tace babu Abbah .

Dama faÉ—a ma zanyi Mamy ta mareni akan ÆŠAN DAKO ko,kuma Abbah agabansa fa,Basai ya rainani ba ya raina ajina?takarasa tana sakin kuka mai sauti.

Take muryarshi ta canza cikin byacin rai yace Mamy taku ta mare ki akan wani banza barni da ita anjima zamuyi magana yakashe wayar yana Huci.

Lokaci guda kuma ya É—auki wayar shi Afusace ya kira Mamy da dai-dai lokacin ta fito daga toilet ta É—auro Alwallah.

Mamaki ya kamata ganin wayar shi bayan yanzu suka gama waya.

ÆŠauka tayi tare da yin sallama......

Amsawa yayi.cikin ɓaci'n rai yace mi"Amnah ta miki da kika Mare ta akan wani Ɗan Dako..
5/18/22, 09:33 - MY MTN 2: D'AN DAKO🌹

MALLAKI🌹

UMMY AYSHA🌹
🅿ï¸5ï¸âƒ£&6ï¸âƒ£

"" Shuru tayi ba Tare da ta ta kaba.

Cikin fushi yasake cewa "kina fa jina Fulani!

Nasha faɗamiki ban yarda da abunda zai shafi ɓacin ran Yarana ba, Akan wani sakarai zaki zauna ki Mari yarin yata ,in kika mata illah fa, mizakice ,Ki kiyaye daga yau ya kashe wayar...

Shuru tayi ranta na ƙuna akan bin bayan rashin gaskiya da yayi.

Sai da ta bada kamar ten mint kana ta É—auki wayar shi tamai Text kamar ''haka."

""Hubby Kayi hakuri banyi wani abu dan ɓata ranka ba Amma ni nason som Amnah halin da take ba mai kyau bane amatsayinta na ya mace, Amma in maganata tamaka zafi kayi hakuri ka yafeni kason fushinka masifane akaina, Har kullum fatan neman yarda Allah da taka nike saboda aljnnata na kasan tafin kafarka, Ina sonka sosai mijin marainiya(SUNAN DA TAKE KIRANSHI KENAN IN TAGA YANA CIKIN FUSHI SABODA YAKAN KARYA MISHI DA ZUCIYA) ta turamai.

Cikin kankanan lokaci wayar shi ta shigo wayar ta.

Murmushi ta saki tare da É—aukar tace'' Ka sirace Hubby..

Murmushi ya saki yace kiyi hakuri da abunda ya faru kinji sweety ,kinson bana iya control din kaina akan soyayya yarana, É—an allah ki daina cewa kedin nan marainiyace bayan kina dani ga kuma NENE ..

Murmushi tayi mai sauti ta ce" shike nan yanda kace.

Daganan sukai sallama ta ajiye wayar tare dayin Sallah.

Bayan ta gama ta É—aga hannu sama tana kwararo Addu'a da hawaye jage- jage a fuskar ta wanda banson na minenen ba.

Aɓan garan Habu Ɗan Dako kuwa cikin sauri yake tafiya baki ɗaya kayanshi sun jike inda suka lafe jikinshi suka fiddo kyakyawan zatinshi na zama cikakken Namiji mai zarra.

Bayyi wata tafiya ba ya ƙaraso kasuwa saboda dama sun kusa.

Koda yazo kai tsaye Rumfar da Baba suke yashiga ya samesu tsaitsaye suna É—aure Buhun hunan hatsin su.

Sallama ya musu suka amsa ya koma gefe tare da kwaso Damen kuÉ—in yaba Baba.

Murmushi yayi yace "Habu ka kasa hakurin ruwa ya É—auke ka taho cikin su.?

Kamar bazai magana ba kuma ya nisa cikin ƙasa da murya yace" Motar ta lalace bata tashi shiyasa na barota acen .

Ido Baba ya zaro cikin ɓacin rai tare da cewa" Wai kai wane irin mutum ne, Haba ina dalili nan da G.R.A din amma sai da kamun asara ɓatamun mota, To da ubanmi zan koma gida ?Habu kana da matsala wallahi badan Amanar kaba da tini na rabu da kai ,kai kason kaf ɗin kasuwar nan babu wanda ya rufama asiri kamar ni ɗan kwal uba har yau banson fuskar kaba na yarda dakai na sakar ma dukiyata na baka Amintatta motata da ba kowa nike ba 'ba , Amma saboda Ƙaton banzane kai sai da ka lakata to Wallahi sai kabiyani yaƙarasa yana neman yin kuka saboda tsananin son motar da yake...

Duk da Habu na cikin ɓacin rai hakan bai hana kwayar idonshi ta kasa fallasa yalwattace. Murmushin dake rufe da fuskar shi ba.

Kallonshi Baba yayi baki asake yake karema idonshi kallo.

Kuka yasaki yace "Habu ni kake ma dariya?Ni ka É—auka mahaukaci ka sacemun mota kuma kazo kace lalacewa tayi Habu ni????

Dakyal ya gimtse dariya dake tasomai yace.

"Baba zaka iya bina muje kaga motar ka tana cikin aminci , Sai dai na ɓalle murfi ɗays data batamun rai yakarasa hankali kwance cikin kuma tabbatar da gaskiya....

Salati Baba yasaki yana zama ƙasa tare da ɗora hannunshi akai yasaki kuka mai karfi da yasanya matasan wajen kwashewa da dariya dan kowa yason yanda yakeji da motar shi da Abun hannushi ,Baya tauyema kowa hakki amma kuma bayasoAmishi asara kota kwabo, Mafarin ko tukin motar bai yarda kowa yayi ba sai shi sai ko Habu daya Amincemawa gashi kuma yau ya zalunce shi...


Cikin shasheka da rikicin tsufa yace" Habu ka cuceni ka zalinceni bansonkaba na baka amana kayi ha'inci Allah yasakamun kuma ba zan bika ba kaje ka saidani babu ni babu kai har abada, Kaje na koreka kai
Iro bishi ka karɓomun motana yafada yana nuna wani matashi.

Dariya Iro yayi yace walkahi bazan bishi ba nima fa ban sonshi ba kawai kai dai ka aminta dashi ya zauna cikin mu.

Duk kan maganar da suke Habu na jinsu kuma yason Gaskiya sukai su kadai suka aminta dashi batare da sun taɓa ganin fuskarshi ba yazama dole ya cire musu kokwanto a ransu! A'hankali yasanya hannun shi yafara warware Rawanin shi har ya gama tass.

Wata irin zabura Baba yayi tare da ƙoƙarin shiga cikin buhun geron dake gabanshi da bai wuce kwano goma ba.

Iro da jikin shi ya É—auki rawa shida wasu samari guda biyu dake cikin shagon yakamo hannu Baba ya makalkale yana zare ido.

Ihu Baba yasa tare da faÉ—in" DAGA TAIMAKO Ashe aljani muke tare da shi tsawon wata shidda, Wayyo ni Audodo naga ta kaina nashiga ukku na lalace Zai kasheni yau namai faÉ—a, Wayyo Allah na yakarasa cikin kyarma.

Kyakyawar fuskar shi ya ÆŠago ya zubama su Baba ita tare da cewa" Ka kwantar da hankalinka Baba ni mutum ne bawai Aljani ba, Kuma ni ba Macuci bane dole tasani rufe fuskata bawai dan ra'ayina ba , Amma namaka alkawari daga yau bazaka sake ganin fuskana arufe ba amma kataimaka ka barni bakin aikina kai kaÉ—ai kamun halaccin ÆŠaukana.Sama da wata biyu ina cikin kasuwar nan ina yawo lungu da sako dan samun wanda zai taimakamun da aiki amma haka nike gama yawo na inkoma inda nafito bansamu komi ba, Saboda mutane naganin cewa ni wanine ko kuma kyan da Allah yamin yafi karfin ace ina neman Aiki DAKO, bayan Allah shike tsara halittar bawan shi ba wai bawa ke tsarama kanshi halitta ba , Shikenan sai ace gidan talakawa ba zasu samu yara masu kyau ba ko me? Halitta" Ubangiji ke yinta yayi Æaki acikin fari haka yayi fari acikin baÆ™i, Da haka ka daina mamaki inka amincemun zan zauna da kai ,in kuma baka amince ba kana ganin babu yarda zan fita in samu wani aikin..

Illahirin jikin Baba rawa yake jin yanda yake rattafo zance da halshen hausa dan ko makaho yaga Habu yason ƙaryane yace shi bahaushene, Dan ko kaɗan shi bai kama da hausawa ba sai dai ko kasashi cikin jinsin Larabawa ko indiya wa....

Cikin Rawar murya yace Habu kaga dai da gaskiya na rikeka ko? To Dan Allah karka cutar dani ka kama gabanka Dan Allah nagode kuma kamun kwatance inda gidan yake a'ida kai masu kayansu in ÆŠakko motata.

Murmushi ya saki mai ciwo tare da kwatan tabmusu cikin fahimta ya tashi ya musu bankwana da godiya akan Alkhairi da sukaimai na rikeshi tsawon kwanaki.

Cikin sauri Baba yace bakomi bakomi jeka ga hakkinka ya bashi dubu biyar.

Karba yayi tare da turawa aljihu yafita daga rumfa yafara takawo cikin ruwan da basu da niyyar tsayawa.

Gabaƙi ɗaya'n masu shagunna kasuwar kallo shi ake wasu harda fitowa bakin rumfunan su suna leken baturen da yashigo kasuwa yana tafiya da kafa ganin irin cikakkiyar sumar shi tayi linkim da ruwa duk ta balbaje tayi masifar kyau.

Sosai ya tsargu da irin kallon da ake binshi dashi hakan yasashi fara tafiya da sauri cike da sasarfa da kuma ɓacin rai.

Dan kallo na É—aya daga cikin abinda ya tsana arayuwar shi ya rasa ubanda yasa mutane ke kallonshi haka kamar sun samu Tv.

Gabaki É—aya ya fita kasuwar yana fitowa ya tare keke napep ya shiga.

Tinda yashiga napep din kaɗan kaɗan mai napep ya juyo ya kalleshi amma bai ce komi ba shikuma tinda yaga haka ya ƙara haɗe fuskarshi tamau.

''yallabai wace unguwa zan kaika?

"Tudun wada.*
Yabashi amsa agajarce.

Kai tsaye suka nufi unguwar ahaka ya dinga nuna mishi har suka karaso wani dan matsakaicin gida da ƙofar ke saye.

Sauka yayi ya bashi kuÉ—in tare da kutsa kai cikin gidan ya tura kyauran yashiga da sallama.

Yason ruwan da ake bazai ba na ciki damar jiba kamar yanda bazai bashi damar jin ko an amsa ba.

Ɗan ƙaramin gidan nasu yatsaya karema kallo da keda Ɗakuna ukku biyu ajere sai daya dake kallon su sai dan karamin tsakar gida da baifi zaman mutum biyar ba sai toilet da karamin kiching.

Ba laifi tsakar gidan nada kyau dan ashafe yake tas ga pent da yasha komi a'killace yake ba wasu hayaniya.

Dayan É—akin da ke aware yayi saurin turawa tare da shiga ya maida kofar ya rufe tare da danna Sakata

Babu komi.acikin É—akin sai wata tabarma da kuma karama katifa sai Alkur'ani sai wani truly babba guda É—aya ..

Yana shiga yabi É—akin da kallo jin yanda yake ta busa kamshi tsintsiya da akasamai gashi agyare tsaf.

Cikin natsuwa ya fara cire kayanshi tare da sasu awani babban boket dake bayan kyauran, Yana gamawa ya É—aura wani HARAMI akugunsa tare da É—aukar É—aya'n ya yafa akafaÉ—ar sa.

Wani irin mahaukacin kyau yayi kamar wani Balarabe dake filin Arfa.

Soso da sabulu ya É—auka tare da boket din dakayanshi ke ciki ya fita dasu .

Ajiyesu yayi tare da faɗawa toilet din dake tsakar gidan ɗan madaidaici ba laifi yana da kyau akwai shower da toilet sit da ƙaramin pampo ciki.

Wankan ya faɗa tare da murzar jikinshi sosai cikin lokaci ya fito tare da duƙawa ya wanke kayan daya cire tass ya shanyasu akan igiya.

Alwallah ya É—aura saboda Al'adar shi ce zama da Alwallah yana gamawa ya nufi É—akin shi ya zaro wata tattausa brown din jallabiya dake linke mai gajeran hannu ya sanya.

Wani irin mahaukacin kyau tamai gashi ta sake fito da Hasken farar fatar shi da kuma zatin shi da murzazza fatar da Allah yamai mai kama data ya'yan hutu.

Kai tsaye ya fito tare da nufar É—akin dake kallon nashi ya tura guda da salllama a'
bakin shi.

Wata murya ce mai sanyi ta amsamai sallama tare da bashi izinin shigowa.

Shiga yayi cikin ɗakin yana takawa A'hankali kamar wanda ke tsoron ƙasa.

Wata farar matace dake hakim ce akan kujera hannuta rike da littafin Adduo'1i tana dubawa ,hukunta sanye da wani kace mai kyau da tsada.

Kai ta ÆŠago ta kalleshi tare da fadin.

SADEEQ Kadawo?Sannu ya aikin naku?Ina fata komi yana tafiya yanda ya dace? Da fatan dai bakajin yunwa ko? tamai tambayoyin duk ajere.

Wani kyakyawan murmushi ya sakarmata tare da Duƙawa kasa ya ya dafa gwaiwar ta yace. "Ammina Barka da gida kin cikani da tambaya waccen/ kikeso in am'samiki? ya ƙarasa yana turo baki cike da shagwaɓa .

Murmushi Ammi tamai mai tsananin kama dashi ta ya mutsa sumar kanshi tace duka nike so ka amsamin,Saboda É—an jarumi ne ,kuma Nason in akwai wadda tafi wannan zaka amsamun.

Hannunshi da Amnah ta rike ya ɗaga yana murzawa A'hankali saboda yana tinanin tamai rauni, cikin Raɗaɗin da zuciyar shi kemai yace" Ammi nah komi lafiya klau Alhamdulillah , Sai dai inaso kisani Addu'a da bakin ki mai Albarka, wanda nike ƙasan shi sama da wata shida yau ya koreni tinda yaga fuskana yana ganin kamar cutar su zanyi kuma na fahimtar dasu sun kasa ganewa yakarasa cikim.ƙuna rai da taune jajayen lips ɗin shi.

Shuru matar tayi batace komi ba sai kanta da ta sadda ƙasa cikin kankanan lokaci ta fara kwallah masu tsananin zafi da ƙuna rai.

Saurin Ɗago kanshi yayi arikice tare da karasawa wajenta ya rike gwaiwarta illahurin jikinshi rawa yake idonshi yayi jawur cikin ƙanana lokaci,Murya na rawa yace.

"Ammi Dan girman Allah da manzon sa karkimun kuka na rokeki Ammi, ku kanki shine zai raunata zuviyata inkasa zama Namiji na ,Ke kinson waye ɗanki Ammi akan ki zan iya ɗauke komi amma banda ganin hawayen ki, Bani da mafita shiyasa na zaɓi faɗamiki saboda ko ba komi nason zakimun Addu'a kuma addu'arki gareni batada hijabi karbabiyane muyi hakuri mu fauwalama Allah,Domin shi ne zai kawo muna mafita, in kuma kina ganin in dingama fuskana penti kamin in fita sai inyi Ammi, Amma wallahi ni kaina abun na da nike naɗawa na matukar damuna Ammi kinson Ni banason zafi da abu mai nawie...

Hawayenta ta share cike da tausayin yaron nata.

Rungume shi tayi sosai tare da sakin wani mahaukacin kuka taf ara kiran shi da Sadeeq!Sadeeq!!Sadeeq!!! Munga rayuwa, Rayuwa tamuna juyin waina a Tanda, Sadeeq yanzu kaine wai....

Saurin rufemata baki yayi tare da gilgiza kanshi idonshi jawur yace" ki daina wata magana Ammi abunda ya wuce ya wuce munma rasa mahaifinmu mun hakura ballantana wata rayuwa cen ,karki damu Ammi nah ina Hamrat?

Hawayenta ta share tare da nunamai inda wata kyakyawar yarinya ke kwance akan katifa da ba tafi shekara goma ba, Bacci take cikin jin DaÉ—i da kwanciyar hankali.

Cikin natsuwa ya zare jikinshi daga na Ammi ya ƙarasa wajen yarinya ya aza gwiwowayin shi ƙasa tare da riko hannunta ya Ɗan murza ahankali yana kallon fuskarta da ke tsananin kama da tashi...

Kanta yafara shafawa A'hankali yanajin wani irin yanayi mai wuyar fassarawa game da yarinya,baison dalilin da yasa duk sadda zai kasance da yarinya ba yakejin wani tarin rauni dakuma matsanancin tausayin ta ,ƙanƙanuwar yarinya ke cikin wannan rayuwa da suke ciki fatanshi ya nema dan ya wadatasu amma yau gashi an koreshi akan abunda bai kai ya kawo ba.

Amma ya tabbata babu wadda ta jamai kamar wannan yarinya da som batada É—a'a da tarbiyya.

Hannu shi ya kalla inda ta takemai har ya fashe gashi yayi jawur.

Lips ɗinshi ya ƙara taunewa akaro na ba a Dadi..

Mamy ta katsemai tinani da faÉ—in ga abincin ka nan kazo kaci.

Cikin ladabi yace"Ammi minene kika dafa muna?

Murmusi tayi tare da faɗin"Wakene sai shinkafa da salad harma da ƙwai na siyo nasamaka takarasa tana Murmushi.

Tausayi tabashi sosai ganin yanda take farin cikin ta Da ɗaɗamai ta hanyar samai kwai duk da cikin shi a'cike yake amma bazaiso ɓata farin cikinta ba,Haka ya zuba kaɗan ya fasa kwan yaci yanata mata santi ita kuma tana tajin daɗi tare da mai kallon tausayi.

Gidan su Amnah kuwa Baba Habu yaji anama gidan wani mahaukacin bugun da yasashi Ɗakko Sanda da yar ƙaramar wuka ta yanka albasa yafito tare da buɗe kyauren cikin kasada ba tare da ya tambaya ba ya lafe baya.

Iro ne ya turo kyauran da karfi wanda yasashi matse Baba madu .

Ihu ya saki tare da watsar da Sanda da wuka .

Cikin furgici Iro ya juyo tare da fadiyn lafiya malam kake ihu munzo É—aukar mota ne muna tare da Bakanike ba masu Sata bane..

Ajiyar zuciya Baba Madu ya sauke tare da É—aukar waya Yace" Dama Hajiya tace in anzo É—aukar motar a'mata magana Bari in fad'ama ta.

Tsaye sukayi suna jira har ya mata waya ya fad'amaka sai gashi tafiyo ita da Amal suna sanye da hijjob.

Ƙarasawa tayi tana binsu da kallo ganin bataga buzun da ya kawomata kaya ba.

Cikin dube -dube tace yo ina ÆŠAN DAKO kayan yake?

Cikin matsananci Ɗumi dake cin Iro ya fara magana" Ai Hajiya ɓarnar da yama Baba mu ta mota yau shiyasa aka koreshi , Saboda Baba bayaso amai ɓarna ga mota, sabodama yarda da shine yasa ya bashi to amma kinga harda marfi ya cire mata uwa uba kuma Baba baison fuskar shiba tsawon watanni shidda sai ɗazu ya buɗemuna ita, Wallahi Hajiya abun mamaki ashe Bature ne shegen aka turoshi ya ga asirin Dukiyar Baba Dan yaje ya faɗama yan uwanshi azo ayi KIDGWASHIN ɗin Baba asaceshi, Aiko Baba ya korai tin ɗazu ba mu son inda yake ba...

Wata ityin dariya Amal ta kwashe da ita ganni yanda yaketa rattafa zance harda ambatar sunan kidnapper's da kidgwashin ..

Sosai jiki Mamy yayi sanyi hakanan taji yaron ya shiga ranta cikin sauri tace" Toni yanzu wazai ida kawoman sauran kayana, Gashi gobe zanyi rabon nan, Kana dan Allah inda hali ni ku nemomanshi inason ganin shi .

Iro Yace" Ga sauran kayanki nan cikin babbar mota wasu suzo mukama dan gaskiya ni ko Rabin buhu ban iya dakkowa, Saboda Hakarkarina ciwo suke banima da isasa lafiya.

Cikin bacin rai "tace to ina wancen yake ku kiraman jarumin mana sai aturoman lusari irin ka mizakaman wannan ma ai haukane inane gidan su?

Iro yace wallahi bansani ba Hajiya.

Mamy tace "number wayar shi fa?

Iro yace" eh ina da ita gatanan ya faÉ—a yana nuna mata wayar shi.

Karba tayi ta kwafe awayar ta tare da kangawa a'kunne.

Shi kuwa Habu dake É—akin Ammi suna fira yaji wayar shi na Ring. Ganin bakuwar number ne ke kiranshi hakan yasa ya É—auka tare dayin sallama.

Daga ɓangaran Mamy amsawa tayi cikin Dattaku tare da mai bayanin kanta akan tanaso ɗan allah ta Ɗaukeshi aiki duk wata zata biyashi dubu ɗari in ya amince zai dinga kulawa da wasu hidimar gidan sauran bayani dai in yazo yaji.

Shuru yayi kan shi a'kasa saima wani irin ɓacin rai dake tasomai akasan zuciya "Dubu dari yasake maimaitawa akan laɓɓanshi tare da taɓe bakinshi ya saki wani murmuahi Mai ciwo.

Ammi dake jin duk abunda suke faÉ—a ta É—agami kai alamun ya amince..

Bazai iya tsallake umarnin taba duk da baisoba saboda Yarinya gidan amma bazai iya fad'amata ba.

Cikin dusashiyar muryarshi yace" Na amince.

Farin ciki sosai mamy taji inda ta hau zubamai godiya kamar yamata wani abu.

Idon shi ya limshe batare da yace komi ba.

Cikin É—oki tace to kazo yanzu.dan Allah akwai aikin da zakamun.

Uhm yace yana kashe wayar shi.

ÆŠago kan da zayyi yaga fuskar mahaifiyarshi ayalwace da farin ciki.

Hakan yashi tsiramata ido ko kyaftawa bayayi aduniyar da suke ciki yana fatan yagan ya zama farin cikin iyayen shi, Yana so yaga mahaifiyar shi ta samu gata ta dalilin shi da yar ƙanwar shi da baida kamar ta da ta taso cikin halin Rayuwa.

Murmushi ya saki Dan

Please Login or Register in order to submit comment