Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

jin magana, wai da can kece kike kiransa ya zo ne? Ba shi da kansa yake zuwa ba? Sai kin je kin ɓata hanya ai zaki yi bayani".

Zaro idanu waje sosai ya yi tare da faɗin. "Sweetie ina Pretty ɗin ta tafi?".

Ita ma ɗan zaro ido ta yi kafin ta ce. "Kamran kai ne?".

E ya amsa mata tare da sake tambayarta ina Pretty ɗin ta je?.

"Wai ta tafi nemanka dan tana kewarka sosai, tun ɗazun da ka tafi baka dawo ba shi ne wai ba zata iya hakura ba ta je nemanka".

Dafe kansa ya yi tare da juyawa a guje domin ya bi bayanta.

"Kamran! Kamran!". Sweetie ta fara kiran sunansa. Ina ai tuni ya fice, bai sake bi ta kanta ba, dan kada ma ya biye mata Pretty ta je ta faɗa wani wajen.

Yana fitowa ya fara ƴan waige waige yana tunanin to shi yanzu ta wani hanya zai bi ya je ya nemo wannan rigimammiyar yarinyar?.

Fara nemanta a ɗan kewayen wajen ya yi ko Allah zai sa ya ganta bata yi nisa ba, har haɗa zufar dole ya fara yi, damuwarsa ɗaya shi ne kada ta je a garin nemansa ta isa ga in da Mamma take.

Sosai ya fara nemanta ta yankin waje, ya je ya dawo ya je ya dawo, duk ya wahala ya galabaita, ya kuma shiga cikin tsananin tashin hankali da damuwa, duk ya ruɗe, har idanuwansa sun yi jajir saboda shiga damuwa, ga hadarin ruwan sama yana ta kara tsananta.

Idan ka gansa sai ya baka tausayi, sai ka rantse an raba shi da Pretty ɗin kenan, wannan ya kenan idan aka ce za'a rabasu? Ya zai yi da ransa? Ina zai sa kansa? Sun rigada sun zama jinin jikinsa, suma ba zasu iya rabuwa da shi ba, kunga dai bai wani jima sosai da barin wajen nasu ba, barci ne ya dauke shi har lokacin da yake dawowa ya yi bai dawowa ba, amma Pretty ta kasa iya hakura har ta tafi nemansa, hakan zai kara tabbatar maku da suma ba zasu iya rabuwa da shi ba, dukkansu biyu suna kaunarsa sosai. Babbar magana akwai case ranar da Kamran ya bayyana da gaske waye yake so a cikinsu tab!!.

Sosai ya galabaita sai haki yake yi, amma babu ita babu alamarta, kai kamar ma ba'a taɓa yin mai kama da ita ba a duniya. Har kusa da gidansu ya je nemanta, amma shiru. Nufar wajen ƙoramar da suke zama ya yi yana ta mayar da numfashi tare da sauke ajiyar zuciya.

Tun daga nesa ya hangota kamar wata macijiya tana tsaye a samar dutse kamar ƴar tsana tana aikin data saba, wato dai tana sanya hannunta a cikin ruwan koramar ruwan yana fallatsuwa mata a saman fuskarta, hakan ba ƙaramin daɗi yake yi mata ba, mayyar son ruwa ce sosai, ko da yake dama dole ai su so ruwa sosai, duba da in da suka taso. Ita ma Sweetie ba baya ba wajen shegen son ruwa, shi ne abin wasansu da kuma ɗebe masu kewa, idan suna jin kewa cikin ruwan ƙoramar suke zuwa su shiga yana jiƙasu suna jindaɗi.

A dubu ɗari ya ƙariso wajen yana sauke numfashi dan ya tabbatar da cewa ita ɗin ce ko ba ita ba.
Wani irin daddaɗar ajiyar zuciya ya sauke lokacin da ya kalli cewa ita ɗin ce, tana sanye da riga da sket wanda ya fara ganinta da shi, ta ɗaure gashin kanta kamar dai ranar da suka fara haɗuwa.

Cikin wani irin farinciki ya ambaci sunanta tare da ƙarisowa wajen yana murmushin da shi kansa bai san yana yi ba, ya ji daɗin ganinta, da bai ganta ba yau ina zai sa kansa? Ta wahalar da shi ashe tana nan tana aikin da ta saba.

Jin voice ɗinsa yasa ta juyo tare da dirowa kasa, da gudu ta faɗa jikinsa tana dariya tare da gaya mashi ta yi kewarsa sosai.

Rumgumeta ya yi shima yana murmushi mai ƙayatarwa, alamar suna cikin tsantsar farinciki da ganin juna.


🤍KADA KU MANTA WANNAN DADDAƊAR LABARIN DAGA ALKALAMIN FATEEMA ZAHRA MUSA A-K-A PRINCESS TEEMA TAKU TA AMANA YAKE🔥💘



Share fisabilillahi 👏



ALLAH KA KARA MANA SON MANZON ALLAH 🔥🤍

🤍🔥𝗥𝗔𝗪𝗔𝗡𝗜𝗡 👑 𝗭𝗔𝗟𝗜𝗡𝗖𝗜🔥🤍


🔥CROWN OF INJUSTICE🔥







𝗠𝗔𝗟𝗟𝗔𝗞𝗜𝗡

❤️‍🔥FATEEMA ZAHRA MUSA ❤️‍🔥
(❤️A-K-A 𝑷𝑹𝑰𝑵𝑪𝑬𝑺𝑺 𝑻𝑬𝑬𝑴𝑨🔥)






🔥🤍T🔥🤍T🔥🤍W🔥🤍......💻




❤️𝑫𝑨𝑻𝑬 28/8/2024.....✍️📚🌹




For more information 08161390581 Whatsapp me only!!.



🤍𝑺𝑻𝑬𝑷 1......✍️📚🔥





اللَّهُمَّ صَلِّ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا صَلَّيْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ، اللَّهُمَّ بَارِكْ عَلَى مُحَمَّدٍ وَعَلَى آلِ مُحَمَّدٍ، كَمَا بَارَكْتَ عَلَى إِبْرَاهِيمَ وَعَلَى آلِ إِبْرَاهِيمَ، إِنَّكَ حَمِيدٌ مَجِيدٌ❤️






E____________40🔥




Rumgumeta ya yi shima yana murmushi mai ƙayatarwa, alamar suna cikin tsantsar farinciki da ganin juna.

Ruwan sama ne mai karfin gaske ya kece kamar da bakin kwarya. A ɗari ta sake shi tana faɗin. "Kamran mu gudu cikin raminmu ruwan sama".

Hannunta ya riƙo shi ma yana faɗin. "Me ruwan saman zai yi maki sarkin tsoro? Babu komai, zu mu zauna a saman dutsen nan kina mana busa ruwa na jiƙamu".

Ɗan turo baki ta yi. "Kamran akwai sanyi fa ruwan".

Jan hannunta ya yi suka koma saman dutsen suka zauna. "Ai haka kike so, shi ma ruwan ƙoramar da kike shiga kullum ai akwai sanyi".

Kwantar da kanta a saman shoulder ɗinsa ta yi tana faɗin. "Not like rain, shi sanyinsa daban ne, but is so sweet kuma fa".

Tafukan hannunsa ya buɗe ruwan na zuba a samansu. "The water is so very very fresh and cool". Ya yi maganar yana ɗan watsa mata shi a saman face ɗinta.

Jinjina mashi kai ta yi. "Yah ikon Allah kenan, ko iya ruwan saman nan idan ka kallah ya isa ya sanyaka ka kara jin tsoron Allah, ka kara ganin girman Allah, Allah buwayi gagara misali, yanzu idan ka ɗaga kanka ka dubi sararin samaniya sai ka rasa ta ina ruwan yake fitowa, hmmmm wani abin sai Ubangiji, yanzu fa a saman nan akwai ruwan da zai iya cinye duniya da abin da yake a cikinta, kaf duniya babu wanda ya isa ya tare ruwa kada ya wuce idan ya doso waje, amma shi Ubangiji ya rike ruwan da zata iya cinye duniyar nan tas ba tare da ta zubo ta cinye duniyar ba, kai komai ma fa ka gani a duniyar nan idan kana da hankali ya isa yasaka ka kara jin tsoron Allah!!".

Yadda ta yi maganar kamar wata babbar mace, ta kwantar da kanta shiru tana zayyano bayanai cikin natsuwa, ruwan saman na sauka a kansu, abin sai ya ƙayatar da masu kallon.

"Pretty ina son sanin wanene Allah? And ina son samun karin sani sosai a kan abubuwan da kuke yi keda Sweetie". Ya yi maganar tare da juyowa da kallonsa izuwa saman face ɗinta.

"Kamran Allah shi ne wanda ya halicceni ya kuma halicceka tare da sauran mutanen da kake gani suna giftawa a cikin dajin nan, sannan ya halicci sammai da ƙassai, halittun Ubangiji ba zasu kirgu ba, dan sun wuce gaban tunanin kowa".

Juyowa da kyau ya yi ta yadda zai sami damar ganinta da kyau da kyau. "To meyasa Ubangiji ya haliccemu kenan?".

"Bauta, domin mu bauta mashi, kuma sallah da ka tambayeni a kan mecece ita ranar da kasame ni ina yinta to ɗaya ce daga cikin abin da Ubangiji ya haliccemu muzo mu yi mashi, kuma ita ce ma a kan gaba, sai karatun Alkur'ani mai girma, ita ce littafin nan da ka ɗauka a wajenmu ranar, akwai azumi da sauransu, amma ni dai bana yin azumi gaskiya, ba zan iya yunwar nan ba, Sweetie ce kawai take yi, ni kam wlh dana ji yunwa zan ci abinci na, so ban taɓa yin azumi ba". (Sarkin cin abinci ba, yo dama ke a yanzu ai ba zaki iya yi ba, wata kila idan ya zama wajibi a kanki kyayi dan dole😅)

"E ina karanta littafin dana ɗauka a wajenku, kuma yana da matuƙar daɗi sosai, sai dai ban yi nisa a karatun ba, wannan littafin ma yana ɗaya daga cikin abin da ya hanani karanta diaryn da mummynku ta bani, wannan Alqur'anin ya ja ra'ayina sosai, ya ɗauke mun hankali da a kullum a ƙagare nake dana karanta shi".

Murmushin ta sakar mashi tare da kai hannunta ta ja karar dogon hancin nan nasa. "Ka yi ƙoƙari ka karanta zaka ji daɗinsa, aduniya babu abin da ya kaisa daɗin karantawa da kuma sauraran mai karantawa".

Shafa kumatunta ya yi kafin ya ce. "To ɗan karanta mun kaɗan na ji". Ya kai karshen maganar tare da sanya hannunsa a cikin gashin kanta dake ta zubar da ruwa sosai, ga hadari sai kara haɗuwa yake yi, ruwan sama yana kara tsananta karfin zubarsa kamar da bakin kwarya, ga walkiya mai hasken gaske da yake haske arear wajen a duk lokacin daya wanzu a sararin samaniyar, sai tsawa ya biyo baya. Hankalinsu a kwance suke zaune a wajen abinsu, ko kaɗan basu damu da ruwan da yake zuba masu a kansu ba.

Rera mashi karatun Alqur'ani mai girma ta fara yi cikin suratul iklas, ga voice ɗin nata da zaki ga shegen daɗi. Shiru ya saurara yana jinta, har wani irin ni'imantaccen ajiyar zuciya ya sauke, Alqur'ani akwai daɗin saurara, ga kwantar da hankalin mai sauraro.

Ƙarar da suka fara jiyowa daga can nesa da su ne yasa Pretty ta dakata da karatun, a lokacin already ta kammala suratul iklas ta shiga falak, dan ƙasa ta yo. Dakatawa da yin karatun ta yi tana zaro idanun nan nata da suke kara fito da tsantsar kyanta.

"Kamran menene yake kara har haka?". A tsorace ta yi maganar.

"I don't know, amma mu je mu duba mana mu gani". Ya kai karshen maganar tare da riƙo hannunta, shi fa ko tsoro baya ji, wai su je su duba, ita dai Sweetie baiwar Allah tana ciki abinta, ba ruwanta da yawace yawace har sai idan ya zama dole.

"Kamran ina tsoro fa". Ta faɗa tana ƙanƙame hannunsa tare da kara zaro idanu.

Sauƙowa ƙasa daga saman dutsen ya yi tare da juya mata faffaɗar bayansa a kan ta hau ya goyata yana faɗin. "Kada ki ji tsoron komai my Pretty, ina tare dake, mu je muga menene yake kara har haka?".

Ba musu ta haye bayan nasa tana murmushi, idan da sabo ai ya saba goyonta, dan haka sai ta ɗale abinta tare da saƙalo wuyarsa ta kwantar da kanta a gefen shoulder ɗinsa, sai murmushi take saki dimple ɗinta na lotsawa, ga ruwa na zuba mata daga tsakiyar kai, kyalkyawar gashin kanta sai zubar da ruwa yake yi.

Kai tsaye Kamran ya nufi ta wajen da suke jiyo wannan kara a tare da ita. Sai hira suke yi gwanin birgewa har suna ɗan yi nisa. Suna tafiya suna kara jiyo wannan sauti tana kara matsowa kuma tana kara karfin kara.

Sai da suka sake matsawa kusa sosai suka fahimci ashe sautin ƙugin igiyar ruwace mai karfin gaske ne, da alama katafaren teku ce a wajen wadda ta cika take ambaliya sanadiyar wannan ruwan saman, igiyar ruwace ke ƙugi.

A hanzarce ya ƙarisa matsowa sosai, babu ko shakka bare tsoro ya nufi waje. Wannan katafaren tekun nan wanda mum ɗinsu ta faɗo daga ɗaya daga cikin duwatsun dake kewaye da tekun nan ne, sai dai a yanzu iya gane daga ta ina mum ɗin nasu ta fito har ta faɗo ta wannan waje abu ne da ba zai yi wu ba, su bama su san daga ta wajen ta fito ba, so sai basu wani damu ba. Mamaki ne kawai ya bayyana a saman fuskokinsu na ganin tekun a dajin bai sani ba.

Duk zaman Kamran a wannan daji bai taɓa sanin wannan teku ba, sai dai kananan ruwa dake ta wajen tsauninsu, ashe akwai teku mai girman da idan ka bi cikinta zaka je ƙasashe da dama.

"Kamran saukeni na ga tekun nan da kyau". Ta faɗa tana zaro idan, yadda igiyar ruwa ke juya tsakiyar ruwan tekun kawai take kallo. Shi ma Kamran ɗin abin da yake gani kenan, abin ya ƙayatar da su kuma ya basu mamaki sosai. Ba musu ya sauketa dan ta yi kallo da kyau.

"Pretty ina ganin kamar wannan teku ta nan ce hanyar fita daga cikin wannan Forest ɗin ko?".

Ya faɗa yana dawo da kallonsa a kanta, ya jima yana neman hanyar da zata fitar da shi wannan Forest ɗin cikin sauki, ita kuma wannan teku abin da bai sani ba ta kasance kamar border ce, iya kar ƙasashe da damane a wajen, sai dai tabbas ita ce hanyar da zata iya kaisu cikin babbar ƙasar, kuma dai kada ku manta su su Pretty ta nan mum ɗinsu ta fito, kunga hakan na nufin koma dai me ta nan garinsu or ƙasarsu yake. Akwai cakwakiya kenan, da alama su Pretty zasu kai kansu in da ake nemansu ruwan ajallo idan suka yi wasa.

Sai hira suke yi suna ta kallon yadda igiyar ruwa yake jan ruwan har sama sai kuma ya sake sake shi, hakan yakansa ruwan ta bada sauti mai karfin da har suka iya jiyowa ɗazun, sai zancen neman hanya suke yi, Kamran ya kafe a kan shi dai lallai wannan teku a akwai hanya a kusa da ita, ita kuma Pretty ta ce bata ga alama ba, domin kuwa ita dai ruwa take kallo maras iyaka, kuma wlh ita ko kasheta za'ayi bafa zata shiga cikin ruwan nan ba........😅

(Kunga laifinta? Da gaskiyar ruwa ba iyaka haka ace su shiga su ketare?🤔 Ni dai ina bayanta, ko za'a kwasheta kada ta yarda ta shiga😅 ta bar Kamran da Sweetie su je, idan suka isko mutane sai azo da jirgin ruwa a ɗauketa😅😅 saura naji wata magana, shawara na bata🥱😎)

Sun jima tsaye a wajen ruwan sama na jiƙasu, sai da Pretty ta fara rawan sanyi ne ta dube shi. "Kamran sanyi nake ji sosai".

Juyowa ya yi da kallonsa a kanta. "Zo na goyaki mu koma, gobe dole mu dawo wannan waje".

Da sauri ta faɗa jikinsa, sai rawan sanyi take yi sosai, shi ma dai zubar ruwa yake yi.

Ɗagata sama ya yi tare da maida ita bayansa, ya goyata kamar yadda suka zo, dan wannan yarinya ba iya tafiya da kafafunta zata yi cikin bishiyoyi da ciyayin nan ba, sai ta ɓata masu lokaci basu isa in da za su je ba, kuma dama shi Kamran yana jin daɗin goyata idan zasu je yawonsu, saboda hakan zai sa su yi tafiya mai nisa ba tare da ɓata lokaci ba.

Nufar hanyar komawa suka yi, ta kwanta shiru a bayansa tana rawan sanyi, ta wani ƙanƙame mashi wuya. Shi kuma sai tafiya yake yi.

Ko da suka isa bakin ramin nasu sai ya sauketa, miƙo mata wani irin nau'in fruit nasu dake a cikin dajin mai kama da ruman mai kuma kama da Apple haka yake ya yi, ya miƙo mata tare da cewa. "Ina sonki sosai Pretty, ki koma ki cire kayan jikinki ki canza wasu kada sanyi ya kamaki, nima zan je gida, sai gobe, kada fa ki sake fitowa, gobe za mu je yawo sosai".

(Ko a ina ya samo wannan fruit ɗin?🤔 Kila a hanya ya ciro da suna dawowa)

Karɓar fruit ɗin ta yi tare da cewa. "Nima ina sonka Kamran, amma fa gobe kazo da wuri ka ji?".

Jinjina mata kai kawai ya yi, sam baya son rabuwa da su, ji yake yi a wannan yanayi kamar kada ya koma gida, amma ina babu dama, ba hali dole ya koma idan yana son cigaba da kasancewa da su.

Shiru ya ɗan tsaya ya kasa tafiya.

"Kamran lafiya ka tsaya shiru? Ka tafi mana". Ta faɗa tana kallon face ɗinsa.

Ajiyar zuciya ya sauke tare da ɗan ƙaƙalo murmushi kaɗan. "Babu komai Pretty, kawai ina tunanin rabuwa da ku ne, bana son komawa gida na barku".

Shiru ta ɗan yi itama, jikinta ya yi sanyi, har ga Allah bata son rabu da shi ita ma, amma ya zasu yi? Dole su rabu, idan ba haka ba su jawa kansu rabuwa ta har abada.

"Nima bana son ka tafi Kamran, nafi son kullum ka kasance a tare da mu, idan ka tafi bana jin daɗi, ina jin kamar bani da lafiya, duk sai in ji wajen zamanmu ya yi mun zafi babu daɗi, shiyasa ka kallah ina fitowa waje in zauna idan baka nan, bana jin daɗin zaman cikin ne". Tana magana kamar zata yi kuka.

Ɗan rungumota a jikinsa kaɗan ya yi tare da shafa kanta dake ta zubar da ruwa. "Idan nazo gobe zamu yi magana, yanzu kinga kije ciki kada sanyi ya kama mana ke, ki canza kaya kin ji ko? Ki gaishe da Sweetie sosai".

Rungume shi ita ma ta yi kafin ta sake cewa. "Goben fa kada ka daɗe, kazo da wuri".

Okey ya amsa mata da shi, sannan ya saketa tare da ce mata ta shiga ciki. Ba musu ta shige ciki, sai dai ta shige ne tana ruwan hawaye, kuma ya lura da hakan, kawar da kansa kawai ya yi, saboda dalilai guda biyu, na farko baya son ya cigaba da tsayar da ita cikin ruwan nan ga kuma ɗanyen kaya a jikinta, sanyi zai kamata, na biyu kuma baya son kara jan lokaci da su kada mamma ta tashi daga barci ta farga baya nan, hakan yasa ya kawar da kai tamkar bai ga tana kuka ba, amma ya ji zafin hakan sosai a cikin zuciyarsa, sai ya ji kamar shi ma ya yi kukan ko zai ɗan ji sanyi a ransa.

Haka ya juya jiki ba kwari ya nufi nasu gidan, yana tafiya yana tunanin hanyar da zai bi ya isa ga mutanen dake wajen dajin nan, sannan yanzu kuma tunanin mahaifinsa ta yawaita mashi a cikin zuciyarsa, ji yake yi lokaci ya yi da yakamata ya tambayi Mamma ina babansa? Tun da yanzu ya gano cewa ba iya macece kawai take haihuwa ba, dole yana da baba, to ina baban nasa? A gaskiya yakamata Mamma ta gaya mashi in da mahaifinsa yake, kullum da wannan tunani yake kwana kuma yake tashi, sai dai ya rasa ta ina zai fara tunkara Mamma da zancen. Tashin hankali kenan.

Tafiya yake yi sam bashi da wani kuzari a jikinsa, da haka ya isa gida. Yana zuwa ya wuce nashi makwancin, kayan jikinsa ya fara kwaɓewa tas. Yana da kyan jiki kam kamar madara duk da Mamma ta fishi haske nesa ba kusa ba, da alama babansa ya yo a kalar fata, fari ne fa shi ɗin ma, amma a gaban mamma gaskiya ba fari bane.

Canza kaya ya yi tare da kwashe waɗan nan ya kai su in da suka dace, ya sanya kaya masu nauyi sosai saboda sanyi, sannan ya kwanta ya ɗauko Alqur'ani da ya ɗauka wajen su Pretty ya fara dubawa yana karantawa, bai leƙa Mamma ba. A lokacin ita kuma ta tashi daga barcin tana cikin madafarta, tana aiki, tasan da cewa ya fita bayanan, domin tana farkawa daga barci makwancinsa ta fara leƙawa dan ta duba shi, sai ta taras baya nan, so bata wani damu ba, dan dama da lallami ta lallaɓa shi ya dawo, so ba zata takura mashi ba.

🕊️🌼🕊️🌼🕊️🌼🕊️🌼🕊️🌼🕊️🌼🕊️🌼🕊️🌼

GIDANSU KHADIJAH😥💔

Maman Khadija tana durkushe a wajen tana kuka Khadija na rarrashinta, bata tashi daga wajen ba sai ji ta yi an sake banko masu kofar gida.

Bata kula ba, haka zalika bata bi ta kan son sanin su waye bane, ita masifar da take a ciki ma ya isheta, dan haka sai ta cigaba da rera kukanta da sauti baya fita sai dai ruwan hawaye.

Banko labulen kofar aka yi aka shigo, maman Haidar ce da Maman Hanif sai Hajiyarsu, Haidar yana tsaye daga bakin kofa, shi ma Sadiq ya fito ya tsaya a bakin kofar ɗakinsu yana kallon cikin parlourn, abin da ya fito da shi kuma shi ne irin yadda ya ji sun banko masu cikin gida babu mutunci, so yana tsoron kada su yi wa ƴar uwarsa wani abin, shiyasa ya fito, shi dai yana ganin bala'i kala kala bawan Allah, daga nasu maman Haidar yanzu kuma an koma na Hauwa, wannan irin jarbawa sai ka dage zaka iya cinta, Allah yasa maman Zee tana da juriya da karfin imanin iya cinye jarabawarta.

Tana durkushe tana kuka maman Haidar ta fara surfa mata ruwan bala'i a kan ina su Hauwa ɗin suke? Ta fito masu da baban Zainab ita kuma.

Wani irin kallon takaici mai haɗe da tsananin ɓacin rai maman Zee ta wurga masu. Cikin ɓacin rai da fusata ta ce. "Saboda ni kuka raina shi ne dan kinga ni kaɗai ce zaki fara mun hargagin banza ko? Meyasa ɗazun da kika samu Hauwar baki yi mata ba kika yi shiru? Yanzu dan kinga bata nan ne zaki ce na fito maku da baban Zainab? To na cinye shi ɗanya, sai ku fasa cikina ku ciro shi!!". Ta kai karshen maganar tare da miƙewa tsaye, idanunta jajir kamar wuta, yau tasha kuka, kuma a cike take har wuya da bakinciki, idan su maman Haidar suka yi wasa tana iya yi masu hauka, dan Hauwa ta sanya zuciyarta yanzu ya fara bushewa ta dai'na ganin mutuncin kowa, zuciyarta ta kusa fashewa ta fito waje. Tashin hankali, yanzu wasan zai fara!!.

"Ke Aisha ni kike gayawa magana yau? Ni nake magana kike mayar mun da amsa? A lallai kam kan mage ya fara wayewa". Cewar maman Haidar.

"Ke ɗin nake gayawa, an gaya maki ɗin, zaki iya yin duk abin da ya zo maki cikin wannan banzar ƙwaƙwalwar taki, sannan kuma ke dama a tunaninki rashin wayewa yasa bana mayar maki da martanin duk abin da kika yi mun ko? Ko kina tunanin ina jin tsoron ki ne? To idan ma haka kike tunani kin makaro, tarbiya da ilimi dana samu daga wajen iyayena ne yasa nake darajaki a matsayinki na yar miji, nake baki girma kamar yayata uwa ɗaya uba ɗaya, nake kuma ganin mutuncinki, amma yanzu tun da abin yazama babu mutunci, to kuwa zaki ga ainahin wacece A'isha! Yanzu baki isa kiyi mun na kyale ki ba wlh, a baya kin ci banza, amma yanzu zan nuna maki ba wai ban iya rashin kunyar bane, tarbiya muka kwankwaɗa muka ƙoshi, a gidanku kuma kuka shayar da ni ruwan kwatar ƴancina, to yanzu na sha na ƙoshi, duk wanda ta shirya mu buga to ta zo mu buga daga nan har illa Masha Allah, in dai bata gaji ba, to nima ba zan gaji ba! Duk wadda ta ce mun kule sai na ce mata cas, na dai'na yin shiru tun ba mutuncin kuke so ba!!".

Shiru ita dai maman Hanif ta yi, dan ita dama ba wai ta cika shiga irin wannan shirgin bane, kawai ba yadda ta iya ne, idan maman Haidar ta yayuɓota dole ta biye mata, ko dan ma Hajiyarsu, idan bata shigarwa maman Haidar ba ya zama dole ta shiganwa Hajiyarsu.

Gadan gadan cikin fushi maman Haidar ɗin ta nufeta da nufin ta kai mata mari. Ai kuwa maman Zee bata yi ƙasa a gwiwa ba ta yi cap ta rike hannun nata.

"Wlh idan kika kuskura kika ɗaura hannunki a jikina sai na rama, ashe rashin kunyar taki sai kinga wargi kike yi, meyasa baki yi wa Hauwa ba? Kika yi shiru ta gama cin maki mutunci baki da wani kataɓus! Meyasa kika ja baki kika yi shiru a gabanta? Sai ni zaki yi wa hargagin banza? To nima na dawo daga rakiyarku wlh!!".

Ƙoƙarin kwace hannunta ta fara yi, amma ina maman Zee taki sakar mata hannun, ji take yi ma kamar ta kife munafuka da mari, so take ta sauke haushin da Hauwa ta cusa mata a kansu.

A fusace Haidar ya shigo cikin ɗakin, a haukarsa da rashin hankalinsa wai zai daki maman Zainab ɗin. Ai kuwa yana zuwa Sadiq ya tare shi, dan kuwa ya biyo bayansa, saboda yasan halinsa sarai, tun da yaga ya shige cikin parlourn yasan ba zasu yi da kyau ba, shi kuwa ba zai bari su taɓa mashi ƴar

Please Login or Register in order to submit comment