Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Kallon sis R. Nayi cike da k'aguwa da shigowar Alhaji Abdallah, muje zuwa dai sis R. Ta fad'a, sai kuma gobe zakuji posting d'in mu insha Allah.
Amrah and Rerbee'art sk novels

[11:36pm, 23/09/2016] Amrah💓Pinky💓durling😘: 💀 *A YINI 'DAYA* 💀

👹💀 💀👹
👺

*®NWA*
*Na Princess Amrah*
*Da Rabiatu sk msh*

Page1⃣1⃣

Ba'a jima ba kuwa sai ga maigadi tafe Alhaji Abdallah a bayan shi,
A kid'ime Dady ya mik'a mashi hannu suka gaisa tare da cewa "bismillah ga wurin zama",
Alhaji Abdallah ya zauna sannan yace "nazo ne dama inji ko lafiya tun da yamma Ihsan ta baro gida tace nan zata zo wai Afnan bata da lafiya, kuma gashi har yanzu bata koma gida ba"

Ido bud'e momy ta kalle shi cike da mamaki tace "Alhaji ai muma nan tun yamma Afnan tabar gidan nan wai kayi accident da jirgin sama ka rasu",

Salati Alhaji Abdallah yayi a bayyane yana mamaki, a ranshi yace "kenan Ihsan bata zo nan ba?",

Momy tace "innalillahi wa inna ilaihi rajiun! k'arya Afnan tamin kenan dama ba can zataje ba?",

Ummah dai na tsaye cikin tashin hankali tana sauraren su, sun jima d'akin babu wanda ya kuma cewa wani abu kowa da abunda yake sak'awa a ransa, sai daga baya ummah tace "in kuwa hakane tou duk inda yaran nan suke suna tare, babu mamakin ko wani wurin sukaje shine suka tsara mana k'arairayi mu kuma muka yarda, Allah dai yasa lafiya suke".

Dady yace "wannan hakane baiwar Allah! Tou ina yaran nan sukaje ne?",

Alhaji Abdallah yace "nima tunanin da nake kenan, wai yara k'anana har sun san su had'a mana k'arya idan zasu tafi, kuma ni wallahi bana kullen Ihsan sosai, inda ma ace ina mata tsanani ne da sai ince banga laifin ta ba".

Dady cikin tashin hankali yace "barin tafi Office yanzu nasan Sajent Musa yau night gare shi, inspector Bala ma kamar night ne saboda sanda na baro office lokacin yaje, barin hanzarta in tafi",

Alhaji Abdallah yace "na manta ashe tare nake da DSP, ai da sauk'i ma kenan, sai mu tafi tare".

Wayar Dady ce ta d'auki k'ara, dubawar da zayyi yaga Inspector Ashir ne, d'aga kiran yayi tare da fad'in "akwai magama inspector, gani nan zuwa Station d'in yanzu",

"Yallab'ai nan ma dai akwai matsala, mutun biyu sukazo wai suna so a masu cigiyar yaran su sun fita tun yamma basu dawo ba, d'ayan ma wai twins ne yaran", inspector'n ya fad'a cike da girmamawa.

Dady ya kalli Alhaji Abdallah sannan yaci gaba da fad"in "same case da zai kawo ni station d'in, ka jira ni yanzu zan taho" yana kaiwa nan ya kashe wayar tare da d'aukar key'n mota ya fita, Alhaji abdallah ma ya mara masa baya.

Basu jima a hanya ba suka isa station d'in, cikin hanzari Dady ya nufi office d'in Inspector Ashir ya samu mutun biyu dattijai zauna sai raba ido suke kamar sunyi k'arya an turke su (lol..).

Bayan inspector Ashir ya saaraa ma Dady sannan yace "yallab'ai kamar yanda na fad'a maka to ga mutanen nan, amma dai kaji daga bakin su",

D'aya daga cikin su yace "sunana Alhaji Ma'aruf, yara na 'yan biyu Shareef da Shareefat ne suka bat'a",
Cikin mamaki Dady yace "b'ata? Garin ya hakan ta faru?"
Alhaji Ma'aruf yace "d'azu ne da yamma lokacin da bana nan Shareef yaje wurin Mamin su yace wai zasu je wata gaisuwar rasuwa baban classmate d'in su ya rasu, to da naji su shiru shine na gano inda sukace sunje d'in da k'yar da wahala ma na gane gidan, naje sun shaida min su babu wanda ya rasu a gidan su, suma 'Yar su ta fita tun yamma bata dawo ba, duk gidajen dangi da nake tunanin yaran nan zasuje naje amma ban same su ba, ga lambobin wayar su bata shiga, hankali na ya tashi sosai shine nazo nan ko da wani abu da za'a iya yi min".

nannauyan ajiyar zuciya Dady ya sauke, gaban shi ya k'ara fad'uwa yayin da bugun xuciyar shi yake tafiya da sauri sauri, ya jima a haka kafin yace "to kai fa bawan Allah me ya faru?"

D'ayan mutumin yace "nifa tawa 'yar gidan mahaifiya ta tace min zataje ta duba ta wai ta dad'e bata je ba, nikau har da dad'i naji ta kula min da uwa, jn ta shiru har dare yayi bata dawo ba yasa na kira ta amma tak'i shiga, na kira mahaifiya ta tace min ai Nuratu bataje inda take ba, hankali na ya tashi sosai, nayi iya bincike na amma ban same ta ba, shine na yanke hukuncin zuwa nan nasan insha Allahu zakuyi bakin k'ok'arin ku".

Alhaji Abdallah in banda kallon su babu abun da yake yi, to wai miye dalilin da yasa yara matasa suka b'ata a lokaci d'aya? Kuma same case ne kowa k'arya yayi kafin yabar gida? Tambayar da yakewa kansa kenan wadda yasan bata da amsa har sai lokacin da aka gano yaran.

Dady ya gyara murya yace "abunda ya kawo ku nima shine muhimmin abunda ya fito dani a wannan lokacin nida bawan Allah'n nan.." nan ya basu labarin duk abunda ya sani har Ummah dake gidan su akan b'atar 'yar ta itama.

Alhaji Ma'aruf yace "tabbas yaran nan aduk inda suke suna tare, baza'a tab'a kiran wannan da coincidence ba saboda abu ne wanda yake a bayyane, fatan mu dai Allah yasa a duk inda suke suna lafiya",

Alhaji Bashir (Baban Nuratu) yace "ai sai asan abunyi ba wai mu tsaya anan muna magana ba, ko gidajen radio ne sai mu fara xuwa kafin gari ya waye asan abunyi".

Da wannan maganar suka rantaya su duka hud'un a cikin motar Dady, basu zarce ko ina ba sai VISION FM, nan suka bada sanarwar b'atan yara matasa wanda dukan su babu wanda ya wuce shekaru 16-17 ba.

Amrah and Rerbee'art sk novels,
Admins
ONLINE HAUSA READERS📚
[11:43pm, 23/09/2016] Amrah💓Pinky💓durling😘: 💀 *A YINI 'DAYA* 💀

👹💀 💀👹
👺

*®NWA*
*Na Princess Amrah*
*Da Rabiatu sk msh*

Page1⃣2⃣

K'arfe 11:05pm
*~AJIWA DAM~*

Wani irin haske ne mai had'e da guguwa mai k'arfi ya haskaka wurin,
Feenat dake gefe makure har ta sik'e da kuka tana ganin hasken ta saki ajiyar zuciya dan wani sanyi sanyi taji a ranta, d'aga kanta da zatayi taga yanda akayi kaca kaca da *AREWA STARS* kamar wasu dabbobi,
Can kuma hasken ya canja launi izuwa red colour,
Md da Reeshat dake gefen ruwa suna kallon ikon Allah bayan hasken ya b'ullo sukaji alamar motsi ata inda suke, cike da tashin hankali Reeshat ta k'adaddabe Md gabanta sai dukan uku uku yake, bata ankara ba taji anja gashin ta dataima mayen gyara sama ana ta wulu wulu dashi, sosai take jin zafi dan dama a ranar tayi sabuwar relaxer, sai da tayi sama sosai da ita sannan ta jefar a bakin wani k'arfe da akebi ta jikin shi idan za'a shiga ruwa, take ta sume bayan ta sai zubar da jini yake.

Md ma ta up side down ta d'auke shi da k'arfi ta jefar a jikin Reeshat, shima sumewar yayi inda k'afar shi d'aya ta cire tun daga cinyar shi sai zubar jini take, cinyar daban ta fad'a a cikin ruwa sai sauran gangar jikin ne a jikin Reeshat.

Nuratu, Shamow da Sady sun dunk'ule junan su suna kallon yanda wannan halittar take wuji wuji da Md da Reeshat saboda har a lokacin wannan jan hasken bai mutu ba, hankalin su tashe dan sun san dole suma sai anzo kansu, babu mai iya yiwa d'an uwan sa magana a cikin su sai faman rawar lab'b'a suke, ga wata irin zufa na keto masu duk da sanyi sanyin ruwan Dam d'in dake akwai amma bai hana masu jin zafi ba.
A hankali wani irin ruwa ya ringa saukowa a daidai inda suke, ruwa ne bak'i k'irin tamkar ruwan kwata ga wari da yake yi,
Da mamaki a duk inda ya d'iga na jikin su sai yayi wani irin bororo kamar masu gyambo, haka yaita sauka a jikin su har saida yayi masu kaca kaca da jiki kamar wanda suka k'ok'k'one,
A had'e ta jefo masu wani d'an k'aramin dutse wanda baki d'ayan su ya had'a ya sumar dasu a lokaci d'aya basu kuma sanin kome yake wakana ba.

Dariya ta kuma fashewa da ita da k'arfin gaske har sai da itacen wurin suka ringa girgiza da kansu, k'yallayen da akayi decoration dasu kuwa da kansu suka ringa yayyagewa, speakers da generator kuwa rugurgujewa suka ringayi kamar yanda ake rugurguza dunk'ulallen gishiri ko maggi,
Ta dad'e tana dariyar kafin ta d'aure fuska wasu irin blue ruwa suka ringa kwaranya daga idanuwan ta wanda da alama ruwan hawaye ne,
Girgiza kanta tayi taci gaba da waigawa gabas da yamma bata ga kowa ba, ta diba kudu inda taci karo da Samir wanda ya gama kid'imewa amma shi a zaton shi ya tsira saboda a wani lungu ne ya lab'e inda matuk'ar baka san yana wurin ba to bazaka ganshi ba, amma da mamaki wannan halittar ta zira dogon hannun ta ta cafko shi a tafin hannun ta, bakn ta takai a cikn wandon shi sai ga kayan marmarin sa (lol..) a bakin ta had'e da jini sai zirara yake,
Tofar dashi tayi sannan ta jefar da Samir wanda a lokacin har ya sume tsabar azaba da tayi masa yawa.

K'arfe 11:30pm
*~kerry~*
tayi tafiya mai nisa har sai da ta sik'e da tafiyar ta nemi wuri ta zauna sai haki take, hankalin ta tashe sai nishin gajiya take,
A hankali ta fara jin hayaniya a kunnen ta wadda ta k'ara tsorata ta, k'ara kasa kunnenta tayi taji k'arar tana k'ara yawaita,
"Oh Dad help me!" Kawai take fad'a,
Da k'arfi halittar ta jawo ta da hannu ta rik'e ta da tafin hannun ta, wata shu'umar dariya tayi wadda ita kad'ai tasan ma'anar ta sannan ta busa ma Kerry iska da bakin ta adaidai kanta sannan ta jefar da ita, take Kerry ta sume itama.

bakin Dam d'in ta koma ta kalli Arewa nan taga Feenat takure sai rawar jiki take,
Hannun ta tasa ta jawo ta ta rik'e ta, a hankali Feenat ta fara furta *"AU'DHU BI KALIMATULLAHI TAAMMAAT MIN SHARRI MA KHALAKA, BISMILLAHILLADHI LA YADHURRU MA'ASMIHI SHAI'UN FIL ARDI WALA FISSAMA'I WAHUWAS SAMI'UL ALEEM"*

Amrah and Rerbee'art sk novels,

[8:20pm, 27/09/2016] Amrah💓Pinky💓durling😘: 💀 *A YINI 'DAYA* 💀

👹💀 💀👹
👺

*®NWA*
*Na Princess Amrah*
*Da Rabiatu sk msh*

Page1⃣3⃣

Wata irin k'ara ta saki da k'arfin gaske tare da yin wulli da Feenat can nesa da ita,
Wannan blue hawayen ne yaci gaba da kwaranya daga idonta, tsantsar damuwa ce k'arara a yamutsatssiyar fuskar ta,
A razane ta koma inda ta jefar da Feenat ta sake d'aukar ta ta matse ta tam a hannun ta, tsananin girmanta yasa kamar bata rik'e komai a hannun ta ba,
Sosai Feenat ke kuka, a wannan karen ma sai ta kasa yin ko addu'ar ma, a nan ne ta samu damar dunk'ule ta wuri d'aya ta nad'e ta kamar gammon kifi, ta d'aga ta zata jefa a cikin ruwa saboda yanda ta b'ata mata rai, duk cikin su babu wanda yayi k'ok'arin hana ta abunda take yi sai Feenat, hakan yasa kawai ta yanke hukuncin ta jefar da ita a cikin ruwa yanda tasan babu ita babu fita saboda girman ruwan bama za'a gane akwai mutun a ciki ba,
Daidai ta d'aga ta zata jefar kenan Feenat ta sake bud'e baki tace
*"LA HAULA WALA K'UWWATA ILLAA BILLAH, U'I'DHU KUMAA BI KALIMATULLAHI TAAMMAAT WA MIN KULLI SHAID'AANIN WA HAAMMAAT WA MIN KULLI AININ LAAMMAAT, ASTAGHFIRULLAHI WA ATUBU ILAIK, YA ALLAH NASANI NI MAI LAIFI CE, INA NEMAN GAFARAR KA YA ALLAH, ALLAH KAI KAD'AI KAKE DA IKON TSERATAR DANI DAGA WANNAN AL'AMARIN, ALLAH NA ROK'E KA DA SUNAYEN KA TSARKAKAKKU, KA CECE NI DAGA K'ANGIN DA NAKE CIKI",*
Tana kaiwa nan tayi shiru sai wasu zafafan hawaye dake fita daga idon ta, kawai ta barma Allah al'amarinta ne dan tasan shine kawai zai iya fitar da ita, bata da k'arfi ko wata dabara sai Allah.

Da mamaki sai ga wannan halittar ta ajiye Feenat k'asa a hankali tana sauke ajiyar xuciya,
Sumbatar ta tayi a goshi wanda yayi daidai da saukar hawayen ta akan fuskar Feenat,
Da sauri Feenat ta d'ago kanta ta kalle ta tace "yake wannan halitta, nasani mu masu laifi ne ga Allah kuma laifin da muka aikata ne yake bibiyar mu, ina so ki bud'e bakin ki ki fad'a min abunda muka miki saboda mu rok'i gafarar ki" jiki na rawa tayi maganar bayan ta sunkuyar da kanta k'asa saboda halittar fuskar tama kanta abun tsoro ce, just imagine halittu da yawa su dunk'ule su zama guda d'aya, ya girmanta zai kasance?

Kanta ta gyad'a alamar baxata fad'i komai ba, Feenat tace "dan Allah idan kina jina kuma zaki iya magana tou ki fad'a min, wannan ishara ce ga wasu mutanen masu hali irin namu, zan so naji komenene saboda gaba".

Wata irin k'ara ta saki da k'arfi wadda ta k'ara gigita Feenat, hatta da ruwan dam d'in sai da ya canja launi, itatuwan gurin kuwa ganyen su suka ringa cirewa da kansu suna fad'uwa k'asa, jijjiga kanta ta hau yi baki na rawa tana k'ok'arin yin magana amma ta kasa,
Da k'yar ta iya bud'e baki zatayi magana kenan sai ga wani irin ruwa yana fita daga bakin ta, wannan ruwan da yake fita shi ya hana ta fad'in komai amma da alama tana son yin maganar babu hali ne,
Hanya ta nuna ma feenat da hannun ta da alama tana nufin ta tafi ne, amma Feenat tak'i tafiya sai kad'a mata kai take tana hawaye,
"Bazan iya tafiya in bar 'yan uwana anan ba, bazan tafi ba har sai kin fad'a min abunda muka miki",

Itama kan taci gaba da kad'a mata tana yunk'urin magana ta kasa,
Dogon tunani Feenat ta tafi a wani lokaci tun kafin ta shiga group d'in *AREWA STARS,*
Wata rana suna zaune da Ummah tana mata karatu, bayan sun gama ne take bata k'issoshi ciki har da na aljanu a ciki, anan ne ummah ta shaida mata da cewa duk ranar da taji zahirin muryar aljani tou sai ta kurumce, haka kuma duk ranar da kikaga aljani da idon ki sai kin makance ko kuma ki haukace",
Saurin zabura tayi tare da fad'in "bama sai kinyi magana ba amma ki sani nayi nadama, nayi nadamar sanin *AREWA STARS* ina mai baki hak'uri idan akwai abunda muka miki wanda ba daidai ba, zan tafi gida zan shaidama iyayen mu dan suzo su tafi da gawarwakin wanda suka mutu, wanda sukaji rauni kuma a kaisu asibiti" tana kaiwa nan ta kama hanyar tafiya k'afarta babu takalmi kanta ko d'ankwali babu.

Tayi tafiya mai nisa kafin ta isa bakin titi, mutane ne sosai wurin tamkar da rana ne saboda wani mai sai da shayi daya tada gen, daga gefen shi kuma wani mai tsire ne shima da tashi tawagar, ganin haka yasa feenat tayi hamdala tare da k'arisowa inda suke.

Suna ganin ta kuwa suka hau daddarewa, su a tunanin su mahaukaciya ce, sallamah tama sauran da basu gudu ba amma suka k'i amsa mata,
"Dan Allah ku taimake ni wallahi ni ba mahaukaciya bace ina buk'atar taimakon ku ne",
Da sauri wani yace "dama kin tab'a jin inda mahaukaci yacewa kansa mahaukaci ne? Ki gafara ki bamu wuri dallah can kn kore mana mutane daga majalisa",
Kuka ta b'arke dashi sosai tare da tafiya a ranta tana tunani "banga laifin ku ba saboda nayi kama da mahaukatan, duk abunda muka shuka shine muke girbewa, ya Allah mun azabtu hakanan, Allah ka sassauta min".

Wata mota ta gani irin babbar nan (j5) an sako dabbobi a ciki, hannu tasa ta tsaida ita ta tsaya, driver'n ne ya lek'o ta window saboda ta gefen shi take yace "malama lafiya?",
"Lafiya k'alau malan, dan Allah idan cikin katsina kayi ina neman taimako ne ka taimaka ka tafi dani ka sauke ni ko bakin roundabout d'in farko ne"
Mamaki k'arara a fuskar shi yace "ke amma kin raina min hankali, a cikin tsohon daren nan zakice na taimake ki, wata k'ila ma ke aljana ce, ke ban yarda dake bama inga k'afarki" ya fad'a yana nuna k'afar da yatsa.
"Wallahi malan kaga k'afa ta ni mutun ce" ta fad'a tare da nuna mashi k'afar tana kuka.
"Katsina zanje, amma kinga motar duk dabbobi ne daga kasuwar Mai_adua nake nayi dare, sai idan kin yarda zaki shiga cikin su to",
Da sauri tace "wallahi na amince",
Bud'e mata yayi ta shige cikin su tsamo tsamo, sauk'in ta d'aya ma dare ne akwai duhu duk sunyi bacci. A cikin kashi da fitsarin su ta kwanta tana sauke ajiyar xuciya.

Amrah and Rerbeeart sk novels,
Admns
ONLINE HAUSA READERS📚
[8:29pm, 27/09/2016] Amrah💓Pinky💓durling😘: 💀 *A YINI 'DAYA* 💀

👹💀 💀👹
👺

*®NWA*
*Na Princess Amrah*
*Da Rabiatu sk msh*

Page1⃣4⃣

Nan da nan kuwa suka isa katsina, cike da tausayi yace mata "baiwar Allah!"
Amma ina, tayi nisa da baccin ta,
Sake kiranta yayi "ki tashi mun iso katsina ki fad'a min wace unguwa zan kaiki?" Nan ma shiru.
Parking yayi da motar ya fito ya zagayo ta bayan inda take kwance cikin dabbobin ya bubbuga ta a hankali ta bud'e idon ta da suka kumbure sosai,
"Nace mun iso katsina ina zan kaiki?",
Tunani ta farayi inda zata je, nan ta yanke shawarar kawai ta fara zuwa gida wurin Ummanta,
Har ta bud'e baki zata fad'i haka kuma ta tuna da Ummah zata iya yi mata komai idan taje, ta fara zuwa ko gidan su Afnan ne yanda koda sunje gida daga baya baxata mata komai ba a gaban iyayen AFnan,
"Goruba road zanje wurin kalamu waheed shopping mall",
Fita yayi ya koma gaban motar yaja ta sai goruba road.

*K'arfe 12:30am.*

A daidai k'ofar gidan su Afnan aka dire Feenat, a hargitse tama mai motar godiya tare da shigewa gidan duk ta daburce,
Kai tsaye cikin gidan ta dosa, securites d'in suka nemi hana ta shiga d'aya daga cikin su ne yace "k'awar Afnan ce fa, kuma kun san ana case na b'atar su Afnan, ku barta ta shiga wata k'ila tana da masaniya ma".
"Shiga" ogan nasu yace mata, da sauri kuwa ta shiga jiki sai rawa yake mata, tashin hankali k'arara a fuskar ta.

Sallamah tayi murya na rawa ta shiga cikin parlor'n,
Hankalin tane ya dad'a tashi yanda taga manyan mutane zazzaune sunyi tagumi har da masu yin kuka, daga gefe kuwa Ummah ce da momy suna ta faman kuka babu mai rarrashin wani,
Daga can k'arshen kujerun kuma mami (maman Ruky) ce tayi tagumi ta zurfafa a tunani.

Sai da tayi sallamah har sau uku amma babu wanda yaji ta saboda duniyar tunanin da suka lula,
Ata hud'un ce duka suka amsa mata a tare,
Kasantuwar duka mazan basu san ta ba yasa suka bita da kallo dan yanda take a rikice kamar mahaukaciya.

Da sauri Ummah ta d'ago kanta daga kukan da take, cikin hanzari ta isa inda Feenat take ta rungume ta da k'arfi tana sauke ajiyar zuciya,
Wani sabon kukan taci gaba dayi tana mai tausayin ummanta, lokaci d'aya tabi ta xube kamar ba ita ba.

Momy ma tasowa tayi da k'yar ta iya fad'in "Safeenah! Ina kika baro min Afnan? ina fatan kuna tare da ita",
Sakin ummah tayi ta koma ta rungume Momy tana ta faman ajiyar xuciya ta kasa fad'in komai,
Dady jin haka yasa ya tabbatar da itace k'awar Afnan, mik'ewa yayi ya isa inda take tare da fad'in "Safeenah kiyi hak'uri ki daina kukan nan ki mana bayanin inda yaran nan suke"
Nan ma shiru tayi dan bata san ta inda zata fara ba,
Alhaji Abdallah yace "ki taimaka mana kiyi shiru kiyi bayanin inda suke, idan basa raye ne ko gawar su muna da buk'atar gani dan mu sallace su"
Da sauri Alhaji Ma'aruf yace "haba Alhaji Abdallah! Ya zaka ringa fad'in haka? Insha Allahu yaran mu basu rasu ba, suna lafiya aduk inda suke".

Ummah ta share hawayen ta tace "Safeenah ki kwantar da hankalin ki ki mana bayani kinji?",

Mami ce ta taso daga kan kujerar da take tace "duk wannan bashi zaisa tayi bayani ba, idan kun kula ai a rikice take, ya kamata a bata lokaci ta samu tayi wanka taci abinci ko zata samu natsuwa",
Momy tace "hakane kam, muje kiyi wanka idan ana binki bashin salloli ma sai kiyi".

D'akin Afnan momy ta kaita, da k'yar ta iya yin wanka tayi alwala, koda ta

Book Chapters
Chapter 1Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4Chapter 5Chapter 6

Please Login or Register in order to submit comment