Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

fito har momy ta fiddo mata wata doguwar riga ta Afnan, cif ta mata a jiki kuwa sannan ta kama yin sallar isha dan itace kawai a kanta,
Da gamawar ta tayi shafa'i da wutri, ta rok'i Allah gafara sosai sannan ta fita parlor da hijabin a jikin ta.

Ta samu iyayen sun kasa zaune sun kasa tsaye, kowa yana tunanin inda yaron shi yake,
Da fitowar ta duk suka mik'e idon kowa a kanta, kowa cike da son jin inda yaron shi yake.

Zama tayi akan carpet d'in dake tsakiyar parlor'n, wani sabon kuka taji amma a haka ta daure ta fara fad'in
"Da farko ina mai neman gafarar ku a bisa k'arya da muka maku baki d'ayan mu, birthday'n k'awar mu Kerry ne yau sai sa muka shirya maku k'arairayi domin mu samu kubar mu mu fita,
Sai gashi Allah ya gwada mana iyakar shi, ya nuna mana mummunan aikin da muka aikata tun a duniya duk da yake wannan bashi ne na farko ba".

Cike da k'osawa Alhaji Abdallah yace "go to the staright point, ina yaran suke yanzu!?"
Cikn rawar murya tace "suna *Ajiwa dam,* but am sorry to say, duk basa cikin hayyacin su, tayi kaca kaca dasu dan bana sa ran akwai rayayyu a cikin su" tana kaiwa nan tayi shiru sanadiyyar salatin da suka d'auka duka d'akin.

Alhaji Ma'aruf ne yayi k'arfin halin cewa "wacece ita!? Wacece ta mana kaca kaca da yara? Wallahi sai nayi ajalinta matuk'ar ta kashe min yara, yara na 'yan biyu su kenan na mallaka fa, wallahi sai ta raina kanta, zata san ta tab'a iyalin Alhaji Ma'aruf Sale, ku tashi mu tafi wurin ta ni zan maku maganin koma wacece ita, ko ubanwa ya haife ta a fad'in k'asar nan sai ta raina kanta" yana kaiwa nan ya fice sauran ma suka mara masa baya,
Ganin za'a tafi abar su yasa Ummah da Feenat ma suka bi bayan su.

Amrah and Rerbeeart sk novels,

*A YINI 'DAYA* ๐Ÿ’€

๐Ÿ‘น๐Ÿ’€ ๐Ÿ’€๐Ÿ‘น
๐Ÿ‘บ


*Na Princess Amrah*
*Da Rabiatu sk msh*

Page1โƒฃ5โƒฃ

*NOTE:-* *kuyi hak'uri na rashin jin mu kwana biyu, hakan ya faru ne na rashin isasshen time, tests nake sosai ga kuma exam muna facing, am in need of your prayers fans, love youh all.*


**************
A mota d'aya suka d'unguma suka tafi, sai momy, ummah, mami da kuma Feenat driver ya tafi dasu,
Sosai suke gudu nan da nan sai gasu a Ajiwa, a bakin dam d'in sukaje tare da barin fitilun gurin a kunne saboda duhun dake akwai.

Sosai suka razana ganin yaran su a babbaje k'asa kamar marasa gata,
Wasun su kuka kawai suke dan babu alamar rai a tare dasu musamman ma wanda suka hango can gefen ruwa babu k'afa d'aya.

Feenat kuwa jikin ta sai rawa yake dan kar wannan halittar ta dawo dan tana matuk'ar tsoron ta, ta k'ank'ame ummanta sosai tana kuka tana k'ara tuno da yanda aka ringa illata mata abokai.

Alhaji Ma'aruf yaci gaba da dube duben inda zai hango yaran shi, daga can nesa ya hangi Reeshat k'ank'ame da MD duk kansu babu alamar numfashi, wata irin k'ara ya saki cike da tashin hankali, da k'arfi yace "idan ba tsoro ba ki fito mana! Wallahi sai na kashe ki in har yara na suka mutu, ki bayyana kanki inji wanene ubanki a k'asar nan!" Yana kaiwa nan yaci gaba da kukan shi kamar k'aramin yaro.

Su kuwa sauran suka hau bincikar yaran su,
Nan da nan kowa ya gano yaron shi amma fa duk kanwar ja ce saboda babu alamar rayuwa a tare dasu.
Sauran da babu iyayen su kuwa nan aka barsu babu galihu,

A hankali suka fara jin wata k'ara mai had'e da guguwa tana dosowa inda suke,
Sosai hankulan su suka tashi musamman yanda sukaji k'arar tana k'ara tinkaro su, ga wani irin haske daya bayyana a wurin,
Cike da tashin hankali suke kallon al'amarin,
Feenat kuka sosai take tace "ummah gata nan, ta dawo zata kashe ni, dan Allah kice mata tayi hak'uri ta koma"
Ummah ta rungume ta tace "ki kwantar da hankalin ki, insha Allahu babu abunda zata miki, kici gaba da addu'ah kawai kar ki daina, kar kuma tsoro ya hana ki yi kinji?",

Kai kawai ta gyad'a mata idon ta kyam akan guguwar dake nan dunk'ulewa wuri d'aya.

Dady ya rungume momy yana fad'in "mun shiga uku! Ga Afnan bata numfashi kuma ga wannan al'amarin, mu gudu kawai mu kai 'yar mu asibiti dan tabbatar da ko tana da rai",
Cikin tashin hankali momy tace "insha Allahu ma tana raye, Alhaji ban san ya zanyi ba idan na rasa Afnan, itace 'yar budurwar da nake tak'ama da ita gashi mahaifata ta lalace" ta k'ara fashewa da kuka.

Dady yace "ki daina kukan nan kina k'ara tayar min da hankali ne, mu tafi abun mu kawai tunda dama da mota ta muka zo",

Daidai sunbi hanya zasu tafi kenan wannan guguwar ta tare su, da k'arfi iska ya ringa dawo dasu cikin mutane, duk k'ok'arin da suke na tafiya amma dawo dasu iskan yakeyi, ga Afnan dauk'e a hannun Dady, momy kuma ta rik'e shi tam saboda tsabar tsoro, tunda uwar data haife ta bata tab'a shiga tashin hankali irin wannan ba,
Dole basu dan yanda zasuyi suka tsaya cikin mutanen, shi kanshi Dady'n k'arfin hali ne kawai ya hana shi yin kuka,
Dan kuwa Alhaji Bashir yanayin daya ga Nuratun shi ciki dole shima ya shiga tashin hankalin, kuka yake sosai kamar k'aramin yaro, ga wata irin k'ara data sa babu mai jin wani idan yayi magana.

A hankali guguwar ta dunk'ule wuri d'aya inda ta koma wasu irin k'anana k'ananan halittu bak'ak'e wulik, exact abunda ya faru a baya yanxu ma shine, haka suka ringa cin junan su har suka zama babbar halitta guda d'aya.
Feenat na gani ta tabbatar da wannan halittar ce, nan da nan hankalin ta ya k'ara tashi tana k'ara tuno baya, "tou wai ma me ya dawo dani bayan ta sallame ni? Babu fa wanda yace mu bisu mune kawai mukayi niyya" maganar data ringayi a ranta kenan.

Da k'arfi halittar tayi wata irin k'ara wadda sai da komai na wurin ya jijjiga, mutanen wurin kuwa wasu suka ringayin sama da k'asa, basu samu daidaituwa ba har sai da ta tsaya da wannan k'arar ta fuskance su baki d'aya tana k'ok'arin yin magana.

Amrah and Rerbee'art sk novels,

[4:45pm, 2/10/2016] Amrah๐Ÿ’“Pinky๐Ÿ’“durling๐Ÿ˜˜:

๐Ÿ’€ *A YINI 'DAYA* ๐Ÿ’€

๐Ÿ‘น๐Ÿ’€ ๐Ÿ’€๐Ÿ‘น
๐Ÿ‘บ


*Na Princess Amrah*
*Da Rabiatu sk msh*

Page1โƒฃ6โƒฃ



Da sauri Ummah ta k'ara matsawa inda take tace "dan Allah kar kiyi magana",
Duka hankulan su suka dawo kan Ummah suna mamakin dalilin da yasa ta hana halittar yin magana,
A tsorace Feenat tace "nasan dalilin hana ta magana Ummah, amma kuma ya zama dole tayi magana domin sanin musabbabin abubuwan data mana".

Duk kanin su kallon Ummah da Feenat suke, babu wanda ya iya yin magana saboda yanda suke cike da tsoro, tun da suke a rayuwa basu tab'a ganin halitta mai girman ta ba, ko a frictions films basu tab'a gani ba, amma sai gasu yau a gaban ta bayan ta illata masu yara.

Ummah ta juyo gare su tace "tabbas idan muka bari ta mana magana duk kan mu muna cikin hatsari, duk da bani da tabbas amma wannan aljana ce, ta b'oye halittar ta ne saboda matuk'ar muka ga zahirin ta tou no more us, da zarar muka bari tayi magana har mukaji muryar ta komai zai iya samun mu, saboda jin zahirin muryar ta zai iya saka mu kurumce ko ma mu haukace baki d'aya, ina mai bada shawara da indai magana kuke son yi da ita tou mu rok'e ta ta shiga jikin d'aya daga cikin mu sai ta mana bayanin komai".

Kallon Ummah suke sosai saboda furucin ta, Alhaji Ma'aruf daya gama tsurewa yace "indai har sai ta shiga jiki na tou sai dai ta tafi bamu son jin bayanin kuma mun yafe mata",

Dady ma bayan ya ajiye Afnan yace "ai wallahi na yafe, mu dai dan Allah kiyi hak'uri ki tafi kawai, ki bar mu mu koma gidajen mu dare nayi sannan kuma bamu san ya lafiyar yaran mu ba", bayan ya miyar da kallon sa ga halittar.
Momy ta d'aga kai alamar maganar da Dady yayi gaskiya ne.

Alhaji Abdallah yace "bai kamata mu tafi haka kawai ba, mu dai daure ta shiga jikin wanin mu, kunga tanan ma zamu iya samu ta warkar mana da yaran mu data illata",

Mami cikin kuka tace "kayya! Babu maganar warkarwa a halin yanzu, kaga fa yanda tamin da yarinya, Ruky na ta baro gida lafiya lau amma yanzu jita fa, *Allah ya wadaren zuwa party ma baki d'ayan shi"* ta k'ara fashewa da kuka.

Ummah ta sauke ajiyar zuciya tace "ni nasan bazata iya shiga jiki na ba, amma barin gani", ta koma close to halittan babu alamar tsoro a tare da ita.
Sunkuyawa tayi har k'asa tace "idan zaki iya shiga jiki na ki shiga, ki shige ni dan ki masu bayanin komai".

Wata irin k'ara ta kuma saki bakin ta a bud'e kamar zata had'iye Ummah, hakan bai sa Ummah taji tsoro ta matsa ba, sai ma cewa da tayi "ke nake jira".

Kai tahau girgizawa har a lokacin bata rufe bakin ba, wannan blue hawayen sukaci gaba da kwaranya daga idon ta, a hankali ta soma ja da baya kanta sunkuye k'asa tana girgixa kanta.

Mik'ewa Ummah tayi tsaye tace "kun gani! Na fad'a maku bazata tab'a iya shiga jiki na ba, abunda yasa kukaga nace ta shiga d'in nasan wasun ku zasuce k'arya nake kawia dai ina tsoro ne, tou kun gani da idon ku, bazata tab'a koda shafa na ba, haka kuma ina da tabbacin baxata iya shigar Feenat ba, saisa ma kuka ga ita kad'ai ta koma gida ba tare da ta mata wani abu ba".

Kai sukaci gaba da jinjinawa alamar sun gamsu da duk kalaman Ummah,
Dady yace "tou yanzu miye mafita? Nidai a zahirin gaskiya ina tsoron ta shige ni dan kar tak'i fita, tou wai ma baiwar Allah me yasa ta kasa shiga jikin ki da 'yar ki mu kuma kike tunanin zata iya shigar mu?".

Ummah ta ce "ba wai ina da tabbacin zata iya shigar ku bane, ina dai tunanin zata iya d'in ne, akwai wasu abubuwan wanda muka rik'a nida Safeenah wanda ina da tabbacin babu wani abun cutarwa da xai iya cutar damu har sai idan Allah yayi nufin sa akan mu".

*Amrah nd Rerbee'art sk novels๐Ÿ“š*
[4:54pm, 2/10/2016] Amrah๐Ÿ’“Pinky๐Ÿ’“durling๐Ÿ˜˜:

๐Ÿ’€ *A YINI 'DAYA* ๐Ÿ’€

๐Ÿ‘น๐Ÿ’€ ๐Ÿ’€๐Ÿ‘น
๐Ÿ‘บ


*Na Princess Amrah*
*Da Rabiatu sk msh*

Page1โƒฃ7โƒฃ



Dady yace "menene wannan abun da kuka rik'a baiwar Allah?"

Ummah tace ba wani abune mai wahala ba, wasu kalmomi ne wanda baku kad'ai ba hatta da *Amrah and Rabiatu sk Fans* idan suka rik'e su zasu kub'uta daga duk wani aljani namiji ko mace, kai baki d'ayar al-umman musulmai ma nake maka magana. Kalmomin sune:-

*LA-ILAHA ILLA-LLAHU WAHDAHU LAA SHARIKALAHU LAHUL-MULKU WA LAHUL-HAMDU WA HUWA ALA KULLI SHAI'IN KAD'IR* so d'ari ko wace safiya, sai kuma *A'UDHU BI KALIMATULLAHI TAAMMAAT MIN SHARRI MA KHALAK* itama sau d'ari a yini, sai *AYATUL KURSIYYU, BISMILLAHILLADHI LA YA DHIRRU MA'ASMIHI SHAI'UN FIL-ARDI WALA FISSAMA'I WAHUWAS-SAMI'UL ALEEM, U'IDHI KUMA BI KALIMATULLAHI TAAMMAAT WAMIN KULLI SHAID'ANIN WA HAAMMAT WA MIN KULLU AININ-LAAMAT, FALAQ, NAS DA IKHLAS K'AFA UKU UKU* a kowace safiya, idan mutun yana da yara ma yana masu tou insha Allahu babu abunda zai same sa, hatta da sihiri ko kambun baka yana da wuya ya kama mutun matuk'ar ya rik'i wannan adhkar d'in, sune na rik'a kuma koda wace safiya sai munyi su tare da Safeenah inayi tana amsawa kafin ta fita ko ina, kuma kuma inda zaku rik'e su am sure babu abunda zai iya cutar daku".

Dady yace "tabbas wannan wani babban makami ne kuka rik'a, kuma muma insha Allahu daka yanzu mun rik'e su kenan", (ina fatan masu karatu ma zasu rik'e su saboda suna da muhimmanci a rayuwar mu, musamman ma a wannan lokacin da kana baccin ka wasu na maka nasari, Allah yasa mu dace ameen).

Ummah tace "tou yanzu ya kukace? A barta ta tafi ko kuwa akwai wanda zai bari ta shiga jikin sa? Nasan dole tana da maganganu a bakin ta, sannan zamuyi da wajewa in har ta shiga jikin mutun zata fita, idan ba haka ba kuma komai na mata ita taja, ina da babban malamin da zai iya salwantar da rayuwar ta, malam Mu'awuya *(na cikin JINNUL_ ASHIQ)* Zai iya da ita, barin ma nasan bazatayi haka ba".

Alhaji Abdallah yace "babu komai ni ta shiga jiki na, a adhkar d'in da baiwar Allah'n nan ta bamu na rik'e su sosai, kuma nasan koda ta zauna a jikina baxata dawwama ba saboda zan kasance mai yawan yin su insha Allahu".

Dad'i sukaji su duka, Ummah da Alhaji Abdallah suka k'ara matsawa kusa da wannan halittar tace "ga wanda zaki shiga nan, amma ina fatan bazaki cutar dashi ba" kai kawai ta d'aga masu tare da b'acewa b'at daga wurin.

Su duka sai da suka tsorata, har umman ma yanzu ta tsorata,
Bayan 'yan seconds Alhaji abdallah ya fasa wata irin k'ara da k'arfi kamar ba mutun yayi ta ba, nan ya hau jijjikar jikin sa hawaye na fita daga idon sa.

Sun dad'e a haka babu wanda ya iya furta komai kafin ya bud'e baki yace "yaran ku sun illata min duka iyali na (family na), tun daga mamana, babana, yarana uku da miji na, wasu sun mutu a dalilin haihaye su da suka ringayi, babana ya tsufa sosai da mamana, hakan yasa basu da wani k'arfi sosai abu kad'an yana iya yaji masu ciwo, sun mutu baki d'ayan su, sai yaro na d'aya jinjirin da na haifa yau kwana biyu shima ya mutu, miji na da sauran yara na biyu sun ji ciwo sosai. Bayan nan kuma a inda na zauna ina karb'ar gaisuwar mutane ma basu barni ba, sai da suka k'ara kashe min wasu mutanen wasu kuma suka gudu, taya kuke tunanin zan k'yale su? Ni ba muguwa bace saboda bani da ra'ayin shiga bil-adama, Feenat kuwa tafi k'arfi na, a lokacin dana d'auke ta da nufin yi mata wani abu kawai na kasa, kuma ma inda ace na mata wani abun da na cuce tane saboda babu abunda tamin, gefen su take tana dana sanin xuwa wurin da tayi, hakan yasa na bata izinin ta tafi gida, tun kafin ta tafi ta buk'aci na mata bayanin dalilin da yasa na masu haka amma na kasa saboda bana son taji murya na a zahiri, yaran ku kuma babu wanda na kashe sai dai duk sun raunana sosai, zasu farfad'o koba yanxu ba, ku kwashe su ku tafi dasu sannan ku masu gargad'in kar su sake zuwa wurin *party,* koda wani sukaji xaije tou su hane sa da xuwa, ni abun da na masu mai sauk'i ne, na tabbatar da inda wasu ne a cikin jinnu har kashe su zasu iya yi, gashi kuma duk cikin su babu mai neman kariya daga Allah".

*Amrah and Rerbee'art sk novels๐Ÿ“š*
[5:03pm, 2/10/2016] Amrah๐Ÿ’“Pinky๐Ÿ’“durling๐Ÿ˜˜:

๐Ÿ’€ *A YINI 'DAYA* ๐Ÿ’€

๐Ÿ‘น๐Ÿ’€ ๐Ÿ’€๐Ÿ‘น
๐Ÿ‘บ


*Na Princess Amrah*
*Da Rabiatu sk msh*

Page1โƒฃ8โƒฃ



Tayi shiru kafin taci gaba da "akwai abubuwa da dama da mu jinnu bama son su, matuk'ar bil-adama suka rik'e su tou komai muguntar aljani bazai iya ma mutun komai ba, kamar abubuwan da matar nan ta lissafa maku, bayan su kuma akwai yawan amfani da man hulba, bamu son warin shi sosai, sannan kuma akwai miski, shima idan bil-adama yana amfani dashi babu abunda jinnu zasu iya masa, yin addu'ah kafin shiga ban d'aki yana makantar mana da idanuwa, akwai su dai da dama wanda idan na tsaya lissafo su zaku iya kwana anan. Kai kuma bawan Allah" tayi nuni da inda Alhaji ma'aruf yake da yatsa tace "ka kiyaye ni! Zan maimata maka cewa ni ba muguwa bace, inda ace ni muguwa ce da ko gawar yaranka bazaka tayar anan ba, kana tak'ama da kud'i kud'in banza gareka! Sai kuje yanzu kud'in ka su warkar maka dasu ai, na haukatar da uwar birthday d'in saboda itace silar komai, sannan kuma ita da saurayin tane suka kashe min iyaye, saurayin nata ma na haukatar dashi, tunda iyayen su masu kud'i ne sai su neman masu magani, bana buk'atar ku sake nema na saboda na gama daku" tana kaiwa nan Alhaji Abdallah yayi atishawa da k'arfi had'e da yin hamma.

Koda na duba naga duk jikin su a sanyaye yake har dai Alhaji Ma'aruf da hawaye ke kwaranya daka idon sa, fatan shi dai Allah yasa yaran sa zasu mik'e da k'afafun su.

Dady da momy dai kuka ne kawai aikin su, sun tasa Afnan gaba da har yanzu bata da alamar tashi, baccin ta fad'a masu cewa bata kashe su ba da sunce Afnan bata da rai.

Bayanin komai suka ma Alhaji Abdallah, wurin 'yar sa ya koma ya d'aura ta akan cinyar sa yana fad'in "why Ihsan? Mesa kika zab'i wannan rayuwar? Mesa kika d'aukarwa kanki wata tarbiyyar da ban sanki da ita ba? Gashi yanzu kin jawa kanki, ga yanda Allah ya maku, wannan ishara ce ga duk masu hali irin naku, musamman matasan yanzu da suka miyar da *party* tamkar ruwan shan su, suma iyayen su k'arya a kowane lokaci kawai dan su tafi *party,* ga yanda tayi dasu *A YINI D'AYA* ta gama da rayuwar su" yaci gaba da kuka sosai yana jijjiga ta.

Haka Dady ma ya ringa jijjigar Afnan wai a nufin shi ko zata farka amma babu ko alama, Momy da kuka ya gama cin k'arfin ta tace "Afnan ki rasa irin k'aryar da zaki mana sai ta mutuwa? Ki danganta mahaifin k'awarki da rasuwa? Kenan dama ciwon k'arya kike min a lokacin da nace miki ki tafi islamiya? K'arya kike min da kikace zakije school d'in ku siyen kayan practical? Fita *party* kawai kuke zuwa Afnan? Haka kike so yaran ki su miki Afnan? Na gama yarda dake har abada, na gama yarda da duk abunda zaki fad'a min, ina fatan Allah ya gwada min ranar da kema 'yar ki zata miki haka, bana fatan Affan yayi koyi da mugun halink..." Bata k'arisa maganar ba sanadiyyar toshe mata baki da Ummah tayi tana fad'in "kar ki mata baki Hajiya, kefa uwa ce kuma duk bakin da kuka mata zai iya binta, dan Allah kar b'acin rai yasa ki fad'in munanan kalmai akan 'yarki da kika haifa".

Cikin kuka Momy tace "dole ne yasa ni fad'in haka, Afnan taci amana ta taci amanar mahaifin ta, ni a kowane lokaci ina tink'aho da ina bama 'yata tarbiyya mai kyau, ina alfahari da yanda nake basu tarbiyya ita da k'anin ta, ashe duk a banza, tana jefar dasu ne a cikin gida kafin ta fita, aikuwa kinma kanki, 'yar secondary School d'in da kike shekarar k'arshen ma bazaki k'arisa taba aure zan miki, mu koma gida wallahi sai kin fitar da miji, idan ma baki dashi zan kai hoton ki masallaci mai so yazo zan basa sadakar ki"

A hankali Afnan ta fara bud'e idon ta, tana d'ora shi akan Momy da sauri ta rufe tana rewinding d'in abubuwan da suka faru tun daga k'aryar da tayi kafin ta baro gida, casun da sukayi da kuma yanda wannan halittar ta ringa yi dasu, wasu zafafan hawaye suka ringa kwaranya daga idon ta, "tou me ya kawo su Momy nan? Ya akayi suka san muna nan? Me ma ya same ni naji jiki na duk babu dad'i?" Maganar xuci ce tayi amma bata san ta fito zahiri ba.

*Amrah and Rerbee'art sk novels๐Ÿ“š*

[10:42am, 13/10/2016] Amrah๐Ÿ’“Pinky๐Ÿ’“durling๐Ÿ˜˜: ๐Ÿ’€ *A YINI 'DAYA* ๐Ÿ’€

๐Ÿ‘น๐Ÿ’€ ๐Ÿ’€๐Ÿ‘น
๐Ÿ‘บ


*Na Princess Amrah*
*Da Rabiatu sk msh*

Page 19-22


"Lokacin tonuwar asirin ku ne yayi" momy ta fad'a tare da watsa mata wani mugun kallo.

Duka wurin shiru kake ji babu mai magana in banda sautin kukan Afnan dake tashi,

Da k'yar ta iya furta "momy sharrin shaid'an ne dan Allah kiyi..." Bata gama maganar ba sanadiyyar tsawa da ta yi mata da k'arfi dolen ta tayi shiru.

Nan iyayen suka hau harhad'a su wuri d'aya suna k'ara tausaya masu musamman ma Md da cinyar shi ta fita daga gangar jikin sa baki d'aya duk jini ya gama b'ata shi.

Alhaji Ma'aruf ne yayi waya a asibiti yace a kawo masu mota, ya kwatanta masu inda suke sannan ya kashe wayar yaci gaba da kukan shi, babban tashin hankalin shi bai wuce yanda yaga jikin Reesha duk ya zagwanye ba, babu fata kwatakwata a jikin kamar ya k'one, ga kanshi babu ko alamar gashi yayi fari fat. Reeshat ma can jikin k'arfen shiga ruwan ya gano ta jikin ta duk ya fashe har a lokacin jini bai daina zuba ba, kuka kawai yake yi kamar k'aramin yaro.

Ba'a wani jima

Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5Chapter 6

Please Login or Register in order to submit comment