Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

DASHI A WANNAN LITTAFIN.




______________Murmushi yayi ya nufi part ɗin sa a ransa yana faɗin ina sonki amanata bayan ya shiga ɗakin kiran Abbas ne ya shigo wayar tasa ɗaga kiran yayi da sallama ɗauke a bakin sa amsawa Abbas ɗin yayi yana faɗin "ranka ya daɗe na samu labarin hajiya Aisha tayi bukin ɗin jirgi zuwa senigal gobe" zumbur ya miƙe daga kashin giɗar da yayi ya ce "mene dalilin zuwan nata ka nemo minshi kafin tafiyar ta" ya faɗi haka yana yanke kiran dafa kasan yayi ya rasa ina zaisa ransa yaji daɗi kewar mahaifiyar shi ta kama shi yasan daya na kusa daita damuwar sa zatayi sauƙi gashi wadda da ta maye masa gurbinta ta rasu hawayen daya gangaro masa ya goge ya ce "meyasa daddy meyasa ni baka sona kamar sauran tunda ka haifeni baka nuna min so kamar sauran na samu duk wani abu na more rayuwa amma na kasa samun mai maye min gurbin Mommah na wadda tamin haka ta rasu Allah sarki Mommy insha Allah zan riƙe miki amanar ƴar ki Safna kamar yanda kika riƙeni nima.




"Granny wai meyasa baki son zaman lafiya ne ke kullum kin fiso a dinga tashin hankali a gidan nan kawai kin kira daddyn mu sai faɗa kike masa akan ɗansa bai fiki son sa ba aka faɗa miki" Mimi ce ke maganar cikin ɓacin rai dajin haushin abinda kakar tasu tayi ma mahaifin su a gaban yara ita kuwa tsohuwar sakin baki tayi tana kallon ikon " kin gama nace kin gama mara kunya ni yarinyar nan narasa ubanwa kikayo a rashin kunya mahaifiyar ki ba haka take ba haka mahaifin ki amma shima Safiyanu tun yana ƙarami bayaji ko kaɗan kuma bari in gaya miki wallahi yarinya nafi ƙarfin ki fasa miki baki zanyi ni zaki yiwa rashin kunya" ta ƙarasa tare da fashewa da kuka tsaki Mimin tayi ta fice daga part ɗin ita kuwa granny kayan ta ta fara haɗawa tace wallahi sai na bar gidan nan Aliyu tun kan ƴaƴan ka su fara yimin duka Mommah ce ta shigo taga abinda tsohuwar take haƙuri ta samo bata tana rarrashin ta ta ƙyar ta haƙura tana faɗin " anci darajar ki da tafiya ta zanyi" zama Mommah tayi tana tayata hira har ta sake.




tunda ya ɗauko ta zai kaita makaranta ya fahimci akwai abinda ke damunta tayi shiru yau ba tsiwa sam sai yaji ransa ba daɗi har suka iso makarantar bata sani ba ta tafi kogin tunani cewa yayi " ranki ya dade mun zo" cikin sanyi jiki ta buɗe murfin motar zata fita muryar sa taji yana faɗin "sorry madam" ɗan satar kallon sa tayi ta fice daga motar haka kurin yaji shima duk ransa ya 'baci dan baya san ganinta a damuwa tafi kyau in tana tsiwa da rashin kunya...

*WACECE SAFNA*




*KASH LAIFIN DAƊI ƘAREWA KUDAI KU BIYONI*



*INA GODIYA A GAREKU MASOYANA*




*#ZAINAB KABIR JAEN*
*{GARKUWAR💪ROYAL STAR🌟}*
3/7/24, 9:03 AM - my lovely sister: https://chat.whatsapp.com/CVoFH73vk0nCnVISlZC9uU
❤‍🩹 *WAYE SHI?*❤‍🩹



*MARUBUCIYAR LITTAFIN*

*1:-RAYUWAR ZAINAB*
*2:-RASHIN MAHAIFIYA*
*3:-YARIMA ASLAM*


*YANZU KUMA GAMU ƊAUKE DA SABON LITTAFI MAI SUNA WAYE SHI ?*


*STORY&WRITTING* *BY* *ZAINAB KABIR JAEN*
*{GARKUWAR*💪 *ROYAL STAR🌟}*





*FREE BOOK* 📚📖.






*Littafi mai d'auke da soyayya,Sadaukarwa,tausayi,ilimantarwa,har ma da nishad'antarwa,*faɗa karwa*ku dai ku biyo garkuwar taku*





*🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}

https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_

*Alk’alaminmu ‘yancinmu*










🅿️..........1️⃣1️⃣↔1️⃣2⃣.


BISIMILLAHI RAHMANU RAHIM DUKKAN GODIYA TA TABBATA GA UBANGIJI MAƊAUKAKIN SARKI WANDA YA BANI IKO NA KAMMALA LITTAFINA MAI SUNA YAREEMA ASLAM SANNAN YA BANI IKO YAU NA KAWO MUKU SABON LITTAFINA MAI SUNA WAYE SHI ? INA FATAN ZAKU BIYONI DAN JIN SAƘON DANA ZO DASHI A WANNAN LITTAFIN.




______________Safna ƴace guda ɗaya tilo ga babban ɗan kasuwar nan mai suna Alhaji Abubakar matawalle ɗan kasuwane wanda yai shura a jahar mu ta kanon dabo Nigeria matar sa ɗaya mai suna Maryama, yana zaune lafiya da matar sa shekarar su goma da aure ko ɓatan wata bata taɓayi ba hakan yasa dangin mijin nata suka sako ta gaba da gori rashin asali dana haihuwa sam bata sakewa a gidan mijin nata koda yaushe yaran su da manyan su suna kan hanyar gidan gashi in suka zo suyi ta 'bata mata gidan haka take haƙuri saboda bata da kowa sai mijin nata ana haka suka haɗashi aure da ƴar uwar sa bazawara ce kuma tayi haihuwa biyu a gidan data baro dan haka suka ce tunda ita ba juya bace tazo ta haifa masa ƴaƴa abun mamakin kuma shine tunda akayi auren shekarar Amaryar tasa bakwai ba haihuwa dan haka sai duk surutun da suke sukayi shiru kuma sai da tasan yanda tayi tasa suka dena musu suntiri a gida dan ta lura in tayi wasa irin na Maryama zasuyi mata itada kishiyar ta sam basu da matsala suna zaune lafiya sun haɗa kansu yanzu Maryama ta samu natsuwa sosai a gidan mijinta dan Amaryar tata irin matan nan ne goggagu sam bata ɗaukan raini ita kawai duniya ce gaban ta business ɗinta take gari-gari ana haka Maryama ta samu ciki murna a wajan Alhaji matawalle ba,a magana haka Saratu dan ita ko a jikinta dan dama ita ba haihuwa ce a gaban ta a lokacin Safwan shekarar sa ɗaya da fara aiki a gidan kuma tun zuwansa Allah bai haɗa jinin sa da Amaryar Alhaji ba wato Saratu amma shida Mommy ya ɗauke ta kamar mahaifiyar sa.




Tare da Safwan ake rainon cikin dan in ya fita haka zai siyo ma Mommy su ɗata yalo da sauransu takan ce indai mace na haifa Safwan zan baka ita matsayin mata indai inada rai har mijinta saida ta faɗawa lokacin da cikinta ya isa haihuwa bata iya aikin komai wataran safwan ke mata har Allah ya sauketa lafiya yarinyar taci sunan mahaifiyar Alhaji matawalle ana kiranta da Safna cewar Mommy zata masa takwara sanda yarinyar ta fara wayo ta shaƙu Safwan sosai duk inda taji muryar sa ta sani in bai ɗauketa ba ta dinga kuka kenan shekarar safna biyar a duniya Allah yayi wa Mommy rasuwa sakamakon ciwon ciki datayi na dare ɗaya amma duk da tana cikin ciwo saida ta nana tawa mijin nata cewar indai Safna ta girma ya taimaka ta cika mata burin ta ya aurawa Safwan ita tasan zai riƙe mata Amanar ɗiyar tata sannan shima Safwan ɗin ta bashi amanar ƴar tata.


Mutuwar ta daki Safwan da Matawalle sosai nan riƙon Safna ya koma hannun Saratu wato Ammi kasancewar tana son yarinyar yasa take gatan tata kamar ƴarta amma sam bata yarda Safwan ya ɗauke ta tun yarinyar na kuka in ta ganshi har ta haƙura haka shima tun yana damuwa har ya haƙura sanda yarinyar ta girma gaba ɗaya sai halayen ta suka koma na Ammi har ma ta fita dan indai rashin kunya ne da rashin girmama manya kuma da izza Safna ta haɗashi kaf gidan Safwan kaɗai take shakka dan shi sam baya sake mata fuska amma sauran ma'aikatan gidan duk ta raina su ta dinga sasu aiki kenan sam ta tsani talaka a rayuwar ta dan a cewar ta duk ƙazamai ne wannan hali na Safna yana damun mahaifin ta danshi mutum ne mai son jama'a ga kyauta.

wannan shine labarin jarumar tamu a taƙaice

*CIGABAN LABARI*









*KASH LAIFIN DAƊI ƘAREWA KUDAI KU BIYONI*



*INA GODIYA A GAREKU MASOYANA*




*#ZAINAB KABIR JAEN*
*{GARKUWAR💪ROYAL STAR🌟}*
3/7/24, 9:04 AM - my lovely sister: ❤‍🩹 *WAYE SHI*❤‍🩹


*NA ZAINAB KABIR JAEN* *{GARKUWAR💪ROYAL STAR🌟}*

🅿️➡️1️⃣3️⃣


______________Yau tunda suka taho motar tayi tsit ita Safna ta ƙurawa gefan titi ido har suka iso makarantar bata sani ba, bai san abinda yake damunta ba amma sai yaji ransa duk babu daɗi dan bubbuga kujerar da take zaune yayi a hankali ta ɗago tsintar kansa yayi yana faɗin "Madam meyake damunki?" bata kulashi ba duk da dama ya tsammaci hakan.

Jakarta ta ɗauka zata fita yakuma faɗin "sorry Madam" still dai bata kulashi ba ta juya ta nufi ajinsu juya motar tasa yayi zuciyar shi sam babu daɗi, kiran Abbas ne ya shigo wayar tasa ɗagawa yayi yana faɗin "Abbas ya ake ciki kasamo wani evidence ne ?" a ɗaya ɓangaren cikin rashin jin daɗi Abbas ɗim ya ce " boss har yanzu shiru dai ni bama wannan ne yasa na kiraka ba dan Allah Safwan ka daure kazo funtua kodan saboda mahaifiyar ka....." cikin tsawa Safwan ɗin ke faɗin " wait Abbas na gaya maka babu ruwan ka da abinda ya shafi tsakanina da iyayena ka tsaya iya matsayin ka wannan ba matsalar ka bace" ya ƙarasa yana katse kiran jingina kansa yayi akan sitiyarin motar zuciyar sa na tafarfasa nan da nan idanun sa suka kaɗa sukayi jawur zuciyar sa sai tafarfasa takeyi bai san meyasa Abbas keson fama masa ciwon daya daɗe a zuciyar shi ba why Abbas why meyasa bazaka barni na zauna lafiya ba bana son zancen gidan bana so ya ƙarasa yana dukan sitiyarin a hankali ya lumshe ido rayuwar sa ta baya ta fara dawo masa tana tuna masa WAYE SHI.


Safwan Asalin ɗan garin Funtua ne mahaifinsa Alhaji Habib Funtua ɗan kasuwane wanda ba,a iya nigeria yayi suna ba a ɗaukacin duniya baki ɗaya Alhaji Habib mutun ne mai zafin rai da zuciya gashi sam baya son talakawa bashida taimako sam tsakanin sa da talaka yayi masa aiki ya biyashi Mami itace matar sa ta farko suna da yara shida Anty Suraiyya wadda take aure a kaduna itace babba tana kula da companyn Abbun nasu nacan sai Anty Shukura ita kuma tana aure a Abuja kuma itama ita take kula da companyn mahaifin nata sai Anty Saudat a lagos sai Samira ita kuma a gombe sai Safwan sannan Mimi ƴar auta duka matan suna kula companyn mahaifin su kasancewar duk ƴaƴan shi sunyi ilimi mai zurfi Safwan shine kaɗai ɗansa na Namiji saidai shi kuma Safwan sam babu abinda ya rage a halin Mahaifiyar su na son taimako da son jama,a sannan tun yana ƙarami bashida burin daya wuce ya zama soja.



Kowa a gidan nasu yasan da hakan shekarun sa sha shida a duniya ya kammala secondary kasancewar sa yaro mai matuƙar hazaƙa a lokacin me ya sanar da mahaifin sa ƙudirin sa nason aikin soja amma sai ya ce sam bai yarda ba business zai karanta kamar sauran ƴan uwan sa ya kula masa da babban companyn sa dake kano ya roƙi mahaifin nasa kan ya barshi yayi aikin sa saboda bashida wani interest akan business ɗin amma yaƙi sanin halin mahaifin nasa yasa ya haƙura Turkey aka turashi karatu amma me saiya juya akalar karatun nasa zuwa taraining ɗin sojoji a wata babbar makarantar ko yarda sojoji anan Turkey ɗin shekara biyu yayi yana training sannan ya fito da babban muƙami a makarantar sojojin kowa yana son Safwan saboda yanayin maida hankalin sa shiyasa suka so su riƙeshi anan ya musu aiki yaƙi yarda saboda shima ya bautawa ƙasar sa sanda ya dawo Nigeria bada sanin mahaifin shi ya dawo ba kasancewar course ɗin shekara shida aka tura shi mahaifiyar shi kawai tasan da hakan. dan haka sai ya wuce gidan sa na kano yake aikin sa acan a ƙananan shekarun sa da basu wuce ashirin ba ya taka matsayi da dama wanda duniya take alfahari dashi ba iya ƙasar sa ba SGS FUNTUA kenan ɓoyayyen matashin daya ɓoyewa duniya kamannin sa saidai aikin sa tantirai suna tsoron sa dan ko sunanshi aka faɗa a gaban mai laifi saiya razana.


a shekaru shidan nan ya taka matsayi da dama sannan yasamu kyaututtuka iri-iri cikin lokaci ƙanƙani yazama matashi mai kuɗi.


KASH KU BIYONI.

NGD DA ƘAUNAR DA KUKA NUNA MIN
INA NEMAN AFUWA MA RASHIN POSTING DA MAYI KWANA BIYU INSHA ALLAH DAKA YANZU MUN DAWO POSTING BABU KAMA HANNUN YARO NGD


Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CVoFH73vk0nCnVISlZC9uU

*🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}

https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_

*Alk’alaminmu ‘yancinmu*

TAKU ZAINAB KABIR JAEN GARKUWAR ROYAL STAR
3/7/24, 9:04 AM - my lovely sister: ❤‍🩹 *WAYE SHI*❤‍🩹


*NA ZAINAB KABIR JAEN* *{GARKUWAR💪ROYAL STAR🌟}*

🅿️➡️1️⃣4️⃣.


______________Ranar daya cika shekara shida da tafiya karatu Walima mahaifin sa ya haɗa masa ta tarbar sa da kuma murnar damƙa ma ɗan nasa companyn sa yaran sa gaba ɗaya sun zo daga gidajen auren su kowa burin sa ya ganshi saɓanin mahaifiyar sa da zuciyar ta take cike da tsoron hukuncin da zai yiwa ɗan nata inya gane yana aikin soja suna zazzaune a palourn suka fara jiyo jiniyar motoci mamaki ne ya kama dukkannin su suna mamakin waye yazo haka da jiniya gaba ɗaya suka fito harabar gidan dan ganin wane baƙon sukayi.

shi kuwa Safwan tunda suka shigo gidan zuciyar shi ke tsananin bugawa har motocin su suka gama parking wani security ɗin nasa ne ya zagayo ya buɗe masa ƙofar motar a hankali ya zuro ƙafafun sa kafin ya gama fitowa gaba ɗaya haɗaɗɗan matashi ne ya bayyana jikin sa sanye da kakin sojoji kansa babu hula saidai sumar kansa dake a kwance luff tasha gyara tayi masa kyau sosai baƙin glass ne a fuskar sa fari ne soll irin farin nan da babu sirkin ja a ciki cikeda da dakewa ya fara takowa a hankali ya nufi wajan da mahaifin sa dake tsaye yayi mutuwar tsaye ganin abinda ya gigitashi da sauri Safwan ya tafi zai rungume shi cikin wata iriyar tsawa ya dakatar dashi "dakata karka taɓani Safwan ni zaka tozarta ni zaka kunyata a idon duniya" cikin sanyin muryar ya ce "sorry Abbu" wanke shi da mari yayi yana faɗin "baka isaba wallahi baka isa ka tozartani ba wallahi kaje ka barmun gida babu ni babu kai na cireka a ƴaƴana banida wani ɗa namiji a yanzu" zubewa yayi kan gwiwoyin sa yana bawa mahaifin nasa haƙuri amma cikin zafin rai ya tureshi daga riƙon daya yiwa ƙafar tasa.



Idanun Safwan ɗin sun kaɗa sunyi jawur ganin irin tozarcin da mahaifin sa keyi masa a gaban security ɗin nasa kasa tashi yayi a gurin cikin wata tsawar yaji mahaifin nashi na cewa " zaka fita ko sai na sa an fitar da kai ta ƙarfine eyeee?" a hankali ya tashi ya hau jikin sa a matuƙar sanyaye da sauri Mamin sa ta biyoshi tana faɗin ka dakata yarona dan Allah karka tafi ka zauna tare damu ta ƙarasa cikin kuka shi kanshi Safwan ya kasa daurewa ganin hawayen mahaifiyar tashi shima hawaye kawai yakeyi kamar ba soja ba cikin zafin rai mahaifin nasa yace "Halima indai kika ƙara taku ɗaya daga inda kike a bakin auren ki na yanke duka igiyoyin auren dake kanki" cak ta tsaya ta durƙushe a gurin tana kuka sauran yaran nata suma sunayi da matuƙar sauri Safwan ya shiga mota suka bar gidan zuciyar shi na masa ƙuna tsanar mahaifin shi da halayen shi suka rufe kai tsaye gidan sa na kano ya koma inda yake zaune a kwana kin nan damuwa tayi masa yawa kewan mahaifiyar shi da halin daya bar ta a ciki sun lulluɓashi dan haka ya yanke shawarar ya nemi aiki a wani gidan ko ya rage damuwa in yana ganin sa tare da mutane shine ya nemi aiki a wajan Alhaji matawalle kuma yaci sa,a ya ɗauke shi a matsayin driver sai dai sam baya baiyyana asalin sa ya buɗe company kala-kala a na kula masa dasu ya tara dukiya dashi kansa bai san yawan su ba dan a yanzu companyn sa yana na biyu a manyan companys na Nigeria daga na mahifinsa sai nasa kasancewar ya samu ma,aikata masu amana suna kula masa da dukiya sosai shi kuma yama cigaba da aikin sa na soja duk da dai ba wanda yasan asalin mai companyn nasa kawai dai kowa yasan SSG Company. wannan shine asalin abinda yasa jarumin namu ya fara aikin driver.


WANNAN KENAN.

cigaban labari.....

ku biyoni dan jin yanda zata kaya ngd




Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CVoFH73vk0nCnVISlZC9uU
*🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}

https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_

*Alk’alaminmu ‘yancinmu*
3/7/24, 9:04 AM - my lovely sister: ❤‍🩹 *WAYE SHI*❤‍🩹


*NA ZAINAB KABIR JAEN* *{GARKUWAR💪ROYAL STAR🌟}*

🅿️➡️1️⃣5️⃣.


Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/CVoFH73vk0nCnVISlZC9uU
*🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}

https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_

*Alk’alaminmu ‘yancinmu*


_____________A hankali yaja motar shi yafara driving a hankali duk zuciyar shi babu daɗi sam baya son tuna abinda Mahaifin nashi yayi masa ya kamata ko yaya ya masa uziri a hankali ya koma gidan zuciyar sa babu daɗi sam kansa yana matuƙar sara masa idanun sa sunyi jawur a haka ya ƙarasa gida kan ƴar katifar sa dake gidan ya kwanta bacci kuwa nan da nan ya ɗauke shi bai farka ba sai gab da za,a tashi su Safna dan haka da cikin hanzari ya tashi ya fito makarantar tasu ya nufa yana zuwa ana tashin su hango su yayi su uku sun fito suna taho wa inda ake ɗaukan ɗaliban zuba mata ido yayi kawai saiya tsinci kansa da sakin wani tattausan murmushi a hankali ta ƙaraso gaban motar ta buɗe murfin ta shiga sai dai ko kallan sa batayi ba shima bai damu da hakan ba suka kamo hanyar gida.




yau ta kama weekend tun safe Safna take shan aiki saida ta gyara ko ina tsaff sannan tayi wanka ta shirya cikin wani material maroon colour da adon milk wanda akayi misa ɗinki doguwar riga harabar gidan tafi to wayar tace tayi ringing ɗaga kiran tayi tana cewa "baby tun ɗazu fa nake jiranka" a ɗaya ɓangaren shima Mahbub ɗin yace "sorry princess ina bakin gate ɗin gidan ku" cikeda murna ta ce "are you serious darling" murmushi yayi yana faɗin "yess of course yanzu ma zaki ganni" yana faɗin hakan motar sa ta shigo gate ɗin gidan duk abinda sukeyi akan idon Safwan ne dake zaune ɗan nesa dasu kaɗan.



mamaki ne ya cika zuciyar sa yaushe Safna ta fara kula samari kuma waye ma Saurayin da take kulawa mamakin sa ne ya katse sanda yaga managern companyn sa Mahbub ya fito a mota ransa ne ya ɓaci matuƙa me yarinyar nan take nufi bazai yuwu ba ya faɗa cikin zuciyar sa ransa kam duk inda yake yayi dubu ya ɓaci yana kallon su suka isa garden sai wani shagwaɓa take zuba masa da suka isa wajan zaman garden ɗin yana kallo Safnan ta jawowa Mahbub ɗin kujera ya zauna cikin wani baƙin kishi ya taso daga inda yake ransa a matuƙar ɓace sam ya ma manta matsayin sa a gidan wajan su ya nufa gadan-gadan suka suna zaune suna shan soyayyar su bama su lura dashi ba Mahbub ne idon sa ya sauka akan SGS ya nufo gurin s, zumbur ya miƙe zuciyar shi tana tsananin bugawa ita kuma Safna mamaki ne ya kamata ganin Mahbub ɗin ya zabura har yana taka ta bai sani ba.


Shi kuma SGS kafin ya ƙaraso hankalin ya dawo jikin sa da sauri ya dai-dai ta natsuwar sa ya ƙarasa ya miƙa ma Mahbub hannu yana faɗin "barka da zuwa ranka ya daɗe" sanin waye Safwan ɗin da yanda yake ƙoƙarin ɓoye kansa kansa yasa shima Mahbub ɗin sakin murmushi yana faɗin "barkan mu dai kana lafiya" ya ce "Alhamdulillah" haushi ne ya kama Safna ta ce " baby wa kake cewa ranka ya daɗe wai driver nawa bana son irin haka fa" murmushi Mahbub ɗin yayi mata a zuciyar sa yana faɗin baki da hankali baki san dawar garin ba a fili kuma ya ce "oh baby Sorry bazan ƙara ba", kallon Safwan Safna tayi cikin tsiwa da rashin kunya tana faɗin "kamin tsaye aka ka kauce ka bani guri zanyi magana da mijina" ji yayi kamar ta soka masa wuta da tace mijinta amma saiya dake ya ce "to ranki ya daɗe" a fakaice kuma yayi Mahbub in kiya da ya bashi minti biyu yana jiran sa a waje sannan ya bar gurin......



Wannan kenan.
Kudai ku biyoni.

Taku ako da yaushe Zainab kabir jaen
GARKUWAR ROYAL STAR
3/7/24, 9:04 AM - my lovely sister: ❤‍🩹 *WAYE SHI*❤‍🩹


*NA ZAINAB KABIR JAEN* *{GARKUWAR💪ROYAL STAR🌟}*

*🌟ROYAL STAR WRITER'S ASSOCIATION🌟*
{R.S.W.A}

https://www.facebook.com/Royal-Star-Writers-Association-101607075594165/?ref=py_c
*_Marubuta masu aiki da fasaha da zallar amana, Fad’akarwa, ilimantarwa da kuma nishad’antarwa_*
_(R.S.W.A) Ruwa kad’ai ke maganin k’ishi_

*Alk’alaminmu ‘yancinmu*


🅿️➡️1️⃣6️⃣.


______________Ko minti ɗaya Mahbub kasayi yayi a gurin saboda son cika umarnin ubangidan nasa yana barin gurin shima ya miƙe yana faɗin "Beb saƙon gaggawa daga office ana jirana zan dawo next week insha Allah" bai jira amsar ta ba ya bar gurin a ranta taji ba daɗi sosai amma sai tayi masa uziri da kiran daga office ne a waje ya taradda Safwan ɗin buɗe gaba motar yayi ya shiga sannan yayi masa umarni da su tafi har suka fita a unguwar ba wanda ya ƙara cewa ƙala sai can Safwan yaja numfashi ya ce "menene haɗin ka da Safna?", ɗan sosa kai Mahbub ɗin yayi kafin ya ce"ranka ya daɗe she's my girlfriend" ɗan kallon sa yayi kafin ya ce "auren ta zakayi?" ƙasa da kai yayi kafin ya ce "No Oga ai na kusa aure ma da yarinyar ancul ɗin mu auren family za,a mun" cikin ɓacin rai Safwan ɗin ya ce "kenan yaudarar ta kake?" ƙasa da kansa yayi saboda ya fahimci ran ogan nasa ya ɓaci.


Shi kuma Safwan cikin faɗa ya ce "kar na ƙara ganinka a gurin ta as from today babu kai babu ita" cikin ladabi ya ce "insha Allah oga".

Dai-dai lokacin suka iso ƙofar gidan Safwan ɗin sauke sa yayi shi kuma ya tafi.


To tundaga ranar Safna bata ƙara jin Mahbub ba ko wayar sa ta kira sai dai ta ƙaraci ringing ɗinta ba,a ɗaga ba in tayi masa text message ma ba zai mata reply ba ta damu ƙwari kafin daga baya ta watsar da lamarin sa dan yanzu tayi wani sabon saurayin Ameer ɗan gidan ministan kuɗi yaron bayaji yana wasa da ƙudi sosai class ɗin su ɗaya ya daɗe da cewa yana sonta amma bata yarda sun fara soyayya ba sai yanzu.



exam ta ƙarato su Safna sunyi busy da yawa kasancewar jarabawar da zasu zana itace shaidar su ta kammala Secondry wato Neco da waec karatu suke babu ji babu gani domin son su samu nasara duk da a ɓangare ɗaya sam bataji daɗin zana jarabawar don ba zata dinga ganin sahibin nata ba koda yaushe.


To sun zana jarabawa lafiya kuma sakamako yayi kyau sosai yanzu Safna babu abinda tasa gaba sai soyayyar ta Ameer dan daddy ya ce bazata fara karatu ba sai tayi aure yanzu Ameer har gidan yake zuwa kuma koda yaushe akan idon Safwan ne abun yana ɓata masa rai sosai dan yana ganin wannan zubar da mutunci ne yasa Safna kula wannan yaron da, da kaɗan zai girmeta a ransa ya ce dole inyi wani abu ya kamata inyi gaggawar auren yarinyar nan tun kan yaran nan su ɓata mata tarbiyya dan haka ya samu Alhaji da maganar yaji daɗi sosai ya ce " dama Safwan jira nake naji kayi magana nima nayi tunanin ya kamata a cika alƙawarin mahaifiyar ta tunda yanzu ta gama makarantar ta amma safwan ya kamata ace zuwa yanzu ka sanar mana da iyayen ka" sosa kai yayi ya ce "Alhaji iyayena ne zasu neman mun aure gidan nan ni asalina ɗan ƙauyen funtua ne nazo birni ne neman kuɗi sai Allah ya haɗa ni da kai daddy zanje ƙauye in turo magabata na" ya ce "Allah sarki to shikenan sai ka turo sun bama lokaci da yawa za,asa ba ai" ya ce "to daddy".


Safwan da kansa yaje dangin mahaifin sa wanda mahaifinsa ya wulaƙanta dan yana ganin su talakawa ne ya wofantar dasu Safwan ɗin ya gina musu rayuwa ya taimake su yaje ya faɗama yayyen mahaifin nasa duk abinda ke faruwa kuma ya sanar dasu idan sunje neman auren kar su sake su faɗi asalin mahaifin sa. .

Sunji daɗi sosai kuma a satin sukazo nemar wa ɗan nasu auren Safna Alhaji matawalle ya karramasu sosai kuma anan

Book Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3

Please Login or Register in order to submit comment