Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

zama gimbiya😂)




Haba ai masarautar mure sai ta rud'e da murna aka fara shirye-shiryan taran amarya kuma gimbiya khaujut, gimbiya Haleematun-sa'adiya tunda taji zancen ta k'ara saka kanta cikin damuwa da bak'in ciki.






Ba'a Dade ba Nan ma suka fara Shirin barin k'asa Mai tsarki zuwa Nigeria kasar mu ta gado sarki Fahad Abdullah sai lallashi amaryar shi yake dan kukan Nan da take ji yake kaman ana yanka zuciyar shi.






Sai da suka je Haram suka k'ara d'awafi sannan suka wuce airport, tana manne a jikin shi Daman gashi khaujut bade na san jiki ba, Nan da nan kuwa suka shiga jirgi ya Lula dasu Nigeria.






Babban tarba ake shiryawa mai-martaba sarki Fahad Abdullah Wanda an Dade ba'a Yi irin bikin ba a masarautar mure, komai yayi dai-dai jiran isowar sarki Fahad Abdullah kawai ake.






Gimbiya Haleematun-sa'adiya kon tana D'akin ta kwance bakin ciki ya ishe ta kaman ta kashe masu wannan busa da kid'e-kiden take ji.




Tun kafin jirgin su ya sauka fadawa sun zagaye airport d'in jiran su kawai suke, akwai ba'a Dade ba jirgi ya fara k'asa-k'asa har ya sauko k'asa.




Nan da Nan mutane suka fara fitowa a Haka har su mai-martaba sarki Fahad Abdullah suka sauko shima fadawa ne suka zo da sauri suka rufe shi har sai da suka shiga mota shi da gimbiya khaujut.




Nan suma fadawan suka shiga suka fara tafiya ba'a Dade ba suka iso babban shiga Gate d'in masarautar tun daga Nan aka fara musu marhaba da zuwa, Busan da ake yi ya karu suna shiga kon cikin gidan nan aka fara fitowa ana musu albarka da dawowa.






Iyayan shi Mata suka zo Dan fito da amarya khaujut daga mota....








Vote
Comment
&
Share








*Aunty baby ce* 😉✍
[1/6, 10:37 PM] Mum Irfaan🤱🏻: 🦚🦚🦚🦚🦚🦚🦚
🦚🦚🦚🦚🦚
🦚🦚🦚
🦚🦚
🦚


🤴🏻 *IZZAR SARAUTA*🤴🏻



















®☄
*GASKIYA WRITERS ASSOCIATION✍*
{ _Gaskiya ɗaya ce daga ƙinta sai ɓata, burinmu mu faɗakar da al'umma domin ribantar duniya da kuma lahira._ }




🎐 ```G•W•A```🎐
*_GASKIYA DOKIN ƘARFE•_*🏇🏼










*Story*
*&*
*written*
*By*
*Aunty baby* ✍






*DEDICATED TO..*
*MISS XERKS*








*BISMILLAHIR* *RAHMAIR RAHIM*










📝 *Page* 7⃣⏩8⃣










*____________* 📖 *Nigeria* kuwa, komai na tafiya dai-dai duk abunda sarki ya Bari ai ma talakawa ana musu sannan kuma.






K'annin shi Aliyu na kula da komai gimbiya Haleematun-sa'adiya tana ta rainon cikin ta da yanzu yake wata hudu.






Kuma tana samun kula daga mahaifiyar sarki Fahad Abdullah da kuma yan uwa shiyasa hankalin ta kwance bata da matsalan komai.








*Saudiyya* Al'mustapha ya samu iyayan shi akan maganar Amma ina duk yanda yake tunanin abun ya huce nan sosai mahaifiyar shi.






Ta fara fad'a Wai baya son yar uwar shi tunda gashi har yana tunanin auran da Ita a Nigerian.






Sosai ya shiga tashin hankali dan gaba daya sarki Fahad Abdullah ya koma abin tausayi kullum zancen shi ya taimaka mai in be samu khaujut ba mutuwa zaiyi.






Daga karshe ma har cewa yayi bazai koma Nigeria ba zaice wani ya amsa sarautar, hakan da ya fad'a shi ya k'ara bawa Al'mustapha tausayi.






Ya dau aniyar insha Allah sai ya aura mishi khaujut, gurin wani babban uncle d'in su yaje Wanda duk family din su suke ji da shi kuma zasu ke jin maganar shi.




Duk ya gaggaya mai abunda ke faruwa sannan yace, shi tausayin abokin nashi yake kuma yana da hankali sun zauna har na tsawon shekara biyar Babu wani abun na banza da yake yi.




Jinjina Kai uncle d'in yayi sannan yace, "ita khaujut d'in tana son shi in dai tana son shi ba matsala".




Rasa abun da zaice Al'mustapha yayi kawai sai ya d'aga Kai alaman tana son shi tunda yasan halin khaujut tana da hakuri kuma yasan zata amince.




Uncle d'in yace. "to yanzu su tashi suje gidan iyayan nasu ya musu magana" hakan nan Al'mustapha ya tashi jikin shi duk a sanyaye, tunda ita khaujut ma bata san abunda ake ba shi kad'e yake kidan shi yake rawan shi.






Ko da suka je gidan uncle d'in yama iyayan nasu magana amma ina gaba daya sunce basu yarda ba sabida basu san ya Nigeria take ba, yayi ta basu hakuri da lallashi amma abun yaci tura har yayi fushi ma ya bar gidan.




Sarki Fahad Abdullah yana can masaukin su kuma ba lafiya sabida shi fa Allah ne ya daura mai san wannan yariya be iya zatun zai iya cire ta a ranshin mutanan shi hankalin su ya tashi sosai ganin yanda lokaci daya ya rame ya daina wal-wal kaman ba sarki Fahad Abdullah ba.




A haka har aka kwashi tsawon sati biyar suna cikin wannan halin gashi Al'mustapha yayi yayi abun ina kowa a family sun basu amince ayi wannan abu ba.




Wata ranar Friday Al'mustapha ya shirya yace Ita ma khaujut ta shirya zasu fita nan da nan ta shirya direct masaukin su sarki Fahad Abdullah suka je.




Yana kwance duk ya rame na lafiya gashi yanzu sauran sati daya su bar saudiyya shiyasa ya k'ara shiga tashin hankali, Al'mustapha da khaujut suka ganshi a cikin wannan halin duk da khaujut yariya ce amma be hana ta tausaya mai halin da ta ganshi a ciki ba.






Kallon ta Al'mustapha yayi yaga yanda tayi shuru tana kallon shi yayi murmushi sannan yace, "ya ukutee ki taimaki wannan bawan Allah nasan yar uwata tana da tausayi da sanin ya kama Dan Allah kinji my ukutee".






Hawaye ne suka fara zubowa sarki Fahad Abdullah ya taso daga in da yake zaune ya durkusa gaban ta yace, "dan Allah kiyi hakuri ki ceceni Wallahi zan iya mutuwa akan ki yanzu haka ciwan da nake ji a zuciya ta kaman za'a dauka raina ki taimaka min khaujut".




Kuka sosai khaujut ta fashe da shi sannan ta kalle Al'mustapha tace, "bani bace matsalan iyayan mu ne Ni na yarda in dai sun yarda".




Jinjina kai Al'mustapha yayi sannan yace, "ba komai daman buk'atata ki yarda Allah ya miki albarka khaujut Allah yasa yanda kikai farantawa wani ke ma Allah ya faranta miki".




Tashi tayi ta fita a D'akin mota ta shiga ta k'ara fashewa da kuka tana ganin Bata cuci kanta ba kuwa Anya zata iya bin shi Nigeria ta bar iyayan ta anan.




Haka dai take ta tunani iri-iri, Al'mustapha ya kalle sarki Fahad Abdullah yace, "abokina zanyi duk yanda zanyi in aura maka khaujut amma da alk'awarin zaka rik'e min ita Amana".






Da sauri ya d'aga Kai yace, "na yarda Wallahi na yarda duk abunda na Mata Kai min ko kashe ni ne kayi".




Dafa kafad'ar shi yayi sannan yace, "ba zancen kisa amma Wallahi ka batawa khaujut ba maganar abota, sabida a tsarin k'asar mu... " Ai be Bari ya k'arasa ba yace,




"Wallahi nayi maka alk'awari khaujut baza ta tab'a shiga wani hali ba kuma zan rik'e ta kaman yanda zan rik'e Kai na insha Allah".




Tashi Al'mustapha yayi yace, "ka shirya da Wanda zasu tsaya ma insha Allah yau za'a daura maka aure da khaujut".






Ai ya rasa wani irin farin ciki ma zaiyi kawai sai ya duk'a yayi sujjada ya gaida Allah yana nuna farin ciki mara musaltuwa.




Murmushi kawai Al'mustapha yayi yana jin dadin yanda yake nuna ma yar uwar shi soyayya, sannan yace, "su hadu a Haram bayan sallah JUMA'AT".




Sannan ya fita, sarki Fahad Abdullah ji yayi kaman an saka shi a aljanna Kiran yan Nigeria yayi ya sheda musu duk abunda ya faru, ba k'aramin murna masarautar mure ta shiga ba.




Barin ma iyayan shi Dan Daman burin du kenan dan ba'a tab'a sarki da Mata daya, haka mutan fada ma kowa ka gani yana cikin farin ciki.






Gimbiya Haleematun-sa'adiya kuwa tana Jin wannan maganar sai da ta suma nan fa ta fara kuka ita ba ai Mata adalci ba ko haihuwa batai ba za'a ce zaiyi aure.




Maman ta da kanta tazo tana lallashin ta kuma tana gaya Mata cewa ai Daman sarki baya Mata daya tayi hakuri ta kwantar da hankalin ta amma ina nunawa tayi bata san zancen ba.




Haka dai kowa ya hakura yasa Mata Ido sabida haukar da take tayi yawa.






Saudiyya kuwa bayan fitowa daga sallah JUMA'AT Al'mustapha da uncle d'in su suka daura auran khaujut da sarki Fahad Abdullah.




A iyayan su Al'mustapha ba Wanda ya sani duk da Al'mustapha yana cikin tashin hankali Amma hakan be sa ya sare ba.




Sarki Fahad Abdullah kuwa ai ya kasa rufe baki sabida tsabagin murna hamdallah kawai yake ma Allah da khaujut ta zama matar shi.




Bayan daurin aure uncle da Al'mustapha da sarki Fahad Abdullah suka huce gidan su Al'mustapha, lokacin kon duk kuwa na gidan na Nan Banda khaujut da take bedroom tana kuka.




Shiga sukayi babban parlour gidan sannan uncle d'in yace duk kowa na gidan yazo yana da magana da su, duk kon suka hadu sannan yayi gyaran murya ya fara magana da harshin su na larabci.




"Haka Allah ya tsara khaujut matar wannan bawan Allah ne ba yanda zamu iya sai dai hakuri tunda yau na daura musu aure".




Tashi tsaye mahaifin Al'mustapha yayi cikin kid'ima da tashin hankali yace,












*Vote*
*Comment*
*&*
*Share*








*Aunty babyn ku ce* ✍


[1/6, 10:37 PM] Mum Irfaan🤱🏻: 🦚🦚🦚🦚🦚🦚🦚
🦚🦚🦚🦚🦚
🦚🦚🦚
🦚🦚
🦚








🤴🏻 *IZZAR SARAUTA*🤴🏻









*Story*
*&*
*written*
*By*
*Aunty baby* ✍






*DEDICATED TO..*
*IZZAR SARAUTA* *fan's*






*BISMILLAHIR RAHMAIR RAHIM*








📝 **Page**1⃣3⃣to1⃣4⃣




Tace, "Allah ya baka yawan rai gimbiya khaujut Allah ya sauke ta lafiya" da sauri mai-martaba sarki Fahad Abdullah ya daga hannun shi sama yana kabbara, sannan yace,




"Da fatan dai tana cikin koshin lafiya? ".




Murmushi jakadiya tayi sannan tace, "Allah ya kara ma nisan kwana baka tambaya mai aka samu ba".




Murmushi yayi sannan yace, "to Mai aka samu? " Cikin zumud'i jakadiya tace, "magajin ka insha Allah namiji ta samu mai kama da Kai".






Nan da nan farin ciki ya mamaye shi ya rasa ma ina zai sa kan shi dan murna bakin ciki ya kasa rufuwa, sabida be taba kawo wa zai samu namiji ba cikin farin ciki yace, "jakadiya kin zo min da albishir mai girma dole ki amsa kyauta mai girma".




Zubewa kasa tayi tana mai kirari da mika godiya sannan ta fita cikin farin ciki.






Nan da Nan masarautar mure ta san da wannan haihuwa kowa ka gani murna yake mai-martaba ya samu magaji,




Gimbiya khaujut tana can an kaita part d'in ta an gyara ta da jaririn ta da ka gan shi kaga jinin larabawa Amma fuskan shi sak na sarki Fahad Abdullah ne.




Ita ma tana cike da farin ciki sosai ganin Allah ya bata abun da bata taba tunani ba, sarki Fahad Abdullah ne ya shigo cikin farin ciki, ya zauna kusa da Ita yana jin sonta na k'ara shiga jikin shi.




Murmushi yayi sannan yace, "ban san da wani baki zan mik'a godiya ta ga Allah ba da ya bani ke sannan ya bani d'a namiji Wanda na dade ina so Allah nagode ma Allah na kara gode ma".




Shuru kawai gimbiya khaujut tayi tana jin kaunar mijin nata na Kara shiga zuciyar ta, tashi yayi ya dauko jaririn da yake kwance gadon shi irin na sarauta.




Kallon yaron yayi wani irin son shi da kaunar shi yaji ji yake kaman ya maida shi ciki Dan so, addu'a yayi mai sannan ya rungume shi a jikin shi yana kara gode ma Allah.




Gimbiya Haleematun-sa'adiya kuwa...












🥴 *Wallahi yau bani jin typing sai anjima ko gobe*












*Vote*
*Comment*
*&*
*Share*








*Aunty baby ce* 😁✍
[1/6, 10:37 PM] Mum Irfaan🤱🏻: 🦚🦚🦚🦚🦚🦚🦚
🦚🦚🦚🦚🦚
🦚🦚🦚
🦚🦚
🦚


🤴🏻 *IZZAR SARAUTA*🤴🏻



















®☄
*GASKIYA WRITERS ASSOCIATION✍*
{ _Gaskiya ɗaya ce daga ƙinta sai ɓata, burinmu mu faɗakar da al'umma domin ribantar duniya da kuma lahira._ }




🎐 ```G•W•A```🎐
*_GASKIYA DOKIN ƘARFE•_*🏇🏼










*Story*
*&*
*written*
*By*
*Aunty baby* ✍






*DEDICATED TO..*
*MAMAN MUHAMMAD*
*MAI-GWAZA*






*BISMILLAHIR RAHMAIR RAHIM*










📝 *Page* 1⃣1⃣⏩1⃣2⃣








*____________* 📖 Gimbiya Mabaruka matar mai-martaba ita ta fito da amarya khaujut daga mota sannan ta shigar da ita babban parlour gidan, nan kuyangu suka fara gud'a masu busa nayi.




Wata kujeran sarauta aka zaunar da ita sarki Fahad Abdullah ya zo ya zauna kusa da ita, gimbiya Ameena ce ta matso kusa da ita tana Mata barka da zuwa masarautar mure.




Khaujut duk da Bata San abunda ake cewa ba Amma abun ya Burge ta ganin yanda ake murnar ganin ta sai ta tsinci Kan ta cikin farin ciki duk wani bakin ciki sai taji ya gushe.






Jakadiya tana kallon kyau gimbiya khaujut ta fita parlour da sauri har tana tuntube part d'in gimbiya Haleematun-sa'adiya ta shiga cikin rawan jiki irin na munafukai.






Gimbiya Haleematun-sa'adiya tana kwance bak'in ciki duniya ya ishe ta Dan anyi anyi da ita taje tayi ma mai-martaba sarki Fahad Abdullah sannu da zuwa tak'i.




Jakadiya ta shigo ta same ta cikin rawan Baki ta fara magana, "barka da hutawa uwar gijiyata uwar gida gun sarki Fahad wacce Babu kamar ki, in kin bani dama nazo Miki da wani labari".




Tashi tayi zaune tana kallon jakadiya sannan tace, "fad'i Ina sauraran ki".




K'asa da murya tayi sannan tace, "Allah ya taimake ki mai-martaba Ashe balarabiya ya auro yanzu na ganta da Ido na kyakyawar gask.." bata k'arasa ba sabida wani gigicacan Mari da taji saman kuncin ta.




"Wannan bak'in labarin kike gaya mai to Wallahi Bari kiji duk lokacin da kika k'ara zuwa min da irin wannan labarin sai kin fuskan ci hukunci Mai tsauri" cewar gimbiya Haleematun-sa'adiya.




Shuru jakadiya tayi dafe da kuncinta sannan tace "a min afuwa ya sarauniyar kyakyawa uwar gidan da Babu kamar ta zan iya tafiya? ".




Daga Mata Kai tayi kawai sannan jakadiya ta fita tana data sanin zuwa,




Shagali ake sosai sun nuna farin cikin su da zuwan ta duk wata al'ada da suke in an kawo amarya gidan sai da sukai Mata shima mai-martaba sarki Fahad Abdullah ba k'aramin Dadi yaji ba ganin yanda suke murna.




Yarima Aliyu k'anin sarki Fahad Abdullah sosai yake nuna ma gimbiya khaujut kauna ganin ta yake kaman k'anwar shi, ita ma tunda ta fuskanci Yana kula da ita sai take sakin mai fuska.




Haka masarautar ta kasance har na tsawon kwana biyu ana shagulgula, duk wannan shagalin da ake gimbiya Haleematun-sa'adiya bata tab'a zuwa ba, sarki Fahad Abdullah kon ko a jikin shi be nuna ya damu ba shi ta khaujut kawai yake dan ya sama ranshi insha Allah baza ta tab'a kukan yan uwan ta ba.






Bayan an gama duk wani shigali da ake komai yayi dai-dai sarki Fahad Abdullah ya had'a gimbiya khaujut da gimbiya Haleematun-sa'adiya yayi musu nisiha sosai yace khaujut ta dunga girmama gimbiya Haleematun-sa'adiya kowa dai ya gimama dan uwan shi.




Duk suka ce insha Allah sannan kowa ya tashi ya tafi part d'in shi, tun daga ranar gimbiya Haleematun-sa'adiya bata kara saka gimbiya khaujut a Ido ba dan ko ganin ta bata son yi so da dama tana zuwa gaisheta sai tace ace tana bacci.






Haka zaman nasu ya kasance sarki Fahad Abdullah yana kokarin ganin yayi adalci a tsakanin su dun da haka dai yafi son gimbiya khaujut dan kullum ya ganta sonta k'aruwa yake a zuciyar shi.




Rayuwar gimbiya khaujut a masarautar mure tana jin dadin shi sosai Amma Abu biyu ne kawai yake damunta na daya iyayan ta da kullum sai tayi kuka in ta tuna yanda suka rabu Amma.




Sarki Fahad Abdullah yana lallashin ta akan tayi hakuri insha Allah zai kaita ta gansu ko lokacin zuciyar su tayi sanyi.




Na biyu kuma shine yanda kishiyar ta take nuna Mata tsana wani abu da ta lura da shi shine in a gaban mai-martaba ne tana janta a jiki sosai Amma in ita da ita ne ko kallo bata ishe ta ba.




Cikin gimbiya Haleematun-sa'adiya nata girma yanzu har ya shiga wata tara addu'a kawai take Allah yasa namiji ne duk hankalin ta yanzu a tashe yake burin ta kawai ta haife namiji.




Lokacin kuma gimbiya khaujut take dauke da cikin wata uku sarki Fahad Abdullah yayi murna sosai haka masarautar mure cike take da murna.




Ranar wata alhamis gimbiya Haleematun-sa'adiya ta tashi da nakuda mahaifiyar ta kawai ta kira nan da nan tazo suka tafi asbitin cikin masarautar.




Ba'a fi awa biyu ba Allah ya sauke ta lafiya, tana haihuwa bata tsaya komai ba ta fara duba abunda ta haife Kash mace ce kuka ta fashe da shi, wani irin bakin ciki ya rufe ta kaman ta kashe jaririyar taji.






Nan da nan aka gyara ta da jaririyar ta, mai-martaba yana fada aka Kira shi aka gaya mai murna sosai yayi Nan fada ma ta cika da farin ciki.






Tun daga ranar kullum cikin bakin ciki take ita taso ta haifi namiji tasan dai shi zai gaji masarautar mure amma bashi ta haifa ba gashi ta lura khaujut ciki gare ta sai ta k'ara shiga cikin damuwa kar ita ta haife namijin dole kon ta san yanda za'a yi.






Haka akai suna yariya taci sunan matar mai-martaba tsuhon sarki gimbiya Maimunatu, anyi shagali k'ala-k'ala.






Bayan wata hudu lokacin cikin gimbiya khaujut watan shi bakwai a lokacin kuma sarki Fahad Abdullah ya shirya musu tafiya zuwa saudiyya dan ziyaran Yan uwan ta.






Gimbiya Haleematun-sa'adiya ki yarta tana da wata hudu tayi bul-bul abinta,




Ranar da zasu tafi har airport gimbiya Haleematun-sa'adiya ta raka su sai da taga jirgin su ya tashi sannan ta koma gida, suna Isa saudiyya masaukin su suka huce.




Wanka suka yi suka huta sannan suka huce Haram Dan sauke umrah bayan sun sauki sai sarki Fahad Abdullah ya Kira abokin shi Al'mustapha Dan ya fad'a Mai sun zo.




Amma wayan baya shiga haka yayi ta kira a kashe sai kawai suka huce gidan su khaujut d'in, shiko Al'mustapha yayi tafiya ne zuwa Dubai shine yasa ba'a samu wayan shi ba.




Bayan sun Isa gidan sarki Fahad Abdullah da gimbiya khaujut suka shiga gidan, jikin ta ne yayi sanyi sosai Dan bata San da wani Ido zata kalle iyayan nata ba.




Noking suka fara yi da sauri wani yaro yazo ya bud'e yana ganin khaujut ya juya da gudu cikin gidan yana fadin, "khaujut ga khaujut ta dawo".




Maman tane ta fito da sauri tana tambayan yaron "wata khaujut d'in?" Kafin yaron ya bata amsa su khaujut sun shigo.






Da sauri khaujut taje ta rungume mahaifiyar ta tana kuka itama rungume ta tayi tana shafa kan ta, tsawan da suka ji ne yasa ta saki khaujut da sauri ita kam khaujut sai da cikin jikin ta ya murd'a.






BABAN ta ne fuskan Nan nashi a daure ya matso kusa da mahaifiyar ta kamar zai bige ta yace, "bana ce Karta k'ara zuwa min gida ba menene dalilin da ta zo kika kulata? ".






Kasa magana ma maman nasu tayi sabida ita a ganin ta be kamata suyi musu wannan tarba ba, kama hannun khaujut yayi ya fara tafiya da ita dai da ya kaita har kofar Gate d'in gidan sannan ya saki ta.




Sarki Fahad Abdullah yana tsaye Yana kallon ikon Allah nuna Mata waje yayi yace, "kin ga kofar gidan Nan na kara ganin ki a wajan Wallahi sai na kusa kashe ki kije can wajan Wanda suka daura miki auran Ni yanzu na tashi a uban ki ban sanki ba Baki sanni ba".






Kuka khaujut ta fashe da shi sannan tace, "ya Kai mahaifina ka yafe min laifin dana ma Allah ya riga ya tsara wannan abun bazan iya jure fushin ku ba" ta k'arashe maganar tana zubewa a gaban shi.




Juyawa yayi yayi shigewar shi ciki ko kallon ta beyi ba, da sauri sarki Fahad Abdullah ya karaso ya rik'e Mata hannun ta mik'e sabida cikin da yake jikin ta.




Kanta ta daura a girjin shi ta saki kuka Mai tsuma zuciya, mota ya shigar da ita Yana lallashin ta Nan direba ya tada motar suka tafi masaukin su.






Haka suka zauna a k'asa Mai tsarki har na tsawon sati biyu, sun je gidan uncle ya amshe su da farin ciki da murna har ta kwana.




Kullum sai taje gidan su Amma baban su ya Hana ta shiga ranar da zasu koma Nigeria ma Sai da taje Amma ko kallon ta beyi ba.






Haka suka komai Nigeria duk wal-walan ta ya ragu duk in ta tuna fushin da iyayan ta suke da ita, kullum Yana k'ara kwantar Mata da hankali akan tayi hakuri komai zaiyi dai-dai.




Haka take ta rainon cikin ta har yanxu ya Kai wata Tara cib kullum jiran haihuwa ake, gimbiya Haleematun-sa'adiya kuwa ta gama shirya duk wani abu da zata ma duk Dan da ta haife shiyasa yanxu Bata gaban ta.






Wata safiyar juma'a gimbiya khaujut ta tashi da nakuda Wanda tun shida na safe aka kai ta asbiti har kusan sha-biyu tana Abu daya.




Hankalin kuwa na masarautar ya tashi dan mai-martaba ya kasa zauna ya kasa tsaye, jakadiya ce ta shigo D'aki nashi da sauri tace.......








*Vote*
*Comment*
*&*
*Share*








*Aunty babyn ku ce* 😉😉✍
[1/6, 10:37 PM] Mum Irfaan🤱🏻: 🦚🦚🦚🦚🦚🦚🦚
🦚🦚🦚🦚🦚
🦚🦚🦚
🦚🦚
🦚








🤴🏻 *IZZAR SARAUTA*🤴🏻











®☄
*GASKIYA WRITERS ASSOCIATION✍*
{ _Gaskiya ɗaya ce daga ƙinta sai ɓata, burinmu mu faɗakar da al'umma domin ribantar duniya da kuma lahira._ }




🎐 ```G•W•A```🎐
*_GASKIYA DOKIN ƘARFE•_*🏇🏼










*Story*
*&*
*written*
*By*
*Aunty baby* ✍






*DEDICATED TO..*
*MOM AYSAR*
*Masoyiya Allah ya huce zuciyar ki* 💘💘💘💘💘






~VOTE & FOLLOW 4Wattpad @ GaskiyaWritersAsso.~








*BISMILLAHIR RAHMAIR RAHIM*










📝 *Page* 1⃣5⃣⏩1⃣6⃣








*___________*📖 Gimbiya Haleematu-Sa'adiya kuwa tunda taji ance gimbiya khaujut ta haihu ta bazama asbiti, lokacin tuni an huce da gimbiya khaujut gida.






Taji haushi sosai da Dan ba Haka ta so ba, sai a lokacin ta tambaya mai gimbiya khaujut ta haifa aka ce Mata namiji cikin tashin hankali ta furta, "namiji? ".




Sai da kanta ya sara jiri ya fara d'ibar ta da k'yar ta iya Kai kanta cikin part d'in ta tana zuwa kuwa ta zube kan Bed tana kuka Bata San ma wani irin bakin ciki take a lokacin ba, "shikenan wannan matsiyaciyar zata gaje masarautar Ina bazai tab'a yuhuwa ba" Haka take fad'a sai kace wacce ta haukace.




Masarautar mure kuwa ta kid"e da bushe-bushe da kid'e-kide kowa murna yake, mai-martaba sarki Fahad Abdullah da Kan shi ya bud'ewa talakawa D'akin abinci kowa ya d'ibi yanda yake so.






Matan tsohun sarki rabon atamfa da shadda kawai suke Yarima Aliyu kuma ragona kawai yake fitarwa ana yanka wa.




Haka dai masarautar mure ta cika da shagulgula har ranar suna, ai ranar ba'a magana, yaro yaci sunan tsohun sarki Abdallah, gimbiya khaujut take kiran shi da Dameer wato( *heart* , *conscience* ).




Gimbiya Haleematun-sa'adiya kuwa tun da gimbiya khaujut ta haihu so daya taje ta ganta ko jaririn ma bata iya Bari ta gani ba sabida bak'in ciki da take ciki,






Anyi taron suna na lafiya an tashi lafiya, Bayan suna gimbiya khaujut taci gaba da rainon Dan ta Dameer cikin kwanciyar hankali Wanda a duniya ba Wanda take so a yanxu barin shi.






Hmmmmm Daman larabawa ba dai na son 'ya'ya ba a gaban kowa nuna Mai so da kauna take, haka ma ta fannin mai-martaba sarki Fahad Abdullah sosai yake nuna Mai so har fada yake zuwa dashi.




Wannan soyayya da yake nuna Mai sai ya dasa wa gimbiya Haleematun-sa'adiya tsanar yaron kwata-kwata a duniya taji Bata da mak'iyi kamar shi sabida tana ganin ai 'yarta ita ce babba Amma ba'a nuna ma 'yarta so kaman yanda ake wa wannan yaron.




Haka Nan sai ta aiko a Kai Mata shi ta nunawa kamar tana son yaro, Amma Ina ba Haka bane ana Kai Mata shi zata Fara gana Mai azaba yaro yayi ta kuka a rasa Mai ke damun shi.




Har dai gimbiya khaujut ta fara ganewa sai ta daina Bata shi kwata-kwata nan ma Sai da tayi ta bala'i gimbiya khaujut tayi kamar Bada ita take ba.




Kwance tashi ba wuya yanzu Dameer har yayi wata shidai a duniya lokacin yayi masifar wayyo, kyawun shi ya k'ara fitowa irin na jinin larabawa kowa son yaron nan yake sabida wayyon shi.




Sarki Fahad Abdullah ya dau son duniya ya daurawa wannan yaron ko kukan shi yaji ko d'aga Ina ne sai ya bar fada ya tafi gurin shi, Haka ma k'anin shi Yarima Aliyu yana bala'i son yaron.




Ya shiga wata na bakwai mai-martaba sarki Fahad

Please Login or Register in order to submit comment