Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

makaranta makaranta ko karuwanci? Baba Sani yace"Ayuba bama wannan ba abin da ke bamu mamaki yanda ta maidamu kamar almajiranta idan munason wani Abu sai munzo mun tambayeta,to baki Isa ba banza tsintacciya kawai,tsintacciyar mage,dama ance tsintacciyar mage Bata mage......Cike da bacin Rai Shakeerah ta buga kofan falon duk cikansu suke duban ta Ammi kuwa kuka take ganin Shakeerah yasa cikin Sauri ta goge tears din, Shakeerah tace"ai gwanda tsintacciyar mage Akan wasu masu iyayen domin ku naku matan Babu abinda suka Sani sai duddura muku bakin ciki,na rantse da Allah duk Wanda yasake batawa mahaifiyata Rai sai na ci du........Ammi tace"ke ke ke Shakeerah.
Cikin bacin Rai Shakeerah tace"Ammi don Allah kiyi shiru,har yaushe su baba Sani da baba Ayuba zasu Dena cimmiki Kashi kina shiru?wa billahillazi bazan dauka ba Ni sai na yiwa mutum rashin mutumci.
Saria su baba Ayuba sun San halinta yasajikinsu na rawa suka bar gidan.


Nan Ammi tayiwa Shakeerah ta tas sannan Tace tashirya taje tabawa 'yan uwan babanta hakuri.
Da toh Shakeerah ta'amsa ma Ammi bawai Yana nufin taji ba,sannan tasake bawa Ammin tata hakuri.


Shiryawa tayi cikin wani Riga da wando Pakistan purple nd white gaskiya Sunyi Mata kyau sosai part din fulani taje gaisheta,ta cidda mota a harabar gidan hannunta rike da foodflask ne a hannunta da sallama ta shiga falon wata mata tataras a zaune a zaune mai Kama da Goggoji duk cikansu da fara'a suka dago suna duban Shakeerah,fulani tace"A'ah Shakeerah ur welcome,da Murmushi ta Isa wajen gaida fulani tayi sannan tagaida bakuwar,amsawa tayi face nata dauke da Murmushi aje foodflask tayi tace"fulani ga alalen inji Ammi.


Murmushi tayi tana jawo cooler din ta bude"Wow Masha Allah fulani tafada,ita kanta bakuwar hadiye miyau tayi,duban matar fulani tayi tace"Kinga Shakeerah jikata jikan arziki.
Shakeerah wannan 'yata ce itace ta hudu.
Murmushi Shakeerah tayi tana kallon matar tace"Allah sarki ai Ina ganin ta naga kamar ku,mikewa tayi tashiga kitchen ta dauko mata roban wanke hannu da plates biyu da spoons,duk cikansu suka wanke hannnayen sannan matar tazuba ma fulani abinci itama ta zuba nata.
Shakeerah tace"Fulani n atafi zanje kasuwa.


Fulani tace"Toh Shakeerah Sai kin dawo,fita tayi ta nufi part dinsu.
_I need ur comment_








Xahratty ce✍🏽
Lallai Alqalami 🖋️ Yafi takobi 🗡️
💕💕
❤️
[7/18, 2:05 PM] Xahratty🥰😘: 💐✨ *DIAMOND LADIES* 💐✨
(Daukar Fansa)







Story&writing
By
PATEEMA ZAHRA LAWAL
_______✍🏽_______




*TAMBARI WRITER'S ASSOCIATION*
🔱(( Home of Expert and talented writers,da tamvarin mu muke tafe domin kawo gyara da cigaban Al'ummah))

*T.W.A*
_________________________
https://www.facebook.com/Tambari-writers-Association-106058867819812/
_________________________




Marubuciya:-
_ *A DALILIN 'YAR TSUNTUWA*


_ *MIJIN ZAHRA*

*ND*
*NOW*
*DIAMOND LADIES*
(Daukar Fansa)




*Littafin diamond ladies (Daukar Fansa)na kudi ne duk maiso ya turo katin Naira dari 100 na waya ta wannan number 08060719719,sai nayi adding dinsa a group din*




Bismillahir-rahmanir-raheem.


*Da sunan Allah mai rahama mai jin kai....*






_FREE PAGE_




Page:2️⃣2️⃣--2️⃣3️⃣🖊️






__________Mezai hana muhada wannan yarinyar da Jalaludden Aure?duk cikansu suka ce Eah,tadai Hjy Kaltume tana ta kallon su,hjy shamsiyya tajuyo tace"Aunty Kaltume ko a kika gani? Hjy Kaltume tace"hjy shamsiyya idan matanshin ce ita Allah ya Sanya alkhairi.
Hjy shamsiyya ta dubi fulani tace"fulani to kefah? Fulani tace"tun Ranar da na fara ganin ta nayiwa Jalal sha'awar ta a matsayin mata.


Hjy shamsiyya tace"to Alhamdulillah abun kam yayi kyau sai ayi zaman meeting na musamman koh? Gaba dayansu su suka amsa da Eah,cigaba sukayi dacin dambun naman zabin da kunun ayar sai Santi Sukeyi,suma su Alhj kabeer ba'a barsu a Baya ba,domin suma sunci.


Washegari Shakeerah da sassafe da wuri ta nufi kd domin suna da Exam da karfe takwas da Rabi, direct KASU ta wuce,tayi mamaki matuka na ganin su Fauzi,nan sukayi Exam suka fito,nufar capteria sukayi don zuwa susha coffee.


Nan fa aka dasa hirar yaushe rabo,Baya sun sake fitowa Exam suka wuce gida,a lokacin da suka Isa a zahar yayi,don haka suka gabatar da sallar da ke kansu.


Shakeerah taciro musu dambun naman da Ammi ta hada musu,cike da farin ciki suka fara ci Fauzi tace"Wallahi Shiyasa nakeson Ammi domin ita din akwai kula,khadee tace"kedai bari,kunsan matsalar da nake fuskanta kuwa diamond ladies?
Cikin Sauri suka girgiza kai tare da mai da hankalin su kanta khadee taci gaba"Hmmm kannena yaran amaryan Daddy gaba daya anwayi gari sun rasu,biyu a ciki mata ne duk an kwakule musu Ido,dayan na miji ne anyanke masa joyst*ck nasa.


"Innalillahi wa Inna ilaihirraji'un su Shakeerah suka ambata ita da Fauzi,Fauzi tace"gaskiya khadee matsalar ki yakamata a fara warware wa yanzu,domin bai kamata a bar Daddy yana cigaba da wannan aika aikar ba.
Shakeerah tace"haka ne nidai a bangare na matsala daya ne wanda Kuma bazai yuwu ba,duban ta sukayi suna cewa menene matsalar?
A jiyan zuciya Shakeerah ta sauke tace"a cikin mu biyu nida ke fauza sai wata ta auri Daddy,duk cikansu su a firgice suka dube ta,tace"Yes ta haka ne kawai zamu iya cimma burin mu na daukar fansa a wajenshi babu wanda zai iya hakan sai makusan cinshi,wato matar shi,zufa ne yafara kwararo musu.


Yake Shakeerah tayi tace"Diamond ladies ku kwantar da hankalin ku lokaci yayi da zamu fara daukan fansa fa nasake jaddada muku,idan dame mgn Ina saura ransa.


Khadee tace"Shakeerah wannan shawarar ba me yuwuwa bace gaskiya yakamata a canza ta a memi wani.
Duban khadee Shakeerah tayi tace"Yaushe ne akayi rasuwar? Khadee tace"jiya ne Wallahi.
Shakeeerah tace"to Kingani,abinda za'ayi shine insha Allah yazama wajibi wannan week end din muyi shi a gidan Daddy.....duk cikansu su a firgice suke duban ta,bakin Fauzi na rawa ta dubi Shakeerah tace"Shakeerah kada kiman ta Daddyn khadee nada matukar hadari.


Shakeerah tace"yess I know but hakan shine mafita,pls kada kuman ta taken mu mana,mun day alkawarin daukan fansa ga duk wani azzalumi,Muddin bamu cire tsoro a zuka tanmu ba to tabbas Babu yanda za'ai mu cinma buri kanmu,mudai musa Allah Daya a zuciyan mu,kuma Yana tare damu a duk inda muke, duk cikansu suka ce hakane kam.
Mikewa Shakeerah tayi ta nufi dakinta don gyarawa sai dai ko da tashiga taga dakin fesss Banda kamshin turare babu abinda yake,juyowa tayi face data dauke da smile Tace"Wow dakinfa yayi kyau ngd muku sosai diamond ladies domin nasan mutum guda bazata gyaramun daki ba sai guda ta hadaka,suma murmushin suka mai da mata.
Cigaba sukayi da zuwa school, yanzu Exam saura 1week su gama cikin ikon Allah suka shirya Ranar friday ita da Fauzi don tafiya bauchi,da yake duk after 2 weeks suke zuwa week end shiyasa wannan week din nan bazasu gida ba,sun samu damar zuwa bauchi.


A motar Shakeerah suka nufi garin bauchi Cike da kewar khadee,sai dai sunja mata kunne akan fita tinda da komai a gida pls kada tafita ita kadai har sai sun dawo.




Tun 7:00am suka fita Basu Isa ba sai 5:00pm,a gajiye suka Isa gidan Daddy tabbas gidan sa abun kallo ne sai da suka tabbatar da gidan Alhj Sani Bukar Mai Iyali ne sannan suka kutsa kai cikin gidan bakinsu dauke da addu'an shiga gida" _bismillahi walajna wa bismillahir-rahmanir-raheem kharajna wa'alallahi rabba na tawakkal na_,sannan suka shiga yanacan sama yana hangen su,zumbur ya mike don 'yan matan sun Gama tafiya da imanin sa,duk abinda yakeyi Shakeerah na ankare dashi.
Direct dakin Mai gadi suka nufa,tambayar shi sukayi ko yasan part din hjy saddiqa? Amsawa yayi da Eah yasani,ya nuna musu wani part yace gashi can shine nata.
Shakeerah tayi wani makirin Murmushi tace"pls idan Babu damuwa zanso ka hadamu da ita wato Kai Mana iso gareta.
Diddilo idanuwa Mai gadi yayi yace"bayin Allah ai yanzu shekaru kusan goma Kenan da rasuwar hjy saddiqa........." _Innalillahi wa Inna ilaihirrajiun_ suka fada a tare suna dafe chest Cike da pretending,babu zato babu tsamanni Shakeerah tafara hawayen munafinci,"Kingani Koh Fauzi Shiyasa naso tun kafin motaho mukira ta mom tace bata da number nata sai dai adrees ai gashinan.
Muryan fauzi na rawa tace"mun shiga uku to yau ya zamuyi? Mai gadi yadu besu yace"meke faruwa ne?ko da matsala ne?
Ko kafin su bashi answer Alhj Sani ya kariso Yana tambayar Mai gadi"Mal sale meke faruwa?nan me gadi yake sanar dashi duk yqnda sukayi dasu Shakeerah.
Dawo da dubanshi yayi ga su Shakeerah yace"Ayya 'yan mata sai dai kuyi hakuri,but mushiga ko ruwa ne kusha don na ganku da niki-nikin akwati,tafiya yafara sukuma suka bishi a baya wannan ta kalli wannan,wannan ta kalli wannan a haka duk suka shiga Falon gidan.


Wata kyakkyawan mace suka tarar akan 3sitter tana zaune tasaka tagumi,gyaran murya Alhj Sani yafara cikin Sauri ta dago tana fadin sannu da zuwa Alhj.
Daure face Daddy khadee yayi tamkar Murmushi bai taba wanzu wa a face din sa ba yace"Yauwa pls shiga Daya ciki ki bamu waje,sannan ki dauko ma baki lemu.
Gaishe ta su Shakeerah sukayi face nasu dauke da murmushi,itama mayar musu da murmushin tayi ta shige.

Gaishe shi su Shakeerah sukayi daga nan daddyn khadee yafara tambayar su daga Ina suke,ko su 'yan uwan marigayiyar ce?lokaci daya Shakeerah karyan da zata shirya mai yazo mata a kwakwalwa tafara magana kaman haka"Daddy mu ba 'yan uwan ta bane,wata shekara ne sukayi aikin hajj da mom namu shine fa suka hada kawance tare da zumunci Bayan sun dawo sukayi exchanging din address tayi kwatan cen gidan nan shine fah mom namu tunda ga garin zaria ta turomu don duba mata ita.
Girgiza kai ya shiga yo a hankali,yace"lallai kam ai tun tuni tarasu to gashi dare yayi 'yan mata ya Kenan?
Shakeerah tace"No bb komai yanzu zamuje munemi hotel da safe sai muwuce.
Murmushi yayi yace"A'ah ai ba za'ayi haka ba Muddin muna garin nan ai ba zaku wulakan ta ba 'yan mata yayi maganar Yana lashe harshe kaman tsohon maye yana duban Shakeerah.
Shakeerah tace"Toh Daddy GODIYA muke.
Daddyn khadee yasa hannu a mouth yace"shiiiiiiii babu godiya tsakanim mu,kuma kada kisake cemun Daddy as from today.
"Ok daddy.....bata karisa ba tace"Au Ok tohm bazan sake ba,Murmushi yayi yace"kyawawan 'yan mata dakin ku daya? Cikin Sauri Shakeerah tace"Eah dakin mu daya baban mu daya.
"Ayya anyway Bari nasadaku da daya daga cikin Mata na.


Da toh suka amsa mishi sannan ya mike yatafi.


Ba'a dauki wani dogon lokaci ba,matar da suka tarar a falon still itace ta dawo fuskanta still dauke da Murmushi cikin sanyin murya tace"kutaso muje ciki koh? Mikewa sukayi tare da binta ciki,sosai dakunan nasu ya burge su Zahra wani daki da basu da alamu dakinta ne,nan suka gabatar da sallolin da basuyi ba,suka kimtsa tare da wanka,ko suka fito matar ta dubesu tace"Alhj yace kuje waje Yana jiranku ku tafi, diddilo idanuwa sukayi gaba daya.
Shap shap suka shirya ciikin arnayen wasu dogayen riguna masu tsada wadanda suka gaji da kyau da duwatsu.

Fita sukayi suka sameshi a cikin motar sa yaci babban Riga,tun daga nesa yake sakem musu murmushi har suka kariso,baya duk kansu suka bure domin shiga,daga murya yayi yace"pls Shakeerah dawo nan mana.
Sai da tayi dan jim tare da yatsine face sannan tashiga gaban,hadadden park ya kaisu suka sha ice-cream Banda kallon Shakeerah yake zuciyar sa na raya masa abubuwa da dama akan yarinyar,duk suna ankare da halin da Daddy ya shiga,ta wutsiyar Ido suke ma juna magana itada Fauzi.
Daga nan wani super market yawuce dasu ya siya musu kayan shafa da takalma.
Godiya sosai suka masa,daga nan daukan su yayi suka wuce gida,ledan balango ya siyo hudu da gasassun kaji Suma hudu.
Koda yafaka motar a harabar gidan Fauzi tafara fita,itama Shakeerah ta balle murfin motar don fita,hannunta yariko,cikin Sauri Shakeerah tajuyo jikinta na wani irin shock don tunda take ba'a taba kokarin taba ta haka ba.
Wani irin kallo ta wurga masa Wanda yasashi sakin hannun ta batare da ya shirya ba,a jiyan zuciya yayi sannan ya dubeta yace"Shakeerah yarana kusan goma sha Amma yau duk Allah yamusu rasuwa Banda sauran ko daya, sannan mata na biyun nan duk Basu haihuwa sai dai yanzu inason haihuwa sosai.
Cikin bariki da sanyin jiki Shakeerah tace "ayya Allah yayi musu gafara yasa suna kyakkyawan matsayi.Ameen! Daddy ya fada can dai yace"Shakeerah Aure nakeson na kara,Ina neman wacce zata kula dani sai yau Allah yanuna mun ita.
Duban shi tayi yanda yake magana like saurayi dan 30 da wani Abu.
Shakeerah tace"wacece ita? Kece Mana Shakeerah kece macen da nakeso
_I NEED UR COMMENT_






Xahratty ce✍🏽
Lallai Alqalami 🖋️ Yafi takobi🗡️
💕💕
❤️
[7/18, 2:05 PM] Xahratty🥰😘: 💐✨ *DIAMOND LADIES* 💐✨
( Daukar Fansa )








Story& writing
By
PATEEMA ZAHRA LAWAL
______✍🏽______








*TAMBARI WRITER'S ASSOCIATION*
🔱(( Home of Expert and talented writers,da tambarin mu muke tafe domin kawo gyara da cigaban Al'ummah))


*_T.W.A_*
_________________________
https://www.facebook.com/Tambari-writers-Association-106058867819812/
_________________________




Marubuciyar⬇️


_ _A DALILIN 'YAR TSUNTUWA_




*DA*


_ _MIJIN ZAHRA_




*Littafin diamond ladies (Daukar Fansa) na kudi ne duk maiso ya turo katin Naira dari#100 katin waya ta wannan number 08060710719,sai nayi adding din mutum a group din.*




Bismillahir-rahmanir-raheem.




*Da sunan Allah Mai rahama Mai Jin Kai....*






_FREE PAGE_




Page:2️⃣0️⃣--2️⃣1️⃣🖊️






_________Koda ta nufi part din fulani jitayi hayaniyar tasake yawa,cikin Sauri tashiga Falon, fulani tagani duke a kasa tana kuka,wata yarinyace tsaye akanta a kalla bazata wuce sa'an marigayiya Aunty saudah ba sai wasu mata manya akan sofa su uku duk tana Kama da fulani sai guda a cikinsu,fulani tace"Hjy baraka a gabanki jikanki na zagina ba zaki tanka ba? tabe baki wacce akakira da hjy baraka tayi tace" Ai anyimata ne,nikaina Yaya kinbani mmki Saboda Kuna da kudi shine duk wulakancin da kuka ga dama sai ku sauki kan laweezah Saboda ta auri Jalal?to Meye Jalal din yakedashi da ake wannan abun?


Su dai sauran matan babu wacce tatanka Banda zare Ido babu abinda suke,Laweezah ta juya tadubi fulani tace"Ku rabu da munafukar tsohuwa,tsohuwar banza wacce a haka zaki Kare.




Kutumar uba kayyasa, Shakeerah tafada tana shigowa falon, gabadaya suka tsaya kallon ta ko da takariso jikake tassss! Ta dauke Laweezah da Mari,ko kafin ta Kuma cewa wani Abu tasake dauketa da Mari ihu Laweezah tasaka tana sake dafe kuncinta.


Shakeerah tace"Bura ubaki wacece ke Dan Ubanki?da Zaki Zo kitsaya a gaban tsohuwa kamar wannan kina zaginta sa'anki ne?
Mikewa hjy baraka tayi tace"wacece ke kekuma daga Ina kike harda zakizo kishiga fadar da ba'a gayyace kiba?


Harara Shakeerah ta maka ma Hjy Baraka tace"Sanin ko Ni wacece Sam baida amfani,mgnr shshhigi kuwa yanzu nafara indai Akan fulani ne.
Tajuyo ta dubi fulani tace"kekam baki da tarbiyya wallahi tallahi Muddin Ina Falon nan Kika sake zagin fulani sai na hada Miki jini da majina,tsoro sosai Shakeerah tabawa Laweezah,su kansu matan dake falon Sunyi farin cikin faruwar wannan lamarin.


Karisawa wajen fulani Shakeerah tayi tare da sharemata tears ta dagata ta dorata Akan sofa,dubanta fulani tayi tanason tayi magana tasaka.
Kama hannun Laweezah hjy Baraka tayi tace muje diyar albarka,wallahi kuma Marin nan dakika mata kisan cewa kinci bashi ne zanga ubanda yatsaya maki,dage kafada Shakeerah tayi tare da tabe mouth tace"Ganinan daram dam dakam a turo ubanda za'a turo dai-dai nake da kugun kowa.
Fita sukayi daga cikin Falon suna zage-zage,Daya daga cikin matan tadubi Shakeerah tace"yarinyar nan Allah yayi Miki albarka wallahi duk cikin zuri'ah namu Mutane suna tsoron Hjy Baraka ake da iyalenta kamar ba 'yan uwa ba,kinganmu nan uwa daya uba daya muke da bala'i Hjy Baraka tasa Jalal babban jikan fulani ya auri Laweezah ba don Yana sonta ba,shine fa kullum Basu da aiki sai korafe-korafe.


Shakeerah tace"Allah ya kyauta Babu mnyan 'yaya ne?
Matar tace"Akwai mana Aida ana biye tatasu da tuni anyanke zumunci,Bata da kirki Saboda taga fulani nada hakuri sosai.
Dayan matan tace"Shiyasa Sam Auren zumunci yafita kaina domin gashi a dalilin halinta na yanke zumunci da ita.
Shakeerah tace"Allah dai ya kyauta kawai shine abin cewa itakuma Allah ya shiryeta.


Ameen gabadaya suka fada.


Duban fulani Shakeerah tayi tace"Fulani zan koma school gobe insha Allah.
Duk cikansu fatan alkhairi suka yima Shakeerah sannan tamusu sallama tafita.


A harabar gidan taga motoci sun shisshigo akalla zasuyi motoci uku a tunanin Shakeerah ko Hjy Baraka ce tadawo da iyalenta,sai Kuma taga maza ne manya sosai su uku domin zasu haifeta ma tare da mata biyu.


Wucewa part dinsu tayi cikin Sauri.




Sukuwa da sallama suka Isa part din fulani kyawawan yara masu tashe da jindadin rayuwa,ilimi,kyau,addini,uwa uba Nairaaaaaaaa.
Cikin Sauri duk cikansu sunkai su biyar suka Isa wajen fulani suna tambayarta meke faruwa?
Itadai fulani Bata tanka ba tace Babu komai,kuyanginta gidan suka shiga hidima dasu sosai.




_WACECE FULANI_




Sarki Abdallah Sarki ne na garin itophia Sarki ne Mai adalci Wanda iyayenshi shi kadai suka Haifa, yataso talakawa na alfahari dashi a rayuwa Yana kula da talakawa,duk zaluncin da sarakan Bayan sukayi shi Sam baiyyi ba.


Akwana atashi Allah ya azurta shi da 'Yaya hudu duka mata,da hjy Rahma (Fulani) da Hjy Baraka da Aisha sai autansu hjy Maryam.


Manyan garin azzalumai da Basu son mulkin adalci sukayi kokarin kashe Sarki Abdallah,suka bashi zabi ko ya zabi iyalensa ko ya zabi mulki.
Jin haka yasa Sarki Abdallah ya hakura da mulkin ya zabi iyalensa,shi yasanya ma fulani suna fulani,sannan suka bukaci ya bar kasar sa na haihuwa tare da dukiya Mai tarin yawa.


Nigeria yadawo da Zama ya sauka a garin maidugri,Bayan zuwansu da shekara guda mahaifiyar su fulani ta rasu Sarki Abdallah ya cigaba da kula da 'yayansa mata,jikin hukuncin Allah,Allah ya kawowa fulani miji hamshakin mai kudi da sarauta domin Dan Sarkin ne Alhj yunusa Hameed dan garin Senegal,kasuwanci yakawo shi Nigeria nan yayi arziki sosai Bayan iyayenshi sun rasu.


Sosai yake son fulani da Bata kulawa na musamman a haka aka daura Aure cikin hukuncin Allah tasamu cikin danta na fari Bayan tahaifeshi yaron ya rasu.
Still ta kuma Samun cikin Allah ya azurta ta da haihuwan 'ya mace hjy Kaltume kyakkyan jinjira me sirrin wani irin kyau,bayan ta haifi Alhj kabeer shima kyakkyawan namiji mai jida kyau,sai Alhj Khamees shima haka,sai Hjy shamsiyya sai Alhj Ahmad shine autan ta.


Itakuma Hjy Baraka tayi Aure a garin zamfara wani kauye ne duk da bawani kauye bane can-can Amma Basu da wani wayewan kai,sai dai suna takama da rashin mutumci 'yan garin basa saurarawa kowa,dama Hjy Baraka fitinanniya ce tafison kanta akan komai.
Sam 'yan uwanta da mahaifinta Basu Jin dadin hulda da ita don ya zame musu Dole ne,itama hjy Aisha tayi Aure sai dai bata taba haihuwa ba, Hjy Maryam ma tayi Aure don tanada yara biyu.




Hjy Kaltume dan ta daya ne a duniya Jalal Bayan ta haifeshi tayi aure ta auri wani babban costume yanzu suna garin Abuja,domin mahaifin Jalal dan Sudan ne,shine babban jikan fulani jalal daga baya Allah ya ma mahaifinsa rasuwa,itama babban jikan Hjy Baraka itace Laweezah tunda tataso takeson Jalal duk da cewa shi Sam baya sonta,hasalima dabi'unta da habbit nata sam basuyi masa ba,bata cikin tsarin kalan matan da yakeso,hakanan yayi ma fulani biyayya ya aureta domin yana kallonta kamar uwace a gareshi.


Dalilin zuwan fulani kaduna kuwa nan mijinta ya'ajeta tare da kuyangi,ko Bayan rasuwarsa batai Aure ba.


A hakadai aka daura Auren Jalal da Laweezah Yana karatun Dr ne a Saudiya bangaren zuciya,sai dai Sam bai tafi da Laweezah ba.Sun haifi yara biyu Bayan sun girma yatafi da su saudiyya yasasu a MAKARANTA to shine rikicin da akeyi suna cewa fulani ke zugashi.



_CIGABAN LABARI_




Nan su hjy Maryam suke sanar da su Alhj kabeer duk abinda yafaru,da labarin Shakeerah ajiyan zuciya hjy Kaltume tayi da yake macece mai sanyin hali,hjy shamsiyya ko Banda huci Babu abinda take tace"Jar uba! Aiko da inanan sai naga ubanda yatsaya mata Kuma wannan yarinyar Allah ya mata albarka.


Cikin sanyin murya hjy Kaltume tace"Fulani ina yarinyar take ne?Fulani tace"Suna can bangaren nan bana cemuku na siyar ba?duk cikansu suka ce suka amsa da hakane Akira musu Shakeerah,Kiran daya daga cikin kuyangin fulani akayi akace ta Kira Shakeerah,cikin biyayya ta amsa da to ta fita.


Shakeerah kuwa Bayan fitan ta direct part din su ta nufa ta cidda Ammi tana kitchen tana hada Mata dambun naman zabi Wanda zata tafi dashi gobe,Shiga kitchen din tayi tafara tayata aiki sunayi suna hira batare da tasanar ma Ammi abinda yafaru a part din fulani ba, knocking din kofar Falon su akafara,cikin Sauri Shakeerah ta nufi kofan tare da budewa.
Kuyanga ta dubi Shakeerah tace"ranki yadade fulani na san ganinki cikin gaggawa,da Sauri Shakeerah tace"toh kice mata ganinan.
Juyawa tayi ta Shiga bedroom dinta ta dauko long hijjab dinta pink colour ta zira,Shiga kitchen tayi ta sanar da Ammi xataje sashin fulani tana kiranta,da toh Ammi ta bata amsa,har ta juya zata fita, Ammi ta kirata.
Dawowa tayi sannan Ammi tace"bude cikin carbinet dinnan ki dauko min karamin bowl.
Budewa Shakeerah tayi ta Ciro taba Ammi,amsa tayi ta cika shi da dambun nama,sannan tace ta dauki jug ta zuba mata kunun ayar da tahada a cikin firij.


Duk haka Shakeerah tayi ta dauki Kayan niki-niki ta nufi part din fulani,da alamu bakinnan na falon,kamar ta juya sai dai ta daure da kyar ta nufi cikin farlon.


Da sallama tashiga,duk cikansu suka amsa tare da zubama mata idanuwa sosai,kura mata idanu tayi gabanta na faduwa duk da tasan face din sai dai ta rasa inda tasan face din.


Karisowa tayi tana murmushi ta nufi wajen fulani,dire Mata jug din da bowl din d ke rufe da murfinshi tayi tace"fulani gashi inji Ammi na,cikin Sauri Hjy kaltume ta Kuma kallon ta,tasan muryan sai dai ta mance wacce tasani da muryan.


Shakeerah ta juyo ta gaida duk bakin dake falon,da Murmushi ko wannen su ke amsa was,hjy shamsiyya tace"munji abin arzikin da kikayi 'yan Mata,yabaki miji nagari mai kula dake.
Shiru Shakeerah tayi tana me amsawa da ameen a zuciyar ta,hjy shamsiyya tace"kinsan me nakeso dake?girgiza Kai Shakeerah tayi.
"Ga amanar fulani nan a hannunki duk Wanda yayi mata ba dai-dai ba kici kaniyar sa kada ki saurarawa kowa ninasaki.
Murmushi Shakeerah tayi tace"Aunty aini ko ansa ni ko ba'asani ba,ba'a Isa ataka fulani Ina wajen na kyaleva Koda kuwa kashe ni za'ayi.
Dariya ma abun yabawa su Alhj Khamees dariya, Alhj Ahmad yace"hjy shamsiyya adaiyi hudubar arziki Koh? Duk cikan su dariya sukasa hjy shamsiyya tace"Wallahi abun ne daban haushi sai kace Laweezan 'yar gwal ita ba kyau ba ba komai ba,Wallahi bacin zumunci da tuni yadanna mata saki kowa ya huta.
Shakeerah tace"Fulani gani. Dafa kanta fulani tayi tace"tashi kitafi Shakeerah Allah ya Miki albarka,kicema Maryam din ina gaisheta da aiki Allah yajikan Muhammadu.
"Ameen Shakeerah tafada sannan tamike tatafi.


Bayan fitan ta su Alhj kabeer suka Mike Dan zuwa masallaci.
Hjy shamsiyya ta dubi su hjy Maryam tace"Inna Maryam gani da shawara.


Gaba Daya maida hankali sukayi wajenta don jin shawarar.
_I NEED UR COMMENT_












Xahratty ce✍🏽


Lallai Alqalami 🖋️ Yafi takobi🗡️
💕💕
❤️
[7/18, 2:05 PM] Xahratty🥰😘: 💐✨ *DIAMOND LADIES* 💐✨
(Daukar Fansa)









Please Login or Register in order to submit comment