Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

jima awajena sai na dawo da ita gareka.


Daganan nayi nadama na shiryu na daina fashi,haka kuma nayi alkawarin rike haneefa.


Daga baya kuma danaga xata taso cikin kuncin talauci yasa na yanke shawarar dawo da ita gareka ta yadda baxaka fahimta ba,nayi takardar karya akan tsintar ta nayi.




Lokaci lokaci ina bin diddigin halin da take ciki agidannan,tanan ne na gane tana samun kyakykyawar kulawa daga gareka.




Daga bisani rashin lafiya mai tsanani ta kamani,wadda har yau ban warke ba.


Yau ina kwance naji sanarwa haneefa ta gudu,shiyasa na yanke shawarar xuwa na bayyana abinda yake gaskiya ne,amma dan Allah ka gafartamin.








By
Hauwa s.Ahmad
Maryam y.Ahmad




💞💞💞💞








[10/21, 8:47 PM] ‪+234 814 443 8844‬: 🌺'YAR MULKI🌺
2016


6⃣7⃣






📚✍




Sarki salahuddeen yasa wani irin kuka da har sai da sautin sa ya fito,hawayene kawai ke kwarara daga idonsa,ya matso gaban malam jibrin a fusace,ya daga hannu ya kwada masa mari,bai tsaya a daya ba saida yayi masa guda biyar kyawawa.sannan yace ka cuceni da baka sanar dani haneefa 'yata bace tun farko.


Tun batan da maman haneefa tayi mai martaba bai karayin kuka ba kamar yau ba,saboda kullum kukan xuci yake tare da fitar da hawaye,kuma yana jin kamar hajiya maryam ba rasuwa tayi ba,bata tayi,yau kam sosai sautin kukansa yake fita saboda yasan baxai kara ganin maman haneefa ba.


Kowa na wajen saida yayi kwalla banda Amal da momyn ta,ba haka sukaso ba.


Ni kuwa nace to ya xasuyi?




Abdul da naseer ma kukan suke,da sauri Abdul ya karasa kusa da maimartaba ya rike shi,tare da fadin Abba kayi hakuri,yanxu abin da yakamata muyi shine mu nemi haneefa,kar lokaci ya kure.sarki yana kuka yace I can't resist.


Fadawa kuwa basu taba ganin bacin ran mai martaba kamar ranar ba,cewa suke Allah ya huci xuciyar sarki mai adalci contineously....!!!


Lami kuwa(matar jibrin) kuka take haka talle suka xube kasa suna bawa sarki hakuri.


Sarki ya daka musu tsawa tare da fadin ku bace min daga gabana banason ganinku,sannan ya nuna sallama yace ka bisu har kauyen su kasan inda gidan su yake.ya ansa angama ranka ya dade.




Already Abdul da Naseer sun fita duba haneefa cikin gari,duk inda ransu ya raya nan suke bi ko xasu ganta ko kadan inda take banan suka nufa ba,ita tayi gabas su sunyi yamma(hannun riga kenan).




Kafin kace meye wannan har labari ya yadu cikin gari,within a very short period of tym.cewar Haneefa 'yar sarkice.


Nan da nan 'yan jarida suka cika gidan,suka fara suburbudawa mai martaba tambayoyi,wanda suke bukatar amsa daga malam jibrin,hakan ne yasa aka tashi driver da sallama suka dawo da malam jibrin don ansa tambayoyin da suka kamaceshi.




Abin ka da lamarin manya a ranar gabadaya 36 states na Nigeria labari ya yadu,sarkin kano da malam jibrin ake nunawa a kowanne gidan television ga kuma hoton haneefa.




Ummiey matar sarkin yola kenan,na ganin wannan sanar wa ta sanar da mai martaba sarkin yola,nan da nan suma members na family'n kowa ya shiga rudani,basu iya jurewa ba,a lokacin kowa ya shirya suka tafi kano cike da alhinin yadda akayi lamarin ya kasance.





HANEEFAH......


Tunda tayi pillow da akwatin ta ba abinda take sai kuka,mai gadin gidan ne ya fito yace lafiya kike kuka malama,me kike anan da wannan daren haka?tace dashi bakomai amma dan Allah so nake ka taimakamin na shiga gidannan ko xasu bani wajen kwana kafin gobe,mai gadin ya nisa yace masu gidannan basu cika zama ba,yanxu haka da muke magana basanan,jiya jiyan nan suka tafi abuja,acan uban gidana yake aiki,haneefa tace to dan Allah ko a harabar gidannan ne ka tai makamin na kwana,inyaso gobe da wuri sai in wuce,yace to ba damuwa,haka haneefa ta shiga da kayanta tayi shimfida akasa ta kwanta.


Washegari.....


Tayiwa mai gadin godiya tare da yi masa sallama,taja trouly'n ta ta tafi gently,shiruuuu unguwar ba mutane sosai,sai kayi awa bakaga mutum ya wulga ba ko da ranane balle yanxu da sassafe.haka taci gaba da tafiya har ta gaji,taja ta tsaya don jiran abin hawa.




Haneefa tayi xurfi sosai cikin tunanin inda xata,but she did not find out,eyyyahh..!
Kawai sai ji tayi mota ta tsaya a daidai saitin ta,bata ganin fuskar wanda ke cikin motar saboda glass din tinct ne,guy din dake cikin motar ya xuge glass slowly,ya risina kansa kadan ta yadda xai karewa haneefa kallo.




Idon sa na sauka akan haneefa,xuciyar sa tayi shaking aransa yace wawwwww,such beauty,yace amm 'yan mata ina xuwa haka da wuri? Haneefa bata amsa masa ba sanin cewar batasan inda xata ba,ya sake cewa,idan baxaki damu ba muje na rage miki hanya mana,




Haneefa tace nooo,thank u,yace kiyi hakuri mana idan na tafi baxan ji dadin rejecting kyautatawar danakeso nayi miki ba,please let's go


Haneefa ta danyi murmushi kadan da kyanta ya sake bayyana,wanda ba har xuci ba,Adnan ya fito ya karbi akwatin dake hannun haneefa yasa a boot,ya bude mata gidan gaba,ta shiga,ya rufe ta sannan ya koma seat dinshi,ya fara driving slowly.








By
Hauwa s.Ahmad
Maryam y.Ahmad





💞💞💞💞
[10/21, 8:47 PM] ‪+234 814 443 8844‬: 🌺'YAR MULKI🌺
2016




6⃣8⃣






📚✍




Adnan ya juya ya kalli haneefa wadda ba karamin birgeshi tayi ba,aransa yace baxan taba bari wannan kyakykyawar yarinyar tayi escaping daga gare ni ba,har sai bukata ta ta biya.ya saki wani shu'umin murmushi,sannan yace amm menene sunan ki? Ta dan basar sannan tace sunana haneefa,Adnan yace,sunan akwai dadi,ni kuma sunana Adnan,amma yanxu dole na koma haneef just because of u haneefa.


Ta danyi murmushin yake,sannan ta kawar da kanta,Adnan yace ina xakije haka da wuri?


Nan da nan idon haneefa ya ciko da kwalla,tace ni kaina bansan inda xani ba,bani da kowa agarinnan dawowata kenan jiya daga makaran na tarar gidan mu ya kone har iyayena gaba daya,gashi bani da relatives.




Adnan yace it's ok please,don't cry,kamar dagaske tausayin haneefa yake,nan kuwa,tsanananin pretending ne,aransa yace yessssss dole ki kasance tare dani.




Yace karki damu haneefa,bari xan kaiki gidanmu,wajen mamana,nasan xakiji dadin kasancewa da ita,haneefa taji wani irin dadi,tace to na gode.




Adnan yayi horn a kofar wani makeken gida,mai gadin yayi sauri ya bude,cikin gidan Adnan yashiga da motar yayi parking a harabar gidan,ya bude boot ya dakko akwatin haneefa,ita kuwa rike take da hand bag dinta,Adnan ne yayi mata jagora xuwa cikin gidan.


Tunda haneefa take bata taba ganin gida mai kyau kamar wannan ba,haka ta wangale ido tana kalle kalle kamar ba a gidan sarki ta taso ba,baxan misalta kyau da kuma tsananin girman gidan ba.


Suka haura saman gidan Adnan yacewa haneefa nan ne dakin ki akwai bandaki a ciki,haneefa tace ok,muje na gai da mama,then sai na dawo,Adnan yace nooo relax,xan je nadan yi wanka,kema nasan kina bukatar haka,idan na shirya xanzo na rakaki har part din mama ku gaisa.haneefa tace alright.




Kowa acikinsu yayi wanka ya shirya,haneefa ash doguwar riga tasa,mai kwalliyar pink amma bai yawaita ba,tayi kyau sosai,ta xauna a gefen gado tana jira Adnan ya xo don rakata wajen maman shi su gaisa.




Sai gashi kuwa yayi knocking,haneefa ta bude ita kanta ya mata kyau,ba karya adnan kyakykyawa ne kam.


Ko ni na shaida...😂 ga kuma ji da Naira.




Yace muje kici abinci kafin mama ta fito tana toilet,haneefa tace ok,dama wata muguwar yunwa take ji,saboda rabonta da abinci tun jiya da yamma.




Haka suka sauka,ta xauna a dining taci abinci tsaf ta kora da ruwa,da lemu sannan ta dau tissue paper ta goge bakin ta.




2hours later.....


Shiru shiru,haneefa bata ga maman Adnan ba balle su gaisa,sai tace amm Adnan ko mu karasa ciki mu gaisa da maman?




Adnan yace bari na fito freely na fada miki gaskiya,ba kowa acikin gidan nan bayan ni sai masu yimin hidima,nan da nan cikin haneefa ya duri ruwa tayi sensing akwai abinda Adnan yake nufi da kaita wannan gidan,yace dan haka ki shirya xama dani,kuma bawai ina nufin xan aureki bane noooo,xaki xama kamar matata dai kuma duk lokacin da bukatata ta taso xaki biya min,danni aure baya gabana ko kadan.




Haneefah tasa kuka tace,please karkamin haka Adnan ni marainiyace bani da kowa na gode da taimakonka,ta nufi saman benen da gudu ta janyo akwatin ta sannan ta nufi kofar fita,shikuwa Adnan tafa hannu ya shiga yi irin na mugayen basawan nan,




Haneefa na murda kofar da nufin xata fita taji is locked,ta juyo cikin yanayin tausayi tace pleasee Adnan this is d first tym na sanka arayuwa ta,dan Allah ina rokon ka kayi hakuri kar ka cutar dani.




Adnan ya ciji lebensa ta gefe daya,tare da yin murmushin mugun ta,yace relax,u can't leave this house haneefa, because every where is locked,so get ready to stay with me okay?.




Cikin fushi,haneefa tace,Never no matter how,no matter what,i can't stay in this house any longer,ta ajiye akwatin ta a gefe daya ta shiga jijjiga kofar da nufin xata balle,Adnan yasa hannu ya riko hannun ta,sannan yace idan xaki shekara kina jijjiga kofarnan baxata taba budewa ba,so ina ganin da kin hakura kawai kinyi abin da nakeso.


Haneefa tace leave my hand,har alokacin Adnan bashi da niyyar sakin ta,ta sake fada cikin tsawa "I said leave my hand"!!! Da taga dai bashi da niyyar sakin ta kawai ta ja hannun ta da kyau ta fisge daga cikin na Adnan.






EMIRS HOUSE....


6:00pm.....


Naseer da Abdul suka dawo sunsha bakar wahala sosai wajen neman haneefa amma Allah baisa sun sameta ba tun safe.Hankalin mai martaba ya tashi sosai ya kasa tsayar da hawayensa.


Haka mutanen yola(Dangin maman haneefa da Abdul) sun karaso,kowa yana cikin damuwa.


Amal da hajiya fati kuwa dan bakin ciki sun rasa inda xasu sa kansu.


Mukace sai dai su mutu....




IT IS MORE APPRECIATED U GUYS FOR UR PRAYER.


THANKS...!


By
Maryam y.Ahmad
Hauwa s.Ahmad




💞💞💞💞
[10/21, 8:47 PM] ‪+234 814 443 8844‬: 🌺'YAR MULKI🌺
2016


6⃣9⃣






📚✍








Sarki salahuddeen yace wa hajiya fati,kinga irin sakarcin da yarinyar nan Amal tayi ga abinda ya jawo mana,cikin fushi sarkin yake magana.




Hajiya fati ta ririta muryarta tace,Allah ya huci xuciyar mai martaba,sannan tace kasan d'a Amal tasan matsayin haneefa baxa ta taba goranta mata ba,ko ba komai ai itama ai 'yar uwartace.cikin sigar munafurci.


Sarki ya hadiyi yawu irin na bacin rai yace ke kike goya mata baya kenan? Tayi duk abinda take so,ko ma haneefa ba 'yar uwarta bace ai wannan furicin bai kamata ba,akan koma waye.


Amal dake gefe kuwa sai wuri-wuri take da ido irin na rashin gaskiya,saboda tana tsoron mai martaba,dakyar Amal ta iya bude baki dan bawa mai martaba hakuri,tace Abba dan Allah kayi haku-..anan maimartaba ya katseta,cikin tsawa yace dalla rufemin baki mutuniyar banxa! Ko menene bake kika jawo ba?? Amal ta fashe da kuka.




Momy'n Amal tace dan Allah kayi hakuri yarinyar nan fa haryanxu akwai sauran kuruciya atare da ita.


Sarki ya dagawa momy'n Amal hannu da nufin dakatar wa,yace ya isheni haka,nariga nasan cewa dake da Amal kuka takurawa haneefa acikin gidan nan.
Jiya ba abinda ba'a fada min ba akan kuntatawar da kukayi mata,yayi kyau..!!!


Momy'n Amal tace kayi hakuri duk akan rashin sanine,ni dai fatana Allah ya bayyana hanneefa,amma a karkashin xuciyar ta ba hakan take so ba.


Jin addu'ar da tayi yasa mai martaba ya sakko kadan,ta sake cewa yakamata muje kaci abinci,tun jiya rabonka da abinci,mai martaba yace banajin yunwa,idan ina bukatar hakan xan sanar dake.suna cikin haka




Abdul ya shigo cikin falon,mai martaba yayi xumbur ya mike tare da jefawa Abdul tambaya cewar ansameta?? Idon Abdul yayi ja sosai,ya jijjiga kai yace nooo Abba bamu sameta ba,sarki ya saki wata irin doguwar ajiyar xuciya.yace Allah ka bayyana mana haneefa ka kareta daga kowanne irin sharri a duk inda take.Abdul yace Amin ya rabbi.


Sannan yace Abba ni abin ne ma yake bani mamaki,sanarwa ake ba kakkautawa amma shiru kake ji ba wani alamar samunta,ko a dan kawo labari ma ace an ganta a wani waje babu,is unfurtunate.Allah yasa haneefa is safe some where else.




Sarki yace Amin Allah dai ya bayyanata.








GOVERNMENT HOUSE.....🏤




Naseer ne a kwance ya rasa abinda yake masa dadi,banda hawaye ba abinda yake fita daga gefen idonsa masu xafin gaske,yasa hannu ya janyo wayar sa daga gefen bed side drawer,ya fara dialing number'n hanny,amma switched of,yasan cewa number'n akashe take amma ya kasa resisting dole sai yayi dialing sannan yake samun peace of mynd,yanajinta arufe sai ransa ya shiga tafarfasa.juyi kawai yake amma ya kasa jin dadin kwanciyar,yaji wani irin haushi ya kamashi kawai ya kashe wayar gaba daya,dan bayason ganin call din kowa idan ba na haneefa ba.




His excellency yace da momy'n Naseer,let's go and pleaseee Naseer nasan yana cikin damuwa sosai dan na fahimci yana son yarinyannan sosai,Her excellency tace ni kaina abin ya dameni ba yadda banyi da Naseer ba yaci abinci amma totally yaki,let's go and c him,suka dunguma dakin.


Ganin yanayin da naseer yake ciki yayi matukar basu tausayi,suka xauna kowanne daga gefen naseer sai faman bashi baki suke.


Naseer shi kadaine dansu tilo,shiyasa suke bala'in ji dashi,ko kadan basason bacin ransa,haka suka ci gaba da rarrashinsa amma inaaaaaa shidai kawai ganin haneefa shine kwanciyar hankalinsa.






ADNAN.....


Yace haneefa ina ganin kiyi giving up,ki shirya xama dani,dan ko kin gudu daga gidannan sai na dawo dake na fada miki.


Baxan ci gaba da takura miki akan bukatata ba,saboda inason amincewar ki,amma ki xauna kiyi naxari,ni dai baxan taba bari kibar gidan nan ba,ya rage naki,na baki nan da gobe,ina jiran amsarki.




Haneefah ta fashe da wani irin kuka na ban tausayi,jiki ba kwari ta tsugunna,tafi awa hudu a bakin kofar nan amma ba alamar Adnan xaiyi releasing dinta,ganin ba sarki sai Allah ta hakura ta koma dakin da Adnan ya nuna mata a matsayin masaukinta ganin magrib ta yi don tayi sallah,ta jingine akwatin ta gefe daya sannan tayi locking dakin da mukulli gudun kar Adnan ya shigo,ta xauna agefen gado tana ta tunanin yadda xa'ayi ta gudu daga gidan.




Ta nisa aranta tace kaico,ina tausayawa rayuwar Adnan,gashi kyakykyawa ga arxiki Allah ya bashi,kyau kamar shi yayi kansa? Amma halinsa baiyi ba ko kadan,ya Allah ka kare ni daga sharrin Adnan,ta tashi ta shiga toilet dan yin,Alola,tana shiga tace Alhamdulillah ganin ta fara fashin sallah,wani irin dadi taji,ganin ta sami babban uxiri da xata fakewa Adnan dashi,kafin nan kuma sai ta shirya wasu 'yan dabaru don barin gidan,wanka kawai tayi mai makon alolar ta fito ta shirya tsaff,amma har alokacin hankalin ta bai kwanta ba,sanin cewar lallai Adnan shu'umin kansa ne.zai iyayin komai don ganin burin sa ya cika.




Mu kam mukace ai bai fi karfin Allah ba...!




LUV U MORE 'YAN SAUYIE....!






By
Hauwa s.Ahmad
Maryam y.Ahmad





💞💞💞💞 Downloaded from GNOVELS.COM.NG




This Novel is downloaded from https://GNOVELS.COM.NG
to download more hausa novels visits our site at www.GNOVELS.COM.NG

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/gnovels

Twitter : https://twitter.com/gnovels

Telegram : https://t.me/gnovels


Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4
Chapter 5

Please Login or Register in order to submit comment